Cinikin Rai Book 2Hausa Novels

Cinikin Rai Book 2 Page 24

Sponsored Links

24 I’m not king, I’m king maker

Kura mata idanu yayi yaga yadda ta koma can kuryan dakin, sai jikinshi yayi mugun sanyi. Zama yayi yana faɗin. “Zainaba meke damunki?” Dauke kai tayi tana haɗe rai ta ce. “Wani mutum nake son na nime. Ban san a ina nake ba yanzu?” Shiru yayi jikinshi yana kara yin sanyi ya ce mata. “waye haka mutum?” “A wani gari nake yanzu?” “Kina Demark ne!” Yayi shiru yana kallonta. “Zai kai mu yaushe, mu koma Keivroto?” “Zai kai mu wata biyar, domin sai kin warware, me zaki yi a can!” Cikin salon yan jagaliya ta ce mishi. “Akwai tsohuwar gaba ce nake son naje na kaddamar da shi.”
“Wani irin tsohuwar gaba?” “Mutumin da ya kashe min iyayena zan je nima joha ko waje na manta amma zan tafi fisto ne binciken ahalina!” Bai tab’a shakkar wani ya san gaskiyar waye shi ba, amma yau kalaman Zeeno ya karya mishi zuciyarshi. Tsoron kada ta rabu da shi ya bayyana a cikin idanunshi. Bai tab’a zaton zai zama fool akan soyayya na, sai ga shi ya zama mara amfani. “Baki rike sunanshi ba ne?”
. “Idan da na rike sunanshi zan gaza gaya maka ne? Ban san sunan mutumin banza ba!”
Hadiye yawu yayi yana kallon yadda take wani, rangaji tabbas Zeeno da ya sani dama can suna da wata a kasa, amma kuma tana dai rage mishi wani abu idan ya kira sunan Ammy. “Tow shi kenan! Zo mu kwanta!” Ya janyota zai rungume ta. Ta dauki wukar da ta yanka fruit. “Kada ka sake ka tab’a ni!” Hadiye yawun bakinshi. “Zainaba meye matsalarki ni mijinki ne!!”
“Wannan matsalarka ne, bana sonka tab’a ni. I hate that!”
Riko hannun wukar yayi yana faɗin. “Ban san me nayi ba, amma baki daya na fuskanci sauyin ƙaddara daga gare ki, I’m sorry Ina sonki. Ba zan iya rabuwa da ke ba” ya rungume ta a hankali. Daura kanta yayi a kirjinshi. Tana jin bugun zuciyarshi. D’ago kai tayi tana kallonshi kafin ta ture shi. Sake riƙe ta yayi yana tambayarta. “Meye nayi mara kyau? Soyayyarki ce bata min adalci ba ko me nayi?” “Fansar kashe iyayena zan tafi na dauka, kana da halin kai ni ko yau ne!”

Girgiza kai yake yana faɗin. “No Zeeno! I can’t, ba zan iya ba. Na kawo ki nan don mu huta ne ban kawo ki don na ƙara mai dake ba, ki tuna saboda ke na bar kome na tawo nan” “Ni? Tow waye kai?” Kamar an watsa mishi ruwan zafi yaji tambayarta. “Me yasa ka dame ni? Me yasa ka shiga rayuwata?” Rike kanta tayi tana jin abu me dumi yana zuba ta hancinta ta ce mishi. “Me yasa ka dame ni?” Da sauri ya koma bayanta ya rungume ta, tana jin bugun zuciyarshi, a hankali ya juyar da ita, tare da riko hannun, sakewa yayi ya cire rigarshi ya fara goge mata hancinta. “Zan gaya miki waye ni idan har kin amince!” Yana gama goge mata jinin ya shiga sumbatar bakinta, tare da ƙoƙarin goge mata hadda. Wani azzababben kewarta da yake yi, yasa shi kara matseta. Yana kara jin wani, abu na taso mishi. Jikinta ne yayi sanyi, ta kara rungume shi. Tana sauke ajiyar zuciya. Izuwa yanzu zuciyarta tayi na’am da lamarinshi, bai tab’a nimanta a irin wannan yanayin ba, ko bai tab’a jin ya nimeta ta wani yanayi ba, amma yau sai da ya danganta da jikin wall na dakin, sannan ya shiga wani irin sauri-sauri yana me kara jin wani bala’in kaguwa akanta, sai da ya rungume ta gam, sannan ya shigeta da karfi. Ajiyar zuciya suka dauke once. Yana sumbatar habbarta. “Kin fahimci waye ko na cigaba!” Rungume shi tayi tana me daura kanta a kafadarshi. Hada kafafunta tayi a bayanshi ta makale shi. D’ago kanta tayi ya shiga lasar wuyarta har zuwa fuskarta. “A tsawon watanni da kika dauka baki da lafiya, hakuri nayi banyiwa shukata ban ruwa ba, a yanzu zan juye kome na kara tuna miki ni naki ne baki ɗaya ba zan iya cutar dake ba!” Ya fadi haka yana matse bom-bom dinta, sama yayi da rigarta ya shiga matse na shanun da suke kara haukata shi yana jin kamar yayita ihu, juyawa yayi da ita ya zauna a bakin gadon. Ya shiga juyi a tsakanin su, yana kara jin wani irin shauki. Musamman yadda take wani deep moaning da groan kamar ranta zai fita. Wannan nishin yana.daga cikin abin da yake kara mishi confidence. Shi daya yasan yadda yake jinta, shi.daya yasan me yake bukata a jikinta, don haka baya ji ybaya gani yake zungureta. Yana shiga da fita a ko ina na jikinta, ji yake kamar kome na shi ya ƙare, akanta amma ba sai iya rabuwa da ita. Ba zai tab’a rabuwa da ita ba. Ko zata na yankar namar jikinshi ne kuwa yana makale da ita, ba zai taba rabuwa da ita ba, she meant to only him, don haka zai ta shiga cikin rayuwarta kafin ta gano waye shi, ya gama fahimtar da ita tsantsar kaunarshi.

Ba zai d’aga kafa ba, ba zai d’aga hankalin ba, amma zai zame mata kamar kaska zai addabi rayuwarta har sai ta fahimce shi. Zai matsa mata da soyayyar shi yadda ba zata tab’a tsare mishi ba. Zai ta bibiyar rayuwarta har sai ta ji ta gaji da takura mata tayi accepting dinshi ai yasan, ba shi ya kashe iyayenta ba, taya zai addabi kanshi da damuwa. Zai yi farin ciki idan har ta gane matsayinshi a ranta. Zubewa suka yi a gadon. Tana kwance a jikinshi. Tayi masifar laushi sai ajiyar zuciya take tana me juya kanta. Haka yake fatan a koda yaushe ta gane shi jarumi ne ba lusari ba.
Ta fahimci shi na musamman ne, ta gane bayan shi babu wani namiji. A hankali ya janyen ta daga jikinshi yana shafa bayanta, barci me nauyi ne yayi gaba da ita, shima ya shiga ban daki yayi wanka ya fito ya shirya cikin kananun kaya, sannan ya koma saman restchair ya zauna yana sauke ajiyar zuciya. Kallonta yake yana kara jin gajiya. Amma baya jin zai iya rabuwa da ita.
Sai yamma likis Zulfa da Yasir suka iso gidan, tana zaune a dakin kamar mayya domin bata son shiga harkan kowa a gidan tun da Malik ya gama nikata, ta farka a barci take zaune a wurin. Dakatar tayi wanka shima dai da ya kamata da nufin zai mata, shi ne tayi tana. Sanye take da riga da skirt, sai hula da ta saka. Tana wurin kamar me tunanin wani abu. Turo kofar yayi Zulfa tana biye da ita. Ta zuba mata idanu. “Zeezeen Abba!” D’ago kai tayi tana kallon Zulfah. Kafin ya dauke kai tana kallon can gefe. _Ki Zulfah dawo ki ɗauke ta, ki bisu Zeezeena_ karar wayar Zulfah yasata razana tana kalle-kalle! Ta tashi zata gudu, ya riko hannunta. “Ina zaki?”
“Zanje Abbana ne, zasu kashe shi!” Ta faɗa da karfi tana rike shi, rungumeta yayi tana ta kokuwar kwatar kanta, amma ta mata riko me kyau, kuka ya saka tana me kwantar da kanta. Komawa yayi da ita cikin dakin ya kwantar da ita, kusan ma tare suka kwanta, tana ta kuka. “zan je na kashe mugun da ya kashe min Abbana, akan idanuna suka kashe min Abbana!” Kara rungumeta yayi yana faɗin. “Zamu kama su insha Allah” ya faɗa yana shafa bayanta. A hankali barci yayi gaba da ita. Sai da ya saka mata pillow a bayanta sannan ya fito waje, ya zauna yana kallon Zulfah itama kuka take. “bata tuna da mu ba!” “Zata tuna da ku, ki daina kuka ai da sauki tunda ta fara tuna wancan abin da ya faru!” Ya faɗa yana cigaba da tafiya kitchen, ruwa da juice ya kawo musu, sannan ya ce musu. “Dole mu kama waɗanda suka aikata wannan abin a gurfanar da su, Nayi magana da matar da ta zauna a wurinta ta ce min, Zainab tayi fama da trauma na tsawon shekaru, tare da karfin harsashin kanta, wanda ya kara mata karfin gaske, Zainab tana bukata kulawa da janta a jiki.

Ta haka ne zai saka ta fahimci cewa ta rayu da mu. A wani lokaci da ya wuce. ” Sosa goshinsa yayi yana faɗin. “And dole a bude file din shakaru goma sha uku baya, ta hana ne zamu goge abin da ya faru a kuma bankad’o gaskiyar da take rufe.”
“Kana nufin sabon bincike za a fara?” Yasir ya tambaye shi.
“Yes!” Ya faɗa tana shan ruwa, Ya zubawa Zulfah idanu. “Na samu labarin kina digging case din file din yana hannunki.”
“Ya zamu yi da ma’ikantan tsaro?” “Zanji da su!”
“Yan majalisar kasa da zartarwa, majalisar koli na shugaban kasa, dole sai mun samu haɗin gwiwan su!” “Ku bar min kome a hannuna. Zan ji dasu.”

Shiru suka yi, kafin suka mike a tare, “zamu tafi yallabai!” “Ok” ya mike tare da raka su. “Kafin ki bar garin nan, make sure kin kuma zuwa kun gana da juna, tana bukatar wani a tare da ita, kamar nata.” Gyada kai tayi tana faɗin. “Zan zo insha Allah!” Daga haka suka mishi sallama, komawa ciki yayi ya shiga dakinshi, kayanshi ya bincika sannan ya ciro wayar karama ce, ya kira wani layi da shi. “Mr Haris Jabir!” Daga can aka ce mishi.” Malik Menk Jordan! Kana ina ne? Ƙasa ta hargitse da tashin hankali!” Murmushi Malik yayi sannan ya ce . “Zan dawo kowani lokaci, amma a bawa mutane na izinin fara binciken mutuwar Aswad Al Yemini da Nasr Hadejia. Zasu iso kowani lokaci!”
“Malik zan yi murabus, idan aka gama binciken. Kai sai ayi nominate dinka a matsayin PM!” “A’a Mayor din ma, zan ajiye muku ni i’m not king im king make, na zabi wanda nake so,na ajiye wnada bana so. Keivroto nawa ne, nawa ne Keivroto!” “Malik duk yadda kace”

Daga haka ya kashe wayar, ko Mayor ya karba ne, domin cusawa Khuldu Jahid Khan haushin ya rasa kujerar da ake ganin kamar gadon shi yayi, ya hana shi. Ya kuma kafa daula babba wanda kowa zaiso ya kasance shi daya a wurin, Allah ya bashi arziki, ya bashi karfin iko. Uwa uba yana da makiya son ranshi, me ya rage mishi? Babu don haka zai sake shiga filin dagga ne domin Zeenobia ba don kanshi ba. Daga ranar da aka samu labarin yana raye daga ranar ko ina makiyanshi bayyana zasu yi, yana son haka ya gansu suna nufar shi. Yana kara mishi shaukin da jin dadi.
Don haka ya shirya tsaf, ya tura da sakon cewa. *A saka live zan yi magana a Keivroto baki daya*
_An gama!_ aka turo mishi. Daga haka ya ajiye wayar, sallah magariba yayi da isha, sannan ya koma dakin ya tashe ta. Tayi sallah. Bayan ta idar ya dauko sweatcoat ya saka mata, ya daure mata shi, sannan ya riko hannunta ya daura mata mayafi. “Ni bana son haka!” “Zan yi haka domin ina so!” “Auren wata biyar ne next month zamu rabu kada ka manta da wannan” gyara mata mayafin nayi. “ba zan tab’a danasanin rabuwa da ke ba, domin nasan ina sonki, kuma zan amshi kasa ko gazawa daga gare ki. Amma ba zan tab’a sake ki ba wannan shi ne alkawarin da na dauka miki.”
“Tow Ni nace bana sonka!”
“I’m sorry baby you too late, ina sonki muje muci abinci!”
“Ka ajiye ni kana biyan bukatarka da ni, ka ajiye ni kana yadda kake so da ni ka kyale rayuwata ko na baka mamaki!” “Babu mamakin da zaki bani, domin yarjejeniyar mu Ammyn ta wargaza shi, aurenmu fresh ne babu cantract!'”
“Zan kashe ka kuwa!” Tab’e baki yayi yana faɗin. “Thank God Mayor zai mutu a hannun matar da yake masifar kauna!”
“I hate you!” “I love you!” Wuce shi tayi zata tafi ya dawo da ita, da karfi. “Ashhhhhh!” Ta rike cikinta, saboda karfin fisgota da yayi……🤔🙄🥺 Me haka yake nufi wani abu yana min Dillin dillin 🤔 Happy weekend 🌸🥳
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata:

Leave a Reply

Back to top button