Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novels

Kurkukun Kaddara 16-17

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*

_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E16-17

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

dukkan ilahirin jikin shi rawa yake yi, kusan suman kwance ya yi saboda tsabar tsoratar da ya yi jin Angel saman jikin shi ɗungurugum, zuciyarta har wani tafarfasa take yi saboda tsabar fusata, a rayuwarta ta tsani jikinta ya haɗu dana ɗa namijin da ba daddynta ba, kamar ta haɗiyi zuciya take ji, tayi Niyar idan ta ɗago ta kwashe shi da zazzafan mari, Sai dai wani yanayi da ta tsinkaye shi a ciki ya yi silar dakatar da ita, lokacin da jikinta ya haɗe da nashi wani irin zafi taji rau tamkar hucin garwashin wuta, lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai, ta fahimci cewa baida ƙoshin lafiya, da alamun zazza6i attare dashi numfashinsa kanshi da hucin zafi yake fita, gaba ɗaya jikin nashi a raunace yake, Ga fargabar angel dake a kwance saman shi, yasha jinin jikinshi a tsorace yake da tsiwatarwa, baiso ta tayar mashi da lalurarshi

daddagewa tayi tare da yunƙurawa ta ɗago daga jikin shi, tarwatsastsiyar sumar kanta ta sauka har saman wuyan shi, a raunace ta kalli kyakkyawar fuskarshi, sama sama yake numfashi ya lumshe sexy eyes ɗin shi bai kai ga datse su ba, shima ɗin ita yake kallo, farar fatar wuyan shi tabi da kallo, ta ko’ina Jan tabon yakushin da ta yi ma shi ne,

Sun ɗauki tsawon lokaci A saman gadon Batare da wani ya furta wata kalma ba, idanuwansu acikin na juna, Jira yake ya ga wani Irin hukunci zata yanke mashi don yasan ba ƙyale shi za ta yi ba, tana iya cewa xata karanta mashi charman dudu, Cikin shi ya kumbura,

saukowa ta yi daga saman gadon nashi jikin ta duk ba daɗi, Sai yanzu ta lura da irin illar da ta yi ma shi, tana zargin kanta da alhakin Ciwon nashi, Ji take kamar taje ta faɗa ma tsohuwa cewa baida lafiya, amma ta kasa sam ba ta so yasan ta damu dashi, kuma ba ta son taje wurin tsohuwa saboda tsanar matar da ta yi,

zuciyarta a karaye ta koma saman gadonta ta kwanta, Ita kanta tasan bazata Iya runtsawa ba, Saboda zullumin rashin lafiyar danish, gani take kamar idon ta rufe idanuwanta zata farka ta taras da gawarshi ne, tana da hanyoyin da zata iya taimaka mashi sai dai bazata iya ba, saboda batason Raini ya fara shiga a tsakaninsu,

“I don’t know why I’m worried about him,” ta ambaci hakan acikin zuciyarta tare da juyawa don ta saci kallon shi, a kwance yake kanshi saman fillow, idon shi biyu ya yi lamo yana kallonta,

Gyara kwanciya tayi Ita ma ta fuskance shi, don yau taci alwashin bazata bari ya runtsa ba, kodan kada yayi bacci daga nan ya zarce zuwa barzahu, zullumin da take yi kenan,

Ganin yaƙi daina kallonta yasa ta ɗan ɗaure mashi fuska tare da cije lower lip ɗinta, ƙasa ƙasa da murya tace”Stop looking at me or else i will poke ur eyes” ta yi maganar tana kwatanta mashi yadda zata zungure ma shi idonshi da yatsan hannunta, har wani lumshe ido ya yi, tamkar yaji saukar yatsan nata acikinsu,

Slowly ya kuma ware manyan idanuwan nashi akan fuskarta,

Ƙura ma juna ido su kayi kallo na ƙurulla, ta jima tana mamakin wani abu atattare da prisoners ɗin da take atare dasu, gaba ɗayansu babu mummuna acikinsu, sam ba su yi kama da ƴa’ƴan malam shehu ba, sunfi kama da rainon madara, ƴan gidan Mommy da daddy, Expecially danish da Batool da Azeeza Hasken fatarsu sam bana baƙar fata bane, Kamar dai ita da take half cast, Launin fatar Su Hanna da su javed Dukansu irin na ya’yan Hutun nan ne, Ko’ina Aka samu kyawawan yaran nan? Zaiyi wuya su kasance ya’yan talakawa ne , Sai dai irin ƴa’ƴan hamshaƙan masu kuɗin nan, wannan ɗan shilan da take kallo, Yanayin shi tamkar akwai jinin sarauta atattare da shi, Baisan magana baisan hayaniya, kullum yana naɗe saman gado yadda kasan ɗan wani basarake, idan ka kalli soft skin ɗinshi ko tabo babu, fari ne sol, ga kyan ido ga kuma kyan sumar kai, Anya wannan ba ɗan wani shegen bane, ta yi tambayar acikin zuciyarta,

Bawan Allah, duk ya tsargu da irin kallon da angel ke yi mashi, Ga bacci yana ji amma yaƙi yarda baccin ya ɗauke shi saboda gudun kada ta yi ma shi wani abu, yasan dole ta hukunta shi,

kallon juna suka cigaba da yi da zarar taga ya fara lumshe ido zai yi bacci sai ta Ambaci kalmar charman dudu, a firgice yake ware idanuwanshi , ta hana shi runtsawa gashi in bai samu isasshen bacci ba, yana samun matsala, kusan raba dare su ka yi ita da danish, sai da Allah ya taimake shi bacci ya fara ɗaukarta tukunna ya samu shima ya runtsa_

In the morning🌹

Mutsu mutsun farkawa daga bacci ta soma yi, a cikin zuciyarta tana karanto addu’ar ta shi daga bacci, tunawa da danish yasa tayi hanzarin buɗe idanuwanta A hanzarce ta yi wuff ta miƙe zaune tana kallon shimfiɗarshi, babu kowa asaman mattaress ɗin sai Bargonsa da pillow dinsa, hankalin ta ya yi matuƙar tashi, ta shiga tambayar kanta Ina danish ya shiga? Meyasa kowa yana a kwance saman gadon shi, sai shi kaɗai ke babu? Ko dai ya shiga toilet ne?

Ta ƙarasa zancen zucin a lokacin da take sauko daga saman gadonta, cikin takun sauri ta nufi ƙofar shige toilets ɗinsu, hannu tasa ta tura ƙofar ta shiga daga Ciki, sai da tabi kowani toilet ta bincika amma babu danish,

Dawowa tayi da sauri taje gaban gadon batool,

Bubbuga ƙafarta tayi tare da Kiran sunanta”Batool! Sister!” saboda tsiwar muryar angel hatta su Azeeza sai da su ka farka,

“Meya faru sister” muryar batool a disasashe tayi mata maganar, tashin ta kenan daga bacci, idanuwanta sun ɗanyi ja saboda bacci,

“Na duba ko’ina banga danish ba, Jiya ya kwana da zazza6i yanzu kuma na farka ban same shi ba,”

“What? Danish bai da lafiya”? Haris ne ya yi maganar tashin shi kenan shima daga bacci, Fuskarshi da alamun ruɗi don ba ƙaramin Jin danish yake ba acikin zuciyarshi,

Jinjina kai angel tayi alamar eh kafin tace”Bansan inda ya shiga ba, tun ɗazu nake neman shi” Ta shi xaune batool ta yi, idonta akan angel tace”meya faru da danish ɗin mu”? Ina ya shiga”? Ta yi tambayar tana faman yin hamma,

Javed yace”Ni dama tun jiya na lura bai da ƙoshin lafiya, kunsan halin shi idan baya da lafiya yana da juriya baya bari mu sani kodan kada mu tashi hankalin mu akanshi, Amma nasan yanzu duk inda yake yana a tare da GIANTS, zai iya yiyuwa sune suka so su ka ɗauke shi”

Batool tace”taya zamu iya tabbatar da hakan”?

Hibba tace”Idan mu ka tambayi tsohuwa zata faɗa mana inda ɗan uwan mu yake, Bari naje na sanar mata,” Ta karasa maganar tare da saukowa daga saman gadon nata, da azama ta nufi ƙopar ɗakin tsohuwa,

Kowa yayi zugudum yana jiran tsammani, Knocking ƙopar Hibba ta yi, Almost 3 times, suka soma jin mutsu mutsun buɗe ƙopa ta cikin ɗakin,

Fitowa tsohuwa ta yi hannunta ruƙe da sanda kamar kullum dai Cikin shigar nan tata, ta gado, wato doguwar riga launin Ja,

Haɗa ido su ka yi da hibba, Cikin girmamawa hibba ta gaishe da ita, ta amsa mata gaisuwar ta ta, tare da cewa”Zan iya sanin meke faru”?

“Dama danish ne, Angel tace jiya taji zazza6i a jikin shi, yanzu kuma mun farka bamu ga ɗan uwan mu acikin mu ba, bamu san inda ya tafi ba” Hibba ce ke magana amma idon tsohuwa yana akan angel dake daga can cikin ɗakin tsaye ta ruƙe qugu a bakin gadon batool, wani irin kallo take yi mata, murguɗa mata baki angel tayi tare da galla mata harara,

Ƙayataccen murmushi tsohuwa ta saki wanda bai kai zuci ba, ta ɗauke idonta daga kan angel ta mayar dasu kan Hibba,

“Giant ne yazo ya ɗauke shi, yanzu haka danish yana a treatment room, da zarar yaji sauƙi za’a dawo maku da ɗan uwanku,” tana kai ƙarshen maganarta, ta juyawa ta koma cikin ɗakin nata, taja ƙopa ta rufe,

Kowa ya ji Amsar da tsohuwa ta ba hibba, hankalin su duk bai kwanta ba, Mamaki ƙarara akan fuskar angel tace”dama har treatment room ke akwai a Cikin prison ɗin nan”

Batool ce ta bata amsa da cewa”Eh, amma bakowa ne idan baida lafiya, ake kai shi can ba, Tsohuwa ce take duba lafiyar jikin mu,’

Yau tsawon shekara ɗaya da rabi, bata ta6a jin Zancan wani treatment room ba, sai yau, kuma tun da take da su, da wuya wani acikin su ya yi koda Ciwon kai ne, wani iko na Allah, Lafiyarsu ta banbanta dana sauran Jinsin bil’adaman da ta sani, ita dai hankalin bai kwanta da Treatment room ɗin nan ba, saboda me za’a ɗauke shi daga Cikin su, maimakon tsohuwa ta bincika lafiyar jikin, Shi ne sai an wani ɗauke shi daga cikin su,

Zuciyarta duk ta karaya, Batasan a wani hali yake ciki ba, juyawa tayi tare da nufar toilet ɗinsu, Tana ƙoƙarin shiga ta jiyo muryar haris yana cewa”Ke ce silar Ciwon Danish, saboda jahilin bugun da ki kayi ma shi jiya, idan har muka rasa ɗan uwanmu, kema ki fidda rai da rayuwa” Kasa buɗe ƙopar toilet ɗin tayi Kamar wadda aka dasa ma aya

Muryar batool ta kuma ji tana cewa”Haris dan Allah kadaina wannan maganar, Angel ba ita bace silar rashin lafiyar shi ba, lafiya lou muka wuni da danish, daga baya ne Ciwon ya same shi”

Tsawa haris ya daka mata”Shut up! Dama ae kina bayanta, wa kika fara sani acikinsu? Danish tun kafin ki mallaki hankalin ki kike a tare da shi, amma saboda wata can wadda bamusan da zamanta ba, gaba ɗaya kin kwaye mana baya,” yana huci yakai ƙarshen maganar,

“Dama ba ƙaunarsa take yi ba, shiyasa take son raunata shi,” acewar deeja,

Ta yi niyar ta juya taje ta nakaɗa masu bugu, amma saita fasa, saboda a halin yanzu ita kanta zuciyarta ta karaya,
Buɗe ƙopar ta yi tare da shigewa Ciki, Ta jingina bayanta Jikin bango, siraran hawaye masu ɗumi suka soma gangarowa saman kuncinta,

Ta ɗauki tsawon lokaci bata motsa ba, har saida Taji motsin shigowar mutun a toilet area ɗin, Firgit ta ɗanyi tare da kai idonta kan wanda ya shiga, Batool ce a tsaye tana kallonta,

“Angel meyasa kike kuka? Ko dan saboda abunda suka ce? Bafa laifin ki bane,”

Cikin sanyin murya tace”Ba saboda su nake zubar da hawaye na ba, idan naso zanje in bubbuge su ne, Kawai ina jin ba daɗi, saboda bugun da nayi ma danish jiya, baki ji jikin shi ba jiya yayi zafi sosai, yana a cikin wani hali, kuma nasan Nice silah,”

Dafa kafadarta batool tayi”Dan Allah ki kwantar da hankalin, ki daina zubar da hawayenki, danish fa zai dawo cikin ƙoshin lafiya, tsautsayi ne kuma ya riga da ya faru,’

Murmushin takaici angel ta yi withouth sayin anything,

Saukar tafin hannun batool taji a saman fuskarta, tears ɗin da take zubarwa ta shiga goge mata,

“Ina da saurin kuka, abu kaɗan yake harzuƙa ni,” angel ce ta yi maganar cikin ƙunar rai,

“Koda ace kowa zai juya maki baya, Ki sani Ina atare dake, a koda yaushe zan kasance a hannun damanki,” da ƙwarin gwiwa batool tayi maganar,

Wani irin kallo angel ta ke yi mata mai nuna tsantsar so da ƙauna,

“Da ace mu tagwaye ne Iyaye na suka haifa da sai ince ke ce twin sister ɗina, saboda yadda kika damu dani, kika mayar da damuwarki tawa, Idan ina farin ciki kema kina farin Ciki, haka zalika idan ina baƙin ciki kema kina baƙin ciki, Batool you’re so special, Ina roƙon Allah ya bani damar taimaka ma rayuwarku,’

Ƙayataccen murmushi batool ta ɗan saki,

Kafin tace”Muje muyi wanka, idan muka fito, zan gyara maki gashin kanki, naga duk ya hargitse,” tayi maganar tana ruƙo doguwar sumar kanta, Gashin yayi tsayi sosai har ya zarce waist ɗinta ga uban yawa, yayi datti babu gyara har tashi yake yi, ita fa mantawa take yi da wani gashi akanta, Tun zuwanta kurkukun sau biyar ta ta6a wanke shi,

Cikin shessheƙar kuka tace “Na saba daddyna yake wanke mun kaina, shiyasa nake jin wahalar wanke shi da kaina, ya saba mun da komai, yanzu gashi bamu atare da shi,” zuƙunnawa ƙasa tayi tare da fashewa da matsanancin kuka, da sauri batool ta zuƙunna agabanta, tana lallashinta

“Ashe dama haka rayuwar duniyar take? ni ban ta6a tunanin akwai wani lokaci da zaizo ba, wanda zanyi rayuwa ni kaɗai batare da daddy na ba, kuma ba’a cikin gidan mu ba, sai gashi yau na tsinci kaina a wata sabuwar rayuwa Cikin mutanan da banta6a yin tozali ba, duk yadda naso in jure nakasa, ina kewarka daddyna, inason naganka, nasan bada son ranka ka jefa ni cikin ruwa ba, kayi hakan ne donka ceci rayuwata, meyasa baka bini cikin ruwan ba? Ka tsaya har saida suka kashe ka’?

Natsuwa batool ta yi tana sauraron sambatun da angel take yi, da alama tafara fita hayyacinta,

Mahaifina shine sanyin idaniyata, shine komai nawa, ya gatanta ni tamkar sarauniya, Ya Allah duk wanda yayi silar tarwatsa ƙaunar dake a tsakanin zuciyoyin nan guda biyu, Ya Allah ka ƙasƙantar da rayuwarshi, ka haɗa shi da bala’e da masifa, wanda zasu hana shi runtsawa,’

Duk da batool batasan kan zancen ba, hakan bai hana zuciyarta yin sanyi ba, hawaye suka soma sintiri saman fuskarta,

Girgixa kai ta shiga yi, idanuwanta cike tab da kwalla, fuskarta tayi jawur da ita,

Kallon batool tayi Jin shessheƙar kukanta, ƙaƙaro murmushi angel tayi”meyasa kike kuka”?

Cikin muryar kuka batool tace”Saboda ke angel, ina tausayin rayuwarki”

Itama Cikin muryar kuka tace”Bani bace abun tausayi ba, kune abun tausayi, Nifa na taso ta tare da iyaye na, nasan dangina, Naje makaranta, kuma nayi rayuwar ƴan ci, Ina sanya sutura mai tsada, Inci abinci fiye da sau uku arana, Daddyna yana ɗaukata a cikin motarsa yakaini duk inda nake so, Amma kufa?….daƙyar takai ƙarshen maganar saboda kukan daya ciyota,

“Ba…tool, An cuci rayuwarku, An ƙuntata ku, an hana ku duk wani jin daɗi na duniyar nan, tun kuna yara kuka tsinci kanku acikin gidan kurkukun nan, Bakusan komai game da rayuwar duniyar nan ba, bakusan su wanene Iyayen ku ba, ku kanku bakusan suwaye ku ba, rayuwar kawai kuke yi a kurmance, mutumin da baisan mahaliccinshi ba, idan ya faɗi ya mutu yau, ya farka ya same shi acikin ƙabari Ya zaiyi? A lokacin da yasan gaskiya bayan lokaci ya qure masa, Wlh an cuci rayuwarku, ni kuma indai ina araye duk runtsu duk wuya bazan ta6a bari rayuwarku ta qare ahaka ba, koda kuwa zan rasa raina ne wurin ceton rayuwarku, xan roƙi Allah ya bani tsawon rai saboda ku…………’

tana kai ƙarshen maganarta, ta kifa kanta saman gwiwowin ta, taci gaba da yin kuka kamar ranta xai fita, itama batool ɗin kukan take yi har yanzu hawayenta basu daina zuba ba
Ƙara matsawa tayi tare da ɗaura kanta saman bayan angel, su ka cigaba da yin kukan atare, sun ɗauki tsawon lokaci, kafin batool ta ɗago da kanta daga saman bayan angel,

Calmy ta furta Sunanta”Angel” a hankali ta ɗago tana ƙoƙarin buɗe idanuwanta da suka raunata sosai saboda kukan da ta sha,_

“Batool kinsan komai game da gidan kurkukun nan saboda acikin shi aka raine ki, meyasa ba zaki iya yi mun bayani yadda zan fahimta ba”? Muryarta a sanyaye tayi maganar,
Girgiza kai Batool tayi tare da cewa”Angel bansan komai ba, da ace na sani, bazan iya 6oye maki ba, Ni dai tunda na taso acikinsa, a killace nake bama zuwa ko’ina, bamu san komai ba”

Jinjina kai angel ta ɗanyi tana faman matse hancinta da ya yi jawur,
“Yanzu duk acikin ku, babu wanda yasan wani abu dangane da prison ɗin nan duk irin tsawon shekarun da ku kayi acikin shi”?
Zurfin tunani batool ta shiga, ƙasa ƙasa da murya ta furta sunan”DANISH”

A ruɗe angel ta maimaita sunan”Danish? Ya san wani abu? Ki yi mun bayani pls……’

Cigaba da magana batool ta yi” Idan ma akwai wanda yasan wani abu, To shi ne, danish ne, duk da bani da tabbaci, ” a matuƙar ruɗe angel ke kallonta,
“Sai dai danish bazai ta6a baki haɗin kai ba, saboda yana da wuyar sha’ani fiye da tunaninki, baida yarda, tun fil’azal balle kuma yanzu daya samu lalurar rashin son hayaniya, sai ya ƙara burkicewa,’

“Kina nufin lokacin baya Danish ba haka yake ba’?

Jinjina kai batool ta yi”Eh, daga baya ne ya koma haka, lokaci ɗaya muka rasa gane kan shi, ko bacci yake yi ya dinga furgita kenan yana sambatu, yanzu ne abun ma ya ɗanyi sauƙi,

Dafe kai angel tayi”Ni nasan koda me nake yawo danish bazai ta6a sakewa dani ba saboda ya tsane ni,”

“yana da sauƙin kai angel, sai dai yarda ce baida ita, bai yarda da kowa ba a cikin mu, tsohuwace kaɗai ya yarda da ita,”

Wani wahalallan Murmushi angel ta saki wanda bai kai zuci ba, dafa kafadar batool ta yi”ngde ssai batool, muje mu shiga wankan, idan muka fito sai ki gyara mun gashin kaina,” amsa mata tayi da toh, Atare suka miƙe kowa ya shige cikin toilet,’

Bayan wasu ƴan mintuna kusan atare suka fito daga Cikin toilet ɗin lemar ruwa kwance saman sumar kansu da suka wanke, Lokacin da suka shigo cikin ɗakin a zaune suka samu kowannan su Saman Red Carpet ga kayan breakfast ɗinsu nan an kawo masu,
Giants Suna a tsaye Sun goya hannayensu saman ƙirjinsu,

Yau fa ta 6aci saboda rashin danish, Sun gaza sakin Jiki su ci abinci, Ji su ke kamar ɗan uwansu bazai dawo Cikin su ba, sanin cewa a lokacin baya duk wanda aka ɗauka zaiyi wuya adawo da shi,

babu irin lallashin da Batool batayi masu ba akan suci abinci amma sunƙi Ci, kowa sai dai ya tsakuri kaɗan kamar anyi ma su dole, ganin zasu wulaƙanta abincin yasa ta ɗauko kwandon da take ajiye abinci a cikin shi, ta kwashe rabi da kwata aciki, Ta ajiye masu shi tasan da anjima dole su 6uƙaci cin abinci, idan yunwa ta addabe su,

Bayan tafiyar su Giants, Batool ta ɗauko Comb, ta zauna saman gadonta daga gefe, tace ma angel ta zo ta zauna ta gyara mata gashin kanta,

Angel kaɗai tayi niyar gyarawa gashi, sai gasu rubina dasu Hanna, Sun jera layi suna jira ta kammala gyara mata ga shi, Suma ta gyara masu nasu gashin,

Baƙamar wahala batool tasha ba, Wurin taje masu sumar kawunan su, kowa cikinsu tubarkallah Yawan gashi gare su ga tsayi, In ka cire deeja ita kaɗaice keda gajeran gashi, amma yana da yawa cike da kanta,

Mutum biyar ta yi mawa, ta miƙa ma angel comb ɗin tace Ta gyara ma sauran Huɗun gashi idan ta kammala itama ta gyara mata nata gashin, yinin ranar abunda su ka yi ta yi kenan, hada mazan suma duk saida suka sharce sumar kawunansu, su kansu ba ƙaramin daɗi su kaji ba, da su ka gyara Sumar kawunansu.

*Boss Bature🌷✍️*

Wasa wasa Har dare ya yi ba’a dawo da danish ba, duk sun damu, kowa yana zaune saman gadon shi, ita kanta angel da bata shiri da shi saida ta damu da son sanin a wani hali ya ke ciki, kallon kowannan su ta yi”me zai hana ku kwanta ku yi bacci nasan cikin dare zasu dawo maku da ɗan uwanku,”

Batool tace”angel bazamu iya runtsawa ba, mun saba kwana atare idan har danish bai dawo ba, a zaune zamu kwana”

Ba haka angel taso taji daga gare su ba, taso ace sun kwanta bacci ya ɗauke su, ko dan ta samu damar Bincikar inda danish ya 6oye wuƙar shi,

Takun tafiya suka jiyo da sauri suka kai idanuwansu kan mutumin dake fitowa, tsohuwace ta shigo cikin ɗakin hannunta ruƙe da sanda, ta tsaya tana binsu da kallo,

Da sauri haris dasu Hannah suka sauko daga saman gadajensu su ka nufi wurinta har suna haɗa baki wurin gaishe ta, ta amsa masu fuskarta asake, kafin tace”me ya hana ku yin bacci ne”?
Atare suka haɗa baki wurin furta sunanshi” Danish, har yanzu ba’a dawo mana da shi ba, muna ta jira” ta lura da irin halin da suka shiga,

“Kamar yadda kuke kewarshi shima haka yake kewarku, kuna aranshi,”

“Amma jikin na shi da sauƙi”? Haris ne ya yi tambayar a ƙagare,

Kafin tsohuwa ta basu amsa angel ta sauko daga saman gadonta, ta nufi inda suke a tsaye ido cikin ido suke kallon kallo tsakaninta da tsohuwa,

“Muna so mu gan shi, mu kuma yi mashi ya jiki,” Acewar angel

“Kada ku damu kanku, zuwa gobe danish zai dawo cikin ku,” acewar tsohuwa

“Me zai hana akai mu treatment room ɗin mu duba lafiyar jikin shi”? cike da tuhuma angel ta kuma yi mata tambayar,

“Ba’a bada iznin zuwa inda danish yake ba, saboda ciwon nashi baya son hayaniya”

“Idan muka je ba zamu yi surutu ba, kawai muna so mu ganshi ne” angel ta kuma tambayarta, Hannah tace”pls tsohuwa kibari muje mu duba shi, we really missed our brother”

Girgixa kai ta kuma yi”dare yayi yanzu zuwa gobe zai dawo”

“A yanzu muke son ganin shi, kibar mu muje mana ko akwai wani dalili dayasa baki so muje ne”

“Ke da baki jituwa da shi, meyasa kika damu dashi ne”? Tsohuwace ta jefa mata tambayar, fuskarta ɗauke da wani shu’umin murmushi,

Tur6une fuska angel tayi tare da haɗe rai tace”wannan bai shafe ki ba, wai taya ma akai kikasan cewa bana jituwa da danish? Bayan wannan taya akai kikasan Halin da danish yake ciki, ta wace ƙopa kike bi ki fita daga Cikin ɗakin nan ne? Don ni bana ganin gifcinki, bansani ba ko bangon ɗakinki, kike ratsawa ki wuce, ko kuma layar zane kike yi ki 6ace,

Matashin murmushi tsohuwa ta saki, Yayin da idonta ke akan angel tace”duk yadda kika ɗauka haka ne,” ta6e baki angel ta yi, su haris duk suna sauraronsu batare da wani ya sanya baki ba,

“Danish zai dawo zuwa gobe, iya amsar da zan iya baku kenan, kowa yaje ya kwanta” tana kar ƙarshen maganarta, ta juya tana dogara sanda ta shige ɗakinta tare da jan ƙopa ta datse,
“Wannan munafukin ɗakin ko menene acikinsa, wata rana saina san yadda nayi na kutsa kai cikinsa,” angel ce ta yi maganar acikin zuciyarta, kafin ta kalli su hanna tace”har yanzu kun yadda da matar nan”?

Jinjina kai su kayi alamar eh, harish yace”Tsohuwa bazata ta6a yi mana ƙarya ba, danish yana kar6ar treatment ne, Idan ma akwai wanda ya kamata mu ga laifin shi to ke ce Angel, jiya kamar xaki kashe shi duk Kika yakushe wuyan shi hada cizo saboda tsanar da ki ka yi ma shi” rai a6ace haris ya yi maganar tare da jefa mata harara,

Ya yi tunanin zata mayar mashi da martani, amma sai yaga tana nannaɗe hannun rigarta, tuni yasha jinin jikin shi

“Wlh duk wanda ya kuskura ya ƙara ɗauramun alhakin ciwon danish, Sai na yi mashi jahilin Bugun da zai gaza ta shi” A harzuƙe ta yi maganar, nan da nan kowa yasha jinin jikin shi,

Murya na kerma azeeza tace”dan Allah kowa ya yi haƙuri, nidai bana son tashin hankali, tun da tsohuwa tace mana gobe zai dawo to mu haƙura muje mu kwanta mana”

Sai da batool ta lalla6a kowannan su kafin ta samu, Suka nufi gadajensu kowa ya haye sama ya kwanta

Ya rage saura angel kaɗai a tsaye tana binsu da kallo, Yayin da tunaninta gaba ɗaya yana akan Danish,

Gyaɗa kai tayi tare da juyawa ta koma saman gadonta, har dare ya tsala bata runtsa ba, Allah na gani ta damu da rashin danish acikin su, tana ji aranta kamar wani abun ne zai faru da shi, ko a wani hali yake a yanzu oho Allah wa’alamu,

Lokacin da kowannan su ya yi bacci, tana cikin saƙe saƙe acikin zuciyarta, tajiyo motsin mutun, da sauri ta ƙyalla idonta don taga wanene

Wannan mutumin ne me jajayen kaya har ƙasa, hannun shi ruƙe da kaskon turaren wuta, sai yawo yake yi acikin ɗakin su, yana tafiya yana karanto wasu ɗalasimai, hannun shi ɗaya ruƙe da kaskon turaren wutar ɗayan hannun kuma yana amfani da shi wurin kora hayaƙin zuwa kowani sashe na cikin ɗakin,

Mamaki ne ƙarara akan fuskar angel ga tsoro tana ji, da sauri ta ƙudundune cikin bargonta, ta sanya tafin hannayenta ta toshe hancinta da bakinta kamar yadda ta yi jiya. Aranta tace”Yau ma ya dawo kenan”

Ya jima acikin ɗakin nasu yana turara masu hayaƙin, kafin taji tsit alamar ya tafi, da sauri ta yaye bargon tana faman sauke ajiyar zuciya,

Saukowa ta yi daga saman gadon jikinta na kerma, hasken fitilun nan guda uku ne ya ɗan haskaka Cikin ɗakin, fitila ta ruƙo a hannunta tana haska wurin gadajensu,

Kamar yadda tabi kowanansu jiya har gadon shi ta tottofe shi da addu’a, haka yau ma tabi gadajen su ta yi masu addu’o’i,

A daidai bakin gadon danish ta tsaya tana kallon shimfiɗarshi, bakomai ya faɗo mata aranta ba face jiya da tazo yi ma shi addu’a, ya damƙo hannunta yayi tunanin wani mugun abunne take yi mashi, ɗan abunda ya faru jiya atsakaninsu ya tsaya mata arai, matsawa tayi zuwa gefen gadon ta tsugunna tare da leƙa ƙarƙashin gadon tana haskawa da fitila, ganin babu wuƙar anan, yasa tayi tunanin ɗaga katifarshi,

koda ta ɗaga ƙarƙashin Katifar bata samu wuƙar anan ba, ba ƙaramin takaici taji ba, taso ace Ta gano inda wuƙar take kota samu ta lalata glass ɗin dake ajikin windon toilet ɗinsu,

Allah kaɗai yasan inda ya jefa wuƙar, wata’ƙil ma, ya maida ma tsohowa ita, guntun tsoki taja, yanzu shikenan narasa damar da nake ita? Babu wani makami da zan iya yin amfani dashi wurin rotsa gilashin, kodai naje toilet ɗin In ƙara dubawa? tana yin wannan tunanin ta miƙe da sauri ta nufi Cikin toilet ɗin, Ta tura ƙopar ta shiga daga Ciki, tana haska ko’ina da fitilar hannunta,

Abu biyu ne Yazo mata aranta, na farko Bokitin da ke acikin toilet ɗinsu Na ƙarfe ne, Na biyu kuma wannan tukunyar fulawar dake ajiye Jikin bango, waswasi ta shiga yi kodai tayi amfani da bokitin? ƙwara shi akan tukunyar fulawar, saboda Zata Iya rugujewa azo kuma buƙata bata biya ba, Anyi asara kenan,

Bata kaiga yanke shawarar dame zata yi amfani ba, ba zato ba tsammani Taji saukar hannun Mutun saman kafadarta, awani irin Firgice tayi kwakkwaran juyi Ta daddage ta ɗaga fitilar hannunta zata kwaɗawa mutun daya dafa kafaɗarta, wani irin ihu batool tasaki a tsorace take faɗin”wayyo! Ke ni ce fa, batool ce,’

Nauyayoyar ajiyar zuciya angel ta sauke, Tare da janye fitilar, ta daidai ta natsuwarta, ba ƙaramin dariya batool ta bata ba, ganin yadda ta gigice,
“Allah ya taimake yau, da kin kwanta jinya,”
Dariya batool tayi”Kin ban tsoro me kike yi acikin toilet ne”?

“Ke zan tambaya, dama baki yi bacci ba,? Taya akai kika faɗo mun Cikin toilet batare da neman izni ba, yanzu da ace wani uzirin nake yi fa?

Hannu batool ta sanya tana sosa kai, tace”raina ya bani cewa ba abunda kike yi ne, shiyasa na shigo Ciki, Kuma na ganki Ɗazu zuƙunne agaban gadon Danish bansan me kikeyi ba, Amma ina hasashen wuƙar shi kika je nema halan”

Yatsina fuska angel tayi”I don’t know why kin sa mun ido, ” ta yi maganar da zolaya,

Batool tace”saboda na damu dake”
Ruƙo hannunta angel tayi tare da janta suka fito daga Cikin toilet ɗin, a bakin ƙopar fita daga area ɗin suka ɗan tsaya suna magana,

“Na duba ko’ina batool banga wuƙar ba, kodai ya maida ma tsohuwa ne?”

Girgiza kai batool ta yi “I don’t think so, nafi tunanin yayi mata wani mugun 6oyan ne, shiyasa na baki shawarar ki shirya dashi, Ku samu kusanci sosai, ta hakanne zaki samu damar sanin inda ya ajiye wuƙar,’

Tur6une fuska angel tayi”Anya zan samu yardar danish, Kin fa ce yana da wuyar yarda da mutane, balle ni kuma daya ɗaurawa karan tsana,”

“Ki jaraba ke dai, Danish yana da sauƙin kai sosai, ya danganta da yarda kika tafiyar dashi, amma wani hanzari ba gudu ba, har yau baki faɗa mini me zaki yi da wuƙar Ba!? I ave to know,’

Ta tsareta da ido tana jiran jin amsar da zata bata, ƴan kame kame angel ta shiga yi don batasan batool ta gane ainihin abunda zata aikata, tasan bazata bari ba, zata yi kokarin dakatar da ita ne

Ganin tana ƙoƙarin ƙara tambayarta yasa tayin saurin katse mata hanzarinta da cewa
“Ko kinsan akwai wani mutumi da ke zuwa ɗakin mu tsakar dare yana yawo da kaskon turaren wuta a hannunshi?

Tayi maganar a kokarin ta nata gusar mata da zancen wuƙa,

“Yaushe kika ganshi”? Angel tace”ko yau yazo, jiya ma na ganshi, idan yazo Sai yaita yin magana cikin wani irin yare mara daɗin ji, sannan yana bin kowani gado yana kora hayaƙin zuwa kowani sashe na ɗakin mu,”

Maimakon taga mamaki akan fuskar Batool, sai taga ta saki murmushi tare da cewa” kada ki damu kanki angel, tsohuwace ae kullum idan dare ya tsala sai ta shigo ɗakin mu, ta turara mana hayaƙin Kariya,”

Maimaitawa angel tayi’hayaƙin kariya kuma? Jinjina kai batool tayi eh, mun ta6a tambayarta hayaƙin menene tace mana hayaƙin kariya ne daga sharrin baƙaƙen aljanu domin kuwa akwai su acikin kurkukun nan, kuma hayaƙin yana da waraka acikin shi, shiyasa zaki ga ko ciwo bamu cika yi ba”

Angel tace”Ni a iya sani na, idan har za’a ba mutun kariya ba hayaƙi yakamata ayi mashi ba, addu’a ya kamata ayi ma shi, sam ni ban yarda cewa hayaƙin kariya bane, dole akwai wani 6oyayyan sirrin a tattare da shi,”

Kafin batool ta kuma cewa wani abu, suka jiyo sautin shessheƙar kuka daga can cikin ɗakin su,

“Wanene ke kuka”? Angel ce tayi tambayar tana kallon batool,

Batool tace “Muje mu duba, ina tunanin Aziza ce, ”

da sauri suka fito daga area ɗin toilet, suka faɗo cikin ɗakin, haskata Angel ta yi da fitilar hannunta, a tsaye suka ganta tsakiyar ɗakin sai kuka take yi tana laluban hanya saboda lalurar da take fama da ita, ta makantar dare (nyctalopia) bata iya gani idan dare yayi, ko kuma idan babu wadataccen haske, haka suke fama da ita, in ta farka zata shiga Cikin toilet, sai ta dinga kuka tana ambaton sunayensu har sai wani ya farka acikinsu ya rakata,

Tun lokacin da angel tayi noticing lalurar yarinyar, sai da tayi ma batool magana ta tambayeta tun yaushe take fama da ita? Batool ta bata amsa da cewa”tsohuwa tace haka aka halicce ta, da zarar dare yayi ganin ta ya ke ɗauke wa, koda an kunna hasken fitila biji biji take gani” tun daga wannan lokacin angel take jin tsananin tausayinta, tana matuƙar jin yarinyar acikin zuciyarta,

 

*(Mu haɗu Next episode in sha Allah Idan Allah yakaimu da rai da lafiya,)*

*Mutane sun fara yi mun magana kan abu biyu, Na farko meyasa suke jin turanci bayan basu je makaranta ba? Ae ba dole sai wanda yaje makaranta ba yake jin turanci, sun taso suna jin yaren da ake yi masu magana dasu, shi yaro ae da yaren da ake mashi magana da shi zai taso koda kuwa harshe uku ne, zai taso yana jinsu, a gidan kurkukun ƙaddara Suna yin hausa kuma suna yin turanci, abun daga waɗanda suka raine su ne, fatan an fahimce ni,Na biyu kuma meyasa angel bata yin sallah? shin baku karanta inda aka ce ta sha jaraba yin sallah ba wani mummunan abu na faru wa da ita ba wanda ya ke affecting din brain ɗinta? nasan me nake yi, faɗarkawa nake yi ba zan rubuta abunda bai da dalili ba, idan ku kayi haƙuri a sannu zan fayyace maku komai😊 idan har mutun nada tambaya game da littafina pls ni zai tuntu6a ashirye nake dana amsa tambayoyinku, its better akan mutun yayi magana ta ta bayan idona, sannan masu tambayata ina da aure, bani da shi, matashiyar budurwace mai jini ajika,🤣, adaina tambayata ya yara ya mai gida, nauyin abun nake ji🤣,*

*Domin neman ƙarin bayani 08103884440*

Much luv My novel’s fans, Allh yabar xumunci a tsakaninmu, Keep sharing my novel✍️

*Boss Bature💋*

Leave a Reply

Back to top button