Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novels

Kurkukun Kaddara 20-21

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

 

 

Daga alƙalamin Boss Bature✍️

 

 

Dedicated to Aunty kubra❤

 

E20-21

 

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

 

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

 

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

 

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

 

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

 

*Maijego package (virgin gain)* 📦

 

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

 

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

 

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

 

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

 

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

 

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

 

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*

*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*

*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*

*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*

*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*

*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

 

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

 

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*

http://wa.me/+2347069711327

 

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

 

 

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

 

 

Muryar Javed su ka ji yo daga bayansu

 

“Nima ina neman yafiyarki angel, duk da bana ɗaya daga cikin masu ƙuntata maki” raba jikinsu su ka yi daga cikin na juna, kowannansu idanuwanshi ya kaɗa yayi ja saboda kukan da suka sha, still hawayen basu daina sintiri saman faces ɗinsu ba,

 

 

Kallon javed su ka yi dake a tsaye, Shima da alamun nadama atattare da shi, cikin sanyin murya angel tace”basai kun nemi yafiya ta ba, saboda ba laifinku bane, nayi maku uziri tuntuni’

 

Ƙarasa shigowa Cikin toilet area ɗin yayi ya tsaya a kusa da su, sannan yace”Angel, muna so mu tabbatar da gaskiya, a tsakanin ki da tsohuwa, sai dai babu wata ƙwaƙƙwarar hujja da zamu shaida hakan,” yakai ƙarshen maganar idon shi akan fuskarta,

 

“Ku bani lokaci, bi’iznillahi Zan kawo maku ƙwaƙƙwarar hujjar da zan wanke kaina, ZAN TABBATAR MAKU DA CEWA GIDAN KURKUKUN ƘADDARA BA GIDAN MARAYU BANE, SANNAN ZAN TABBATAR MAKU DA CEWA AKWAI ALLAH WANDA YA HALICCE KU, BA DAGA SAMA KUKA FAƊO BA,”

 

Baƙaramin daɗin maganarta su ka ji ba, batool ta ruƙo hannayen angel biyu acikin nata, cikin natsuwa ta soma magana”Ina yi maki fatan nasara Angel, muna atare dake,”

 

Angel tace”Bana so ku nuna mun shirya agaban tsohuwa, Ku cigaba da pretending cewa Kuna goyan bayanta baku atare dani, ta hakanne zan samu damar bayyanar maku da gaskiya,’

 

Atare suka haɗa baki wurin amsa mata da toh, Kallon azeeza ta yi wadda ke atsaye tana jinsu amma bata iya ganinsu,

 

“Mu koma Ciki mu kwanta, Azeeza ta gaji da tsayuwa” ta ruƙo hannun azeeza, Batool da javed su ka yi gaba a cikin ɗakin suka yi ma juna sallama, Kowa ya wuce gadonshi, sai da tafara kai azeeza saman gadonta ta kwanta ta lullu6eta da bargo, kafin Ta koma nata gadon, daga ƙasa ta ajiye fitilar hannunta, ta haye saman mattress ɗin taja bargo ta lullu6e jikinta zuwa saitin neck ɗinta, kasa runtsawa tayi, ɗan juyawa ta ɗanyi tare dakai idanuwanta saman shimfiɗar Danish, why Har yanzu ba a dawo da shi ba? Allah yasa dai ba jikin nashi bane yayi tsauri sosai ba, duk da babu sabo a tsakanin mu, naji na yi kewarsa sosai, inaso na sake ganin danish, Fatana Allah yasa adawo dashi, kada maganar batool ta tabbata na cewa duk wanda aka ɗauka ba’a dawowa da shi ya tafi kenan har abada! To wai ina ake kai su? Idan suna araye meyasa ba a ta6a dawo da su ba? Ni dai a iya sanina mutuwa ce kaɗai idan akayi ta ba’a dawowa!!!!!

 

Ɗaura hannunta na dama tayi asaman goshin ta zagoyo da shi, idanuwanta na fuskantar ceilling,

 

“Menene ma’anar Gidan Kurkukun ƙaddara? A iya sanina Gidan Kurkuku Yana nufin Gidan Gyara hali, Amma wannan kurkukun meyasa last name ɗinshi Ya ƙare da ƙaddara! Dole ya kasance ɗaya Cikin biyu, Kodai kyakkyawar ƙaddara ko kuma mummuna, ‘ lumshe idanuwanta ta yi a hankali ta ware su, Zuciyarta Cike fal da tunani, Tun lokacin da daddynta ya gudo da ita daga Gidansu, Take lissafin kwanaki, bata ta6a bari lissafi ya kwace mata ba, ko babu calender tana iya hasashen Yau nawa ga wata, ku ma ta canka dai dai,

 

Tana Cikin Yin tufka da warwara, Tajiyo Takun Tafiyar Mutun, Tunkafin ma takai idonta kan wanda ya shigo ɗakin nasu, Ta yi hasashen tsohuwa ce, daga kwance ta wurga eye balls dinta kan tsohuwa dake shigowa Cikin ɗakin, Sanye cikin shigarta, ta gado jar doguwar riga me hula, hannunta ruƙe da kaskon turaren wuta, zagaye ɗakin ta soma Yi tana kora hayaƙin ta ko’ina, murmushin takaici angel ta saki, yau ta ƙudiri aniyar sai tayi mata magana ga da ga, batare da jin tsoro ba, ta mike tare da saukowa daga saman gadonta, Cikin sanɗa take tafiya har ta ƙaraso bayan tsohuwa ta Cigaba da binta suna tafiya atare, batare da tsohuwa ta ankara ba, kasa kunne angel tayi tana sauraran ɗalasiman da take karantawa, kai daga jin yadda take Karanto su zaka shaida cewa ba abun arziƙi bane, wani mugun abunne take ƙulla masu,

 

 

“ƴar nan Kina tunanin bansan Kina bin bayana bane”? Tsohuwace tayi maganar, batare da ta juyo ta kalli bayanta,

 

Koda angel taji maganarta, bata ji wani fargaba ba, saima ƙwarin gwiwa da ta samu na cewa” nasan kinsan ina bin bayanki mana, Taya ki aiki nake yi, naga kina ta wahala ke kaɗai, Me zai hana yau Ki bani Kaskon turaren wutar In rage maki aiki”? juyowa tsohuwa tayi suka fuskanci juna ita da angel, Wani irin balagaggen murmushi ne ɗauke akan fuskarta tsohuwa,

 

Ɗaure fuska angel tayi tamau ba fara’a ko misƙala zarratin,

 

“Bibiyata kike Yi kenan? Da alama har yanzu baki daddara ba, Ina mai baki shawarar Ki ajiye makaman yaƙin ki, Ki yi rayuwarki tamkar salihar dabba, ki ajiye wannan Girman kan naki, da taurin kan nan da kafiya, Muyi rayuwa Cikin salama,’ takai ƙarshen maganar tana washe wawulan bakinta,

 

Still angel bata tanka mata ba, Jira take ta kammala Suratan nata marasa kan gado,

 

“Ƴata faɗa da aljani ba riba, Ko har yanzu Kina tunanin zaki Ci galaba akaina ne eye? Tsabar takaici Ji take kamar ta shaƙo wuyan matar, mummunar banxa kawai, ta ambaci hakan acikim zuciyarta, a fili kuma tace”tun yaushe kuma? Cin galaba akanki tuni na fara, bari na faɗa maki abunda kike tunanin bansani ba,’ ƙura mata kwarkwararrun idanuwanta tsohuwa tayi tana jiran jin me zata ce,

“Kafin na faɗa maki irin nasarar dana fara samu akanki, zan fara faɗa maki babban kuskuran da kuka tabka,” fuskarta ɗauke da murmushi takai ƙarshen maganar, Tsohuwa dai tayi kasaƙe tana kallonta,

 

A tsanake angel taci gaba da cewa”Kuskuren kuwa shine, ɗauko ni da ku kayi zuwa Cikin gidan Kurkukun nan, ganganci ne mutun ya ɗauko ajalinsa ya raine shi da hannunsa, ada ina tunanin meyasa na kasance acikin gidan kurkukun ƙaddara? Amma yanzu na samu amsar tambayata, inaji araina Ba hakanan Allah ya ƙaddara mun rayuwa acikin gidan kurkukun nan ba, babu shakka Nice zanyi silar tarwatsewar……..” bata kai ƙarshen maganar ba, Sakamakon wata ƴar iskar dariya da tsohuwa ta fashe da ita, Ta wage wawake bakinta, Haƙoran nan jawur dasu, kasancewar angel na a kusa da ita, Da sauri ta kawar da kanta gefe Jin ƙarnin Jini na fita daga cikin bakin tsohuwa, lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai zuciyarta ta shiga ruɗani, gaba ɗaya ta rikice tana zare ido, fuskarta ɗauke da tsantsar mamaki da aljabi ta ɗago tana kallon tsohuwa a lokacin ta dakata da yin dariyar,

 

Da shaƙaƙƙiyar Miryarta ta tsoffi tace”Your dream will neva come true angel, Wasiƙar jaki ce kike saƙawa aranki, wadda bazata ta6a zama gaskiya ba, har yanzu akwai sauran kuruciya atattare dake, shiyasa nake yi maki uziri, bakisan komai game da gidan kurkukun ƙaddara ba, ki kalli ginin da kyau, Tsohon ginine wanda tun kafin zuwana duniya aka ƙirƙire shi,”

 

Angel fa ta shiga ruɗani, Idanuwanta azazzare take kallon tsohuwa, sama sama take fahimtar zancenta, wata irin narkakkiyar zufa ce ta shiga tsastsafo mata ta ko’ina ajikinta, saman goshinta duk ya jiƙe da zufa, bakomai ya tsara mata arai ba, face wannan ƙarnin Jinin da taji abakin tsohuwa,

 

“Gidan Kurkukun ƙaddara, Baida ƙopa a lokacin da aka Ginasa, Kurman ginine, Ke Ko mutuwa bata isa ta fidda gawar mutun daga Cikinsa ba idan har ya shiga Cikinsa, Duk wanda muka ƙaddara ma rayuwa acikinsa, Anan zai rayu Anan kuma zai mutu, Ƴar nan ta ina kike tunanin zaki iya tarwatsa Gidan kurkukun ƙaddara? Ta yi mata tambayar tana sakin shu’umin murmushi,

 

Tuntsirewa Angel tayi da dariyar yaƙe, tana girgiza kai, hada dafe Ciki, tsohuwa ta zuba mata ido Itama da murmushi akan fuskarta,

 

“Halan wani shaƙiyancin ne zaki yi mun shine kike dariya” ? Tayi tambayar tana kallon angel,

 

Dakatawa tayi da yin dariyar, Tare da sanya hannu tana kore hayaƙin kaskon turaren wutar dake a hannun tsohuwa daya takura mata,

 

Sai da ta daidaita natsuwarta tukunna tace”Ubangijin mu Allah subhanahu wata’ala, mamallakin Komai da kowa, mahaliccin Maginin gidan kurkukun ƙaddara da kuma tsohuwa ita kanta dake agabana, da iznin shi komai ke wakana, wanda idan yaso a yanzu haka da muke atsaye sai ki fadi ki mace shikenan, An shafe babinki rayuwarki, duk wani ƙarfin iko da kike taƙama dashi kinga ya qare, Zaki je ki fuskanci reality, Allah kenan da shi na dogara, Kuma shi zai bani Ikon tarwatsa ku, wai ke har kina da bakin cewa duk wanda kuka kaddara ma rayuwa acikinsa Bai isa ya fita ba? Anan zaiyi rayuwa anan zai mutu? Ke wacece? Kin manta ta ƙofar da kika bi kika zo duniya? Kin manta yadda aka halicce ki tun daga ɗigon maniya har zuwa gudan jini? Ke kanki fa baiwace ta Allah ƙasƙantacciya butulu, waɗanda ma suka fiki hatsabibanci irinsu fir’auna Yanzu suna Ina?

 

Jin wannan tambayar ta angel yasa Walwalar dake akan fuskar tsohuwa ta gushe zuwa tsananin fushi da 6acin rai,

 

“Dama nasan bazaki bani amsa ba, ƙarya ta ƙare, Idan Allah yaso arana ɗaya dake da kurkukun duka zai shafe babinku, Shi kaɗai yake da iko akan komai, Bansan A ina kika samu kwarin gwiwar Yin magana a gadarance ba, akwai fa ranar da wannan sihirin naki bazai ta6a taimakon ki ba,

 

Zaro ido tsohuwa ta yi tana kallonta, Cike da mamakin Jin ta ambaci cewa tana da sihiri taya akai tasan hakan? Bata kai karshen zancen zucin nata ba Angel tace”Kina mamaki ne? Ta yi tambayar fuskarta ɗauke da murmushi, Kafin taci gaba da cewa”Ɗaya daga Cikin nasarorin da na fara samu kenan, Kina amfani da sihiri wurin sarrafa Tunanin waɗannan bayin Allah, Kun Hana ayi ibada acikin gidan kurkukun ƙaddara saboda Itace Lagwanku, wannan dalilin yasa Duk wani prisoner dake rayuwa acikinsa, kuka hana shi yin addini, Hakan na nufin ku kanku Kuna tsoron Allah saboda kunsan cewa shi kaɗaine zai Iya kawo ƙarshen ku, shiyasa kuke gudun dun wani abu daya shafi addini musulunci, sai dai kunyi abanza, domin kuwa kome kuke Yi Allah yana kallonku, dama ce na ɗan lokaci ƙanƙani, ”

 

Ajiyar zuciya ta sauke kafin taci gaba da cewa”Ke kanki kin fara Jin shakkata, dalilin dayasa kuwa nace haka, Saboda kinga addu’ar da nake Yi masu tafara tasiri ajikinsu, Har sun fara gaddama dake, Wannan dalilin ne yasa Kika Koma Yi masu hayaƙin sihiri domin juye tunaninsu, sai dai kash aduk Lokacin da ki ka turara masu hayaƙin sihiri ni kuma ina bin kowani gado In tottofe su da addu’a, wannan yasa kike jin haushina saboda ina ruguza maki shiri, sabo tsabar makirci kikayi ƙokarin cusa masu tsanata acikin zuciyoyinsu, duk don saboda kisa in karaya, shima kinyi abanza,”

 

yadda take magana babu tsoro tamkar zata shaƙo wuyan tsohuwa, daurewa kawai take yi tana yin magana da ita, saboda munin fuskar matar, Ƙyamarta take Ji, fuska duk ta lalace ta ta6ar6are,

 

“I ave alot to say, Amma bazan Iya jure Yin magana mai tsayi dake ba, saboda 6ata lokacine yin magana da matacciyar zuciya,” fuskar tsohuwa babu annuri take kallon angel, Kaskon turaren wutar dake a hannunta tuni garwashin ya mutu, hayaƙin ya daina wanzuwa

 

 

Dogon tsoki Angel taja, tare da juyawa zata je ta kwanta, har ta kusa kaiwa bakin gadonta, ta ɗan dakata da yin tafiyar ta waiwayo ta kalli tsohuwa dake a tsaye ƙiƙam uwa saƙago, ta kafe ta da waɗannan kwartayen idanuwan nata,

 

“A’uzubillahi minasshaiɗanirra’jim, Aniyarki ta biki, Kuma ina nan ina zuba ido, Gobe adawo mana da ɗan uwan mu danish, idan ba haka ba komai zan iya aikatawa wlh, zan nuna maki hatsabibanci na, zan addabi rayuwarki,

 

“takai ƙarshen maganar tare da jefa mata harara ta murguɗa mata baki, gyaɗa kai tsohuwa tayi Batare da ta furta wata kalma ba, ta dogara sandarta zuwa kopar ɗakinta, ta buɗe ta shige tare da jan ƙopa, tafiyarta keda wuya angel tabi kowani sashe na ɗakin ta tottofe shi da addu’o’in neman tsari kamar yadda ta saba, ta kuma bi kowani gado tun daga kan gadon su Hanna duk ta wanke su da addu’a, bayan ta kammata ta koma saman gadonta, A tsakiyar gadon ta zauna tare da ɗaga hannayenta tana addu’a, akan Allah yabata Ikon yin nasara akan miyagun mutanan nan, Allah kuma Ya tsare mata daddynta aduk inda yake, idan kuma Ya mutu Allah ya kai rahama ƙabarinshi, Hatta danish sai da ta yi ma shi addu’a, Ta kuma roƙi Allah daya kawo masu ɗaukin fita daga Cikin Gidan kurkukun ƙaddara, Ta jima tana yin addu’o’i kafin daga ƙarshen ta janyo bargonta, ta lullu6a ma Jikinta,

 

Cikin ƙanƙanin Lokaci Bacci Yayi awon gaba da ita, can cikin dare wata irin zufa ta soma wanke fuskarta, wani irin matsanancin zafi ta ko’ina ajikinta, mutsu mutsu ta dinga yi tana matse idanuwanta, yayin da ta dunƙule hannayenta, tamkar ƴar dabbe, duk ta hargitsa shimfiɗarta, da alama mafarki take yi, ciccije la66anta tayi har sai da ta fasa su, ƙasa ƙasa take karanta duk wata addu’a da tazo mata a cikin kanta, a daren ranar bata yi bacci mai daɗi ba,

 

Tun daga saman gado Ta mirgino ta ƙundumo ƙasa ta daki floor ɗin sosai, har cikin kanta taji zafin buguwar da ta yi, Lokaci ɗaya ta farka kamar wadda Aka tsakura ta ware manyan gray eyes ɗinta tana kallon ceilling, Sai faman haki take yi kamar wadda ta yi gudun famfalaƙi,

 

 

Ƙoƙarin tariyo abunda tayi mafarki akanshi tayi, A cikin mafarkinta wasu baƙaƙen Maguna Guda uku sun farmake ta asaman gadonta, Faɗa ya kaure a tsakaninsu, Ta dinga yakushinsu tana kai masu cizo suma suna kokarin yakushinta sai dai Allah bai basu nasara ba, a ƙarshen itace taci galaba akansu ta yi masu jina jina sukai ta kuka, har suka sauko daga saman gadonta suka watsa aguje,

 

Nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke, wani irin sanyi ya ratsa zuciyarta, lokaci ɗaya ta saki murmushi har dimples ɗinta suka lotsa, da alama taji daɗin damben da tayi acikin mafarkinta, bata motsa daga kwancen da take a ƙasa ba, hada bargonta da pillow ɗinta duka suna rungume a hannuwanta, Suma hadasu akayi artabun,

 

“Gidan kurkukun ƙaddara Ba gidan marayu bane Gidan Matsafa ne” yanzu ta ƙara tabbatar da zarginta akan cewa Gidan Mallakin Matsafa ne, Sai dai batasan wasu kalar matsafa bane, masu shan Jini, ko kuwa masu Cin naman mutun, akwai sauran rina akaba, dole sai ta bi asannu tukunna zata gano ainihin me waɗannan matsafan suke aiwatarwa da mutane ,

 

Ta yi zurfin acikin tunaninta muryar batool ta katse ta”Sister lafiya? Me kike yi a ƙasa”? Wurga idonta tayi akan batool dake A zuƙunne gabanta, ba tasan Lokacin da tazo wurinta ba,

 

“Sai faman sakin murmushi kike Yi kamar wadda akayiwa albishir da mukullin fita daga Cikin Gidan kurkukun ƙaddara” fashewa angel tayi da dariya Jin abunda batool tace, haƙiƙa maganarta ba ƙaramin daɗi tayi mata ba, wannan babban albishiri ne kuwa mutun ya mallaki mukullin fita daga kurkukun ƙaddara, Har tafara ayyana irin shagalin da zatayi aranar da tabar gidan kurkukun nan, zatayi farin Cikin da bazata Iya misalta shi ba,

 

“Faɗamun me kike ma dariya? Wata’ƙil nima ya sanya ni farin Ciki”acewar batool fuskarta ɗauke da murmushi tayi maganar,

 

Mikewa zaune angel tayi still pillown ta na rungume a hannunta, sumar kanta duk ta tarwatse saman bayanta, hada side by side na fuskarta, hannu batool takai tare da ruƙo gashin kanta tana fadin”yakamata In rage maki sumar kannan naki, idan ba haka ba nan gaba idan kina tafiya sumar zata dinga taɗiyo ƙafarki ne,” dariya suka saki atare,

 

Angel tace”baki lura gashin ki yafi nawa yawa ba? Kalli Fa yadda sumar kanki ta Cika ko’ina kamar kin kifa kwando asaman kan naki, Gashin duk ya nannaɗe kamar taliyar indomie,”

 

Ta6e Baki batool tayi ta ɗan kai idonta kan sumar kannata, ita kanta tsoron kallon yawan sumar ta take Yi, saboda yadda take ha66aka,

 

“Kwanan nan zan samu abunda zan datse ta, Don ni banga amfani gashin kaina ba,” acewar batool,

 

Angel tace”da ace a waje kike rayuwa da baki faɗi hakan ba, saboda gashi abun ado ne ga ƴa mace, yana ƙara ƙawata kyan mace sosai, kuma yana jan hankali mutane, idan Allah yasa muna da rabon fita daga Cikin kurkukun nan, ke da kanki zaki shaida abunda nake faɗa maki, mutane ma rububinki zasu dinga yi saboda kyanki,”

 

Duk wannan maganganun da angel ke yi batool fa bata fahimtarta, domin kuwa batasan Ya kyan fuskarta ya ke ba, tun da Allah ya halicce ta Bata ta6a kallon madubi ba, tadai san kyau a fuskar danish da kuma fuskokin su Azeeza, Amma Ita batasan Ya kamanninta suke ba, kamar yarda suma su Azeezan basu ta6a kallon madubi ba, Basusan Ya suffarsu take ba, Sai an kwatanta masu,

 

“Angel nifa bansan Ya ake ganin kyau na ba, Saboda bansan ta wace hanya zan ga fuska ta ba,” tayi maganar tana kallon angel,

 

Tuntsirewa angel tayi da dariya Hada dafe Ciki, Batool ta daure fuska”stop laughing at me bana son wasa fa ” daƙyar angel ta samu ta dakata da yin dariyar, A tsanake Ta kalli batool tana zayyana mata kyawun fuskarta,

 

“Farko dai ke doguwace, fara sol son kowa ƙin wanda ya rasa, idanuwanki Dara dara dasu manya farare ƙyal launin su brown colour, ga dogon hanci, tausasan la66anki brownish colour ne yadda kasan yankan tumatur saboda tsabar kyansu, ke fa ɗin kyakkyawa ce ajin farko, tun da angel ta soma magana batool ta saki baki galala tana kallonta, Tsabar farin Ciki ya hana ta furta komai, Daɗi take Ji ana zayyana mata irin kyanta,

 

Wani abu da angel bata sani ba, tun lokacin da Ta soma zayyana kyan fuskar Batool, Gaba ɗaya su Hanna dasu azeeza, rubina Hibba, eve, yasmin, da deeja da parveen Kaf ɗinsu Suna a zuƙunna kewaye dasu, Jira suke ta kammala Zayyana ma Batool kyawun fuskarta suma ta faɗa masu Ya nasu Kyan yake, Tofa angel ta zama Mirror,

 

Baƙaramin wahalar da ita su ka yi ba, Sai da tagama da matan sai ga Javed da mubeen, hada naufal suma suka tasa ta gaba sai ta faɗa masu Ya kyawun fuskarsu yake, har wani jiri take gani acikin idanuwanta saboda tsabar gajiya, Ga gunwa tana ji sunƙi bari ko toilet ta shiga ta watsa ruwa ajikinta, sai daɗi suke ji an faɗa masu cewa su kyawawane, Sai da ta kammala Javed Yace”Yanzu ki faɗa mana waye yafi kowa kyau acikin mu”? Suka tsareta da ido suna jira su ji amsar da zata basu, Kowa sai gyara sumar kanshi yake yi don ta ce shine yafi kyau,

 

“Zan fada maku tsakani da Allah, wanda yafi kowa kyau acikin ku, Baya atare daku yanzu haka,” gaba ɗaya taga sun kwashe da dariya, Da mamaki akan fuskarta tace”meya baku dariya” Mubeen yace”saboda Kin canka dai dai, Wannan wanda baya atare damu shine yafi kowa kyau acikin mu,”

 

Murmushin gefen fuska angel tasaki tare da ɗaura idonta kan batool tace”Amma duk da kyanshi, Batool itace zata zo na ɗaya saboda Ita macace, bayan batool kuma sai Azeeza kodan saboda wannan kyakkyawan murmushin nata, Daga azeeza kuma sai Javed….” duk wanda ta ambaci sunanshi sai taga yanata washe baki

 

“To ki faɗa mana wanene Yafi kowa muni Acikin mu”?

 

Batare data yanke shawara da zuciyarta ta basu amsa da cewa”Haris ne, Cikin mata Kuma deeja ce”

 

Deeja dake atsaye Ta ruƙe qugu tuni ta tur6une fuska, jin an kirata da mummuna, dama a ƙule take da angel ganin yadda sauran Ƴan uwanta duk suka Saki jiki da ita, bayan irin Ƙarairakin da tayi masu, ita kanta angel tayi mamakin zuwan da su ka yi wurinta, bayan Irin juya mata bayan da su kayi amma yau sai gashi sun sake da ita, duk da tasan Zaiyi wuya ayanzu su yarda da ita, kamar yadda suka yarda da ita a lokacin Baya,

 

Duk wannan abun dake faruwa Haris Baya acikin ɗakin bai jima da farkawa ba, Ya wuce Toilet, baisan wainar da suke toyawa ba,

 

“Kowa ya ta shi yaje ya shiga wanka, ya tsarkake jikin shi, kafin giants su kawo mana breakfast ɗin mu,” batool ce tayi masu magana, ɗaya bayan ɗaya kowa ya mike Ya nufi Toilet,

 

Lokacin da suka kammala Yin wanka, bada jimawa ba, Giants Suka kawo masu Abinci, Yau Hada Chocolate Cake aka kawo masu Kowa ɗaya, ba ƙaramin dadi suka ji ba, Saboda suna matuƙar son cake,

 

Yanzu sun saba da zarar Sun kammala Cin abinci, Sai a haɗu a motsa Jiki, Bayan sun gama, Kowa zai zauna ya huta ne, Yau fa tun da aka ta shi basu ga walwalar haris ba, Hatta angel tayi mamakin halin daya shiga yau, ya saba kullum sai ya ƙunsa mata baƙin Ciki, amma Yau kota kanta baibi ba, ko abincin shi bai ci ba, kamar wanda ɗan kanoma Ya kama haka ya dinga yi masu safa da marwa acikin ɗakin, idan ya gaji da yin zarya ƙafafuwanshi suka soma yi ma shi raɗaɗi sai ya koma saman gadonshi ya kwanta ya kalli ceilling, damuwace ta ishe shi ya rasa ina zai tsoma ranshi yaji daɗi, Ya gaza samun kwanciyar hankali, kowa ya kasa gane kanshi,

 

 

A lokacin suna zazzaune Saman gadajen su suna hutawa, Haris Ya sauko daga saman nashi gadon, Buguzun buguzun yake tafiya har zuwa bakin kopar ɗakin tsohuwa yaci burki ya tsaya tare da kai hannu ya kwankwasa ƙopar, Duk suka zuba mashi ido suna kallon shi, kusan sau uku yana buga kopar kafin, Ya soma jin alamun ana buɗe kopar ta Ciki,

 

Tsohuwa Ce ta fito hannu ruƙe da sanda, tun daga kan yanayin yadda ta ganshi ta tabbatar da cewar ba a hayyacin shi yake ba, ya haɗe rai zuciyarshi har wani tafarfasa take Yi,

 

“Harisu Lafiya ka ke buga mun ƙopa”? Yana huci yace”Nagaji da jiran dawowar danish, So nake naganshi, ko bai warke ba adawo mana shi cikin mu mu cigaba da yin jinyarshi, hankalin mu sai yafi kwanciya,” tunkan haris yakai ƙarshen maganarshi, Sauran ƴan uwan nashi duk suka sauko daga sama beds ɗinsu suka nufi inda tsohuwa da haris suke atsaye, banda angel dake hakimce saman gadonta, tana kallonsu,

 

Marairaice mata fuska Azeeza ta yi, Cikin sanyin murya ta wanda ya karaya tace”Idan har dagaske Kina son Mu, adawo mana da danish ɗinmu mu cigaba da yin jinyarshi acikin mu, mun yi maraicin rashin shi acikin mu,”

 

Ɗaya bayan ɗaya suka shiga Yi mata magiya akan adawo masu da danish ɗinsu, Su suke Yi mata magana amma idonta na akan angel, dake kallonta fuskarta ɗauke da kayataccen murmushi, aranta tace”nasan yanzu zata ƙara jin haushina saboda sun fara tuhumarta akan bazata dawo masu da ɗan uwansu ba, Yanzu ya rage naki tsohuwa kodai ki dawo da danish ko kuwa sufara zarginki,”

 

Gyaɗa kai tsohuwa tayi fuskarta a tur6une tace”Ku kwantar da hankalin ku, Yau danish zai dawo Cikin ku, Kuje ku xauna,” Takai ƙarshen Maganar tare da juyawa ta shige Cikin ɗakinta,

 

A bakin ƙopar ɗakinta, suka Zazzauna don yau sunci alwashin indai Danish bai dawo ba anan zasu kwana, angel dai na can kwance daman gadonta bata motsa ba, ta zuba ido tana jira taga ta wace ƙopa za’a shigo masu da danish, Dagaske zai dawo yau ko kuwa? Lumshe idanuwanta ta ɗanyi tana jin bacci sama sama,

 

 

Har wuraren marece ba’a dawo masu da ɗan uwansu danish ba, sai da kowa ya fidda rai da dawowarshi aranar

 

Kwatsam Ba zato ba tsammani, suna zazaune a bakin kopar ɗakin tsohuwa wasu har sun fara gyangyaɗin Bacci, Suka soma Jin motsi buɗe ƙopa, zumbur kowan nan su Ya miƙe Cike da sa ran Ganin danish, sun tabbatar shi ne saboda yanzu ba lokacin kawo masu abinci bane sun riga sunci tun ɗazu da safe,

 

takun Tafiyar Giant suka Jiyo daga Can kusurwar Benan, Jiki na Rawa suka Watsa da gudu Xuwa bakin stairs ɗin Kowa Ya ci burki yana faman Baza Idanuwanshi, Tuni Giant ɗin daya kawo shi Ya juya ya fuce Ya datse door,

 

 

 

Tun daga ƙasa suka soma Kallon shi, doguwar ƙafarshi sai kerma take yatsun ƙafar duk sun manne ma juna, jikin shi sai rawa yake yi idanuwanshi sun zazzaro tamkar ƙwayar idonshi zata faɗo ƙasa, jijiyoyin wuyanshi duk sun fito ruɗu ruɗu saman farar fatarshi,

 

Kayan jikinshi duk sunyi uban squeezing, sumar kanshi ta hargitse duk ta cukuikuiye

 

Lamarin ya yi matuƙar ta6a zuciyoyinsu, Duk sun gaza yi mashi magana, haris ne ya yi ƙoƙarin furta sunan shi”DANISH lafiyarka kuwa? Ko har yanzu jikin ne”? Ya yi tambayar yana ƙoƙarin matsawa kusa danish,

 

Dafe kai suka ga yayi da hannuwanshi, Ya fasa wata irin gigitacciyar ƙara, wadda ta razanar dasu, Angel dake niyar nutsawa Cikin baccin ta, Sautin ƙarar danish ya farkar da ita, a firgice ta ware idanuwanta tare da kallon inda suke a tsaitsaye Cirko cirko abakin Benan, Da sauri ta sauko daga saman gadon Jikinta har 6ari yake yi, ta cikinsu ta ratsa ta tsaya Dab dashi tana kallon shi,

 

Ya ƙanƙame Jikinshi yana Girgiza masu kai, la66anshi na kerma ya soma faɗin kada su matso kusa da shi, baison ganin kowa, ya tsani kowa” yana kai ƙarshe maganar shi, da gudun gaske ya bi ta tsakiyarsu ya bangaje su bai nufi ko’ina ba sai Cikin toilet area ɗinsu Ya shige ɗaya daga Cikin toilet ɗin Yaja ƙopa ya datse yadda baza su iya shiga ba,

 

Fashewa da kuka Aziza tayi saboda tsoran da taji,

 

Da gudu suka ɗunguma zuwa bakin ƙopar ta farko, Haris ne ya shiga bin ƙofofin toilets ɗin yana kwala mashi kira”Danish! danish! Baka ji ina kiran ka? Wai meke faru ne? Pls ka buɗe mana ƙopa, Munyi kewarka sosai,” a ƙopar toilet na ƙarshe yaje ya bubbuga ta yaji ta a garƙame alamar Nan ciki danish ya shiga,

 

A ruɗe rubina tace”Bari naje na faɗa ma tsohuwa tazo taga halin da ɗan uwanmu yake ciki, kada mu rasa shi” ta yi maganar tare da juyawa da gudu ta fuce,

 

Cikin shessheƙar kuka aziza tace”Wayyo Allah danish meya ke faru dakai ne? Dan Allah ka buɗe ƙopar,”

Hawaye ne acike da idanuwansu Javed, Eve tace”Ban ta6a ganin shi cikin wannan mawuyacin halin ba, sam danish baya a hayyacin shi,” tana rufe baki deeja tace”Ai duk laifin Angel ne, itace sila da ace bata ta6a lafiyar jikin shi ba, da duk hakanbata faru ba,”

 

Cike da takaici Angel tace”Nifa bani ce silar shigar shi cikin halin nan ba, koda ace ni ce amma ae an kai shi treatment room ko? meyasa daya dawo babu sauƙi ajikin shi? Kenan ba duba lafiyar jikin shi akayi ba, Wani abunne daban su ka yi mashi……..”tsawa Haris ya daka mata”Idan har Danish ya rasa ranshi, ke ma ki shirya binshi, ƙafarshi kafarki, muguwa kawai,”

 

Fashewa angel tayi da matsanancin kuka tana faɗin ita ba ita bace sila,

 

Faɗo wa cikin wurin rubina tayi har suna haɗa baki wurin tambayarta ina tsohuwar take, idonta cike tab da kwalla tace”Na kwankwasa ƙofar ɗakinta, bata buɗe ba”

Guntun tsoki Haris yaja, Yaci gaba da bugun ƙopar yana kiran sunan danish amma shiru bai amsa masu ba,

 

Gaba ɗaya sun taru agaban toilet ɗin Sai faman ƙwala mashi kira suke yi ya yi shiru babu magana,

 

“Me zai hana mu sanya ƙarfi mu buge ƙopar wata’ƙil ta buɗe,” batool ce ta kawo wannan shawarar, gaba ɗaya suka shiga bugun ƙopar, idan wannan yayi ya gaji sai wannan ya jaraba, duk anan ƙarfinsu ya ƙare dama ya lafiyar gwiwa, abinci sau ɗaya arana,

 

Gaba ɗaya sun fidda rai da fitowar danish, duk jikin su ya yi sanyi, ransu yana basu cewar danish ya mutu acikin kewayan,

 

Ransu duk a jagule suka fito daga wurin toilet din, suka koma cikin ɗakinsu a ƙasa kowa ya zauna, angel tana a tsaye bakin ƙofar farko ta shiga toilets ɗinsu,

 

Idanuwanta sun Cicciko tab da kwalla, zuciyarta acike take fal da tunanin Meya faru da danish? Yau 5 days kenan Yana a treatment room meyasa baiji sauƙi ba? Anya kuwa duba lafiyar jikin shi akayi ko kuwa ƙara mashi ciwon akayi? Duk yadda ta ƙagara ta yi toxali da danish sai da taji ƙuncin halin da ta ganshi aciki, kwata kwata Baya a hayyacinshi tamkar an canza shi, runtse idanuwanta tayi tana tuna Yanayin da tayi arba dashi, gwanin ban tsauyi kamar wanda aka zaƙulo daga bakin kura,

 

 

“Yanzu ya zamuyi? Munbar shi acan ciki, Allah kaɗai yasan halin da yake Ciki” mubeen ne ya yi maganar fuskarshi jaga jaga da hawaye,

 

Naufal yace”muna ji muna gani zamu rasa ɗan uwanmu, Wai meke faruwa da danish? tsohuwa tace an kaishi treatment room, ana duba lafiyar jikin shi but why danish baiji sauƙi ba”? Ya yi ma kanshi tambayar da baida amsarta,

 

hibba tace” ga shi tsohuwa bata nan, nasan da ita zata ceto rayuwarshi” daga inda angel take tana iya juyo maganganun su, ta tsani taji sun ambaci sunan tsohuwa, kuma har suna da yaƙinin itace kaɗai zata iya ceton rayuwarshi,

 

Aziza sai kuka take yi tamkar ranta zai fita, shi haris Yama rasa ta cewa saboda tsabar ƙululun baƙin Cikin daya tokare mashi maƙoshin shi, zuciyoyinsu sun karaya, ba haka su kayi tsammanin zasu ga ɗan uwansu ba, ba ƙaramin sage masu gwiwa akayi ba, sun rasa yadda zasu yi danish Ya buɗe masu ƙopa, Ko magana baiyi balle ma su sanya ran yana araye,

 

Gaza jurewa angel tayi, Juyawa tayi tare da komawa cikin toilet area ɗin, A bakin ƙopar toilet ɗin da yake aciki ta tsaya tare da kai hannu ta ruƙe handle ɗinta, Zurfin tunani ta shiga yi akan yadda zata samu Ta 6alle ƙopar, sam babu wani makami dazata yi amfani da shi, ƴan dabaru ta shiga yi na yadda zata 6alle ƙopar, Allah ne ya taimake Cikin sa’a, Sakatar ta saki, Ƙopar ta buɗe batare da tasha wahala ba, ajiyar zuciya ta sauke tare da tura ƙopa ta shiga ciki tana faman wurwurga idanuwanta, tun abakin kopar tayi arba da wandonshi yashe a ƙasa, ras! Taji gabanta ya faɗi, cigaba da tafiya tayi tana bin ƙasan da kallo, rigarshi ta gani a ƙasa itama ya yi wurgi da shi, tsayawa tayi a tsaye cike da fargabar halin da zata yi tozali dashi,

 

Yana acan Gefen tukunyar fulawar nan, anan ya zauna, daga inda take tana iya hangen fuskarshi, wuyanshi har zuwa ƙirjin shi, sai kuma ƙafafuwanshi daya zuro dasu ta ƙasa,

Ya lumshe idanuwanshi sai nishi yake yi tamkar wanda yasha gudu,

 

Muryarta na kerma ta ambaci sunanshi”DANISH”

 

buɗe idanuwanshi ya ɗanyi Sunyi jawur dasu daga gani yana acikin mawuyacin hali, jikin shi duk zufa ta wanke shi kamar wanda aka tsamo daga cikin kogon ruwa

 

Ta wutsiyar idonshi yake kallonta, juyawa tayi da sauri ta ɗauko mashi rigarshi da wandonshi,

 

Matsawa ta ɗanyi nesa da shi, yadda bazata iya ganin tsiraicin shi ba

Cikin sanyi murya tace”bansan me yake damunka ba, amma ina zargin kaina akan halin da ka ke ciki, dan Allah ka yafe mun ka yi haƙuri,” har lokacin bai motsa lips ɗinsa ba, balle ta yi tsammanin zaiyi magana magana,

 

Miƙa mashi kayan shi tayi”dan Allah ka mayar da kayan ka, bazan so ƴan uwanka su ganka a haka ba, hankalin su ba a kwance ya ke ba, duk sun damu dakai”

 

Wurga mashi kayan tayi a saman fuskarshi suka sauka,

“Dan Allah ka sanya kayan ka,” ta kuma maimaita mashi, cikin sigar lallashi,

Gani tayi ya runtse idanuwan shi sosai, ya ciccije soft lips ɗinshi duk ya fasa su, wata irin gigitacciyar ƙara ya saki,

Afirgice angel ke kallonshi, Su Batool dake acan cikin ɗakin Jin sautin ƙarar Danish Yasa suka Watso a guje, kafin su ƙaraso angel ta yi saurin juyawa zuwa bakin ƙopar ta datse ta,

 

Tana jiyo sautin bugun ƙopar da suke yi suna ambaton Sunan danish, tayi masu hakanne don bazata so sugan shi tsirara babu kaya ba,

Kafin ta dawo inda yake, tuni Yayi watsi da kayanshi data wurgo mashi, kwance ƙasa ta hangoshi sai burgima yake yi wannan karan hada hawaye akan fuskar shi lamarin ya yi matuƙar ɗaure mata kai, tana so ta taimaka mashi amma tana jin tsoron kallon tsiraicin shi

Rufe idanuwanta ta yi, amma bata rufe su sosai ba, tana gani biji biji a ahaka ta lalla6awa ta cigaba da tafiya zuwa inda yake kwance ta lalubo Wandonshi, ta soma kiciniyar mayar mashi a jikin shi, daƙyar ta samu ta zura mashi, Ajiyar zuciya ta saki tare da buɗe idanuwanta akan fuskarshi,

 

Sai faman nishi yake yi, idanuwanshi suna arufe, long eye lashes ɗin shi duk sun jiƙe,

calmly ta furta sunanshi”Danish are u ok”

Jin muryar angel acikin kewayan yasa suka gane cewa tana a ciki, sunyi mamaki yadda akai ta buɗe kopar, nan fa suka shiga kwala mata kira suna fadin ta bude masu ƙopa

 

Ɗaga murya ta yi tare da ce Masu Bazata buɗe ƙofar ba, saboda sun ƙala mata sharrin cewa itace silar jefa shi cikin halin da yake Ciki, don haka idan har sunga ta buɗe masu ƙopa, danish ya samu sauƙi ne”

 

Bugun ƙopar haris yake yi tamkar zai 6alleta” Bazaki zo ki buɗe mana ƙopar ba? a harzuƙe tace”Bazan buɗe ba,”

Sassauta murya haris ya yi”pls angel ki buɗe mana ƙopa, nasan bakya son danish kada kice zaki ƙarasa shi,”

 

Girgiza kai ta ɗanyi cike da jin takaicin maganar haris,

 

Tafin hannunta takai saman fuskar Danish ta shafa a hankali tare da ambaton sunanshi”Danish”

 

Dogon numfashi taga yaja gami dasauke ajiyar zuciya, yana so ya buɗe idanuwanshi amma ya kasa, sai lumshewa eyes ɗin nashi suke,

 

“Danish pls try to open ur eyes,”

 

Sama sama numfashinsa ke fita da hucin zafi, hannayenta ta sanya tare da tallabo kanshi ta ɗaura saman laps ɗinta,

Shafa gefen fuskarshi taci gaba dayi, yayin da ta soma karanto addu’o’i acikin zuciyarta, tana ɗan tottofa mashi saman fuskarshi,

 

Ba’a ɗauki tsawon lokaci ba, ya fara dawowa cikin hayyacin shi,

 

Lokacin dare ya fara yi, su biyu acikin toilet, ya yin da su batool ke zazzaune bakin ƙopar shiga toilet ɗin, sun galabaita har sun gaji da bugun ƙopar suna yi mata magiya akan ta bude masu, suga a wani hali ɗan uwansu yake ciki, wasu har sun fara gyangyaɗin bacci,

Itama angel ɗin baccin ta soma ji a cikin idanuwanta,

A lokacin da bata yi tsammani ba, taji ya ruƙo hannunta a cikin nashi sosai ya damƙe mata hannu, firgigit tayi tana kallon shi,

Lumshe idanuwanshi suke bai kaiga ƙarasa rufe su ba, He was calmly looking at her face without blinking his eyes,

 

Furta sunanshi tayi”danish” muryar shi so cool ya ambaci sunanta “angel” for the first time da danish ya ta6a ambaton sunanta,

 

“Are u ok,”? Ta kuma tambayarshi, bai amsa mata ba, ƙoƙarin miƙewa zaune yayi amma jikin nashi yaƙi bashi haɗin kai, da sauri ta taimaka mashi wurin tallabo shi ya miƙe zaune, tare da kwantar da kanshi saman kafadarta, still numfashin shi da huci yake fita, tana jin shi saman fatar wuyanta, saitin inda dogon hancin ya shafa,

 

*(To jama’a Mu haɗu Next page in Allah yakaimu da rai da lafiya) Game neman ƙarin bayani 08103884440) wanda suka shirya Biya 500 ne, Suyi magana Free pages end of this month zai ƙare)*

 

Boss Bature ce✍️ keep sharing My novel Allah Yabar zumunci,

Leave a Reply

Back to top button