Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novels

Kurkukun Kaddara 14-15

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

Daga alƙalamin Boss Bature✍️

Dedicated to Aunty kubra❤

E14-15

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

Angel taci gaba da cewa” ina zargin jiya ke ce kika kwaɗe mun kaina da sandar hannun ki, Saboda kinga ina ƙoƙarin kwance shirinki, wato so ki kayi nima ki ɗaure mun kaina ta yadda zan manta da komai, tabbas kinso ki yi nasara sai dai Allah bai baki ikon yin hakan ba, farkawar dana yi daga bacci komai dana manta sai da ya dawo cikin kaina, Kuma bazan fasa faɗa masu Allah ba, har sai na fargar da su,
“Taya kenan zaki iya aiwatar da hakan? Ko kina tunanin zaki iya sarrafa tunaninsu ne? Yaran da ni na raine su da hannu na, na gatanta su, tun da suke basu ta6a shan wahalar rayuwa ba, komai suna samu ba’a abunda ban yi masu ba, matsayin uwa nake a wurinsu, a haka kike tunanin zasu ji maganarki fiye da tawa”? Tsohuce ta yi maganar yayin da take sakin wani irin bazawarin murmushi,
Wani irin kallon rainin wayau angel tayi mata”Wlh tun da nake arayuwata ban ta6a ganin Muguwar maca ba, Azzaluma kuma macuciya irin ki ba!”
Yadda tayi magana batare da jin ɗar ba, ya yi matuƙar girgiza tsohuwa,
“Wai ke baki jin tsoron Allah? Ki tuna fa komai kike yi Allah yana kallon ki, har kina da bakin da zakice kin basu gata? Kin raine su? Kuma har kike kiran kanki a matsayin uwarsu? Tirr wlh ji nake kamar inyi kakin majina in watsa maki akan fuskarki saboda natsane ki, Wlh nafi son mutuwa ta so dubu dake!” Zuba mata ido tsohuwa tayi tana kallon Ikon Allah,
Sassauta murya angel tayi Idanuwanta cike tab da ƙwalla tace”Kin cuci rayuwarsu, kin gama dasu, ni banmasan ya zan kwatanta irin cin zalinsu da ki kayi ba, kuma ga dukkan alamu kin sani kike take sani, dan baki yi kama da jahila ba, Kawai salon tsabar mugunta ne, Yaran nan ko nonon raƙuma suka sha iya abunda zasu yi kenan, Ga sunan Wasu kala da su they don’t even know anything about the one who created them because you never told them, cos of your wickedness Kin barsu a cikin duhu, sun zo duniya a wahalce kuma zasu koma a wahalce, Idan yau ɗayansu ya faɗi ya mutu menene makomarshi dan Allah meyasa ki ka yi musu haka? Meyasa?……….” kasa ƙarasa maganar angel tayi saboda wani irin ƙuntataccen kuka daya kubce mata, kuka sosai ta fashe da shi,
Tsohuwa kuwa ta kafe ta da waɗannan Kwala kwalan idanuwanta nata, masu kama dana ƴan ƙwaya,
Cigaba da magana ta yi”Idan wani zunubi suka aikata maki, bai kamata ki ɗauki fansa ta wannan hanyar ba, balle ma nasan basu aikata maki komai ba, To kodai cikin danginsu wani ya yi maki badaidai ba, shiyasa kike ɗaukar fansa akansu” ta yi tambayar idanuwanta jawur hawaye duk sun wanke fuskarta,
Tun da suka soma magana babu wanda ya farka daga cikin masu yin baccin, tamkar wasu matattu,
Jinjina kai angel tayi”dama nasani bazaki bani amsar tambayata ba, sai dai ki kafe ni da ido kina kallo,” ta yi maganar cikin sanyin murya tare da sanya hannunta da dama tana share hawayen dake silalowa,
Kafin ta ɗaura da cewa”Allah ba azzalimin bawansa bane, Allah zai bi masu haƙƙinsu, inda na gode ma Allah, Mutuwa tana akan kowa, Walau mutun walau aljan, akwai kwanciyar ƙabari akwai kuma hisabi, Ina fata duk kin shirya ma wannan……..” Muryar Batool ce ta katse ta ta hanyar kiran sunanta”ANGEL” koda tsohuwa taji muryar batool, Sai ta juya da sauri tana dogara sanda ta nufi ƙopar shiga ɗakinta,
Har ta kusa shiga ciki muryar angel ta sake katse ta da cewa”Baki san Su ji me muke tattaunawa ne shiyasa kika nemi hanyar guduwa? Allah dai yana a madakata yana jiranmu, kuma inaso ki sani Zanyi amfani da ilmin da nake da shi, da kaifin basirar da nake da shi wurin Sarrafa tunaninsu, Kuma zansa su kar6i addinin musulunci, after that I will fight for our freedom, because no one deserves to live a locked up life!
Tsawon mintuna tsohuwa bata motsa ba, kuma bata juyo ta kalli inda angel take ba, can dai taci gaba da dogara sandar, har samu ta shige cikin ɗakinta taja ƙopa ta rufe,
Fashewa da wani sabon kukan angel ta yi, da sauri batool ta sauko daga saman gadonta, tazo gaban gadon angel ta zauna daga gefenta,
Muryarta aruɗe take faɗin”Sister what’s wrong with u? and why are u crying”? Kallonta angel tayi da idanuwanta da suka rune, muryarta a karye tace”Batool ina kuka ne saboda ku”
“But why”?
“it will be hard for you to understand me, even if i tell you, so just forget about it,” cikin shessheƙar kuka ta yi maganar,
Dafa shoulder ɗinta batool tayi”Pls ki faɗa mun meyasa kike kuka sabo da mu”?
“Baki ga tsohuwa ba”? Angel ce ta yi mata tambayar, girgixa kai batool ta yi”Banganta ba, tazo ne? Ita ce ta saki kuka”?
Girgiza kai tayi”A’a, Mubar maganar, inaso zan shiga toilet,” daga haka ta zuro da ƙafarta daga saman gadon ta sauko, ta nufi toilet ɗinsu, Ta tafi tabar batool da tunanin dalilin kukanta, meyasa ta ke yin kuka saboda mu? ta yi ma kanta tambayar da bata da amsarta,

Tunda ta shiga Cikin toilet ɗin taci burki ta tsaya Idonta na akan Window nan dake a jikin bango, wadda ta ƙwallafa ma rai akan son Fasa glass ɗin jikinta, don ta samu damar dura wa Cikin kurkukun.

Hannu tasa ta share hawayen dake akan fuskarta, Cikin zuciyarta ta soma yin magana”rana ta farko dana tsinci kaina cikin gidan kurkukun nan, A ƙagare nake dana nemi hanyar da zan fita daga Cikinsa, Amma Ayanzu bana sha’awar Barinsa batare da waɗannan bayin Allahn ba, Kuma batare da ƙwaƙƙwarar hujja da zan yin amfani ba, wurin ganin na tarwatsa duk wani shirinsu, Zanbi komai asannu domin Cimma nasara, Bi’iznillahi,’

Angel yarinya ce mai kaifin basira Fiye da tunanin mai tunani, wayan dake gare ta yafi ƙarfin shekarunta, wasu ɗabi’un nata da halayanta sam ba irin na yara bane, she’s genius”

Lokacin da ta fito daga wankan, A tsaye ta samu Batool tana jiran na ciki ya fito ta samu ta shiga itama tayi wankan” Kallon juna su ka yi,

Murmushi Batool ta sakar mata tare da cewa”tun ɗazu nake jira na ciki ya fito in samu nima in shiga in yi wanka,
Angel tace”Wani ya shiga sauran toilets ɗinne”?
Jinjina kai batool tayi”Eh, Hanna ce ta shiga ɗaya, ɗayan kuma Danish ne da deeja suka shiga Ciki,” Har wata zabura angel ta yi jin abunda batool tace”What! danish da deeja ne suka shiga atare? Saboda me”?
Fuskar batool asake tace”Dama idan babu wuri kuma uziri ya kama mu, mutun biyu suna amfani da toilet ɗaya…….”
tunkafin Batool takai ƙarshen maganarta, Angel ta yi gaba zuwa ƙopar sauran makewayin, Rai a matuƙar 6ace takai hannu tana Bubbuga ƙofofin tamkar zata Fasa su,
“zaku fito ko saina 6alle ƙopar”? Tana huci ta yi maganar, Bama tasan wanne suke a ciki ba,
Kusan atare suka buɗe ƙofofin toilets ɗin, na biyun Hanna ce ta leƙo kai, Na ƙarshen ne Deeja da danish suka fito, wani matsiyacin kallo Angel ta shiga binsu da shi from head to toe, hannun shi na a ruƙe da rigarshi, ita kuma iya rigarce har guiwarta, wandonta na hannunta,
“lafiya kike bubbuga mana ƙopa”? Fuska aɗaure deeja ta yi mata tambayar”
Dakuwa angel ta sakar mata”Ungo nan, Ku dukanku ku kar6a ku raba,”

Kallon juna su ka yi don basu fahimci me take nufi ba, Runtse ido tayi zuciyarta na tafarfasa ta ambaci”Allahu ajirni fil musibati……
Batool sai faman tamyarta take yi lafiya? Meya faru”? Ware idanuwanta ta yi akan fuskar deeja da ta danish, sae faman lumshe eyes ɗin shi yake yi, da alama bacci bai ishe shi ba, Sam tarasa ta ina zata fara, wato su awurinsu ba laifi bane idan mace da namiji sun shiga toilet ɗaya, tun zuwanta bata ta6a sanin suna yin hakan ba, Sai yau da take ji awurin batool ta kuma gani da idanuwanta,

Cizon lips ɗinta tayi tamkar zata fasa su, Cikin fusata ta nuna Deeja da hannu”Zoki wuce, Ki jira idan ya gama ki shiga” maƙe kafaɗa deeja tayi”babu inda zanja, meye naki aciki?
Wata irin gigitacciyar tsawa angel ta daka mata, Saboda tsabar ruɗi a firgice danish Ya koma Cikin toilet din,”
Da gudu Sauran Ƴan uwansu dake acikin ɗakin suka faɗo Toilet area ɗin, Haris da su aziza,
“Meke faruwa ne”? Javed ne yae tambayar, Batool tace”Nima bansani ba, ranta ya 6aci ne saboda na faɗa mata cewa idan uziri ya kama mu kuma babu wuri mutun biyu suna shiga toilet ɗaya shine take fushi,”
Harara haris ya watsa mata tare da cewa”To ke meye naki aciki da har zaki nuna 6acin ranki akai”?
Matsawa angel tayi Saitin inda haris yake a tsaye, Kafin ta soma magana atsanake,
“Saboda hakan bai dace ba, Koda kuwa Namiji da namiji ne su shiga toilet ɗaya balle kuma Mace da namiji, bazan bari ana aikata 6arna batare dana hana ba, don haka daga rana irin ta yau, idan har na ƙara kama mutun biyu acikin toilet ɗaya, Saina Karanta ma shi charman dudu Cikin shi ya kumbura ya mutu kowa ya huta”

Jin wannan maganar ta angel yasa hankalin kowannansu ya tashi, musamman deeeja tuni idanuwanta sun cicciko tan da ƙwalla,

“Ya kike so muyi idan uziri ya kama mu, a lokaci ɗaya”? Hanna ce tayi mata tambayar,
“Sai ku matse koma menene ku ke ji, idan na ciki suka kammala suka fito sai mutun ya shiga”
“Ammaaaa…….”kasa ƙarasa maganar haris yayi ganin tana nannaɗe hannun rigarta alamar za ta yi dambe,
“Abi Umarni na azauna lafiya, Shine kawai idan kuma mutun yace zaiyi mun gardama, yasan me zai biyo baya,”

Gaba ɗaya duk suka sha jinin jikinsu, juyawa tayi tare da kallon deeja”Ke kuma Munafuka, zoki wuce ki jira idan ya kammala ki shiga, ni dama sam ban yarda dake ba, da wasu idanuwanki tubarkalla kamar na kwartan mazuru, idan shi yana da ta6in hankali ai ke da hankalinki, Sullu6iyo kawai, zaki wuce kosaina Zubar maki da haƙoran gaba”? Jiki na rawa deeja ta ƙarasa fitowa daga cikin toilet ɗin Taja ƙopar ta rufe,

Kallon sauran ta yi”Kowa Ya kama harkar gabansa, kuma Allah yasa wani yayi gulmata acikin ku, Aljanata kamila zata faɗa mun ne, daga nan ni kuma zan tofa ma mutun charman dudu” takai ƙarshen maganarta tare da sa kai ta wuce su tamkar damisa, Ta nufi Cikin ɗakin sai da ta shiga ta zauna gefen gadonta, Taci gaba da tiƙar dariya, can kuma ta dakata da yin dariyar hawaye suka soma shararowa daga cikin idanuwanta,
Hannu biyu tasa ta dafe kanta, wani irin tsananin tausayinsu take ji, har cikin ranta take jin tsananin sonsu da ƙaunarsu, a halin yanzu babu wanda bata so acikinsu, saboda tausayinsu da take ji, ashirye take data taimaka masu wurin gyara rayuwarsu,

Jin motsin shigowar su Cikin ɗakin Yasa ta yi saurin share hawayen dake akan fuskarta, ta kishingiɗa saman gadonta,

A jere suka shigo kowa sai satar kallon Angel yake yi, cike da jin tsoronta, Ko zama ba suyi ba, Giants suka turo ƙopa suka shigo Hannunsu ruƙe da kayan breakfast ɗinsu, ba ƙaramin daɗi angel taji ba dama daren Jiya da wata irin matsiyaciyar yunwa ta kwana,

Bayan sun ajiye Masu farantan, kamar kullum Jiki na rawa suka Nufi saman Carpet ɗin kowa yayi zaman Cin tuwo, Suka zagaye trays ɗin,
Sai da duk suka hallara, Hada danish wanda tunda ya zauna Jikin shi keta kerma sam babu natsuwa attare da shi, Gaba ɗaya tsawar da angel ta daka masu ɗazu ta gama gigita shi,
Tun da suka fara Cin abinci, Wurin ya yi tsit baka jin sautin komai saina taunar abincin da suke yi, ganin nata ya kusa ƙarewa yasa ta fara tsantsani, can data lura danish ba wani cin abuncin yake yi ba, tsakurarsa kawai yake yi kamar baisan ci, da yake suna Fuskantar Juna, ta faki idon sauran ƴan uwan nasu, tayi musayar plate dana danish, ko da taga yana kallonta, saita zazzare mashi ido don kar yace zai anshe kayan shi,’ lamarin yayi matuƙar ɗaure ma shi kai, yana ji yana gani tayi mashi musayar plate, ta ajiye ma shi nata data kusa Cunye, na shi kuwa a cike yake da abinci, bai dai ce komai ba, Yaci gaba da cin nata abincin data tura mashi,

Bayan sun kammala, Giants suka tafi da kayan abincin, Ganin Kowa ya nufi gado zai kwanta yasa tayi saurin cewa”Ku dakata” Tsayawa su ka yi tare da juyowa suna kallonta,
“From now on, when you finish eating food, no one will lie down and sleep, you have to exercise, doka ta ce duk wanda yaƙi bi kuma yasan me zai biyo baya,’
Natsuwa su kayi suna sauraronta, Haris ne yai kokarin cewa”Saboda me”?
“Saboda lalacin ku yayi yawa, idan kuna motsa Jiki zaku yi ƙarfi, ”
“So kike kiyi iko damu”? Kafin ta bashi amsa aziza tayi saurin cewa”pls haris kayi shiru, kada ta karanta mana charman dudu, nidai zanyi abunda kike so angel,”
Murmushin gefen fuska angel tasaki tare da kallon su batool tace”what about u guys? Zaku yi ko kuwa”? Har suna haɗa baki wurin cewa”eh zamuyi komai kikeso” Kallon haris tayi”kaima dole kayi idan har kana son zaman lafiya, idan ba hakan ba ta kanka zan fara aiwatar da aikina, tare da aljanata kamila,”
Haɗe girarsa yai fuska a tur6une yace”Ae bance bazan yi ba”
Ƙumshe dariya tayi abakinta, daƙyar ta samu ta basar da dariyar, ta ɗaure fuska tana hura hanci,
“Sister ya ake yi toh baki faɗa mana yadda zamu motsa jikin ba”

“U will start running from wall to wall, untill i command you to stop, Idan aka kammala sai ayi Jumping,”

Amsa mata su ka yi da toh, jikin bango suka koma suka tsaya a jere, Kowa ya naɗe hannun rigarshi,
Komawa tayi daga bakin gadonta, ta zauna tare da ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, Cike da bada Umarni Tace”Idan Na ƙirga uku Sai ku fara” su ka amsa mata”Toh”

“1,2,3, Oya start” Da gudun gaske suka tafi Bayin Allah, Idan suka kai karshen bango sai su dawo sai su koma, har saida su ka yi kusan sau talatin tukunna ta basu hutu, zuƙunnawa su kayi a ƙasa, zufa ta ko’ina ajikinsu, Musamman danish kamar an tsamo shi daga Cikin ruwa, sae nishi suke yi,
“Lokacin yin jumping ya yi, Maza kowa ya miƙe afara tsalle sau talatin kowa zaiyi duk wanda ya kammala sai yaje toilet ya watsa ruwa,” amsa mata su ka yi da toh, ta tsaresu da ido har saida kowa ya kammala tsallan nashi, sannan ta ƙyale su tace kowa ya watsa ruwa azo ayi fira,
Anan ta zauna tana jiransu, Bayan sun kammala, Jiki amace suka dawo cikin ɗakin Kowa Ya zauna saman gadon shi,
“Yau kin bamu wahala sister, amma naji daɗin Jiki na” batool ce ta yi maganar, Haris da deeeja sunfi kowa Jin haushin angel, saboda ta sanyasu aikin wahala, danish kuwa tuni bacci ya yi awon gaba da shi, sam basu saba da wahala ba,

Kallon su ta yi ɗaya bayan ɗaya tun daga kan danish dake bacci har zuwa sauran dake ta faman yin gyangyaɗi,

Gyaran murya ta yi masu gaba ɗaya hankalinsu ya dawo kanta,
” Jiya kamar Kunyi mun wata tambaya ko’? har suna haɗa baki wurin cewa”tambaya akan me kanan”? Ta gefe ta kalle su “Kun manta? Ku tuna kun tambaye ni wani abu jiya,”
“Eh, muna so Ki bamu labarin rayuwarki,” azeeza ce ta yi maganar,
“Gobe zan baku labarin rayuwata, Yau inaso Mu tattauna dangane da addini ne, Kallon juna su ka yi kafin suka dawo da hankalinsu kanta,
“Addini kuma? Menene ma’anar hakan”? Da ruɗi akan fuskar hibba ta yi mata tambayar,
Tana kokarin buɗe baki taci gaba da magana, Danish dake bacci ya kwatsa wata irin razananniyar Ƙara mai firgitarwa, ” gaba ɗaya Hankalinsu Ya koma kanshi,
A zubure ya miƙe zaune Ya sanya hannayenshi Biyu ya daddafe kanshi, yaci gaba da fasa gigitacciyar ƙara, Da gudun gaske su haris suka sauko daga saman gadajensu. suka nufi gadon danish, Kowa ya shiga Lallashin shi suna bashi baki,
Angel kuwa sakin baki tayi tana kallon ikon Allah. lokaci ɗaya ranta ya bata cewar tabbas Danish ba shi kaɗai bane, Meyasa sai lokacin da take ƙoƙarin yin magana kan addini zai farka yana fasa masu ƙara? Da alama anyi hakan ne don a ɗauke masu hankalinsu daga kanta, gashi yanzu gaba ɗaya sun rasa samun natsuwa sun duƙufa suna lallashin shi,
Wani irin wahalallan murmushi angel tasaki tana kallon ikon Allah, wato da tsiya dai sai an dakatar da ita, jiya an kwaɗe mata kai da sanda yau kuma ta 6angaren danish aka biyo mata,
“Danish Pls can u talk to me? kana ganin fuskokin mu? Meya faru dakai? Atare suke jefa mashi tambayoyin nan, Angel ta kasa kunne tana sauraronsu,
“Danish ka yi mun magana meke damunka? haris ne yae tambayar yana shafa dogon wuyanshi, Sae faman kerma jikin shi yake yi, ga wata irin zufa dake tsastsafowa daga Cikin sumar kanshi, ya runtse idanuwanshi sosai, duk ya ciccije lips ɗinsa,

Zurfin tunani ta shiga yi, shin wata hanya zata 6ullo masu, tun da nan an toshe ta, sai yanzu ta ƙara yarda cewa akwai wata maƙarƙashiya, bakomai take tunawa ba face Wani American film da ta ta6a kallo na Magicians, a gidan aunty aneelerh, A cikin Film ɗin matsafa ne suke canza ma mutun tunaninshi su sarrafa shi, ko su sanya mashi tsafi a jikin shi, ko kuma suyi amfani da shi,’ Jiya daga za ta yi magana an kwaɗe mata kai, kuma bata ga kowa ba, hakanan ta ke zargin tsohuwace kuma ga dukkan alamu zarginta ya tabbata tsohuwarce, sanan meyasa Basa son duk wani abu daya shafi Addini? A lokacin da ta kalli film ɗin ta ɗan shiga ruɗu harta tambayi aneelerh,
“Su matsafan ba’a iya yin maganinsu”? aneelerh tace”Allah shi ne maganinsu, idan yaso duk wannan 6acewar da suke yi sai kiga an kama su har an ɗauki mataki kansu, shiyasa ake so mutun ya kiyaye kuma ya dage da neman tsari awurin Allah, saboda su mutanene masu hatsarin gaske, ta kowace hanya zasu iya 6ullo maka,” aneelerh tayi mata bayani akansu sosai, Natsuwa tayi tana bin ko’ina na ɗakinsu da kallo, tana ji acan ƙasan Zuciyarta kamar ta manta da wani abu, wanda ta gaza tunawa acikin kwakwalwarta, Aranta tana ji kamar ta ta6a kasance acikin gidan kurkukun ƙaddara, tsayar da idanuwanta ta yi akan red carpet ɗin da suke zama Su ci abinci kanshi, tunawa tayi da maganar aneelerh a inda tace”ɗaya daga Cikin alamomin matsafa, shi ne launin Ja, suna sanya jajayen kaya ko kuma A gidansu suna yawan amfani da jan abu kamar labule haka da sauransu,
Jinjina kai angel tayi tare da cewa”Tsohuwa tana sanya jajayen kayan, Kuma carpet ɗin ɗakin mu Shima ja ne, kuma duk in aka kawo mana abinci, a saman trays ɗin ana sanya janƙyalle a rufe shi, Menene ma’anar launin jan nan na gidan kurkukun ƙaddara? su Giants suna sanya Baƙaƙen kaya shima launin baƙi bako da yaushe yake kasancewa abu mai kyau ba, dole nayi kokari wurin gano ma’anar waɗannan kalolin guda biyu Black and Red, kuma dole Nayi bincike akan lalurar dake damun danish domin kuwa wannan ciwon nashi Ba Misophonia bace, Kirkirarta a ka yi domin shi kawai,

Hankalin angel fa yaƙi kwanciya, Saima ƙara ta shi da yake yi, Babban abunda take ji ma tsoro, Abunda take hasashe ya zamo gaskiya, saboda taji ance matsafa idan suka ɗauki mutun suna amfani da shi ne, Ko su cire sassan jikinshi, Ko su ɗibi jinin jikin shi, idan kuwa har hakane, To kuwa bata ga ta zama ba, duk da tana kokwanto akan hakan saboda su Batool sun faɗa mata cewa ba’a ta6a cutar da su ba, Kuma suna samun abinci, Matsafa ina suka ga lokacin ba mutun abinci, da zarar sun kamo shi kashe shi suke yi bayan sun gama kwashe amfanin jikin shi,

Duk ba wannan ba, tambayoyi da yawa da take neman amsarsu WACECE TSOHUWA? SU WANENE GIANTS DAKE ZUWA KAWO MA SU ABINCI? A INA GIDAN KURKUKUN ƘADDARA YAKE? TA FARA HASASHEN GIDAN KURKUKUN BA’A CIKIN NIGERIA YAKE BA, ZAIYI WUYA MA ACE ACIKIN GARI YAKE, SHIN SU KAƊAI NE ACIKIN GIDAN KURKUKUN KO KUWA AKWAI WASU MUTANAN? MEYASA AKA HANASU SHIGA CIKIN SHI”?

ta yi zurfi a cikin tunaninta muryar batool ta katse ta da cewa”Angel har yanzu baki yi bacci ba”! Firgigit tayi tare da kallon batool dake a zaune gefen gadonta hannun ruƙe da fitila, tsananin mamaki ne ya kamata, ganin duk sunyi bacci, ita kaɗaice zaune saman gadonta, batasan tsawon lokacin da ta ɗauka ba, Sai da batool ta fargar da ita, ashe dare ya yi har sun kwanta, ita a yadda tabarsu suna akan danish dake ta fasa ƙara, Yanzu ga danish ɗin nan kwance cikin bargonshi sai bacci yake yi, su azeeza ma duk sun kwanta,
“Yansu na farka zan shiga toilet shine na hango ki a zaune, nayi mamaki” murmushin yaƙe angel ta sakar mata tare da cewa”Bana jin bacci ne, ya jikin danish”?
“Ya ji sauƙi, baki ga ma har yayi bacci ba” tayi maganar tana haska gadon danish ,
Gyaɗa kai angel tayi”Nima yanzu zan kwanta, kije ki shiga toilet ɗin,”
Batool tace”ae har na shiga na fito, zan wuce ne na lura dake a zaune”
Shiru angel ta ɗanyi, ganin kamar tana acikin damuwa yasa batool tace,”Baki da lafiya ne? Ko wani abu na damunki”?
da sauri angel tace”bakomai, kawai ina tunanin rayuwar duniya ne”
“Yau da kika samu motsa jiki, ga6o6in jikina sai ciwo suke yi mun, amma yanzu dana ta shi daga bacci sai naji daɗin jiki na,”
Angel tace”idan kuka saba kullum zaku ji dadin jikin ku, zai saki sosai ba’a son mutun daga yaci abinci ya kwanta, anfi son kadan motsa jikinka, “bayani tayi mata dangane da amfanin motsa jiki, batool tace”Daga yanzu duk in muka ci, abinci zamu dinga yi, bari naje na kwanta” tana kokarin miƙewa angel ta yi saurin ruƙo hannunta, kallonta batool tayi tare da cewa”Lafiya”?
“So nake na tambaye ki, A gidan kurkukun nan Ana kiwon kaji ne”? Cikin rashin fahimtar zancanta, batool tace”Kiwon Kaji kuma? Meye ma’anar hakan”
Dafe kai angel tayi”Ina Nufin kaji da ake kawo mana muna ci kusan kullum, Ana kiwonsu ne a gidan nan ne? Still batool bata fahimci zancenta ba, ta dai san kaza da ake kawo masu a soye suci, amma batasan ma’anar kiwon ba,
“Shikenan tunda baki sani, Amma kin ta6a shiga cikin kurkukun nan? Naga ranar da aka kawo ni, Ni kaɗai nafarka acikin ɗakin nan, Ku kuma daga waje kuka shigo Ciki, Ina kuka je ne”? Ta yi tambayar tana kallonta”
“Bazan iya tuna komai ba,” cike da takaici angel tace”Komai baki sani ba ke, to faɗa mun a gidan kurkukun nan ku kaɗai ne kuke rayuwa a cikinsa”?

Girgiza kai tayi”A’a bamu kaɗai bane, Kinga wannan numbobin na bayan rigunan mu, akwai me 400,” waro ido waje angel tayi muryarta har shaƙewa take yi wurun cewa”Are u serious”? Ɗaga mata kai batool tayi alamar Eh, taci gaba da cewa”idan zan iya tunawa kafin zuwanki, Munyi rayuwa acikin wasu Prisoners ɗin waɗanda Ke rayuwa a killace cikin kurkukun nan, bamu kaɗai bane, muna da yawa,” mamaki ƙarara akan fuskar angel ta kuma cewa”Amma ku meyasa aka ware ku daga Cikinsu”? Batool tace”nima bansani ba,”
“Yanzu faɗa mun, duk wani abu da kika sani game da kurkukun nan,”
“Bansan komai ba”
“Ke dai ki tuna” shiru batool tayi tana kokarin tunano abunda ta sani, tsawon lokaci kafin ta soma magana
“Idan aka ɗauki mutun ba’a dawo wa da shi, idan muka tambayi tsohuwa ina ƴan uwanmu suke waɗanda aka ɗauka daga Cikinmu, sai tace mana mu kwantar da hankalin mu, Suna nan cikin ƙoshin lafiya wata rana zasu da…..” bata kai karshen maganarba, ta miƙe da sauri ta dauki fitilarta, ko kallon angel ba ta yi ba ta wuce saman gadonta ta kwanta,
Zuba mata ido angel tayi Cike da mamakin yadda ta miƙe zumbur ta tafi batare da ta ƙarasa maganarta ba, kodai itama an zungureta ne? Ta yi tambayar a cikin Zuciyarta,

Kafin ta yi Shirin kwanciya, kamar kullum ta ɗaga hannayenta sama tana yi masu addu’o’i, Hada daddynta kullum ne bata mantawa da shi, Yana acikin ranta……….🥺

*ANEELERH*

Mami ce zaune gefen gadonta har ta yi shirin kwanciya, jikinta na sanye da Sleeping gown, ta ƙura wa screen ɗin wayarta ido,
fitowa abie Yayi daga Cikin toilet yana gyara wuyan jallabiyar jikin shi,
gyaran murya yayi mata ta ɗago tana kallon shi, fuskarta da alamun damuwa tace”Ina ta kiran aneelerh bata ɗaga ba, ”
“Bansan meyasa kika tashi hankalin ki ba, sai kace wadda ta tafi wata uwa duniya,”
“Dole na damuwa, saboda ni bata faɗamun cewa a can xata kwana ba, kuma na kira layin Uncle bash ɗin tana ta ringing bai ɗaga ba, itama dr Aisha na kira layinta bata ɗaga ba, idan acan zata kwana ae yakamata su kira su sanar dani,”
Murmushi abie ya saki”Na lura ba ƙaramin ji kike da ƴar nan taki ba, Ko da yake nasan saboda wa kika hana idonki bacci,”
“Bai wuci kace saboda baby junaid ba, ae dole na damu da jika na, shi kaɗai fa nake da shi kwallin kwal an tafin mu da shi, sai da nace tabarmun shi a wurina, amma ta kafe akan saita je can da shi,”
“In banda abunki, taya zata tafi tabar maki shi, bayan ba’a yaye shi ba, idan ya yi kuka ya zakiyi da shi”?
“Nima ae macace, Kaima kasan ina da abunda zan bashi” Dariya abie yayi a lokacin ya dawo gefenta ya zauna,
“Yanzu dai ki kwanta kiyi bacci, zuwa gobe da safe, zasu dawo kiga jikanki,”
Ba don taso ba, ta ajiye wayar Suka kwanta bacci atare,

A 6angaren Aneelerh Kuwa, tun Bayan magbrib suka baro gidan Uncle bash, Drivern gidansu Musa ne ke yin driving ɗinta, Tana a zaune Cikin back seat na motar, Jikinta na sanye da Arab gown ta yafa mayafi akanta, Baby junaid na rungume saman kirjinta, Yasha kayan sanyi ajikin shi,

“Ba gida zamuje ba, Gidana nake so ka kaini akwai wasu kaya da zan ɗauka”musa dake driving yace”Amma Ba mu yi da Alhaji cewa zan kaiki gidanki ba,”
“Eh na manta ban faɗa ma shi ba, ka kaini ba matsala,” acewar aneelerh,
Shi dai hankalin shi bai kwanta da su je gidan nan ba, ganin dare yayi kuma gidan yana a karkashin Binciken ƴan sanda bai son wani abu ya faru,
“Amm hajiya naga dare yayi yanzu, me xai hana mu bari sai gobe da safe in kaiki gidan’?
ɗaure fuska aneelerh tayi sam batasan gaddama”meyasa ka ke yi mun magana sai kace wata ƙaramar yarinya? Bani nace ka kaini ba? Ae ba jimawa zanyi ba, akwai abunda nake so in dauko ne Ko minti biyar bazan yi acikin gidan ba,’
Muryar shi na inda inda yace”Zan kai ki mana kawai dai naga dare yayi ga kuma yaro ahannunki,’
“Muje kawai nidai” Amsa mata yayi da toh, ya juya sitiyarin motar ya haura saman titin da zai sada shi da unguwarsu Uzair,
Lokacin da suka ƙaraso unguwar tsit babu hayaniya ko gifcin mutun baka gani, kowa ya shige gidanshi, akwai hasken street light ta ko’ina,
A bakin gate ɗin Gidan, Musa yayi parking ɗin motar, ya fito da sauri ya buɗe ma aneelerh murfin motar, Fitowa tayi hannunta rungume da junaid, Key ɗin gidan yana a hannunta, Dama biyu gare su ɗaya na uzair ɗaya nata, wanda ke a hannun jami’an dake bincike na Uzair ne,

“Madam kodai in bi ki mu shiga Ciki”? Kallon shi tayi ganin duk ya tsorata”Motar fa wa zaka barma gadinta”? Muryarshi a sanyaye yace”hakane kuma bari na koma Ciki na jira ki, dan Allah Aunty kiyi sauri” murmushi tasaki jin ya canza mata suna, ya kirata da madam ya kuma kirata da aunty, Maimakon sunan da yake kiranta da shi Hajiya,
Wuce wa ta yi zuwa bakin ƙopar dake a jikin gate ɗin gidan, ta sanya key ta buɗe ta, ta shiga daga Ciki, duk akan idon musa dake a tsaye ya jingina bayan shi jikin motar,

A tsanake take tafiya Cikin Gidan wani irin yanayi take ji atattare da ita, Ko’ina ta shiga bi da kallo, tun daga kan inda suke ajiye motocinsu har zuwa ƙopar shiga falonsu, Bakomai take tunawa ba face rayuwarsu da Uzair, tuni taji hawaye sun wanke mata fuskarta, yau tsawon shekara biyu da watanni kenan, babu su babu alamarsu,
Hasken electric bulbs ne Ya gauraye gidan, tamkar da rana,

Lokacin da tazo bakin ƙopar falon, ta sanya key ta buɗe ƙopar ta shiga daga Ciki, Ko’ina a gyare yadda kasan mutane na rayuwa acikin gidan,

A saman Sofa ta kwantar da baby junaid dake ta bacci, ita kuma ta shige Cikin bedroom ɗinsu, tsayawa tayi tana bin ɗakin nasu da kallo, sai ta dinga ganin kamar fuskar uzair yana sakar mata murmushi,

Girgiza kai kawai ta yi yayin da hawaye ke cigaba da sauka saman fuskarta, Hotonsu na aure dake manne jikin bango ta ƙurawa ido, Sunyi matuƙar yin kyau, kusan minti biyar kafin ta Hau saman gadonsu ta kwanta tana shessheƙar kuka,
Dama babu abunda ya kawota Cikin gidan tazo ne kawai don ta ƙare mashi kallo saboda kewar Mijinta da tayi,,

Bubbuga mattress din ta dinga yi da hannunta tana kuka tana faɗin Wai ina kaje uzair? Meyasa ka tafi kabarni cikin maraicin rashinka, bayan kasan bana iya rayuwa da wani ɗa namiji idan ba kai ba, dan Allah mijina ka dawo gareni wlh ban gaji dakai ba, ina matuƙar ƙaunarka, kazo kaga Babynmu kyakkyawa da shi, so kake ya taso amatsayin maraya wanda bai da uba? Why uzair? Wata amsa kake so na bashi idan ya tambaye ni dangane da Mahaifinsa? Sai sambatu take yi ita kaɗai tana kuka, sam ta manta da Musa driver dake jiranta, ga kuma Yaro da ta bari a palour shi kadai saman Sofa yana bacci,

Kusan awa ɗaya aneeelerh bata motsa ba, wani irin yanayi mara misaltuwa take jin kanta a ciki, sai faman shessheƙar kuka take yi,

Lokaci ɗaya taji mummunar faɗuwar gaba ras! Tamkar ƙirjinta zai dare biyu, bugun zuciyarta ya ƙaru, Jiki na rawa ta sauko daga Saman gadon muryarta na kerma take ambaton sunan Junaid,

Da gudun gaske Ta faɗo Cikin Falon, Tana ɗaura kanta saman Sofa ɗin data kwantar da junaid, taga wayam babu shi sai dai towel ɗin data nannaɗe shi aciki, A ƙasa aka jefar da shi,

Kamar afarmaki take ganin lamarin, Tsabar ruɗi tarasa me zatayi, Tsananin tsoro ne bayyane akan fuskarta, Ƙarasawa tayi gaban sofa ɗin ta sanya hannu tana shafa Saman kujerarar, ta tabbatar cewa an ɗauke Mata Yaronta, tunani tayi kodai Musa ya shigo ya ɗauke shi ne? da gudu ta zabura Ta fito daga cikin falon, Har ta kusa kaiwa Bakin gate ta juyo kukan baby junaid ɗinta, a matuƙar gigice ta juya ta koma Cikin gidan, duk inda ta nufa sai taga babu shi, Rushewa tayi da matsanancin kuka tana faɗin”Innallalahi wa’innna ilaihirraji’un! Wayyo Allah na! dan Allah wanene ya shigo? kada ku cutar mun da yarona na roƙe ku, ku ƙyale mun shi, ‘ tana Cikin maganar nan tajiyo takun tafiyar mutun a firgice ta juya bayanta, gifcin shi ta gani koma wanene yana a sanye Cikin bakaken Kaya, Fuskar shi tana sanye da face mask, Hannunshi na ruƙe da Baby Junaid, Da gudun gaske Aneeelerh tabi bayanshi, sai dai kafin ta ƙarasa tuni ya 6ace ma ganinta,
Gaba ɗaya ta haukace Jikinta sai tsuma yake yi ga wata uwar zufa data tsastsafo mata, ita ba kanta take ji mawa ba, Ɗanta take jimawa ba, shida bai mallaki hankalin shi ba,
“Dan Allah na roƙe ka ka dawo mun da ɗana, Kome kakeso zan baka, Amma kada ka cutar mun shi, idan ma ni kakeso ka dauke ni ka ƙyale mun shi pls,” cikin shessheƙar kuka tayi maganar,

Motsi ta kuma Ji daga can saman stairs ɗin gidan, A hautsine ta ɗaga ido tana kallon mutun dake atsaye, Hannun shi ruƙe da baby junaid, ƙarfin hali hada ɗaura shi saman kafadarshi, yana shafa bayanshi, kuma yaron yayi shiru,

Zuba ma shi ido tayi tana kallon shi batare da ƙyaftawar ido ba, Koma wanene wannan mutumin ba ƙaramin karkarfa bane, Yana da tsayi da kuma faffaɗan Ƙirji, ta ko’ina ya rufe jikin shi, ta yadda mutun bazai iya shaida shi ba,
Muryarta na kerma tace”Dan Allah kada ka cutar mun da shi, kome kakeso zan baka,” ta yi maganar tana kallon shi, zufa ta ko’ina saman fuskarta,
Gani take kamar zai jefo shi ta saman bene ne ya faɗo kasa kanshi ya fashe,
Fashewa ta kuma yi da wani sabon Kukan, Tunawa tayi da musa driver da gudu ta juya ta nufi hanyar fita don taje ta sanar da shi abunda ke faru,
Harta ruƙe handle ɗin ƙopar, Muryar mutumin ta ratsa kunnnuwanta,
Cikin harshen Turanci yace”idan kika kuskura kika fita, zan wurgo da shi ƙasa,” Ras Taji gabanta ya faɗi, Kamar gunƙi haka ta ƙame, zuciyarta a cunkushe Ta juyo tana kallon shi, Har lokacin Yana a can sama,
Muryarta na kerma tace”Na fasa bazanje ba, wlh bazanje ba, dan Allah ka bani ɗana, wlh nayi maka alƙawari bazan ƙara zuwa gidan ba,”
Dawowa cikin Falon Ta yi, A bakin stairs ɗin ta tsaya, fuskarta jaga jaga da hawaye, Bata ta6a ganin tashin hankali ba irin na yau, Ko wanene wannan mutumin? Taya akai ya shigo Cikin gidan? Bayan makullan gidan Suna a hannun jami’an ƴan sanda? Anya kuwa mutunne kodai ta bango ya ratsa Ya shigo?
“Ka faɗamun ko nawa kakeso zan baka ina da kuɗi, Ni dai kawai burina ka bani Yarona,”
Tana magana tana taka staircases ɗin, a kokarin ta nata haura inda yake,
“Hajiya” Muryar Musa driver ce, A firgice aneelerh ta juya tana kallon musa, Ai koda musa yayi arba da mutumin dake A can saman stairs sanye da bakaken kaya, Nan take jikin shi ya hau yin kerma, Ya shiga ambaton”Ƙalu Innallahi wa’inna ilaihirraji’un hajiya wannan kuma daga ina”?
Cikin muryar kuka aneelerh tace”Nima bansani ba, Daga shiga Cikin ɗaki na dawo na taras ya dauke mun baby junaid ɗina, dan Allah kataimaka ka sanya baki mu bashi haƙuri ya bamu junaid mu tafi mubar masa gidan,”
Kallon shi musa Ya kuma yi”Bawan Allah, Don son da kake ma iyayenka Ka taimaka ka bamu yaron nan, Wlh tsautsayi da ƙaddara ne ya kawo mu Cikin gidan nan, dama saida na gargaɗi hajiya nace mata kada mu zo, Amma ta sanya naci akan sai mun zo yanzu ga irinta nan”
Roƙonshi suka dinga yi ko tanka masu baiyi ba, tamkar baijin me suke cewa, Ya ƙanƙame Yaro a hannunshi sai shafa sumar kanshi yake yi,

“Hajiya wannan mutumin fa, ba bamu yaron nan zaiyi ba, Kizo muyi ta kanmu kawai, Allah zai baki wani ɗan, idan ba haka ba mu duka zamu rasa ranmu,”
“Wlh ba inda Zanje sai ya bani yarona, saboda bakasan ciwon haihuwa ba shiyasa zaka ce mu tafi mubar ma shi yaro a hannu, ” rai a6ace takai ƙarshen maganar, Duk yana atsaye yana sauraron su,
Suna Cikin yin maganar nan, gaba ɗaya hasken gidan ya ɗauke, duhu ya mamaye ko’ina,
Aneelerh ta shiga matsanancin tashin hankali, Cikin duhu taci gaba da tattaka matattakalar benan, Tana jiyo muryar musa yana kwala mata kira, amma ina kota kanshi bata bi ba, lokacin da ta ƙarasa hawa benan, Muryarta na rawa take faɗin”Bawan Allah, ka bani yaro na in tafi, nasan kana jina, dan Allah kada ka cutar mun shi,” tana magana tana lalube Cikin duhu,
Motsin shi ta dinga Ji acikin kunnuwanta, alamun yana a kusa da ita, Kamar ma zagayeta yake yi, Jikinta sai kerma yake yi, ga wata uwar zufa dake tsastsafo mata, mugun tsoro take ji, amma saboda soyayyar dake a tsakanin uwa da ɗa, ta kasa guduwa ta kwammace komai zai faru ya faru, koda zata rasa ɗanta ne,
Wani irin daddaɗan ƙamshin turare ta soma shaƙa Cikin hancinta, koma wanene wannan Ba 6arawo bane, Kuma ba da niyar mugunta yazo ba, Lamarin ya rikitar da ita,
Cikin sanyin murya tace”Dan Allah ka bani shi in tafi, wlh bazan faɗi ma kowa naga mutun acikin gidan ba,”
Hannunta taji ya ruƙo, ras taji gabanta ya faɗi, ɗaura mata baby junaid yayi asaman ƙirjinta, da sauri ta tallebe shi, ta rungume abunta ajikinta, Natsuwa tayi tana jiran jin ya furta wata magana sai dai baice komai ba,
Lokacin da ta daina jin motsinshi a kusa da ita, a dai dai wannan lokacin hasken Gidan Ya dawo gaba ɗaya ya gauraye ko’ina,
Nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke, tare da ɗaura idanuwanta kan baby junaid dake ta sharar bacci, saman ƙirjinta,
Ƙara ƙanƙame shi tayi ajikinta, kamar zata mayar dashi Cikin cikinta, Yau da ace ɗan tahalinkin nan ya kashe mata shi, da kuwa har ranta zata iya rasawa,
“Hajiya zamu iya tafiya yanzu”? Musa ne yayi maganar jikinshi sai kerma yake yi, yana daga can down stairs, Harara ta wurga mashi,
“Ka bani key ɗin motar, ka kama gabanka, Sakaran Namiji kawai, hada cewa in bar mashi yarona in Zo mu tafi, ban ta6a ganin ragwon namiji irin ka ba, duk macan da ta aure ka tayi asara, ” zuru musa yayi mata da ido,”
Saukowa down stairs tayi tare da miƙa mashi hannu”bani key ɗin motar”
Cikin sanyin murya yace”ayi haƙuri hajiya ruɗu ne ya jawo hakan”
A fadace tace”dalla ni bani key,”
Zaro key ɗin motar yayi daga Cikin aljihun shi ya miƙa mata, tasa hannu ta fusge shi, Cikin fushi ta fuce daga cikin falon,
Da gudu musa yabi bayanta yana lallashinta.
Bayan ta rufe gidan da key ta buɗe mota zata shiga driver seat, da sauri musa Yayi hanzarin cewa”Dan Allah aunty aneelerh kiyi hakuri wlh bana Cikin hayyacina ne, su6ul da baka nayi wurin furta maganar, ban kaiga tace ta ba,”
Daƙyar musa ya samu aneelerh ta haƙura ta miƙa mashi key din motar, ta shiga passenger front seat ta zauna shi kuma ya zauna a driver seat,”
Da gudun gaske ya fusgi motar, kafin su ƙarasa gida saida ta gargaɗe shi akan karya kuskura ya faɗa ma su abie dangane da mutumin da suka gani Cikin gidan, yaja bakin shi yayi shiru tun da bai cutar dasu ba, su ɗauka tamkar mafarki su kayi, Yace mata toh,

Lokacin da suka ƙaraso Cikin gidan, A parking space Musa ya yi parking ɗin motar, ya fito ya zagaya ta other side ɗin ya buɗe ma Aneelerh mota,
Fitowa tayi hannunta rungume da baby junaid, Har lokacin Jikinta kerma yake yi, ta tsorata sosai da wannan tahalikin da ya kai masu farmaki,
Kallon musa tayi shima kallon nata yake yi, harara ta jefa mashi ya sunnar da kan shi ƙasa, Ni zan wuce ciki, ”
“To hajiya sai Allah yakaimu, Allah ya kyauta gaba,” bata amsa ma shi ba ta nufi Cikin gidan,
Da alama duk sunyi bacci, bata nufi ko’ina ba, Sai Cikin Bedroom ɗinta, a saman gado ta kwantar da junaid, sai baccin shi yake yi hankali kwance,

Rage kayan jikinta ta yi, ta shiga toilet domin yin wanka, after 15 mins ta fito waist ɗinta ɗaure da towel fari,
Walking slowly ta nufi Saman mirror chair ta zauna, tare da ɗaura gwiwar hannunta gaban madubin, ta zabga uban ta gumi,
Zuciyarta a cike take da tunanin mutumin nan, ko wanene shi? Taya akai ya samu damar shiga Cikin gidan dake a garƙame? Kodai bayan shigarsu ciki shima Ya samu damar shiga Cikin gidan? Shin me yaje yi acikin gidan, gaba ɗaya ta burkita ma kanta lissafi, kusan raba dare ta yi azaune tana tunani akan shi, bata iya gano komai ba, a ƙarshe ta miƙe taje gaban closet, ta buɗe ta curo kayan baccinta, Ta sanya su ajikinta,

Komawa saman gadon tayi, ta kwanta tare da janyo junaid ta rungume shi ajikinta, Cikin ƙanƙanin Lokaci bacci yae awon gaba da ita, Ko da gari ya waye Aneelerh bata sanar da kowa game da mutumin da suka gani acikin gidan Uzair ba, ita kanta tarasa gane dalilin dayasa ta kasa buɗe baki ta faɗa masu cewa wani ya shiga gidan, wata’ƙil ta hanyar hakan asamu wata evidence da zata bayyana ainihin meya faru da su tajo, kuma tun daga ranar bata ƙara gigin zuwa gidan ba, gani take kamar mutumin yana bibiyar rayuwarta, kodan kada ta tona ma shi asiri dole ya bibiyeta, shiyasa take tsoran fallasawa,

Back To prison🌷

A kwana a tashi ba wuya wurin Allah A yau angel ta cika shekara 1 da rabi A gidan KURKUKUN ƘADDARA, tun daga ranar da tayi ma batool tambayoyin nan bata ƙara tambayarta wani abu dangane da gidan kurkukun ba, dalili kuwa shine a duk lokacin da zata tambayi batool game da prison ɗin, Sai wani abu ya faru, wanda zai ɗauke masu hankali, Haka xalika a duk lokacin da ta yi yunƙurin sanar dasu wani abu game da addinin musulunci sai wani abu ya faru wanda zai dakatar da ita, ta ko’ina an toshe mata hanya,

Abu ɗaya ne take kokarin Koyar da su shine yawan ambaton sunan Allah acikin maganarsu, saboda kwata kwata basa furta sunan Allah, zuwan angel cikin rayuwarsu sun fara koyan wasu abubuwan wanda basu iya ba, salon maganarsu ya fara komawa irin na angel, ta zama tamkar malama acikinsu, Idan suka kammala Cin abinci, bata bari su koma bacci, motsa jiki take sanya su suna yi, Ko kuma suyi wasa a tsakaninsu, bakomai yasa suke jin shakkarta ba, face rashin tsoranta, da kuma wannan kalmar ta charman dudu da take yi masu barazana da ita, shiyasa a kullum take Cin galaba a kansu, duk wannan tsawon lokacin da angel ta ɗauka acikin gidan kurkukun ƙaddara, har yau babu jituwa tsakaninta da Haris da kuma mr sound hater wato DANISH, su biyun nan sunƙi yarda da ita, duk da sunfi kowa jin shakkarta, kuma in ta bada umarni dole kowa yabi hada su ɗin,

Zaune suke gaba ɗayansu sun kewaye Kayan abincin da aka kawo masu, giants suna a tsaye sun kasa sun tsare suna jiran su kammala Ci su kwashe Kayan su tafi,
Hanna ce ta ya ye jan kyallen da aka rufe saman trays ɗin, tray na farko fried meat ne, sai faffadan plate me ɗauke da Snacks a tray na ƙarshe kuma jug ɗin ruwa ne, sai kofuna Bayan su kuma sai kwandon dake ɗauke da kayan marmari da ƴar ƙaramar wuƙa, wadda zasu yi amfani da ita su yanka fruits ɗin,
Kowa yakai hannu ya dauki fried meat yana Ci,
Gaba ɗaya hankalin angel na akan wuƙar da aka sako Cikin kwandon kayan marmarinsu Cin naman take yi kamar zata shaƙe, so take ta sace wuƙar batare da sun gani ba, ɗagowa ta ɗanyi tana kallon Su Giants dake a tsaye, abinci ma baza a bar mutun yaci a tsanake ba sai an tsare mutun da ido, a cikin zuciyarta ta yi maganar don tasan suna kallon su,
Cikin ƙankanin lokaci ta cinye nata abincin, miƙa hannu ta yi tana nuna jerin Cups ɗin dake a jiye Javed yace”ruwa zaki sha”? Ta ɗaga mashi kai alamar eh,
Da kanshi ya zuba mata ruwan ya miƙa mata, ta kar6a tana yi mashi godiya, bayan ta shanye ruwan ta ajiye kofin, xama ta yi tana jira sauran su kammala cinye nasu, ko ta samu a zo kan fruit ɗin yadda zata ji daɗin sace wuƙar,
Sun ɗauki tsawon mintuna kafin suka kammala, kowa ya sha ruwa Kafin suka kai hannu suna ɗaukar kayan marmarin, ganin basu yi amfani da wuƙar ba, yasa tace ma batool” ba zasu yanka ba” batool tace mata”A jiyewa zamuyi sai anjima mu sha,” yatsina fuska angel ta yi ganin zata rasa damar da take da ita, ta ɗaukar wukar,
Dabara ce ta faɗo mata aranta, miƙewa ta yi tsaye tamkar zata bar wuri, ta ɗan ɗaga kafarta alamar za ta yi tafiya, gaba ɗaya ta yanke jiki ta faɗa saman kayan abincin, aruɗe su hannah suka kewaye ta suna jijjiga jikinta, hankalinsu a tashe suke ambaton sunanta,
Ganin sunyi mata rumfa ta yadda waɗannan Giants ɗin bazasu iya ganin meke wakana ba, a hanzarce ta yi wuf ta zura hannu ta ɗauke wuƙar tare da saƙe ta gefen qugunta, mutun ɗaya ne ya ga lokacin da ta ɗauki wuqar don ta fakaici idon su ne,
Miƙewa ta yi tana faman haki tace su bata ruwa tasha, jiri ne ya kwashe ta,
Da sauri Hibba ta cika mata kofi da ruwa ta miƙa mata, kaɗan tasha ruwan don bata jin ƙishir ruwa duk cikin plan ne,
Ganin sun kammala cin abincin yasa Giants matsowa suka tattara komai da suka yi amfani da shi, har fa sun Kama hanyar fita, danish ya ɗaga murya tare da cewa”She took a knife” tashin sense a razane angel ke kallon shi, kafin ta ɗaura idonta akan giants gani ta yi sunja burki sun tsaya cak, ɗaya daga cikin ne ya jiyo tare da nufar inda suke, tamkar zaki
Saboda tsabar ruɗi tunkafin ya ƙaraso angel ta curo wuƙar ta miƙa mashi yasa hannu ya kar6a, ƙiris ya rage ta fashe da kuka kamar jira take su fita, ta yi wani irin kukan kura ta daka tsalle ta faɗama danish, kokawa ta 6arke a tsakaninsu bugu ta shiga kai mashi, ta yakushe shi da akaifun hannunta, hada cizo ta gartsa mashi gefen wuyan shi,
Su batool suna ta ƙoƙarin rabata da jikin shi, amma ina duk wanda ya yi gigin ta6a ta wurgi take yi da shi, daƙyar haris ya cakumota, rai a 6ace ya yi wurgi da ita gaba ɗaya ta kife ƙasa kanta ya bugu sosai,
Zuƙunnawa su kayi agaban danish dake yashe ƙasa yana fitar da numfashi sama sama, farar fatar wuyan shi tayi jawur ga sahun haƙoran angen nan tamkar an zana su, duk ta 6ata ma shi wuya da yakushi red marks ta ko’ina,
Ran kowannan su sai da ya 6aci, musamman haris, rai a 6ace ya ke faɗin
“Dama ae ba sonshi ki ke yi ba, shiyasa ki ke son kashe mana shi, na rasa me danish ya yi maki, bafa shi bane ya yi silar zuwanki prison ɗin nan ba, ballanta na kice xaki ɗauki fansa a kanshi, ki bar ganin ana jin tsoronki, Allah daga yau idan kika kuskura kika ƙara ta6a fatar jikinshi saina karairayaki,

ɗagowa angel tayi idanuwanta sunyi jawur, batool da aziza suna a 6angarenta,

Cikin shessheƙar kuka tace”Idan ka ta shi ka kashe ni dan Allah, kada ka barni da rai na, meyasa zai ce na ɗauki wuƙa? Ina ruwan shi? Idan har bai shiga hurumina ba ni zan shiga nashi ne”? Ta yi tambayar a ƙule,
Batool tace”ban goyi bayan wani a cikin ku ba, Amma laifin danish nafi gani, meyasa za ka tona mata asiri don ta ɗauki wuƙa? Menene naka aciki? Juyawa ta yi kan angel’ke kuma angel baki kyauta ba, kalli yadda kika raunta shi, sai kace ba ɗan uwanki ba….”tunkafin takai ƙarshen maganar angel tace”danish bazai ta6a zama ɗan uwana ba, bana son shi bana ƙaunar ganin shi,”
Jinjina kai batool ta yi”its okey, daga yanzu zan shiga tsakanin ku, kada wanda ya ƙara shiga hurumin wani ina fata hakan ya yi,”
Javed yace”idan ma suka ƙara ni da kaina zan sanar ma tsohuwa a ɗauki mataki akansu,”
daga haka Haris da su mubeen suka kama hannun danish su kayi mashi jagora zuwa saman gadonshi, kwanciya saman gadon ya yi bawan Allah har wani jiri yake gani acikin idanuwanshi, shifa bakomai yasa ya tona ma angel a sirin ta ɗauki wuƙa ba, face sanin irin tsanar da tayi mashi, tsoron shi kada ace shi zata yanka da wuƙar wannan dalilin ne yasa shi tona mata asiri, ashe da rabon yaci na jaki a hannunta,
Miƙa mata hannu azeeza ta yi”ki tashi muke ki kwanta, ki huta” sai da ta ɗanyi jim kafin ta ruƙo hannun azeeza ta miƙe, saman gado ta koma ta zauna, hawaye sha6a sha6a akan fuskarta, danish ya tarwatsa mata plan ɗinta, taji takaici kamar ta sanya pillow ta taushe ma shi fuska haka take ji,
“Angel me zaki yi da wuƙa”? batool ce ta yi mata tambayar, ɗagowa angel ta yi tare da kallonta, tana a tsaye gefen gadonta,
Girgiza kai ta ɗanyi”babu komai, kawai inaso na mallake ta ne,” ɗan zaro ido batool ta yi”karfa ace wani kike harin kashewa a cikin mu” cikin zolaya ta yi mata maganar,
Cikin sanyin murya angel tace”a’a batool bazan iya kisan kai ba, ni kawai naso ace na mallaki wuƙar,”
“Da ace kina shiri da danish, da ya aro maki wuƙar shi,” da mamaki angel ta kalle ta tare da cewa”yana da wuƙa”? Jinjina mata kai ta yi eh, akwai wata ƙaramar wuƙa da yake amfani da ita wurin datse gashin kan shi, tsohuwa ce ta bashi wuƙar lokacin da ya ta6a tambayarta yana so ya rage tsayin sumar kanshi, shi ne ta ba shi wuƙar to bai mayar mata da ita ba, har yau tana nan a wurin shi,”
Dafe kai angel ta yi tare da satar kallon danish dake a kwance saman gadonshi, da alama bacci ya yi awon gaba dashi, yadai sha wahala,
“Ga samu ga rashi” ta ambaci hakan acikin azuciyarta, tasan koda me take yawo danish bazai ta6a ara mata wuƙar shi ba
Kallon batool ta yi”kinsan inda yake 6oye wuƙar” kallon sama batool ta ɗanyi da alama tunani take yi, can tace”a ƙarƙashin katifar gadonshi naga yana 6oye ta,
Angel tace”ki taimaka kice ya ara maki ita a matsayin ke zakiyi amfani da ita,
Ɗan zaro ido batool ta yi”ae bai yadda ya fiddo da wuƙar nan, kaifi ne da ita tana da haɗarin gaske, kona tambaye shi bazai bani ba, saboda yasan ba abun da zan yi da ita,”
Jinjina kai angel ta yi”shikenan na haƙura” daga haka bata kuma cewa komai ba, ta koma ta kwanta amma fa bawai ta haƙura bane, a can cikin zuciyarta tana shirya yadda zata sace wuƙar danish batare da sanin shi ba, da wannan tunanin ta yini da shi kuma ta kwana,

A daren yau ta kammala shirya yadda zata ɗauke wuƙar, kowa ya yi bacci saman gadonshi, duk sun lullu6e da bargunansu, angel ce kaɗai idonta biyu tana kwance idonta na fuskantar ceilling duk da duhu babu wadataccen haske saina fitilun ɗakinsu da suka kunna,

“Lokaci ya yi da zan tashi inje saman gadon danish in ɗauke wuƙar sa,” acikin zuciyarta ta yi maganar, tana ƙoƙarin miƙewa tajiyo takun tafiyar mutun acikin ɗakin nasu, da sauri ta koma ta kwanta cike da fargabar wanene a dai dai wannan lokacin ya faɗo masu ɗaki,
Ƙyalla ido ta yi daga kwancen da take tana satar kallon inda take jiyo sautin tafiyar, kaskon turaren wuta ta hango a hannun mutumin dake zarya cikin ɗakin nasu, wani irin baƙin hayaki ke tashi daga cikin kaskon, kamar ana turara turaren wuta,
Mutumin dake ruƙe da kaskon turaren wutar, jikin shi na a sanye cikin doguwar riga me hula launin ja, rigar har ja take ƙasa,
Kasa kunne angel tayi tana sauraron muryar mutumin dake magana, kamar muryar tsohuwa sai dai bata iya tantance da wani yare ake magana ba, wani irin gu6ataccem yare mara daɗin ji,
Nan fa hankalin angel ya ɗan tashi, xufa ta wanke fuskarta, duk ta sha jinin jikinta, tsoro take ji kada ace wani mugun ne yazo cutar da su,
Bata kai ƙarshen zancem zucin nata ba, ta hango mutun yana tafiya a bakin gadajen su Hannah, yana tafiya yana hura masu hayaƙin zuwa saman jikin su,
Da sauri angel taja bargo ta lullu6e fuskarta, acikin zuciyarta tana ambaton la’ila ha’illa anta subhanaka inni kuntu minazzalamin,” lokacin da mutumin yazo saitin gadonta, da sauri ta sanya tafin hannayenta duka biyun ta toshe bakinta da hancinta, duk don saboda kada hayaƙin ya samu damar shiga jikin ta,
Tana jiyo takun tafiyar mutumin yadda kasan takun tafiyar jaki,
Lokaci ɗaya tadaina jin takun tafiyar da kuma surutan da mutumin ya ke yi, da sauri ta ya ye bargonta, tabi ko’ina da kallo bata ga kowa ba, alamar mutumin ya tafi, sai dai hayaƙin daya turara masu har yanzu bai gushe ba,
Saukowa angel tayi daga saman gadonta, Zuciyarta cike da ruɗani, ko wanene mutun nan daya zo masu a tsakiyar dare, sanye da jajayen kaya? Turaren menene yake hayaƙa masu a cikin ɗakinsu da kuma saman jikin su? sam bata yadda da hayaƙin nan ba, tafi tunanin wani mugun abunne aka turara masu,
Tunawa ta yi da surori da kuma addu’o’in da malaminsu na makatantar islamiyya ya ta6a koya masu yace su yawaita karansu domin neman kariya daga sharrin mutun sharrin aljan da duk wani abun cutarwa,
“Zan tai taimaka masu, saboda basu da maiyi masu addu’a, a kullum in na kwanta ina bacci, daddyna yana yi mun addu’a, su kuwa basu da iyayen da zasu yi masu addu’a” acikin ranta tayi maganar
Kamar yadda mutumin nan yabi ko’ina na ɗakin yana turara Masu baƙin hayaƙin nan, itama haka ta soma bin kowace kusurwa ta ɗakin nasu tana karanta Ayatul kursiyyu, da amanar rasuli, Suratul mulk, Suratul kafiroon, Suratul ikhlas, falaqi da nasi, duk in ta karanta kowannan su Saita maimaita, daga bisani tabi kowani gado tana tottofa masu addu’oin saman bargunan da suka lullu6a da shi, daga kan gadon hanna ta faro xuwa gadon mubeen har zuwa gadajen su batool, tana zuwa kan gadon danish taja guntun tsoki zata wuce, sai kuma taji aranta kamar bata kyauta ba, don me zata yi ma kowannan su addu’a amma shi ta kasa yi ma shi saboda me? Lafin me ya yi mata? shiru ta yi tana tunani, menene ribar ta idan taƙi yi mashi addu’a,

Har ta kusa wuce gadon shi taja da baya ta koma tare da shiga daga gefen gadon, ranƙwafawa ta ɗanyi saitin fuskarshi ta soma karanto addu’o’in bayan ta kamalla ta tottofa mashi saman fuskarshi, kamar daga sama taji an damƙi hannunta, a razane ta kalle shi ashe ya farka, muryar shi a disashe yace”tsanar takai har ki zo kan gadona kina tofa mun miyau asaman fuskata”? Zuba ma shi ido angel ta yi batare da tace Furta komai ba, tama rasa bakin magana, yadda ya yi mata maganar ita kanta ta yi mamaki sai kace ba wannan mai jin shakkartata ba, bakomai yake jima tsoro ba, face wannan kalmar da take faɗi na cewa zata tofa ma mutun charman dudu Cikin shi ya kumbura, tuna wannan yasa shi ƙara tsorata, shi kanshi baisan yana da ƙwarin gwiwar yi mata magana irin haka ba,
tsawa ya ɗanyi mata tare da cewa”Ba ki ji ina magana ba”? Still ta yi ma shi shiru saboda bata jin zata iya faɗa mashi cewa addu’a take yi mashi, don ma kada yaji kamar tana ƙaunarsa ne,
Ganin ta yi mashi shiru ya ƙara har zuƙa, A tsananin tsorace Ya damƙo ƙasan rigarta da ƙarfi da niyar ya goge abunda ta tofa ma shi asaman fuskar shi, Cikin rashin sa’a ya janyota gaba ɗaya ta faɗa saman jikin shi………………🥱

(Nasha wahala wurin haɗa page ɗin nan, Jiki duk ba lafiya, To jama’a Mu haɗu Next page on monday in Allah yakaimu da rai da lafiya) Game neman ƙarin bayani 08103884440)
Boss Bature ce✍️

Leave a Reply

Back to top button