Hausa NovelsHausa NovelsTabarmar Kashi Book 2

Tabarmar Kashi Book 2 Page 19

Sponsored Links

Book 02 page 19

Da gyar ta garasa gyaran dakin, zuwa lokacin kanta ya fara ciwo sosai saboda damuwoyin da take ta tunawa ta kowanne sashe wanne rayuwa fadeela zata fuskanta daga gurin hajiya garama lokacin da zata rayu babu wani a gefanta da zai zame mata garkuwa?, meye shirin hajiya garama ne? me dame ta sarqa a rayuwar wadan nan bayin Allah wanda basu da babanci da marayu?, tsananin tunanin da ya tsananta mata ciwon kenan. A nan dakin fadeela ta duqunqune ta kwanta tana fatan bayan wasu mintuna kan zai sauka. Bata wuce awa guda kwata kwata da dawowar ba taji muryarsu da alama sun dawo, ba jimawa kuwa sai gata ta iso tana kiran sunanta.
Daurewa tayi ta bude idanunta ta zauna sosai, garasowa tavi ta kama hannunta ta riqe

“Anty N gidan uncle sajjad zamuje ni da sister nadeeya,tace na gaya miki, tana cikin mota tana jirana abby ne yace kada mu batawa driver lokaci” murmushin garfin hali ta saki, tana tunawa yau kwanaki shida kenan amma sau daya tak sukayi waya da afifa, abinda bata taba kawowa ba akwai randa zasu dauki kwanaki basuyi waya da bestie dinta ba,saidai bawai hakan yana nufin ta qullaceta ko taji haushinta ba, ko kadan, uzuri kawai ta bata.

“Ki cewa bestie na ina godiya da kulawa,a gaidarmin da uncle sajjad” maimakon taga yarinyar ta mige ta tafi sai ta kama hannunta sosai tana kallonta

“Anty N. kaman baki da lafiya” kai ta girgiza

“Gajiya nayi sai kaina dake dan ciwo kadan” säahar din ta fada tana kallon tsakiyar idanun yarinya zuciyarta na karyewa,tare da mamakin meye tayi da za’a cutar da ita ne? ita ba kudi ko dukiya ba kaman dai ita,ita ba wata babba ba bare ace ta aikata wani abu,bata mallaki komai ba sai rayuwarta da numfashinta da soyayyar makusantanta, a ciki me ake nema?.

“Bari na gayawa sister nadeeya‚mu zauna dake” yarinyar ta fada a karye. Kai ta jinjina mata

“A’ah, karki gayawa kowa,inajin sauqi,kafin ku dawo na warke in sha Allah” saita sakar mata murmushi don bata qwarin gwiwa. Duk da haka yarinyar tana tafe tana waiwayenta har ta fice a dakin, abinda ya sake karya zuciyar säahar din kenan, ta koma ta kwanta tana lumshe idanunta zuciyarta a cunkushe.

Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi yana duban hajiya qarama dake sharar hawaye hadi da fyace majina bayan kukan data sharba, fuskarta na nuna zallar alhini da bacin rai. Har cikin ransa baiji dadin vadda take kuka tana gaya masa sãahar ta zageta ba tare da gaya mata bat iva kula da fadeela ba, daga yau kuma kada ta sake kusanto inda take, magungunanta da komai nata ta haramta mata tabawa saboda wai bata yarda da ita ba.
Iska ya furzar me dumi daga bakinsa

“I will talk to her,stop crying mommy” ya fada calmly. Kai ta girgiza

“Kada kaie ka tareta da zancan toufeeq taga kamar na hadaku rigima kuna zamanku lafiya ” baice mata komai ba,ya dai fara takawa yana barin wajen.

Bayason kuka gaba daya,bare kukanma na babba,babban ma macen data rainesu har suka kawo haka. Amma kuma ta wani gefen zuciyarsa ta kasa nutsuwa da statement na abinda ya farun,haka kawai kuma yakejin zuciyar tasa ta gaza karba. Ba kasafai yake yanke hukunci kai tsaye ba ba tare daya ji ta bakin mutum ba,wannan ya sanya ya wuce sassansa kai tsaye.

A parlor ya samu Joseph yana sake tsaftace falon,duk da bawai yayi datti bane, a’ah wannan tsarinsa ne, ko yana nan ko baya nan,sharar safe data yammaci irin haka. Rusunawa yayi ya gaidashi, ya amsa sama sama ya wuce yana jiyo motsin jacob daga kitchen,shi kuma yaci gaba da aikinsa yana maida earpiece din kunnensa.

A nutse yake takawa cikin hallway din har ya isa bakin gofar dakin, hannu vasa ya murza handle din sannan ya tura qofar baya ya shiga a nutse. A kintse dakin yake,komai fes fes cikin wadatacciyar tsafta da kulawa,ba abinda ke tashi a dakin sai wani nau’in qamshi me sanyi d kwantar da zuciya. Tsaiwa yayi yana qarewa dakin kallo karon farko tunda aka shirya dakin cikin gidan, komai cikin favourite colours dinsa yake ya sauke hannunsa yana takawa zuwa ciki, duk kuwa da ya fuskanci ba kowa cikin dakin. Gefan gadonta ya qarasa ya zauna,haka kawai yaji weather din dakin tayi masa qwarai, ta kuma saukar masa da kasala,ya cire hannuwansa daga aljihun wandonsa da zummar dorawa saman gadon,sai yaji ya dora saman wani abu ne taushi da santsi. Waiwayawa yayi yana duban gurin. Panties dinta ne da braziers dukkansu farare gal gal kamar hannu bai taba tabasu ba. Janye hannun nasa yayi da sauri tsigar jikinsa tana zubawa,sai ya kauda kansa,idanun nasa suka sauka saman bedside drawer dinta. Hannunsa ya miqa ya dauki litattafan da suke kai na farko al-qur’ani ne ya maidashi ya ajjiye, na biyun littafin azkar dinta ne,ya buda ya karanta wasu daga cikin addu’o’in da suke ciki na wasu mintuna sannan suma ya mayar ya ajiyeshi,na ukun kuma MY DIARY shine abinda ke rubuce a fuskar littafin da manyan harufa da aka yiwa aloo da ruman azurta. Har ye maida ya ajiye ya mige sa ya koma ye sake dauka, ya bude shafin farko. Rubutu ne ekin tsari da daukan hankali kamar haka

-the worst feeling in the worid is knowing you’ve been used and lied to by someone you trusted, and the saddest thing about betrayal is that it never comes from your enemies_

Ya maimaita kalaman sun kusa sau biyar yana jin wani abu yena taba zuciyarsa yana jin kamar saboda shi akayi duke weden nan maganganun, akwai wani abu clin reyuwarta bayan wanda ya bincika ya saniyes… ya san da hakan duk da a wancan lokacin yace bashi da bugater ya sani din, amma a yanzun sai yaji yana da she’awar haken. Maida littafin yayi ya rufe, a maimakon ye maidashi wajensa sai ya fice dashi daga dakin gaba daya

Guri yayi masa a davinsa sannan ya juya ya fito, tunda bai ganta a sassansa ba ya tabbatar tana sahensu nadeeya. Zai iya cewa a kwanakin shida su biyu rak yaga gilmawarta a sashen kwata kwata,duk da cewa shima din ba wai zama yake a gidan ba, yanata qoqarin ganin ya fara hada kan ayyukan da zaiyi a company din dr, so yake yana cika wata guda yabar qasar dawowarsa kuma sai baaba ta gani, abu daya zai masa cikas,ya tabbatar Dr shine mutum na farko da zai fara masa maganar yana da iyali a yanzu, amma yasan yadda zai tafi da komai,yanason ya danyi nesa kadan ya samu zafin da kansa ya dauka ya sassauta.

Sanda taji anyi knocking migewa tavi ta zauna sosai duk da yadda kanta yake ciwo kamar zai cire ta dauka baaba ramatu ce, da muryarta da tayi sanyi qwarai tace

“Shigo” ya murda gofar ya turata ya sanya qafarsa. Ta lumsassun idanunta da kanta data jinginar a fuskar gadon taga shigowarsa, bata tsamamci ganinsa ba,ta miga hannunta a da hanzari ta jawo dankwalinta ta budeshi tana rufe gashinta. Kansa ya dauke kaman bai gani ba,ya qarasa shigowa ya jawo stool zuwa gaban gadon ya zauna sosai yana dubanta. Kwarjini taji yayi mata kamar yadda yake mata wasu lokuta,kanta ta juyar wani bangaren gasan rabta tana mamakin abinda ya shigo dashi. A nutse ya kafeta da kallonsa, mayun idanun nan nasa suka dinga ratsa jikinta suna bata alamun akwai kakkaifan idanu a kanta,batasan me yasa ba,duk sanda zai kalleta sama da second biyu sai taji kallon har cikin jininta,abinda kaf rayuwarta bata taba ji ba akan wani. Yadda baice komai ba haka itama,bataga amfanin zuwan da yayi ya sakata a gaba yake mata kallon daukan alhaki ba,wannan ya sanya ta yaye duvet din ta fara yunqurin saukowa daga saman gadon

“Koma ki zauna” ya fada still idanun suna kanta. Kamar ba zata koma din ba kamar yadda yace,sai kuma ta tuna

da gargadinsa, batason wani abu da zai kawo haduwar jikinsu waje daya ya sake faruwa,don haka ta dakata daga gogarin saukar da takeyi fuskarta na kallon gabanta,baya iya hangen fuskarta da kyau,sai gefen fuskarta dake dauke da kwantaccen gashi ta gefen kunnuwanta. Kansa yadan gyada kadan ya fuskanci gwanar taurin kai ce

“Kina da masaniyar matsayin hajiya a gurina?” Ya tambayeta adan kausashe, tun kafin ya gara komai a kai ta fahimci inda maganar tasa ta sanya gaba

“Ko na sani ko ban sani ba ba wanna bane ya kawo ni gidan nan ba,nazo ne don kula da fadeela, kuma na dauki alqawarin bata dukkan kariya da dukka iyawata,bazan taba barin wani abu ya cutar da ita ba alhali ina da ikon dakatar da shi, saboda haka na dakatar da ita daga bata magani don aiki nane”. Fuskarsa ta dan sauya yana mamakin qarfin halinta

“Kika dakatar da wa?‚are you in your sense?” Zuwa lokacin kasancewarsa a gurin kawai matsi ne da takura a wajenta don haka ciwon kan nata zuwa lokacin kamar an ninka mata shi, har ya fara sauka zuwa idanunta kamar yadda yake mata a yawancin lokuta idan yazo da tsanani. Waiwayawa tayi ta dubeshi kai tsaye

“Yes, na fada na dakatar da ita, bama ita kadai ba kowa a gidan nan, ciki harda kai mahaifinta”. Karon farko kuma lokaci na farko da garfin halinta tare da qarfin gwiwarta ya burgeshi yaso kuma bashi dariya har ya murmusa da wani kalar miskilancin murmushi wanda gefen bakinsa ne kawai ya motsa, saidai hakan ba qaramin qara masa kyau yayi ba. Gefe daya kuma yana karantar yanayinta da ya canza, tabbas akwai abinda yake damunta,yasan kuma ba zata taba fada ba,sannan muddin ya barta ta kwana a haka kota galabaita yayi imani daya daga cikin haqgoqinta kenan da ya gaza saukewa ne.

Ci gaba tayi da sauka daga gadon, tana ganin ta gama bashi amsa,no need ta tsaya wani dogon magana,gefe daya zuciyarta na sake cika da mamakin hajiya qarama,tare da jin cewa ta shiryawa tunkararta da dukka wani nau’in abu da zatazo dashi.

Sai daga gama sauka kaf yana kallonta ba tare da ya sake cewa komai ba yana sake nazartar garfin hali da kafiva irin nata. Sunkuya tayi da zummar gyara takalminta ta saka,sarawar da kanta yayi ya sanyata tallafeshi tana furta

“Wash” ba tare data tuna ma yana wajen ba. Sai a sannan ya mige a nutse, ya tako a hankali zuwa inda take,qamshinsa ya tabbatar mata da garin kusancinsa da inda take
[19/09, 5:33 pm] +234 903 576 5837: *H U G U M A*

Leave a Reply

Back to top button