Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 66

Sponsored Links

66
Dummmmm kunnuwan Safnah sukai mata jinsu na daukewa ahankali tana Jin maganar
Rabi me aikinta Sama sama dake tambayanta ko lafiyanta kalau.
Bata iya Jin me take fada daidai Saida garamin jiri me juyar da Kai ya dibeta Rabin tayi saurin tareta tana kallanta cikin tsoro da mamakin meya sameta a take.
Idanuwanta dake Neman hada mata hadari hadari ta sake budewa da kyau akan Bena wadda ko mutuwa tayi aka binneta ta kwana kabari aka fitar zata Gane itace wlh,
Benazir ‘yar uwarta jininta ce ta Gani takuma tabbatarda ita din ce idanuwanta har Wani rawa rawa sukeyi gurin kallanta harta shige
Take Wani jiri me qarfin gaske ya kuma dibanta gafafunta na kakkarwa ta kasa dagawa da Kanta kaman makauniya Rabi ta kama hannunta zuwa bangarenta.
Suna shiga Palo ta tsaya sbd Bata ganin komai sai duhu duhu ganinta Yana rawa cikin masifa da tashin hankalin da Bata taba saninsa ba a rayuwanta..
Harshenta karyewa yayi tana son tambayar
Rabi wacece wadda suka Gani din Amma batada hali sbd karshenta dake sake karyewa hannuwanta duka na jujjiga ta Ciro wayarta
Bata Gani sosai daqyar ta iya Gane numbern
Momynta ta saka kira sai alokacin ta zamu qarfin halin fizgo magana bakinta da cewa
“‘Waye,waye…wadda.muka.gani”
Ko gama rufe baki bataiba da kalaman data kasa hadawan
Rabi cikin tashin hankalin da tsoron meyake

faruwa ta katseta da Bata amsan cewa
“Aunty Bena ce,dayan Matan Sir DD,maman
Amnah ‘yar marigayi Sir Bial.”
Sankarew Safnah tayi a gurin komai nata na tsayawa cak harda numfashinta da gyar ta iya kemo Kalmar “bana Gane komai me kika fada?”
Cikin tsoro da gara shiga firgici Rabi ta Bude baki ta sake maimaita mata bayanin tana gama maimaitawa
Duhu ne ya rufe idanuwan Safnah gabaki
Daya sai ganinta Rabi tayi ta Yanke jiki ta Fadi a gurin Sume babu inda yake motsi a jikinta
Kuma daidai lokacin Momynta ta daga Kiran
Safnah din Daya shigo wayarta tafara Kiran sunanta sbd Jin ba magana.

hun Kuka Rabi ta sake jikinta na daukan rawan toro itama tafara Kiran sunan Safnah din cikin fargaba da rashin sanin meyake faruwa.
Jin Rabi na Kiran sunan Safnah cikin Kuka da tashin hankali ya saka momyn kashe wayar cikin faduwar gaba da shiga nata firgicin.
Kiran wayar tayi tareda micewa daga zaunen datake palonta ta shige bedroom dinta tareda rufe kofar
Rabi na daga wayar cikin masifa tace
“Ke banasan hauka da jahilci ki nutsu ki fadan meyake faruwa ne?”
Hadiye toro Rabi tayi cikin Dan daidaita kanta tace

“Aunty Safnah ne ta Suma Kuma Bata motsi
Sam harda numfashi ma batayi.”
Wani mummunan yawun tashin hankali momy ta sauke tareda Jin itama nata jikin na Neman daukan rawa idan Safnah ta mutu yanzu ai ita Kuma ta shiga uku da sauran bugatoci da burikan da Bata cimmawaba.
Migewa tayi daga zaman datai bakin gado tace
“Akwai Wanda yasan halinda take ciki ne?”
“Ah ah” Rabi ta amsa tana waiwayawa duk da palon a rufe yake.
“Ki Jata ki Kai daki kada DD ya dawo ya sameku a Hakan karki bari kowa ya sani ganinan zuwa yanzun Nan.”
Kashe wayar tayi tareda daukan key din motarta da mayafi ko handbag Bata tsaya dauka ba ta fito hajiya Bata sani ba ta fice daga gidan tana Hana kanta daukan duk Wani negative tinani.
Cikin mintina qalilan ta Isa kaantes sbd gudun data zabgo Amma tana shigowa anguwar ta rage gudun kwata kwata a natse ta shigo da motarta har ta iso gate aka Bude mata ta shige tinda ansan mahaifiyar Amaryar Sir DD ce
A natse tayi parking harabar gidan ta farko sbd duk bako baya wucewa da motarsa gate na biyu saidai ya ajeta a na farko masu gidan ne kawai ke wucewa gate na biyu suyi parking motocinsu acan.

Bayan tayi parking hakanan ta tilastawa Kanta nutsuwa da kamun kan dole tana Amsa gaisuwan securities harta shige gate na biyu ta wuce zuwa bangaren dazai kaita bangaren
Safnah.
Tana Isa ko knocking bataiba ta Bude kofar ta shigo Kai tsaye dakin Safnah ta wuce ta taddata har lokacin Bata farfadoba da alama idan baa taimaka mata da gaggawa ba zata iya macewa ma Kila a Hakan.
Ruwa ta fada toilet da kanta ta debo tana fitowa ta zuba mata su tana Kiran sunanta cikin mamakin Abinda yake faruwa da zai sakata shiga wannan halin.
Cikin mummunan hali ta sauke ajiyan zuciya a fizge tareda Bude idanuwanta idanuwanta da sukai jajir take sbd mummunan tashin hankali da masifar datafi mata rayuwar gidan Ababa.

Kasa motsawa tayi tana Neman sake somewa a Karo na biyu momy ta saka hannu biyu tayi mata wata irin jujigawa tana cewa
“Ke kimun bayanin meya faru ne kina Neman sakamun hawan jini da wasi wasi da firgici”
Rabi momyn ta kalla tace ta fice daga dakin ta dawo da kallanta kan Safnah dake magana ita Daya kaman ta zauce a rikice tana sake tsinkewa da lamarin ta sake jijigata ta kira sunan cikin tsawa da babban tsoro tace
“WIh zan taflyata na barki koma wace masifar kika debo ta tsaya kanki.”
Kuka Safnah ke nema ta fasa ko Abinda ya danne kirjinta zai fada Amma ta rasa Dan haka ta dago idanuwanta dasukai jajir ta Kalli momy bakinta na rawar fita hayyaci tace “Momy Bena matar D itace Benazir yar uwata, uwa Daya ta haifemu,
Uba Daya ya haifemu,Nono Daya muka
Sha…itace matar Dawood, itace wadda aka fara daura masa aure da ita, itace uwar Amnah yar Bilal dasuka Haifa ba aure.……Somewa ta sake Yi a Karo na biyu momy da tayi mutuwar zaune itama kusan somewan take Neman Yi Saida Rabi tashigo Jin shiru ta debo ruwa ta zuba musu hankalinta na sake tashi tareda shiga tsoron lamarin Dayake faruwan.
Suna farfadowa sai alokacin Safnah ta Dora hannu Akai zata fasa ihu da kukan balai da masifar Datake ji cikin zuciyarta
Momy da itama duka jikinta rawa yakeyi ta rufe mata baki da hannuwanta biyu tana jijigata cikin bushewan zuciya da tattaro nutsuwa tace
“Ki dawo hankalinki ki nutsu ki tabbatarda benazir ‘yar uwarki ce kika Gani ba gizo ba.

Wallahi tallahi Benazir din Dana sani ce,
Wallahi tallahi itace,
Rayuwata tazo karshe,
Komai nawa yazo karshe,
Identity Dina zai bayyana,.
Daddy zai San ni wacece, zai tsaneni, haiia zata tsaneni, ummen D da shi Kansa zasu tsaneni idan sukasan ni wacece dakuma yanda na wulaqanta mahaifiyata na baro gida,ban taba walwayansu ba,
Yaya aurena da D zai qare?
Qanqame hannuwan momyn tayi jikinta na rawa da fizga cikin mummunan tashin hankali tace
“Momy Dan Allah kiyi Wani Abu akan
Hakan banason na rasa Sunana da matsayina a matsayin Safnah basheer bulama,
Bazan iya barwa Bena D ba wlh, bazan iya rayuwa a yanzu ba a Safnah bulama Dina ba,
Bazan iya barin D ba, Karki bari asan Koni wacece sbd zan rasa
komai Dan Allah momy kiyi Wani Dan Allah.
Yanda jikinta ke rawa tana maganganun cikin
ficewan ‘hayyaci da mummunar tashin hankali
vasaka momy sake jijigata da qarfin gaske
tana cewa
“Ke kiyi shiru babu Abinda zai faru a abubuwan da kika fada,
Babu wata Safnah Ababa a dunia yanzu se
Safnah bulama,
Babu wata macen da Dawood kaante zai
zauna da ita sai Safnah bulama,
Waye benazir?
Matar data gama budewa Dan uwansa qafa ya
gama Abinda yake da ita itace zata warware
mana aikin shekara da shekaru??
Wallahi ko Wanda ya tsaya mata bazai
warware mana aikinmu ba, Kina maganar asirinki ya tonu Zaki rasa komai kin manta tonuwar asirinki shine tonuwar
nawa?
Wallahi Bena bazata lalata mana Aiki ba Koda
Hakan na nufin kawar da ita ne.
A razane Safnah ta dago tana sake jiqewa cikin mummunan zufan dake garawa jikinta
rawa.
A zafafe momy tace
“Kinada Wani tsarin ne bayan na kawar da Bena sbd itace mukullin buduwan sirrinmu,
Idan ta kauce babu Wanda zai haramta aurenki da D,hakama babu Wanda zai ganki
anan bare yasan asalin ke wacece.

Girgiza Kai Safnah tayi tana kallan momyn har lokacin cikin tashin hankali tace
“Momy kawar da Bena a yanzu ba shine
Abinda zamuyi na farko ba,
Bena D Yana aurenta tsawon shekarun Nan batareda ta tare ba hakama tin zuwana na samu tabbacin babu Abinda ya taba sniga tsakaninta dashi na aure Kinga kuwa inada
Chance,
Munada wata Daman.
Cikin tinani momy ta Kalli Safnah tana migewa tsaye tana Dan zagayawa kadan kafin ta tsava gaban Safnah din suna kallan juna tace
“Duk tsanani duk wuya kada ki bari ta taba ganinki,
A yanzu babban abin bugata da burinmu shine D yafara kusantarki kafin Bena din Dan idan bamu samu nasarar kauda ita ba aka Samu akasin ta ganki to tabbas sharia zatayi amfani da wadda ya kusanta a cikinku itace matarsa(inshallah),
Amma duk tsanani duk wuya Muna buqatan bacewan Bena idan har munason cigaba da rayuwa baa gidan yari ba.
Shiru Safnah tayi sbd itama duk tsanani duk wuya bazata yarda tayi rayuwar ukuba ba bayan wadda tayi a baya idan kawar da
Bena shine key din tabbatuwarta zama matar
Dawood kaante da zamanta Safnah bulama to tabbas ta shirya Hakan Koda zasu rasa komai sai ta tabbatarda ita D zai fara sani a mace.
Da wannan kudirin suka samu dawowa hayyacinsu Badan hankalinsu ya kwanta ba
Dan Kuma yanzu basuda kwanciyan hankali matiqar ba ganin sukai sun cimma sabon burin nasu na zamanta wadda ita zata amshe sunan matarsa ta gaskia ko a gaban shiria sbd idan ta rasa identity dinta na Safnah bulama zata amsa sabon identity na matar Dawood kaante.
Dagyar suka Dan seta kansu sbd kowannensu dai vana cikin rashin nutsuwan zuciya hakanan suka fito Palo momy ta Kalli Safnah
Safnah din tayi gaba taje ta sakawa kofar shigowa palon key ta dago tareda cakumo
Rabi wadda idanuwanta suka fito take jikinta
Yana daukan kakkarwa.
Cikin Riga momy ta saka hannu ta zaro wata garamar pistol data saka Rabi fara Sakin fitsari jikinta na sake daukan rawa safnah ta sake shago rigarta momy Kuma ta Dora pistol din a saitin kirjinta ta danna mata ita da karfi har
Saida Rabin ta kusa somewa tace
“‘Wallahi tallahi duk ranar da tsautsayi ya aikeki kika fada ko a toilet ne ke Daya kikai maganar
Abinda ya faru anan saina fasa kanki da kiriinki da wannan Abar.”Kasa ko gyada Kai Rabi tayi sai zubewa datai qasa tana kama kafar Momyn tana cewa wlh zata mutu da wannan maganar babu me ji daga gareta.
Sakinta Safnah tayi sbd duk jikinta har lokacin rawa yake Bata cikakken hayyacinta
Sam zuciyarta ta kasa nutsuwa Jin takeyi kaman kanta zai kama da wuta ta haukacr ga
Wani radadi da zuciyarta keyi na Jin idan Bata cika burinta ba na mallaka D zata iya mutuwa ko rasa hankalinta.
##MAMUH#
#DBENA
#SAFNAH
#ABABA
#KAANTES
Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button