Acikin Gidana Hausa NovelHausa Novels

Acikin Gidana 19

Sponsored Links

⚡️A CIKIN GIDANA ⚡️
(SEX,ROMANCE,RUNS)

📝FATIMA ZAKARIYYA

EPISODE1️⃣9️⃣

*****
Toh Masha Allah ,Mungodewa Allah daya nuna mana wannan Ranar ,yaranmu sun Amince sun yarda da junansu ,Allah ya basu zaman lfy ,Rana Irin ta Yau za’a daura Aure ,Allah ya sanya Alkhairi suka fada kowa ya tashi ya tafi ,Maman safiyya ce ta kirata tanata mata fada ,toh safiyya Aure ba abune na wasa bh ,Kiji tsoron Allah ,kiyiwa mijinki biyayya,yi nayi Bari na Bari ,marriage is nothing without biyayya da ladabi da bin miji sauda kafa ,ki yawaita karatun Alqurani ,Ko Baki karanta bh ki dinga sakawa a gidanki ,ki yawaita sadaka ,da sauka ,idan zaki iya da kanki kiyi ,idan baza ki iya bh ki bayar ayi miki ,dangin mijinki Karki zake musu ,Amman ki zamanto me son zaman lfy ,duk Wanda yazo ki karbesa Hannu biyu ,Karki Bari kowa ya rainaki kar kuma ki Raina kowa ,Duk Wanda yake sonki ki soshi Wanda baya sonki babu ruwanki dashi ,Kiso mijinki ki nuna masa soyayya da kwana sosai,babu gurun wace zai samu soyayya sama da matarsa ,ki jashi a jiki duk abun dayake so Kafin ya nema kiyi masa ,kin ganni nan safiyya wataran har tambayar mijina nakeyi ya rubuta abubuwan dayake so ayi masa throughout tun daga safe har dare ,dukdan a zauna lfy ,ki dinga bashi girmansa ,duk abun daya kawo komai kankantarsa ki gode masa,kar ki dinga hangen auren wasu ki dinga hangen naki ,mijinki indai zai Baki Abu ki saka hannu biyu ki karba ,ki tsugunna mh ,durkusawa Wada ai ba gajiyawa bane ,gaisawu ta safe daban ta rana daban na dare daban ,idan kinason mallakar mijinki cikin ruwan sanyi duk yanda yabi dake kibi indai bawai ya sabawa hanyar Allah bh ,maza sunason suga suna bada orders Ana bi ,ai ba namiji kadai ba Ke a mace mh kinason kiga komai kikace ance toh ,ba’ayi miki musu bh ba’aja dake bh ,ki nuna masa Ke tashi ce sai yanda yayi dake ,ta hakane zaki dinga dabarunki kema sai kiga duk abun da kikeso cikin ruwan sanyi anyi miki shi ,Allah ya nuna mana sati daya ,naga babanki baiyi wasa bh sati daya suka saka ,Anjima da dare maza za suzo su kawo lefe ,ga wani Infection Kit can na siyo miki Masu kyau ne sosia komai sanyin jikinki indai kinyi Amfani dasu da yardar Allah komai zai fita ajikinki ,zaki jiki daidai babu wata matasala,Wancan detox dinma idan kina yawan shansa Ko kinyi fitsari gurin da Masu infection sukayi Ke bazaki dauka bh ,yanada kyau da tasiri,haka Wancan MAGIC WOOD din ,duk Dattin jikinki da sanyin daya dade a jikinki sai korasu ya gyara miki jiki ,haka idan kina zubar da ruwan infection duka zai gyara miki ya tsayar dasu ,yana maganin sanyin mara sanyi kashi da jiki sosai ,dafashi zakiyi da cloves idan ya kare mh ki kuma reboiling ,Wannan SUCKING REMOVER din zaiyi cleaning jikinki ,ya gyara miki jiki ,jikinki zai zama brand new babu cuta babu infection babu komai ,ga VAGINAL WASH,duk wani odour na gabanki saiya daina da izinin Allah ,kyakyayin gaba kuwa Saidai kiji anayi ,yana gyara gaban mace sosai da sosai ,zaki iyayin sit bath dashi ,dan ya wanko miki dattin marar ki zakiji gabanki fresh din da Baki taba ji bh ,ki tsaya kiyi treatment dinnan sosai ,shi kadai indai kinyi banida matsala dake nasan jikinki ya gyaru ,kar ki dinga saka pant har sai kin gama treatment dinnan tsaf ,Ga wannan garirikan mah a gurinta na karbi miki tace a Baki ki dinga sha yabi jikinki kafin a kaiki,wanan da madara zakisha ,wannan da zuma wannan a tea ,Sannan tace na fada miki ki yawaita Shan tea da cinnomon kafin a kaiki ,me gyaran jiki kuma Zata fara zuwa Yau da daddare za’ayi miki me kyau ,naga skin dinki mh yayi kyau bakida problem na skin Ke dama yar gayu dake kullum skin dinki kaman na Amarya me kike using ?, Aunty SKINITUP Skincare products nake using ,shiyasa mh gyaran jikin nace na 1week ya isheni,Amman ni Banda Matsala skin Dina ,itama ta bani wani gift na Scrub na Amare kaman na gyaran jikin ne shima tace nayi na 1week ,Masha Allah wannan Ai itace dai na siya miki maganin sanyin A gurinta ,mene number dinta karonto min naji Ko itace,07011607479 ,tabbas shine number dinta to maza ki fara gyara ,Kayan matan tah kuma tace emergency ne sai Ana gobe zaa kaiki za’a kawo miki ,yawwah ga wannan mah itatuwan ruwan tace ki jika ki dinga sha wani sirri ne na Amare ,to tace Nagode Sosai Aunty

Safiyya dai tayi laushi sosai da sosai ,ta tuba ta koma ga Allah kullum istigfari takeyi ,tayi istibra’i ,Sannan tanata Sadaka Akan Allah ya yafe mata ta tuba ta daina kuma bazata sake bh ,mijin kuwa da babanta ya zaba mata ko musu batayi bh expecially mh data gansa very handsome,batada burin daya wuce ta ganta gidan aurenta tanawa mijinta biyayya ta samu dacewa ,itama har islammiya ta koma ,a yanzu haka safiyya batada wasu Kawaye ,kawayenta daga yan uwanta sai yaran gidansu ,An tashi daga islamiyya ne taketa rabawa yan ajinsu card din bikinta ,wata hafsa ce take tsokanarta Amarya bakya laifi,kowa ya ganki yaga Amarya kinga Kyan da kike zubawa kuwa ,Masha Allah ,dariya tayi tace wlh ai daga Yau mh na daina fita,yanzu mh asibiti zanje idan na dawo shknn ,Hafsa ce tace Thom shknn bikin naga guda biyu ne ko ,Eh wlh hafsa guda biyune kawai banson hayaniya yanzu ,na farko sauka za’ayi na biyu kuma dinner ne aka hade duka da kamun shknn ,toh Allah ya sanya Alkhairi hafsa tace ,safiyya bata tsaya Ko Ina bh sai asibiti ,dama tayi Appointment da wani Babban doctor dayayi mata stiches 2 weeks back ,ita surgery mh taso a mata but ance is late kuma sai taje lagos,so kawai stiches din taje aka mata ,an mata dinki cike da waje ,Ko karamin dan yatsanta bazai iya shiga bh ,dubata yayi ,malama safiyya ai dinkin ki Yayi kyau sosia ,bakida Matsala kin warke sosai ,da murnarta kuwa ta masa godiya ta wuce ta koma gida *****A kwana a tashi safiyya ta gama treatment na sanyi ,ta Dora da garirika gyaran jiki da aka bata ,ta warke stiches yayi kyau Sosai ,a Bridal class na Fatima zakariyya data shiga ne taga Ashe fitar da jini First night ba kowane yakeyi bh and it’s nrml ,fitar da jini bashine yake nuna Ure virgin bh,taji dadin class din sosai ta kuma koya abubuwa ta shiryawa auren nata ,gobe za’a fara biki ,Jabir ne ya kirata a waya ,” matata ta kaina ,how you doing?,Kin hanani zuwa in ganki Ko ?,” murmushi tayi A’a ka kwantar da hankalinka ai na kusa zama taka All ,har sai ka gaji da ganina mah ,”,” No Safiyya bazan gaji da ganinki bh “, haka dai suka gama waya sukayi sallama

Yusrah saura kwana biyu a fara biki ,Tasha gyara ciki da waje ,Tana saloon ana mata kitso ,watace ta kalleta sister Ke Amarya ce ?eh tace ,kinfison kitso ne ,eh ,I just want to look simple ,kitson kam ya miki kyau kema kinyi kyau Ana ganinki anga Amarya ,murmushi tayi dan dama yusrah ba gwanar surutu bace ,bayan an gama ta koma gida cike da mutane anzo biki daga garuruwa,kowa dai da kalar fadan dayake mata ,Aunty Saratu ce tace kin gama Shan duka magungunan sanyi nan Ko ,Kai ta daga mata ,Yawwah yusrah Allah ya miki Albarka ,su kadai sun isheki yanzu Ke yarinya ce gyaran jiki da maganin sanyin kawai kikeda bukata ,kuma wannan Kayan sanyin guarantee Masu kyau ne ba Wanda zakiyi Amfani dasu kwana biyu ka lalace bh,sunada kyau da tasiri a jikin mutum ,gadai garirika nan na karo miki ,sbd idan kanada kyau ka kara da wanka ,Sannan Karki yi wasa da Shan fruits ,dan milkshakes dinki na fruits ,su kankana ,Abarba su zama abokan rayuwarki kinji Ko ,Yau miji idan ya kwanta dake yaji yanaci Chicken Mandi gobe yaji lamb Mandi ,kiyita canza masa taste shine abun da sukeso ,dan Ko kaine baza kaso kayita cin Abu daya bh duk dadinsa kuwa ,change is good shiyasa idan kanada kyau ka dinga karawa da wanka ,fruits dinnan da veggies ki rike da kyau ,kinga Zogale dan Allah yusrah kada kiyi wasa da Zogale Ko baya miki dadin ci ki yawaita cinsa sbd yanada kyau Sosai a jikin dan Adam zai Kara miki abubuwa dayawa Wanda Ke da kanki mah bakisan dasu bh ,kada ki yawaita cushe cushe da shaye Shayen magungun Kala Kala ,kar kije kiyita dirkawa kanki magani ,dan sau tari wasu magungunan da muke Shane suke bamu matsala ,idan zakisha magani ki nema me Inganci ,kuma ki dinga siya gurin Wanda yakeda ilimin abun ba Wanda yakeyi abun Kai tsaye bh ,dan wasu idan ka titsiyesu basusan me suke saidawa bh,Sannan ki dinga Neman abun dan daidai me tasiri ba kiyita gabje gabje bh kinji Ko,ba’ason ka hadawa kanka commotion ,dan abubuwan kadan Masu kyau Masu inganci da tasiri sun isheki zaman auren ki ,dan mutunci da darajar nan dai ki dinga kankaro wa kanki ,ki karanci mijinki ki gane inda ya dosa,ki zauna da Abokiyar zamanki lfy ,naji dadi da akace ba gidanku daya bh ,ita din wannan gidan ne nata ? Kai yusrah ta daga mata ,Owk kema naji ance can baya ne kadan ,shima babu nisa da kafa ma za’a iya zuwa Ko ?,shiru ta mata dan ita kunya ce da ita ,toh Allah ya sanya Alkhairi,Allah ya bada zaman lfy ,Allah yasa a gama lfy ,yaro kam yayi kokari wannan uban lefe a dan kankanin lokaci harda mota ,Allah ya saka masa da Alkhairi ,Allah yasa abun dayake nema ya samu fiye da haka a gurinki ,ki rike sallah sauka da karatun Alqurani,ki yawaita sadaka ,dazu mh naji anyi miki saukar biki kuma anje gidanki anyi miki sauka Ko ?kaita daga mata ,toh Alhmdl ,ita wannan saukar idan da hali duk shekara a dinga miki ita a gidanki,bawai da anyi sau daya bh shknn ,kinji Ko ,ni Bari na tafi na kwanta,wannan gumbar sai sanda za’a kaiki da yammah zakisha da madara ,Allah yasa mu dace ,******* In a short period of time yusrah son kamal ya mamaaye zuciyarta,babu abun da takeso a duniya sama da kamal dinta ,gashi kwana biyu bata ganinsa mamanta tace sai an fara biki zai fara ganinta ,saidai suyi waya shima basa dadewa,kullum suka gama waya saita masa Addua ,Allah ya taimakeka Allah ya kareka ,Allah ya biya maka bukatunka na Alkhairi ,Yanajin dadin wannan Adduar har ransa
Tana cikin wannan tunanin ne taji call dinsa na shigowa ,Saidai tayi gyaran murya sanann ta dauka,” An dai hanani ganin princess Dina “,shiru tayi Tana jinsa,” kinci abinci Ko kinata Baccin naki “, “Naci abinci ,kaifa ?,” “Nima naci zan iya ganin henne design din princess Dina ?, pls princess ki turamin ta watsapp,”,Murmushi ta masa “yaya kamal ka bari ai zaka gani “,”Thom shknn since you insist ,gani a kofar gidanku ,aiko khalil ya karba miki sako “,” toh nagaode Allah ya saka da Alkhairi Allah ya Kara Arziki ”,ta kashe wayar , kallon wayar yyi yana murmushi ,kullum dai Addua take masa yanajin dadin wanann ,danshi bai samu me masa Addua bh kullum ,Alhmdl yace ,Khalil ne yazo ya Mika masa su shawarma da drinks ya siyo mata ,text ya mata “ make sure Kin cinye komai ,dan nasan kinata busy Baki tsaya kin cika cikinki bh ,love you “, dataga text din nn farin ciki har ranta ,what a caring husband ,hannu ta daga Allah ka bani ikon faranta masa nima

Ya dade yana kiranta taki picking ,karshe mh rejecting ta dingayi ,cousin dinta Amina na kusa da ita ,Amrah Wai ba mijinki ne yake kiranki bh ,shine mana barshi laifi yayimin ni kuma nace sai nayi punishing dinsa sosai ,saiya gane Kurensa ,call dinne ya sake shigowa ,tsaki tayi ta dauka ,Wai mene ?,Amrah dan Allah Yau dai ki tsaya ki jini ,nagaya miki inason muyi magana dake ,kullum kinata Avoiding Dina ,ki tsaya kiji abun da zance it’s very important,hmm!,kamal kenan ,sanda kaje kayi iskancin kah da Rabi ka tambayeni?Ko kuwa kazo munyi maganar?,sbd haka ko mene kakeson muyi magana ka rike abunka banason ji,gabaki daya yaushe na dawo daga Bauchi ,Ko hutawa ban gama bh kabi ka isheni ,danka ne Gashinan duk sanda kakeson ganinsa kazo ka gansa ban hanaka bh ,kamal ranshi ya baci sosai ,Ko yaushe Amrah Zata koya masa magana me dadi ,yayi laifi anfi wata nawa Amman har Yau kullum saita masa gori ,wannan wani irin abune ,da kakausar murya yayi magana ,Amrah Ina kofar gidanku ,ki fito muyi magana ,how many months Ina binki inason muyi magana kina Avoiding Dina ?Ke babu Wanda yake gaya miki abun daya kamata ne ? is this ryt abun da kikeyi kikewa mijinki ? nifa mijinki ne ko kin manta ne ? Me kikeso ne a duniyar nn Amrah ? is dis how you will countinue treating me ? what is Wrong with you ? ki fito nace miki zamuyi magana kinji Ko ,Wlh kamal bazan fito bh ,idan danka ne Gashinan za’a kawo maka ,waya sani mh Ko gurin Rabi kaje zaka wani fake da gurina kazo ,wlh kaje kaida Allah duk abun da kake ban yafe maka bh kuma Allah saiya sakamin,mayaudari munafuki kawai ,Amrah ni kike cewa munafuki?,shiru tayi tanata tura Baki kaman yana kallonta , murya ya gyara ,Owk Thom shknn ,kinki ki bani time muyi magana Ko ?kar kizo kina neman time Dina muyi magana ,Amrah ni banma San me zance miki bah ,Amman ina rokon Allah ya shiryeki,Ina rokon Allah yasa kisan wane miji kisan darajar miji,Amrah Ko ki yarda Ko Karki yarda na Rabi da Rabi tun sanda akayi abun nan a gabanki ,Amman tunda har yanzu kina zargina babu abun da zance miki ,you may believe what ever you want to believe,dama magana ce daya kamata na gaya miki face to face ,Amman tunda kinki yarda na ganki zan gaya miki ta waya,dan idan na biye miki time zai Kure ban gaya miki bh kuma Azo Ana ganin laifina,Amrah !sai kuma yayi shiru,tunawa yyi idan baiyi sauri yyi magana bh Zata iya katse wa dan yanzu mh ba karamin sa’a yaci bh data tsaya,Amrah jibi Saturday Ko?, mtsww ,Ina jinka fadi abun da zaka fada jibi Saturday mana sai akayi yaya ?, iska ya fitar Sannan yaci gaba da magana ,Ranar Saturday za’a Dauramin Aure ,Amrah kallon wayar tayi ,hello ta kuma cewa ,mene kace?ban gane bh ?, Nace Ranar Asabar dinnan me zuwa za’a dauramin Aure ,zan kaita nan kasa damu wannan gidan nawa Dana Gina zan saka yan haya so yanzu ita zan saka acan na barki a wannan gidan namu ne tunda naga yafi wancan girma kuma nasan zakifi sonsa Ko ?Kan kutumar burouban can!! Wait kamal banason wasa ,if kana hakane dan in dawo banason irin wannan wasan ,kai yaushe mh ka iya zance harda za’a Baka yarinyar har ka aura ,a wanann kunyar taka ,look banason wasa ,am not here to play ka fadi abun da zaka fada ,Hmm yace ,mayb to you bakiga abun da zaisa a bani bh Amman su sun gani ,na barki lafiya idan kin shirya duk sanda kikeso sai ki dawo ,jibi zan kara aure ,Baby muhammad zaiyi new Aunty ,idan da abun da kikeso text me ,love you Saidai safe ya kashe wayarsa ya wuce ya tafi, ihu ta saki ta daka wani uban tsalle ta cillar da wayar da gudu ta fito kofar gida amman inaa !kafin tazo ya tafi ,dawowa tayi da gudu anata kallonta kaman wata zarariya ,gurin mamanta ta wuce tanata nishi ,tsoro mamanta taji Ke lfy ?,menene haka ?, mama….Mama….Ina jinki fadi abun da kikeson fadi ,Mama kinji Wai kamal Aure zai Kara Tana fada ta fadi kasa ,da kyar aka daukota aka yayafa mata ruwa ,kowa yana kanta hardasu mama Talatu Wanda tunda suka dawo daga biki basu koma gida bh ,bayan ta farfado ne maman ta kuma cewa ,Amrah ki natsu kinji ko?kamal ne zai Kara aure? kaita daga musu sai kuka,Mama Wai jibi za’a daura masa aure ,shiru kowa yayi dan basusan ta inda zasu fara magana bh ,mama Talatu ce tace ban gane bh?,Ke ya akayi baki sani bh ,kina nufin sai yanzu kika sani? kai ta daga musu ,Meyasa ?mama talatu ta tambaya ,kuka ta shigayi mama talatu laifi yayimin ni kuma nace zan koya masa hankali,koya kirani bana dagawa sai naga dama Ko idan inason Abu ,ya dade yana gayamin Wai zaizo muyi magana nace ya rike maganar sa ,da zamu tafi Bauchi mh yanata mun maganar na kashe wayata nace kar ya sake kirana,mama talatu kimin rai ,mene laifina anan ? Ance idan miji ya maka idan Baka takasa bh ba’a shiryawa,ance idan ya hau ka hau sai kuyi daidai ,kamal masoyina ina sonshi wlh shima yana sona ,zasu kwace min miji ,hannun mama talatu ta rike tanata kuka mama dan Allah kayimin Rai ku Kira kamal ku basa hakuri ,wlh na daina dan Allah karya Kara aure wlh mama zan iya mutuwa banason kishiya Wayyo Allahna ,kowa saida ta basa tausayi Banda mama talatu ,Maman Amrah ce ta fara magana,Amman yaron nn bai kyauta mana bh ,haka akeyi gabaki daya yaushe akayi auren ? Amrah din gabaki daya nawa take ?,me ta sani ?daga zuwa wankan gida ,munafuki yayita wani simi simi da Kansa ,Ashe shima munafukin ne ,mama talatu ce ta gyara zama mama kar kice haka

Kinajin fah abun da take fada mana ,idan namiji ya hau ka hau ,idan ya maka ka masa shine zakuyi daidai ,IKON ALLAH ,Maman Amrah kece kika gaya mata haka ?kai ta girgiza,Ke yusrah Ina kika samu wannan Karatun ?again kinata Avoiding Dinsa,bakya nuna kulawarki ,baki damu da damuwarsa bh,to wannan wani irin sone haka? ke dama kinason mijin naki Amrah ? Ai ga koya masa hankali nan kin gani,nifa dama dan banason shiga abun da babu ruwana ne Amman maman Amrah harda Ke naga laifinki ,yanzu yarinyar nn tunda ta haihu Yau wata nawa bata koma wa mijinta bh,namiji fah ba irin mace bane ,namiji magidanci kullum yana bukatar mace a kusa dashi ,yayi hakurin Ar’bain dinnan Sannan ta wuce ta tafi Bauchi biki,yanzu farida da mijinta ya hanata kinji wani yace Abu ? Nina haifeta kuma naso taje ,Amman miji ai yafi karfin wasa ,mu a matsayinmu na iyaye sai mu dinga nuna musu girman mazajensu mu tayasu ,haka ta kirani Tana kuka na bata hakuri,tunda ai ba komai yake hanawa bh ,kuma watakila ya duba yaga wata daya shi za’a iya shiga hakkinsa ,nasan da bai wace sati bh watakil ya iya barinta,toh haka ake zaman duniya ,yaranka idan sunyi aure mu bisu da Addua kuma mu dinga tayasu zaman gidan auren ,yanzu wah gari ya waya?,ke kinason mijin naki ba rashin lafiya bah ba komai bh ki tafi ki barsa Wajan wata nawa ,wlh ni Ina ganin kokarin mijin Amrah dinann ,kema Amrah kin samu mijinki shiru shiru shiyasa kike Amfani da wanann kike basa wahala ,Baki ta bude ta fara magana Tana kuka wallahi mama talatu ba wahala nake basa bh,to me na masa?Yimin shiru tace ,yanzu indai dagaske kinason mijinki saiki gyaran ai ,is not late ,uwar dansa ce Ke Idan da Rabo ki dawo da mutuncinki da kika Bari ya zube ,Dan wlh mutuncinki ya zube Amrah ,Ke kowa yana lallaba miji banda ke Ko? A wanann zamanin Baka rage miji da Komai bama yana maka attitudes bare kana zuba rashin mutunci ,kukan takeyi har yanzu mama wallahi Saidai idan Asiri suka masa Amman kamal bashida niyar kara aure kuma ya gayamin ni kadai yakeson ya zauna Dani ,dan ya zauna gidan kishiyoyi yasha wahala bayason irin wannan rayuwar ,aunty talatu ce tace ohooo !!,shiyasa kikayita rashin mutuncinki Ko ? to ai ba wahayi akayi masa bh Akan bazai kare aure bh ,Dama da kin zamo masa mace da Ko wani namiji yake buri wlh banjin zai kara,Amman da halayenki ya saka ya zabi Karen auren ,katseta tayi ,mama yanzu toh baya sona kenan?mama Talatu saida tayi dariya ,yarinya kenan,ke dah Amrah kinasonshi kiketa zaune a gidan nn ? Ko tuna halin da mijinki yake Baki damu bh,to kin makaro,mijinki ya burgeni,kuma lallai yaron Arzikine ,da yaje ya fara bin mata bh gwanda dayayi dabarar yin Auren ya samu sukuni da natsuwa bh ,Amrah men settled where they find peace ,namiji duk inda Kwanciyar hankali yake nan ne yaga gurin zama ,kinsan wani kyanki da durunki da iya gayunki indai bakya bawa miji natsuwa da Kwanciyar hankali wlh dake da babu duk daya, Amrah indai miji bazaije gida ya samu natsuwa bh ,ya kwanta da matarsa ya samu Farinciki bh ,ya dinga Allah Allah mh ya dawo gida toh you fail as a wife ,me zaki bawa miji Wanda ya wuce zaman lafiya da Kwanciyar hankali natsuwa da Fatin ciki ehh??, toh mijinki yana sonki Amrah but dat does not mean Dan yanason ki zaita zama yana tolerating habit dinki ,da ya fada hanyar banza wlh da sai Allah ya kamaki ,Amman Allah ya taimakeku gabaki daya ,and ki cire wanann mindset din na baya sonki ne ya Kara aure ,Noo oo,kamal ga dukan alamu yana sonki Amrah ,is just dat no matter how the love ,A man can love you and still have space for another woman ,kyatatawarki da kalar irin farin cikin da kike basa shine zai kwaceki,mayb mh yaji kin isar masa kin cike all the space ,but if bakyayi dole wannan space din ya fito fili ,gashi dai yana sonki but he will still find a way to love another person ,kinayin komai mh Amrah he may feel that way bare kuma bakyayi ,Sannan wlh ki shiga hankalinki kinga dai aure zai Kara kibar ganin ke uwar dansa ce wlh kika Bari tazo ta fiki iya rike miji idan yara Dari kika Haifa masa kinaji kina gani sai yanda tayi dashi ,ki shiga hankalinki kija mijinki a jiki ,ki zama safe zone dinsa,ya dinga samun natsuwa kulawa da farin ciki yanda Ko wani namiji yake buri,a cikin abokanan sa kisaka ya jisa ya fita daban a cikin mazaje ,Ai Ko manzon Allah (S A W) yace the lucky ones in life are does da suka samu mace ta gari ( Mar’atusallahi) kinga kuwa abun murna ne ,and likewise idan bai samu bh abun bakin cike ne ,dan yanzu mijinki zaiji kaman he is unlucky,shikam bai samu mata bh ,sbd haka idan kunne yaji ,jiki ya tsira ,ki tashi kiyi gyara ki koma gidan mijinki idan dagaske kinasonsa aure kam nasan babu fashi yaron nn baya Abu da wasa ,Maman yusrah ce ta kallesu to yanzu a ina zai ajiyeta?,dakyar take magana Wai a sabon gidansa na bayan gidanmu daya gina,Tana fada tana shesheka,Amina cousin dinta ce ta saka baki,ni wlh Aunty kaman naji Rumors dinnan Amman sai ban kawo shi bh,Akwia wata yusrah kyakyawa a school dinmu take junior dinmu ce mh yarinyar ga kyau ga hankali ,gasu Suma yan gayu naji Ana za’ayi bikinta kuma kaman mh neighbor dinsu Zata aura ,naga card dinma sunan yaya kamal ,kuma nasan a area dinku take Amman ban kawosa bh wlh ,coz I thought idan shine ai zamu sani ,Ashe kuwa shi dinne ,Amrah hannu ta saka a kirji Tana shesheka tanata ihu Tana Wayyo Allah,ga Ac a parlour din Amman firfita ake mata,Innnalilalahi wainaillahi rajiun kawai take fada ,yanzu da gatana da iyayena da komai na ayimin kishiya,kallon mama talatu tayi ,mama kinji Ko?yarinya ce mah kuma neighbor dinmu ,yanzu yarinayr zai auromin,kuma makociyata ? murmushi tayi Amrah kenan,ai Ke kika bada room ,yanzu haka ko Rakasa kofar gida bakyayi har kiga tafiyarsa ,idan kinji motsinsa bazaki fito da murnarki bh ki tarbesa,yanzu kina haka ai tsoron mh ya tsaya da wata a kofar gida zaiji ,Amman yanzu haka kinacan kina kallon nan naki mijinki yanacan yana soyewa da mokaciyarki ,toh Ko nan gaba Ko Ke kake katsewa kake kaje ka taka miji ka bisa da Addua harda dan kiss ma a goshi ,yanzu idan bakiyi wasa bh yarinyar nan saita kwace miki mijinki kinaji kina gani,yaran yanzu kuma ,kuma bada asiri bh babu boka babu Malam kawai tsabagen iya rike miji da biyayya
Mene Amfanin kayi aure bazaka yiwa mijinka biyyaya bh ,ai gwanda ka zauna a gidanku da kaje mh kana kwasan zunubi ,A yanzu Amrah abun daka raina wasu shi suke marari suke burin samu ,wani naki yake hange,shiyasa ka rike abun da Allah ya Baka dakyan gaske ,Allah ya kyauta ,Kowa tashi yayi yana bata hakuri ,itama tashi tayi ta hau hada kayanta ita a lallai yau gidanta Zata wuce,mama talatu ce tace ki tsaya dai kiyi gyara ai aikin gama ya Riga ya gama ,Karki koma kaman dusa dan nasan anacan Ana hada masa matarsa ,Kuma wlh kikayi sake a wannan bangaren Kwanciyar sunanki sorry ,duk kyanki da kokarin birgesa bazai gane bh ,indai bai gani a kan gado bh ,kika Bari mijinki ya kwanta da wata yaji ta fiki dadi da isar masa da sako toh kuwa indai ba me tsoron Allah bane saita fiki Jin dadi mh a gidan ,Amman idan me tsoron Allah ne zaiyi Adalci ,And kinsani basai na Kara fada miki bh ,zuciya dai tanason me kyautata mata ,idan kin natsu ki Kira farida ta hadaki da Matar da take siyan yan kayan gyare gyare a gurinta ta gyaraki ta fito miki da mutuncinki kema ,ko kallonta batayi bh , ta zauna a kasa tanata kuka ,imaginning kamal take Wai shine zai taba wata ,Ya Allah !!

Leave a Reply

Back to top button