Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 3

Sponsored Links

_
3
Sam Hande bata wani tsoro kaman ‘dan nata take duk shi kam na musamman ne a fagen taurin zuciyar da batada tausayi ko taushi ko kadan akan komai da kowa sai akan qaruwarsa,dan haka kai tsaye hande ta fito tsakar gidan idanuwanta a kofa tana qwala kiran Ababa din da karfi sbd ya fito cikin sauri da shirin harbe kafar koma wane shegen ne ya shigo musu gidan…..bakinta kasa qarasa magana yayi lokacinda ta haske kofar da fitilarta me tsananin haske taga samirah dake dukan kofar cikin tashin hankali da neman mutuwa ta dauketa a lokacin idan bazata zamu kubutar tserewaba a daidai wannan mummunan lokacin.

Cikin sauri idanuwa a rufe Ababa din ya fito yana saita doguwar bindigarsa da kofar ba wata wata ya harba da karfi ko ita handen bai tsaya cewa ta matsa daga gurinba saida qarar bindigar yasata zubewa qasa sbd babu abinda yake rabata da nutsuwarta da hankalinta ita kuma sai bindiga sanin aikinta ba wasa lahira take.

Safnah dake daki tun fitowar hande daga daki ta yanke jiki a gurin ta zube sbd mummunan tsoro da firgici mara misalin daya tsayar da bugun zuciyarta duk da ita a daki take boye dan haka kwatanta halinda samirah take ciki zaiyi wuya sbd fitowar mahaifinsu kafin ya harba bindingar zuciyarta ta tsaya cak qafafunta suka sare dan haka koda ya harba bindigar kofar gidan yayiwa mummunar fasawa sbd bullet dinta na fulogon mashin ne.

Cikin wani irin firgitaccen tsoro dukkaninsu dakin suka farka suna tashi zaune idanuwansu na rarrabuwa akan junansu sbd duk irin haka tafari junansu suke fara tabbatarda suna tare guri daya saisu nutsu basa fitowa matuqar ba cewa yayi su fito ba.

Benazir ce tafara bude baki tana rarraba idanuwanta dake wartsakewa daga bacci cikin tashin hankali da tsoro tace,

“Samirah,ina samirah?”

Dukkaninsu sai alokacin suka miqe tsaye cikin rawar jiki da tashin hankalin dayake neman fin karfin bugawar zuciyarsu suna rarraba idon neman samirah din
Sumayyah kuwa kan safnah dake zube tana qanqamewar tsoro da daukewar numfashi tafara girgizata da karfi tana tambayarta ina samirah amma sam safnah bata iya motsi bare fahimtar me sumayya ke fada bare ta iya bada amsa.

Cikin wani irin karaji mai karfi da firgitarwa daya saba kada hanjin cikinsu dashi a zafafe da wani irin fushi da zafin dayake ci cikin kansa yace,

“Guduwa zakiyi?
Ina zaki?
Kin san me kika aikata?
Kinada inda zaki iya guduwane ki tseremun?

Shaqota yayi da wani irin karfi da zafi ya buga kanta da jikin kofar yana take qafafunta da nasa da karaji ya kira sunan Hande yace ina ta samu mukullan bude gidan?

Kallonta hande tayi cikin baqin ciki da takaicin tado musu da hauka da tashin hankalin Ababan ta miqe tsaye daga zubewar datayi rai bace tace,

“Nawa ne ta sato harda barmin daki a bude”.

Wani sabon gigitaccen marin bayan hannu ya sakar mata wanda ya sata zubewa qasa bakinta na tsiyayar jini sakamakon hakorinta ‘daya da ya fita take sbd tsananin zafi da radadin marin.

Damqota yayi ya dago sama ya sake sakar mata wasu mahaukatan marikan guda biyu dasuka dauke dukkanin wutar jikinta ta silale a gurin take ya take hannuwanta dake jini da ruwa a fusace yasake maimaita mata tambayarsa daidai nan su Benazir dasuka fice hayyacinsu suka fito zuciyoyinsu suna rawa da tsallen munannen tsoro saidai dukkaninsu babu wanda ya iya daga kai ya kalli abinda Ababan kewa Samirah saima hana tashin hankalinsu bayyana sukai sbd hakan kaman wani laifin ne.

Anne dake kusa da benazir qasa daukanta kafafunta ke kokarin yi amma benazir ta riqeta tana kokarin hanata bayyanarda masifar dake ragargaza zuciyarta akan ‘yarta datake kallo ana hallakawa amma babu abinda zata iyayi ko ikon dagowa ta kalla batada dashi dan haka takejin kaman ana zare naman jikinta ne daga qashinta,
Sumayyah da rauninta baya dauka tini ta zube qasa da rarrafe cikin tashin hankali da ficewa hayyaci ta koma dakinsu ta zube kusada safnah da har lokacin bata dawo daidaiba jikinta kerma yakeyi duk da babu qarar ihu ko kuka ko kadan dayake tashi sbd azabar datayiwa samirah din yawa gakuma daman horan daya musu duk tsananin azaba basa masa ihu ko kuka dan haka suka taso da iya riqe ciwo a zuciya da ciki.

Benazir ce kawai a tsaye kanta a qasa harya gama yiwa samirah din dukan mutuwa wanda ko hannunta bata iya motsawa bare wani sassan na jikinta,

Juyawa yayi yabar gurin batareda yace komaiba ya shige dakinsa hande ma juyawa tayi tana haska benazir da fitila tace,

“Jata ki maidata daki idan tanada rabo zata shiga hankalinta idan ta warke”
Dakinta ta shige itama ta rufo kofa .

Sarewa qafafun BENAZIR sukayi ta zube a gurin tareda fashewa da wani irin kuka mara sauti ko kadan jikinta na rawa da qyar ta kai kanta gurin samirah din ta janyota jikinta tana sarewa da jini da numfashin da samirahn bata iya ja.

Samirah dake jin BENAZIR din sama sama hannu takeson dagawa ta taba Benazir din amma takasa sbd numfashin datake neman ja amma kirjinta baya karba.

Anne da kanta ta tako tazo hannuwanta na rawa ta kamawa BENAZIR sukai ciki da samirah din wadda numfashinta ya fara daukewa yana dawowa.

Kwantar da ita sukayi kowannensu ya zube gabanta babu mai iya cewa komai sbd basa hayyacin magana,

Sai alokacin safnah da sumayya suka fashe da wani irin kuka mai ciwo da radadi ba sauti,
Anne hawayenta bushewa sukai bayan ido data zubawa samirah din babu abinda take iyawa,

Benazir ma datake da jarumtar batada iyawa bayan hawayenta dake gangara da gudu masu tsananin zafi.

Haka suka zuba mata ido bayan jinin dasuka goge mata a jiki da ruwan zafi komai basida nayi mata dan haka suka ringa binta da addua har gari ya waye.

Koda safiya tayi gabaki dayanta ta kimbura sbd duka,
Kamanninta kuwa gabaki daya sun sauya sbd fuskarta data tashi daga fuskar kuruciya zuwa wani abun tsoron.

Karfe tara ya fito daga dakinsa kai tsaye ya tarasu ya tabbatar musu da babu wanda zai bawa samirah din kowace irin kulawa ta musamman kaman yanda tayi niyar tserewa da kanta haka zata miqe da kanta ta karbi hukincin daya yanke akanta na maidata dakin dabbobinsu acikinsu zata zauna har ranarda sanadin rabuwarsa da ita yazo maana idan ya samu gurin miqata tareda horon ko kofar gida bazata sake kallaba idan ta kalla saiya zuba mata maganin dabbobi acikin idanuwan dan idan ta makance ne kawai zata cire rai daga sake tinani.

Dakin dabbobinsa aka maidata kusan zannuwansu suka hada sukai mata shimfida dashi tareda na lullubawa aka kwantar da ita har lokacin bata iya tayar da kanta saidai mumfashinta daya ‘dan daidaita.

Basuda ikon tsayawa kula da ita matuqar ba sun gama aikin dayake kansu bane dan haka ita kadai suka bari a tsakiyar dabbonin suka dawo zuciyoyinsu ba kuzari ko kadan.

Bangaren dabbobin kaman yanda suka saba shi suka fara dashi ta hanyar kwashe kashinsu tas da hannayensu suka share babban gurin tarefa tsaftacesa suka kwasa suka fitar tareda jerewa a dakin dayake tara takin kashin.

Daganan aikin cikin gidan sukai tareda wankin kayansa dana Hande da kullum sai anyi,
Aikin abinci suke gamawa da wuri kafin su koma aikin kulawa da dabbobinsa,

Basuda hutu ko kadan tunda suka kammala karatun secondary din gwamnati wadda nisanta ma da abin hawa 700 ake zuwa a dawo 700 amma ahaka suke zuwa da qafa su dawo da qafa ba karin kumallo ba ruwa haka yayi musu mummunan horon da sam basa iya zama ko muamala da mutane,
Tamkar mujiyoyi suke acikin mutane har sukai suka gama babu wanda zaice daya daga cikinsu tayi muamala dashi kota gaisuwa saidai idan ka gaishesu su amsa kokuma sallama ita sunayi,

Koda suka kammala babu wadda taqara sanin meyake wakana a duniyar wajen gidan dan kuwa ya rufesu babu inda suke zuwa sbd killace sirrin rayuwar gidansa,

Sam baya tsoro ko shakkar kowa baya shayin fadar maganarsa kai tsaye ga duk wanda yakesan fadawa,
Baa shiga huruminsa ko kadan kaman yanda baya shiga na kowa dan kuwa ya kame kansa ga lamarin kowa abinda ya shafesa yake gabansa kawai yakeyi,

Masifaffe ne,
azababbe ne,
Mara tausayi ne,
Mara shakka ne,
Mayen dollar da naira ne uwarsa data haifesa baza iya cin sisinsa idan ba na ciyarwar datake ci a gidanba,
Tsananin so da qulafucinsa akan kudi yasa su kansa yayan bai yarda ya koresu ya rasasu ba a banza ba batareda ya ci ribar ciyarwar da zaman dayayi mahaifi a garesu,
A karshen buqatarsa duk munin aiki ko sanaar mai kudi zai basa aurensu shiyasa ya danne zuciyarsa ya basu karatu da ilimi ba sbd burinsa na fanshe wahalarsa akansu babba ne.

******duk saurin dasukai na kammala tarin ayyikan bautar dasuka saba basu samu dawowa ga samirah din ba da wuri Anne ce kawai a kanta
Zazzabi mai qarfi ha riga ya rufeta haka zalika raunikanta sunyi munin kallo haka suka sake wanke mata suka gyarata aka sake kwantar da ita.

Abincin da aka basu duk yanda sukaso yashiga cikinta ba dama tunda ba ruwa bane,
Sunaji suna gani ahaka suka ringa jinyar samirah din wadda kusan kaman rubuwa ne hannuwanta sukai sbd wasu irin ruwa da wari mara dadi dasuke fiddawa duk da wanke mata da sukeyi kullum,

Tana iya magana amma a hankali amma bata ita tashi zaune sbd kaman harda bayanta ya samu matsala dan haka haka suka ringa jinyarta cikin sarewa da addua har tsawon sati biyu harta fara warkewa hannuwan ne kawai da rashin tashin sai gashi Kwatsam Allah ya karbi ranta da tsakar dare bayan sunsha kukan alamar tafiya dasuka gani a tareda,

“Mutuwa batada magani tafiya dole ce” itace kalmar data fada a lokacinda takeji itama tafiyar zatayi tabar uwa da yan uwanta a halinda basusan su yaya nasu qarshen zaizoba.

Tayi kuka acikin yan uwanta sosai a raunane sbd tausayin kanta dana mahaifiyarsu da nasu fatanta duk tsanani duk wuya su kasance a tare babu ‘baraka.

*****Rasuwar samirah ya sake taba Annensu sosai haka suma dan kuwa rayuwa taqara tsanani da qunci sbd a zahiri Ababa yace yafara gano asarar dasuke neman ja masa tinda samirah ta bude musu hanyar tinanin guduwa dan haka ya tsananta musu fiyeda shekarun dasuka debo,
Ya zaburar da zuciyoyinsu gabaki daya basada wani motsi da zasuyi batareda tsoro da shakkarsa suna firgatasu ba dan haka ko a mafarki babu wanda ya yarda yayi mafarkin tinanin gudawa,
Zasu zauna tareda mahaifiyarsu wadda ya kafeta daga ranar daya aureta ta yanda bazata taba tafiyaba ko ina har abada sai mutuwa dan haka suma zasu zauna tareda ita har sai yanda Allah yayi dasu din su duka.

Wannan tinanin Benazir datafi kowa tsananin so da kaunar Annensu ne da sumayya amma banda safnah wadda a yanda komai na rayuwarsu ya qara tsanani da qunci tana nan da burin tseratar da kanta daga wannan rayuwar da basuda tabbacin fita ko
Rashin fita har abada.
#MAMUH#
#PURE LOVE
#BENAZIR
#BILLONAIRE
#DEEP
#SISTERS
#MARRIAGE
#ROMANCE

ZAFAFA BIYAR🔥

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-FURAR DANKO
Billyn Abdul

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at
09033181070
09032345899

Zafafa🫶🔥🔥
_*ZAFIN KAI*_
_Mamuhgee_

Leave a Reply

Back to top button