Cinikin Rai Book 1Hausa NovelsHausa Novels

Cinikin Rai Book 1 Page 10

Sponsored Links

: .10
Beauty and the beast.
Mai_Dambu🌚
<<<<<<<<<<<<|=|>>>>>>>>>>>
Tsurawa Mamanta idanu tayi, sannan ta ce mata. “Maama to me yasa ba zaki nima mana shi ta wani hanya ba?” Yar ta kalleta, kura mata idanu tai, sannan ta ce mata.
“Malik baya cikin irin wadannan mazan, don haka dig your food, na gaya miki wwnda zaki yi sauran ki bar min a hannuna.” Gyada kai tayi tana cin abincin.
Ajiye spoon tayi ta ce mata. “Maama Yaran Malik ne Wahiba da Wahida?” Dauke kai tayi, kafin ta ce mata. “A’a ba Yaransho ba ne, Yaran rikonshi ne!” Tura baki tayi, “Amma Maama shi ne yake ji dasu haka?” “Ya isa haka!” Uwar ta fada, tana me dauke kai. Taya zata gaya mata abin da ya faru? Har zata wuce ta ce mata. “Princess! Kada naji ko na gani, kome yana buƙatar sirri don haka koda wasa kada na ji wannan labarin a bakin wani.
Gyada kai tayi, tana me mikewa daga table din, wayarta da yake gefenta ne yayi kara. Idanun Lalla Salmah ne ya sauka kan wayar. “ba na rabaki da Yaron nan ba?” Tsuru-tsuru Maida tayi tana kallon wayarta. “Wai sau nawa kike son na gaya miki, baki dace da shi ba? Kina da rayuwar da tafi tashi.” “Hmm! Maama dan uwana ne, ba wai yana zuwa nan da sunan soyayya ba ne, ko kira ba. Kawai yana kira na ne a matsayin kanwarsa.” Kura mata idanu tayi kafin ta ce mata. “That family basu cancanci dace dake ba, ki nutsu kina da rayuwa sama da tasu, kada na kuma jin wani abu ya hada ki da su, domin zan sab’a miki.” Gyada kai tayi Idanunta yana cika da kwalla. Har zata wuce ta ce mata. “Tun last week ya gaya min, Anyi admitting Abbana a hospital, yanzu ma ya kira ya gaya min ne.” Ta fada hawaye na zuba mata. “Pick the phone;” ta gaya mata tana dauke kai, dauka tayi a hankali ta ce mishi.
“Hello bro! Ya jikinshi.” “Maida jikinsa da sauki, amma yana da kyau kizo ki duba shi, koda ita Aunty ba zata zo ba. Please ki fahimci girman hakkinshi da yake kanki mana my sister shima yana da hakki akanki.” Kallon Lalla Salmah tayi ta ce mishi. “Ok zan zo in sha Allah, ka gaida min shi ka ji sai na zo. ” Ta kashe wayar. Kamar bata ji abin da suka ce ba, so sai tayi fuskar tare da ɗaukar jaridarta ta bar wurin abincin, dama taji ne me ya same shi, kuma taji he still alive. So bata da wani case da shi. “Maama don Allah ku bar ni na je, na ganshi.” “Tunda bai mutu ba, ai da sauki ko? Ya ce miki ya mutu ne?” Inji Lalla Salmah. “But Maama yana da hakki a kaina, Maama mi bar ni naje na ganshi, ko kuma wallahi ba zan tab’a miki yadda kike bukata ba!” Kura mata idanu tayi, wani lokaci Maida kamar Ubanta take, don wani lokaci, bata iya juya su a saukakke sai sun bayyana mata kansu na da ƙarfi. “Ok kina nufin taurin kanki zai saka nace Maida Sheikh jeki ki duba Babanki?” Hàdiye yawu tayi cikin tsananin shakkar Uwarta. Bata mantawa lokacin da ta dawo hannun Uwar, duk da taji labarin a bakin Nanny ta gaya mata sai da Malik Menk Jordan ya saka baki aka bawa Uwarta ita da sharadin zata na barinta zuwa wurin Mahaifinta, amma zata iya cewa har ta gama secondary school, ba zata kirga zuwa ganin mahaifinta ba, domin Babarta ta k’amk’ame kome, ta hanata zuwa wurin danginta da kowa nata, shima wanda Anwar din da yake kiranta, yaso ta tun tana wurin Babanta, kuma har yau shi daya yake zuwa gare ta, amma mamarta bata kaunar alakarta da danginta. Zubewa tayi a gabanta tana kuka ta ce mata. “Don Allah Maama kada ki hana ni zuwa gare shi.” “Zaki je kiyi kwana biyu, daga can zaki na zuwa makaranta. Bayan nan kuwa hmm!” Yadda tayi maganar yasa ta cigaba da abin da take. “Na gode.”. Ta fada muryanta yana rawa, “kin ji dadi?” Gyada kai tai hawaye na zuba mata, domin tasan halin Uwarta, tabbas akwai wani abu a kasan ranta.
★★★
After few days.
Zaune take, tana waya a hankali duk da ba wai ta saba da hakan ba ne, sai dai yadda kanta yake masifar ciwo ta ce.
“Mr Amjad ai na gaya maka bani da lafiya, tow me zan iya yanzu, yar sandan nan ta ishe ni.” Shiru tayi kafin ta ce mishi.
“Look na gaya maka bani da lafiya, idan baka yarda ba, kazo ka duba ni.” Shiru tayi kamar zata yi kuka ta ce mishi. “Ok zamu zo na ganki” gyada kai tayi tana faɗin.”sai kazo ” daga nan ta kashe wayar tana kallon Black. “Sai yaushe za a sallame ni?” Murmushi yayi ya ce mata. “Sai kin samu lafiya, kin ga har yau kanki bai daina ciwo ba” kallonshi tayi na wani lokaci kafin ta ce mishi. “Ban yarda da kai, gaya min me kuke shirya min.” “Yar kunama, Al’umma Charity House aka saka a kasuwa.” Wani irin shake wuyar shi yayi yana zare idanu. “Waye ya baku wannan shawarar?” Dakyar ya ce mata. “Sake min wuyata, wallahi kashi daya gare ki” sake shi tayi ya ce mishi. “Out zan sauya kaya.” Fita yayi ta cire kayan jinyar, ta sako riga da wando 3qrt. Sai farin shirt sai pink top da daura a saman rigar, gashin kanta ta daure da dankwali ta nufi kofar zata fita ta hadu da Dr Saddikah. “Mara lafiya ina zaki?” Wani kallon sama da kasa tayi mata, ta kalli black da yake gefe, cire glass din da yake sakale a aljuhun rigarsa tayi, ta dauka tare da toshe Idanunta ta ce. “na sallami kaina, tunda ba ajiyar dole” riko hannunta Dr Saddikah tayi tana faɗin. “kina jefa rayuwarki hatsari ki hakura a nima miki…” A hankali ta zame hannunta. “Tun daga haihuwata zuwa mutuwata, babu abin da Allah bai rubuta ba, so mazge babu abin da zai faru.” Ta wuce abin ta, tana murmushi tayi tana tafiya, hankalinta kwance. Girgiza kai tayi, tana tausayinta amma kwarin gwiwarta yana kara burge ta, koda yake yarinya ce har yau akwai Yaranta a kanta.

Shiga motar tayi tana faɗin. “Black babu wani abu a account ne, ina son a sauya mota nan.” “Akwai amma babu yawa, dake ance a sayar da kome za a miki aiki!” Ware idanu tayi ta ce. “Kambu! Lallai sai na zane kowa!” Kallonta yayi na wani lokaci kafin ya ce mata. “baki jin abu na zuba a hancinki ne?” Bayan hannunta ta kai ta goge hancinta. Jini ta gani tsaki tayi tana faɗin. “Habbo ne.” Dukar motarsu aka yi ta baya, ta buge kanta da karfen jini ne ya zubo daga kunnunta, ta rike kanta. Tana buɗe Idanunta dakyar. “Na mai da ki asibiti ne?” Girgiza kai tayi tana faɗin. “Mu wuce gida kawai” ta fada tana mai da kanta, saman kujeran. Har suka isa gidan tana goge hancinta. Wayarta ce tayi kara, ya duba. “Ke kin ce kina asibiti muna zuwa an ce an sallame ki.” “Eh na dawo gida ne!” Daga haka ta kashe wayar, tunda suka shiga cikin gidan, ta zubawa mutanen gidan idanun. “Me yasa zaku min haka? Ammyn!!!” Lekowa tayi ta ce. “Kai Black sai ka dawo da ita!” “Ai Hajiya ita tace na dawo da ita. ” “Tsoronta kake ji da zaka dawo da ita?” Kallonta yayi ya kalli Xnoo. A ranshi ya ce. ‘hajiya ko waye ya sha shaƙar Xnoo dan ubansa dole yayi abinda bai shirya ba.”

Fada Ammy ta mata sosai, ita kuwa ta kafe akan babu batun sayar da sayar da gidan, karshe yawan maganar da tayi yasa ta suma, sai da aka kira Dr Saddikah, tazo ta saka mata ruwa da allura, batun sayar da gida Zeeno ta rantse babu shegen da ya isa ya saya gidan matukar tana raye, da wannan suka bar zancen. Sai dare Mr Amjad yazo ya dubata, ya ajiye mata kudi sannan ya bar gidan, duk da tsoronsa kada Malik ya biyo shi ne. Babban burinshi dukiyar Malik Menk Jordan, shi yasa ya nace lallai sai Zeenobia.

Sai da tayi kusan wata guda a gida tana jinya, kafin ta koma aikinta.
Ranar Monday ta isa kamfanin da wuri, cikin nutsuwa ta nufi office din Mr Amjad, tana me gaishe shi, sanye take da white t, sai red top, da skirt black, iya gwiwarta, sai leggis da ta saka, kafarta wani hill ne black. Wuyarta ta nad’e wani dankwali multicolor, duk da bata yawan kwalliya amma yau tayi kwalliya har da lipstick red, kallonta yayi sosai, har ga Allah Yarinyar nan idan baka da imani ba zaka iya dauke kanka akanta ba, domin kuwa tana ji da kuruciya sosai. Tura mata file yayi ya ce mata. “Gashi nan!” Dauka tayi tana kallon file din, a hankali ta ce. “Na waye?” “Malik Menk Jordan!” A hankali ta bude file din Babu hoton kowa kamar yadda sauran ya kasance akwai hotunansu. Sake bude daya shafin tayi ya ce mata. “Elbashir Jamal Arab me kula da harkokin kasuwancin Malik kenan, hannun daman Malik ne, dole ki fara ganinshi kafin Malik.” Sake bude daya shafin gaba tayi ya ce mata. “Khamis Shatima, me kula da harkokin siyasar Malik ne, yana da kyau ku haɗu, idan baki samu ganin Elbashir Jamal Arab.” Shafin gaba ta kuma buɗewa. “Lalla Salmah, ita ce take control din duk wani sukar da Malik yake sha ta fuskar gwamnati, dole zaki iya haduwa da ita, kafin nan, sai kin zama daya daga cikinasu karfin arzikn, dole kiyi wani abu da zai fitar dake cikin al’umma ina bukatar bajintarki, duniya tana yin masu bajinta ne, ba tayi da lusarai ya kike tunanin ta ina za a fara?”

Shiru tayi, tana kallon shi kafin ta ce mishi. “Me zan iya yi anan?” Juya kujeranshi yayi yana faɗin. “Baki da wani hikima da basira ne, sai jagaliyancin? Zenobia wannan harkan kudi ne, kuma nayi ƙoƙarin a iso nan ne domin mu fuskanci wace ce ke? Zaki dakatar da fitowa na tsawon kwana biyu, domin ayi wani aiki. Akwai wani kamfanin mujalla na baazar zaki musu talla, a kasar Amurka.”

“Mr Amjad duk akan haduwa da Malik ne aka son nayi, duk wannan al’amarin?” D’ago kai yayi ya kalle sannan ya ce mata. “Idan ta kama ayi kisa don a hadu da Malik Menk Jordan zamu yi, amma ki saka a ranki, kamar ki zaki hadu da shi ne domin lafiyarki, don naji labarin ana bukatar miliyoyin kuɗi domin a miki aikin kanki. Idan kuma kina ganin haka ba zai yiwu ba, kiyi tunanin makomar gidan Al’umma Charity House mana zaki yi ko A’a……….?
*Hi……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[8/28, 2:22 AM] Maman Sadiq Da Khadijah:

Leave a Reply

Back to top button