Cinikin Rai Book 1Hausa NovelsHausa Novels

Cinikin Rai Book 1 Page 9

Sponsored Links

..9
Beauty and the beast.
Mai_Dambu🌚
<<<<<<<<<<<<|=|>>>>>>>>>>>
Yau babu editing

*Past*
After few hours.
“Alhaji Badaru Daniyal, shawara daya ja nisantatta da wannan garin, ka ɗauke ta kuyi nisa idan ya cigaba da zama cikin su, dole zata rikide irinsu, amma idan tayi nisa ga nan zata tashi da dabi’u na daban, sauya muhalli yana da muhimmanci da taka rawa a rayuwarta. Don haka a nisantatta da nan.” “Shi kenan likita zan yi yadda kika ce.”
Kasancewar garin da Keivroto city tafiya ce ta kilomita talatin ba kusa bane, haka yasa Alhaji Badaru Daniyal, ya yanke shawarar barin garin ya koma cikin Keivroto city domin zai yi kokarin fara sabon rayuwa. Haka kuwa ya faru, a daren ranar suka bar garin Jista, domin rayuwar Zeenobia da Abbas da a lokacin yake fama da matsanancin rashin lafiya na kai, domin tun yana cikin ya hadu da laluran sakamakon yar bashin da Alhaji Badaru ya ci, bai biya akan lokaci ba. Shi ne garin rashin mutuncin Wasim ya ture Ammy da tsohon cikin ta fado, karshe ta haifi yaron da juyayyen ƙwaƙwalwa. Kuma mahaifarta ta samu matsala, tun daga lokacin bata kuma samun ciki ba, amma zuwan Zeenobia sai ya maye musu gurbin rashin da suka yi, domin da zasu kuma haihuwa maybe su haifi me lafiya.

Fitarsu daga garin, Yan sanda da Wasim suka nufi gidansu. Babu su babu labarinsu, kuma basu fadawa mutane, haka suka yi ta bala’i.
——-
Dawowar Keivroto suka sauka a tsohuwar garin Keivroto, wanda a kai barshi mazaunin yaku bayi, duk da ba wani nesa yake da asalin sabon garin Keivroto city ba. Amma akwai banbancin rayuwa a can, a anan kowani mutum yana kokarin kyautata alaƙarshi da na kusada shi, banbancin da sabon gari, kowa rayuwarsa yake. Matsalar tsohon gari getto area ce, anan ma matattarar yan iska da yan jagaliya take. A hankali rayuwarsu Zeeno ya sauya domin kuwa babu ruwansu da wani tsoron ko zata koma wata irin mutum.
Dake Alhaji Badaru Daniyal, mutum ne da yasan kan kasuwanci, don haka da yar kudin hannunshi ya fara gwada sayar da kifin ice, Allah ya kuwa saka mishi albarka.
Ai ganin yana samu ya saka su a makaranta, ita da Abbas duk ba wani sakewa yake da yara yan uwansa ba, amma kuma yafi Zeenobia fahimtar karatu sosai. Domin ita abu daya yake tsayawa a ranta, shi ne taga yadda yan daba suke dabancinsu, burgeta yaƙe.
Alhaji Badaru yayi yayi amma yarinyar nan taki, shekaru uku da dawowarsu garin Keivroto tsohuwa. Tana da shekara goma cif a duniya. Aka turo ispetor Ayuba, kame a unguwar sakamakon cunen da aka yi musu wai akwai yan kwaya da masu safarar kwayoyi. A ranar aka yi wani irin kame har da wani matashi me suna Fa’iz. Kakar Fa’iz suna gida daya ne dasu Zeeno.asalima babu abin da ya aikata kawai kamen ne ya fada kansu, kuma a yadda suke jin labarin kashe su za ayi, Fa’iz yana koya musu karatu ita da Abbas.

A lokacin da labarin ya fito an rigada an bada umarni, daga fadar gwamnati. A lokacin babu wanda ya isa magana. Hakan su da Inna suka yi ta yawon bin ofishin yan sanda, amma babu labarin abin tausayi. Kusan sati daya ana niman inda suke amma babu labarinsu. Sai ranar takwas ana ruwan sama, aka kawo musu gawarsu, ganin yadda gawarsu ke zubda jini yasa Zeenobia ta yanki jiki ta fadi abin da ya faru da ita three years ago ya dawo mata, dole sai da aka kaita asibiti. Sai da tai sati biyu aka sallame ta, nan ma ta manta batun Iyayenta. Sai dai kuma abu daya shine mutuwar Fa’iz. Sosai ya tsaya mata a rai.

Gashi tana da saka abu a ranta, sai ta zama ciwon yana yawan tashi a kai, sai da aka mai da ita asibiti. Ba ƙaramin kokari Alhaji Badaru Daniyal yayi ba, kafin ta koma daidai, sai dai kin karatu ya sake zama a ranta. Shekarunta goma sha uku, ya saya musu wani katon fili. Inda aka fara ginin gidan sama me hawa uku, cikin farin ciki iyalan nan suka gina gidan domin sawwaka rayuwar talakawa, a madadin kudin me yawan gaske da zaka biya a shekara sai ka biya kadan sauran ka taimakawa gidanka, idan ka biya rabi saura zaka yiwa iyalinka hidima.

Sai da aka ɗauki shakara hudu ana ginin, a lokacin da aka kammala. Ginin a ranar wani abu ya faru, wanda ya saka yarinyar nan dawowa mara jin magana sama da shekarun baya. Ranar ana ta bikin murnar bude sabon gidan bakiɗaya alumma murna suke, domin sunan gidan Al’umma Charity House. Anyi shine domin mutane, marasa galihu da gata. Sai dai ranar a madadin farinciki, bakin ciki aka yi. Don kuwa ana cikin walimar bayan budewa aka kira Alhaji Badaru. Tunda ya fita ba a kuma ganinshi ba. Sai gawarsa aka samu. Wasim da goyan bayan Asp Ayuba sun kashe shi, tare da cewa yaci bashinsu ya kashe kansa.
Don sai da suka kashe shi, sannan suka rataye shi, wannan abin ya saka Ammy cikin shock. Kafin a bude gidan ana gobe kenan. Alhaji Badaru Daniyal ya tara su, lokacin Zeenobia tana wurin yan daban unguwar, sai da ya fita ya riko kunnenta. “Ayya Abba idan ka cire min kunnena da wanne zanji nasiharka, don Allah ka bar min kunne na!” Sai da ya kawo ta falo ya ce mata. “Zauna mara jin magana.” Kallon Abbas tayi ta ce. “Tow Abba ka aura min Abbas, sai na daina rashin ji kaji.” Ware idanu Ammy tayi, ta ce mata. “Allah na tuba, Baby ai kin fi karfin Abbas, shi ba irin Mazan da zaki iya xama da shi bane, sunanki yana tafe da tarihi, iyayenki sun saka miki suna me daraja, in Greek mythology language, ke mace ce da zata yi daraja, ba kananun mutane zasu same ki ba. You’re like Queen!” Gyada kai tayi, tana kallon Alhaji Badaru Daniyal yana kallonsu idanunshi cike da kwalla ya ce mata. “Ammynku zata baki takardu, nasan idan yana hannunki ba zai samu matsala ba, har da ta jinyarki, mun samu haduwa da Dr Saddikah, tace za a miki aiki. Amma nace a bari wata shekara lokacin kin cika shatakwas, ga gidan nan na dakunan sama baki daya nashi ne, shagunan kasa Kuma naki ne, akwai shaguna a kasuwa mallakar Ammynku ne, Zeenobia don Allah kiyi karatu ki nutsu, baki daya mutanen da suke wannan gidan, naki ne a kula da rayuwarsu, na baki amanarsu. Ki rike gaskiya da amana, kar ki sake ayi amfani da ke domin ruguza rayuwar wasu, naso nayi nisan kwana na ga yadda zaki zama the great queen Zeenobia Queen of Greek”

Yadda yaƙe musu bayani sai suka zuba mishi idanu, basu san dare yayi ba, sai da suka ji munsharin Abbas,
Har washi gari haka yake kafin mutuwarsa, lokacin da Zeenobia kamar gunki ta koma, bata da wani kuzari. Har aka sauko da gawar Alhaji Badaru Daniyal, gidan farinciki ya koma gidan Bakiciki da kuka. Har aka shirya shi babu wanda ya iya magana aka kai shi gidanshi na gaskiya. Ana tafiya da shi sai ga Yan sanda da Wasim da Asp Ayuba.
A lokacin tana cikin wannan yanayin, suka iso tare da fara surutun su fita su bar gidan na Wasim ne, duk maganar da ake Zeenobia tana kallonsu. Haka suka yi ta destroy kome na gidan, sai da suka kori kowa, ta shiga cikin gidan ta rufe get din gidan. Sannan ta d’ago kai ta kalli Asp ta ce mishi.
“Kuskuren da ka aikata yasa ina ta bibiyarka,amma nasan dole nasan wata rana zaka dawo, zan rufe tarihinku. Kafin yan jana’iza su dawo. Ban san kome ba amma na san Abba.” Dauko chain na karfe tayi ta shiga nad’e hannunta, hawaye na zuba mata, wani irin pain take ji mara daɗin misaltawa, gani take idan ta bude baki zata iya hàdiye su baki daya. Don haka ta shiga dukar, gashi a lokacin da ta rutsa su, babu bindiga, haka tayi ta dukar su, domin she is out of control. Sai ya kasance baki daya ta haukace dukansu kawai take tana hango Gara ta kashe su, wanda haka yasa kawai ta shiga shake su da Chain ɗin. Har suka mutu. Hancinta da kunnenta jini yake zuba. Faruwan wannan al’amarin ya ja aka tafi da ita asibitin mahaukata. Wanda Dr Saddikah ta amshi case. Ta cigaba da kula da ita, har zuwa.

Sai da tayi jinyar wata bakwai, a lokacin da aka yi binciken mutuwar Asp, mutane dayawa da aka bincika sun ce basu san me ya kashe shi ba, kuma hakan suka saka a ransu, musamman Innah da ya kashe mata jikanta, wannan dalilin yasa aka rufe mutuwar Asp da Wasim, babu labari ita kuma Zeenobia tayi jinyar wata bakwai a asibiti, kafin ta dawo da matsin lambar Ammy da Inna ta karasa makaranta, wanda daga baya ta fara diploma, shima wasa da shiririta ya ci karfin ta, jagaliyanci kawai da tsageranci yake damunta, kashe Asp ya saka ta samu girma da daraja da aka saka mata suna yar kunama, daga nan suka shiga harka da yan siyasa, babu ruwanta ta karya na karyawa, na bar su da jinya domin rokon da Ammy take mata na don Allah kada ta kuma kisa, yasa bata kuma.kisa ba, a wannan yanayin Abbas har ya shiga jami’a, dama kuma tafiyar karatunsu ba daya ba, domin yafita kokari da mai da hankali, saboda yana gane karatu. Tunda suka girma sosai, Allah ya daurawa Zeenobia kaunar Abbas, wanda ta kasa ganewa soyayyar aure ce ko soyayyar da iyayensho suka nuna mata ne,

Wani taro da aka yi na siyasa ta hadu da Mr Amjad, sakamakon sakata da wani dan majalisa yayi tayiwa wani mutum barazana, a inda ake taron. Haka yarinyar nan ta ratsa cikin mutane, ta riko wuyar dan siyasan.nan, ta ce zata kashe shi ta kuma jin ya soki lamirin wancan mutumin, wannan abin da tayi ya saka Amjad nimanta..ya kuma fara kashe mata kudi domin kudirin dake ransa.

Tare da bata shawaran tayi karatu domin zata ci gajiyar iliminta. Dakyar da sudin goshi ta gama, domin sai da Ammy da Inna suka yi tsaye akanta, shima ta gama da uban CO, a lokacin ita kanta tayi namijin kokari, take fada amma tabbas rayuwar da take bashi ne mafarkinta ba, mafarkinta yana can wani wurin.
*Present*
After 13 back.
“Dr Saddikah ba za a iya aikin ba ne yanzu? Yarinyar nan tana wahala, idan ta cigaba da zama haka zamu iya rasata!” Inji Ammyy.
“Ba aikin bane wahala, ana yin aikin ne a garin Michigan state, sune kawai suke da alhakin tab’a kanta, anan kuma ana yi a Menk Jordan World cares, shi daya ne s faɗin ƙasar nan, idan aka ce za ayi mata aikin ana bukatar miliyoyin kuɗi ne.”

Shiru suka yi, abin da yazo ran Ammyn gidan da suke zaune, a sayar da shi kadai a mata jinya, ta kare gidan na tsawon shekaru da amana, sai ta tashi za aji ta bakinta.
—-
Amjad.
Kiran wayar shi MD yayi ya ce mishi.
“Yallabai yarinyar nan tana samun takun saka da sabuwar yar sanda da aka kawo, me zamu iya mata?” Tsaki yayi ya ce.
“Kaji shaidaniyar yarinya ba, don Allah ka saka min idanu akanta, zata lalata min shirina ni da nake son a wanke min ita.”
“An gama yallabai ” ya kashe wayar, yana wurgi da ita, kafin ya mike yana me leka waje. Ko sati biyu bai yi da fara kwana a cikin gidanshi ba, tsabagen tsoron Malik Menk Jordan.
Sake labule yayi ya rufe yana ajiyar zuciya , kafin ya nufi uwar dakinshi.
***
Lalla Salmah.
Zaune suke suna cin abinci, kallon yarta tayi a nutse kafin ta ce mata.
“Princess, yau zan tafi ganawa da Malik Menk Jordan.” Sake spoon din hannunta tai, tare da ware idanunta.
“Maama da gaske? Zan bi ki please”
Girgiza kai tayi, tana faɗin. “Zan so haka, amma haduwar mu ba zai min kyau ba, shi mutum ne da baya bukatar ba zata, yana bukatar a sanar mishi kome kafin ya iso gare shi.”
Kwabe fuska tayi tana faɗin. “But me yasa?” “Ki shirya next week zaki tafi Demark wurin su Wahiba da Wahida, tare da Nadrah, ki kame kanki bana son zubda aji, ka da ki manta Nadrah Khamis Shatima har an saka ranar baikonsu da Malik yayi rejected ɗinta, and Malik yana bukatar macen da zata kula da Wahiba da Wahida ne, so ki kula da su. Domin mu samu Malik duk abin da kika yi matukar me kyau ne, zasu gayawa Malik. Kada ki sake Nadrah Khamis Shatima ta rena ki, kin ji ai? Domin Elbashir ya gaya min saura three months su gama karatu, and na shirya miki wani course na musamman, idan kuka dawo zaku sauka a gidan Malik ne, kada ki manta Malik yana cikin jerin members na PEL, na Europe. Iya wannan kawai aka ce ya mutu ya bar miki me kike tunani? And ki san yadda zaki nemi digital dinsa. Da zafi zafi ake dukan karfe. Babban burina na auri Malik na mamaye shi, amma samunki ya rufe min mafarkina, idan kika shiga zan miki bayanin yadda zaki yi da kowa……..
#MaidaLalla
#Nadrahshatima
#Zeenobiahadejia
#Malikmenkjordan

Leave a Reply

Back to top button