Cinikin Rai Book 1Hausa NovelsHausa Novels

Cinikin Rai Book 1 Page 21

Sponsored Links

CINIKIN RAI….21
Beauty and the beast.
Mai_Dambu🌚
Last free page
BOOK ONE

<<<<<<<<<<|=|>>>>>>>>>>
Shigowar Elbashir falon yana zaune a saman sofa, ya mike kafaffun shi yana kallon network news Elbashir ya ajiye mishi tap din a gabanshi.
“Malik sun gudu daga zarrar kuɗin!” Grape ya dauka daya ya saka a bakinshi hankalin shi yana kan tv ya ce mishi.
“Ita yarinyar ta sani?”
“Da alamu bata sani ba!”
“Rigimar shekaru arba’in ne ya dawo sabo fil.” Ya fada hankalinshi yana kan tv.
“Amma kamar babu ruwan, Khuldu Jahid Khan!”
“Da hannun shi mana!”
Ya d’ago kai yana kallon Elbashir, “ko kai ne ai zaka yi abin da ya fi haka.”
“Subhanalillahi, Allah ya min tsari da cin amanarka Malik gara naga mutuwata.”
“Hmm!”
Shiru suka yi, kafin ya sake murmushi yana faɗin.
“Yanzu ya zamu yi? Domin dai kasan kudina ba zai sha ruwa ba.”
“Duk yadda kace Malik haka zamu yi, domin nasan basu bar kasar nan ba. Idan kuma sun bar kasar tow ko suna teku ko suna bakin borda.”
Murmusawa yayi ya ce mishi.
“Yarinyar nan ta ce, wai ina fusace!”
“Sharrin kuruciya ce, baka fusace!”
“Nuratu ma ta gaya min shekaru goma sha takwas baya, ta ce ina fusace amma yanayina a sanyayye yake.”
“Allah ya mata rahama, kasan saura kwana biyu Birthday din yan biyu?” “Na sani!”
“Ka gayyato min yarinyar nan!”
“An gama Malik!”
“An gama kintsa min whiter town?”
“An gama Malik domin kome na cikin gidan sabo ne, idan baka manta ba kome da muka bari babu abin da ya samar.”
“Ina son gobe Keivroto tayi sabon bakon, a gyara min gashin kaina, ina son furfuran nan su fito da kyau, fuskata ta tara kasumba a gyara min ita, ta fito shar na dan samari. Domin bayan sallah Azhar nake son na dira a cikin birnin! Domin na nuna mata ni ba matsoraci ba ne!”
“Allah ya kiya shemu aikin danasani kai ba matsoraci ba ne, tsoro da kanta gudunka take!”
“Hmmm! Me ya bawa yarinyar nan kwarin gwiwa, ta gasa min bakar magana haka?”
“Haka take Malik, bata da kunya da d’a’a.”
Jinjina kai yayi yana faɗin. “Tabbas ba ga haka, naga wannan rashin da’a a cikin Idanunta. Zainabia!”
Girgiza kai yayi sannan ya ce mishi.
“Su shatima su same ni, a whiter town!”
“An gama Malik!”
Sannan ya fita, can sai gashi tare da wani saurayi, ya zo da wani akwati ya fara fidda kayan aikin, sai da ya fara mishi gyaran fuska, sannan ya rage mishi gashin kanshi. Malik baki ne asalin bahaushe wanda jinin hausawa ko nace kanawa yake gudu a jikinshi, sai dai ya biyo siffar Mahaifiyarshi dogo ne, me matsakaicin jiki.
Fuskar shi doguwa ce, wacce ta badawa hancinshi damar bajewa. Domin bai da siririn hanci, hancin a baje take yana da kakkaura leb’a. Ƙwayar idanun shi sak take da ta zakuna, kasancewar uwarshi baturiya ce, Malik yana da fadin kirji, sannan a murde yake sosai, domin ko ba a gaya maka ba, kasan yana cin karfe.
Dan kimanin shekaru hamsin da bakwai, yana da yawan suma sannan a tsaye yake kamar Superman ko Ironman.

Idanunshi manyan ne, wani lokaci da iya su yake barazana, Malik yana da zafi wanda matukar baka kasanshi ba, zaka zata irin mutanen nan ne masu sanyin hali.
Nan kuwa babban mugu ne me shegen bakin halin tsiya. Wani abun dariya shi baya boye furfuran shi.

★★★
Tun da ta koma gida, Shatima ya addabi rayuwarta da waya. Karshe turo mata text yayi.
*Ki dauki kirana!*
“Wannan tsohon da naci yake, da talauci ne da an shiga uku da shi!”
Ɗaukr kiran tayi, ta ce mishi.
“Meye zan maka?”
“Baby gani a kofar gidanku!”
“Eyeeee! Kace?”
T
“Eh gani a bakin get din Al’umma Charity House!”
Ware jdanu tayi ta ce mishi.
“Gani nan tow”
Ta fada a sanyayye, domin bata san da gaske zai zo ba, ta shi tayi ta nufi drower ɗinta, abaya ta ciro tana sakawa akan Bom short dinta, ta fito waje yana tsaye a jikin motar.
“Wai ba na gaya maka gaskiya ba, Ni fa ba zan auri tsoho ba. Gaskiya ni ko dating tsoho ba zan yi ba.”
“Ni kuma gani a gabanki, nazo da nufin soyayyarki.”
Dauke kai tayi kamar ta sake kuka, ta ce mishi.
“Ni gaskiya ka tafi ka da mutane su dauka.”
“Muje na saya miki ice cream!”
Kallon.shi tayi sannan ta ce mishi.
“Ai ni Allah bai daura min kwadayin abin hannu maza ba, jeka na gode.”

Duk yadda yaso yarinyar nan ta bashi hadin kai, fir taki har da koranshi ma tayi, da zai tafi ne, ya riko hannunta. Ya cusa mata kudi me yawan gaske. “Ki sha ice cream!”
Sannan ya bude motar ya shiga, ya ce mata.
*Ina sonki!”
Kallon kudin tayi a ranta ta ce mishi.
“Bana sonka”
Sai da ya bar gidan, sannan ta wuce dakin Inna da kawayenta, ta mika musu kuɗin.
“Ke yar nan! Ina kika samu kudi haka?”
“Wani tsohon najadu ne wai yana sona, ya kai shekaru sittin fa!” Ta ajiye musu tana faɗin. “gashi kuci goro.”
Daga haka ta bar dakin, sai Albarka sukae saka mata.
—–
Tun karfe hudu na asuba, office din yan sanda ya cika makil da yan kai kara, kan Asp kamar zai fashe domin tun kiran sallah farko, aka kira ta haka suka yi ta shigar da korafin akan Kamfanin Digital art, abin mamaki dayawansu Zeenobia ta kirawo su.

“Yanzu me kuke so na muku?”
“So muke a kama ta, ta fitar mana da kudin mu!”
“Ok sai ku bari gari ya waye!”
——–
09:30*
Na safe, watsa mata ruwa aka yi ta ware idanun cikin gajiya da son yin barci.
“Tashi ki bamu kudin mutane?”
Tashi tayi zubur, tana kallon Sajan Barau.
“Kudi wani iri?Ba yana kamfani ba”
“Idan kin tafi Office din CID zaku musu bayani!”
Zubur ta mike hango Asp Zulfa tsaye da wasu mata yan sanda.
“Kan Uba nice za ayiwa wannan rashin mutuncin!”
“Ku fita na sauya kaya!”
Ban daki ta shiga ta wanke fuskarta, sannan ta fito waje, bata tab’a sanin al’amarin ya wuce haka ba, sai da ta m dauki abayarta ta saka.

Sannan ta bi bayansu, haka suka sakata a motar yan sanda, suka tafi da ita. Har Office dinsu. “Ita ce…. Ita ce…. Ki bamu kudin mu!”
Kai tsaye office din Zulfa aka wuce da ita. Zama tayi tana dauke kai. “Meye hadaki da mutanen can?” “Na tuna su, amma ai kudinsu yana kamfanin S….. Digital art.”
“Ya zaki ji idan aka ce miki, ba kamfani ba ne. Yan damfara ne?”
“Kai haba, haka ma ba zai yiwu ba. Domin ni nasan inda Mr Amjad ne ba zai damfare ni ba ”
“Amjad Fahad Albagwi! Damfara a jinin su take, ya zaki confront mutane akan kudinsu? ”
“Kina nufin dama Amjad dan 419 ne? Lallai ma duk inda yake sai na zakulo shi wallahi!”
Kura mata idanu Zulfa tayi ta kira Sajan Barau, ta ce mishi. “Kaita filin nan”
Haka kuwa aka yi ya tisa keyarta da tare wasu yan sanda.
Latsa wayar Zulfa tayi, tana jan hancinta ta saka a kunne tana faɗin. “Yasir tarihi ya maimaita kansa. Abun da ya faru shekaru goma sha ya kuma faruwa da Babysister.”
Ta fada tana share hawayen da yake zubo mata. “My lady, ki bar kuka ba zasu ci banza ba, In sha Allah zasu shiga hannu. Basu san wannan karon sun tab’o kusar yakin ba ne, har yanzu bata gane ki ba?”
Hawaye ne sharrrrr ya zubo mata ta ce .
“”She lose her memory.”
“God! Yanzu ki kula da ita, wasu zasu iya bibiyar rayuwarta.”
“Ok Yasir”
“Love you!” Kashe wayar tayi, tausayin Zeenobia yana kara cika zuciyarta. Mikewa tayi ta wanke fuskarta, can suka dawo.
Idanunta ya kad’ a jajjur.
Zulfa ta ce musu.
“Sajan watsa min ita cell, dama ka mara jin magana kenan!”
“Ke yar sanda, kome lalacewar gawar Giwa tafi ƙarfin Allah sarki. Kuma baki san waye ya tsaya min ba a garin nan zaku sha mamaki!”
Tura keyarta aka yi cell din, kamar ta fasa ihu.
Har karfe daya na rana, ana rikici kuma abu yaki ci yaƙi cinyewa, don haka suka fara shirin kaita kotu. Sannan da gayya Zulfa ta hana belinta.
★★★
_A yau dai jami’an tsaron yan sanda, na garin Keivroto city sun kama daya daga cikin yan damfarar da suka damfari mutane kudi masu yawan gaske. Daga cikin su akwai yar kunama, yar daban da ta addabi rayuwar al’umma. Ita ce wacce ake zargin da janyo mutane cikin al’amarin._
Labarin da ya karakad’e ko ina, kenan labarin abin da ya faru. Shatima yana gidan Malik da ya iso tun karfe biyu, shi kuma ya isa gidan tun karfe hudu.
“Ikon Allah, yarinyar nan babu ruwanta.”
“Ai har da kudin Malik aka gudu da shi. Kuma munafuka ita ta zo da kanta!”
“Elbashir ka yi belinta!”
“”Malik!”.”kayi yadda nace!”
“Kudin da suka tafi da shi fa?”
“Kwandilata idan suka tafi da ita zasu dawo min da hakkina.”
“Malik ya zamu yi da ita a kawo ta nan!” Murmushi yayi ya ce mishi.
“Yanzu tana cikin alhinin abun da ya faru, ka bari a kwana biyu muga.”
Hankalin Shatima yayi masifar tashi, da sauri ya mike yana faɗin. “Malik zan dan fita, zan dawo an jima.” “Ok!” Elbashir ya ce mishi.
Da idanu suka bishi, kafin suka cigaba da abin da suke. Bai yarda ya tafi Office din yan sanda ba, sai da ya koma gida ne yayi ta Safa da Marwa dama dalilin Malik yasa taki yarda da shi, tow yaushe suka san juna?


Elbashir kuwa Office din yan sanda ya tafi sa lawyer din Malik, shi yayi magana da Zulfa. Sannan suka bada belinta gida suka tawo da ita.
“Zuwa nan da jibi Malik zai so ganawa dake!”
Bata iya magana ba, ta wuce abinta.
Koda ta shiga cikin gidan ruwa ta sakarwa kanta, haka kawai take jin ɓacin rai kamar zata yi hauka.
Haka aka yi ya zuwa mata Jajje, har ta kwanta, washi gari Shatima ya zo. Kamar ba zata fita ba, ta fito tana me sunkuyar da kanta. “Ban ji dadin abin da ya faru ba?”
“Ban san damfarar mutane zasu yi ba?”
“Mene ne alaƙarki da Malik?”
Kallon rashin fahimta tayi mishi.
“Ban gane ba?”
“Wacce alaƙa ce tsakaninki da shi?”
“Babu kome, sai akan kudin da ya saka hannun jarin.” Ta mishi bayanin abin da ya faru, shiru yayi yana kallonta. Amma kuma ta wani ɓangaren ta matukar burge shi, idan har ta iya yaudarar Malik haka, tow kuwa hanya me sauki ne ya yi amfani da ita.
“Ok zan tafi! Idan da wata matsala ki gaya min kafin a san abin yi” girgiza kai tayi tana faɗin. “Babu matsalar kome ”
Daga haka suka yi sallama,
Kwana biyu Zeeno ko kofar dakinta bata taka ba, sai washi gari ranar da zata hadu da Malik..
Kamar wacce ruwa ya mata duka, haka ta tashi, ta shirya wurin karfe biyu na yamma aka zo daukarta. Ta nufi motar aka nufi gidan Malik da ita.
A tunanin ta Waterfall zai kaita, sai aka yi rashin dace. Whiter town.

A lokacin da suka shiga cikin gidan, sai da ta rena kanta. A hankali suka yi ta ratsa get zuwa get kafin suka tsaya a wani katafaren apartment, fitowa tayi a sanyayye ta nufi cikin gidan, bisa jagorancin driven da ya kawota.
Malik yana zaune a falon tare da Elbashir, sai Shatima. Zama tayi tana me dauke kanta. “Sannunki sarauniya Zeenobia.” Inji Elbashir.
Bata tanka mishi ba, mikewa suka yi tare da barin falon daga ita sai Malik, aka shiga jero mata abincin.
“Sai kuma naji abin da ya faru!” Ruwa ta kurba tana faɗin. “Eh kasan dukiyarka bata da albarka.”
“Kada ayiwa dukiyata sharri dama, ai ba yau aka fara ba!”
“Kai ma kasan su ne?”
Murmusawa yayi sannan ya ce mata.
“Kici abinci, nasan har yau baki ci abinci ba.”
Murmushi tayi tace.
“Ina azumi!”
“Ok!”
Falon yayi shiru, kafin ya ce mata.
“Tun ranar da abin ya faru naso gaya miki sharadina! Amma kika ki tsayawa!”
Kura mata ido yayi yaga yadda fuskarta yayi, murmushi yayi sannan ya ce mata.
“Kin shirya amsar sharadina, ko kina da hanyar da zaki biya Ni kudina da na mutane?”
Kura mishi idanu tayi, ido cikin ido ta ce mishi.
“”Bani da hanyar da xan biya!”

Murmushi yayi sannan ya ce mata.
“”Zan biya mutane kudinsu nan da kwana uku, nasan shine damuwarki ko?”
Lumshe idanunta tayi ya bude, sunyi jajjur.
“Mene ne sharadinka?”
“Zamu yi cantract marriage na kudina!”
Mikewa tayi zubur kamar an jona mata wuta ……. Dandan-dandan……
Kashi a nan na gama book 1 free page…
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*

Leave a Reply

Back to top button