Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 8

Sponsored Links

 

📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

 

*SAKAYYAH*

_Page 8_

 

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

*Free page ne ƴar uwa in sun ƙare ko kinga littafin SAKAYYAH a a waje ba a cikin Groups na na SAKAYYAH ɗin da nabuɗeba, toh na satane kuma na Allah ya isane, kana na Yaseen doguwane😂 bulluƙutu kuma baƙar mutuwa… Dan haka biya ki karanta cikin Salamah yar uwa ba haƙƙin kowa kanki, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ki karanta abinki Nana lfy fata lfy*

 

Masu son kayan Ɗa’a akwaisu Available.

 

Motar tayo kansu gadan-gadan.

Aruɗe M Jameel yace.

“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n!Hasbunallahu wani’imal wakin!! A’a su waye wannan suna da hankali kuwa!?”.

Cike da al’ajabi Moddibo ya zuba musu ido tare da ƙoƙarin yiwa motar key sai kuma ya gaza yin komai ya zubawa motar ido ganin gada-gadan fa ta nufi kansu haiƙan ƙadaran.

 

Sai da motar tazo gab dasu sai kuma ta kauce ta hau titi ta wuce.

Wani irin nannauyan ajinyan zuciya mai masifan ƙarfin M Jameel ya dire tare da meda kansa ya jingina da kujerar.

 

Shi kuwa Moddibo Idonu ya tsirawa motar cike da mamaki sai kuma ya motsa laɓɓansa a saman lips ɗinshi ya furta.

“Wannan wani irin tuƙi ne?.

Tuƙin ganganci ne ko kuwa dai da nufi ne?”.

Dalilin da yasa ya tsaya ma atunanin sa ko ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne sai kuma yaga saɓanin haka.

Key yayiwa motar tare da kallon M Jameel dake lumshe da ido a hankali yace.

“J nayi zaton ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne ya biyo mu shiyasa na tsaya, amma inaga basu bane wata ƙil ɗan koyon tuƙi ne”.

Ya ida Maganar batare daya ɗauki abin da muhimmanci ba.

 

Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.

“Allah ya kyauta amma na tsorata da ganin yanda sukayo kanmu kamar da gayya suka yi sun tsinka min zuciya saura kaɗan fa su hau kanmu”.

Girgiza Kai Moddibo yayi kana yace.

“Da alama dai ‘yan koyo ne!”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da gyara zamansa, kana suka cigaba da tafiya.

Kai tsaye masallaci suka nufa kasancewar lokacin sallar Azahar yayi, bayan sunyi parking ne suka fito suka nufi cikin masallacin, aƙofar masallacin suka tsaya kusan tare sukay addu’ar shiga masallacin.

_“Auzubillahil Azim,Wabiwajhihil Kareem,Wasulɗanihil Ƙadiym,Minal Bismillahi Wassatu Wassalamu Ala Rasulullah.Allahummaftahliy Abwabal Rahmatik”_.

kana suka shiga.

 

Bayan sun idar sun fito daga masallacin M Jameel ya juya ya kalli Moddibo yace.

“Muje gida muci abinci”.

Da gefen ido

Moddibo ya kalleshi tare damotsa lips enshi  zaiyi magana.

M Jameel yayi saurin ɓata fuska tare da cewa.

“Ba zakaje ba ko?”.

Murmushi Moddibo yayi tare da juyawa akalar motar zuwa gidansu M Jameel.

Yanzu ƙira’ar Sheykh Jabeer suke saurara har suka isa.

 

Bayan sunyi parking suka shiga Babban falon gida Adining suka zauna sukaci abincin shikam Moddibo kaɗan yaci ya bari.

 

Miƙewa sukayi suka fita Fitowarsu daga falon yayi dai-dai da ƙarasowar Hajiya Karima wajen M Jameel yace.

“Aunty Karima ina yini”.

Ba tare data amsa ba ta watsawa Moddibo kallon tsana tace.

“Maƙale anzo kenan?”.

Cikin ɗan sakin fuska yace.

“Ehh”.

Cike da mamakin halayensa da ƙarfin halinsa tace.

“To wai kai dan Allah ka rabu da bawan Allah nan da dukiyar mahaifinsa mana ko zai samu yayi abin kansa!”.

 

Cikin takaici M Jameel yace.

“Dan Allah Aunty ki ƙyale Moddibo da irin wa’annan kalaman mana, na sha faɗa miki shi ba irin mutunen da kike zato bane, ta ya zan fahimtar da ke?”.

Baki ta taɓe tare da juyawa tabar wajen kamar zata tashi sama.

Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓaɓɓansa na ƙasa tare da kiran sunan Allah aransa.

Araunane M Jameel yace.

“Dan Allah Moddibo kayi haƙuri da abinda Aunty Karima keyi maka”.

 

Cikin kula Moddibo ya dubesa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma ƙasaitarsa yace.

“J.kada ka damu inda sabo ai yaci ace na saba da halin Aunty abinda tun tasowar mu a haka nake da ita abinda tun bamu wuce shekaru shida-shida a duniya ba take min, har yanzu da muka bawa talatin baya, ai ya zama man shafawa kawai dai abu biyu ke sawa ban taɓa yi mata wonkin babban borgoba”.

Ya ƙare mgn tare da nufar ɗakin M Jameel.

 

Cikin jinjina kai M Jameel ya bi bayansa  yana mai al’ajabi abinda Modiyke ɓoyewa tsawon shekaru da yake cewa dalilin dake hanasa taka mata birki, yayi ya gaya masa kuma sam yaƙi.

A ha dai suka isa, suna shiga ɗakin Moddibo ya kwanta bisa kujera tare da lumshe idanunsa alamun bacci zaiyi.

 

Acan gidansu Lamiɗo kuwa Mommy ce zaune yayin da Asma’u ke zaune daga ƙasa gefen ƙafafunta ta ɗago kanta tace.

Mommy asatin nan zamu koma makaranta gashi har yanzu Khausar bata dawo ba”.

 

“Wallahi kuwa gashi duk kwana biyun nan ba muyi waya ba, dan munfi sati da yin mgn”.

 

“Ayyah Allah Andi Meyesa”.

Cewar Asma’u

Kai Mommy ta jinjina tare da cewa.

“Kuma Idan ka kiransu ba zai shiga ba sai dai idan su suka kira ka”.

 

Gyara zama Asma’u tayi tare da cewa.

“Gaskiya Mommy Idan ta kira kice ta dawo tasan ana komawa za’a fara karatu gadan-gadan”.

Mommy tace.

“Inasha Allah zan faɗa mata”.

Daga nan sai suka ɗan ci gaba da hida, daga bisani sukayi

Sallama sannan ta tafi.

 

Acan Rugar Jauro Yaya kuwa yau sati da rasuwar Baffa Umaru baki ɗaya basu da cikakkiyar walwala duk da cewa sun dawo da sabgoginsu kamar da sai dai ciwon na nan aransu.

 

Khausar kuwa sosai tayi sanyi tun da akayi rasuwar bata cikin hayyacinta shiyasa bata samu ta kira Mommy ta ba.

Kasancewar jiya akayi adduo’ar bakwai Baffanta da yaransa duk sun koma bayan sunyi exchange na number ita dai ta Mommy ta basu. tare da yiwa Khausar al’ƙawarin kai mata ziyara wataran…

 

Anutse Khausar ta juya ta kalli Yaya Abba cikin sanyin murya tace.

“Ayyah yaya Abba dan Allah ka bani wayarka zan kira Mommy na”.

Kallonta Yaya Abba yayi cike da tausayi duk tayi wata iri yace.

“Toh shikenan amma ki bari sai gobe ki kirasu dan yau network bashi da kyau koda kin hau kan Bishiyar ma ba zaki ji magana ba”.

Kai ta gyaɗa masa kana tace.

“Toh Allah ya kaimu”.

“Amin”.

Ya amsa tare da miƙewa ya fita.

 

*GEMBILA*

Washe gari da safe tunda gari ya waye Malam Arɗo ke ta kiran wayar Moddibo awaya amma ba’a ɗagawa.

Shi kuwa Moddibo Anutse ya farka daga baccin daya koma tare da furta.

_“Alhamdulillahil Lazi ahyana bada amatana wa’ilaihil nushur”_

Wayarsa dake gefe ya janyo ganin Miss call ɗin malam Arɗo bar katai da yayi ne ya sashi ajiye wayar.

Kana ya miƙe ya shiga toilet.

Tare da addu’a a baki nai

 

Wanka yayi wanda ya ɗauke sa kimanin minti talatin kana ya fito yana mai faɗin.

_“Gufranaka”_

Suman kansa yake tsanewa da baby pink towel mai taushi.

Yayinda yake sanye da jibgegiyar bathrobe pink color mai masifar taushi wacce ya saƙale igiyoyinta a ƙugunsa.

A hankali ya zauna agaban dressing mirrow tare da,

Jona handdryer kana ya kunna tare da gyara zamansa da kyau bisa kujerar, dressing mirror ɗin tare da fara busar da sumar kansa mai ɗan karen sulɓi.

56 seconds yayi zuwa 1 minute yayi yana jujjuya kan handdryer ɗin tare da sa hannunsa ɗaya dake riƙe da madaidaicin Kum.

A hankali ya ajiye dryer din tare, da buɗe wani gora mai haɗe da man gashi na musamman, wanda Ummi ce ke haɗa musu, ɗan tsiyaya yayi kana ya murza tafin hannunsa tare da shafa.

Wani irin sheƙi da ƙyalli mai ɗaukan ido suman nasa ya farayi tare da fidda wani ni’imtaccen ƙamshi.

wani ƙum mai laushi wanda yafi na farin ya ɗauka tare da bin gashin nasa ya mishi tafiyar tsutsa,

Wow masha Allah, kamar saƙan taburma haka gashin ya kwanta da salo mai burgewa.

Goge tafin hannunsa yayi da towel ɗin dake bisa ƙafaɗarsa, kanaya

lakato lotion ɗin sa mai daɗin ƙamshi ya shafa jikinsa baki ɗaya.

idonsa ya lumshe tare da kauda kansa lokacin da yake shafawa cinyoyinsa mayin,

fuskarsa ya ɗan shafawa, mai ɗin tare da sa yatsarsa babba ya kwantar da gashin giransa na gefen dama, kana yasa babbar yatsar na hagu ya kwantar da na gefen hagun. sannan ya ɗan tsiyayi man kanshin ya shafawa tattausan sajensa dake kwance lip-lip ya shafa, wani irin sheƙi sajen keyi yana fitar da sanyayyan ƙamshi.

Anutse ya Miƙe ya buɗe durowarsa ya ɗauki jallabiyarsa mai masifar tsada da taushi Kalar Army green, kana ya zaro tattausan boxer and singlet farare ƙal-ƙal,

ɗan sunkuyawa yayi ya sanya boxer ɗin ba tare da kalli surarsa ba.

Kana ya miƙa tare da dai-dai ta zaman robor a gugunsa,

Bathrobe din ya kwance, kana ya saƙalashi bisa wata yar Kekkyawar masaƙali dake gefen drowersa, singlet ɗin ya saka, kana ya zira tattausar jallabiyar dake zuba sheƙi da ƙyalli wacce kai da ka gani kasan taja kuɗi.

baƙin hirami ya jawo, sanya kana ya naɗe kansa da hirami tare da sako jelar ɗaurin ta gefensa na hagu tsayawa yayi agaban Dressing mirrow tare da ɗaukar kwalbar turaren mai masifar ƙamshi ya feshe ilahirin jikinsa dashi wayarsa ya ɗauka tare da sanya wa a aljihun gaban rigarsa  kana ya fice.

 

A motarsa ya shiga bayan ya buɗe gate sannan ya fice kana ya sake fitowa ya rufe gate ɗin.

 

Aƙofar gate ɗin gidan Malam Arɗo yayi Hong mai gadi ya buɗe masa yashiga Babban gida ne sosai sai dai kallo ɗaya zaka yiwa gidan kasan mamallakin gidan mutum nai mugun maƙo da kirta babu wani fentin arziƙi ajikin ginin gidan haka zalika ginin ɗakunan single rooms ne cikin haraban gidan kuwa koda flow babu daga can kusan ƙaramin ƙofar da zai sadaka da cikin gidan rijiya ce babba anyi masa murfin ƙarfe fitowa Malam Arɗo yayi yana murmushi.

 

Ɗan guntun  Murmushin gefen baki  Moddibo ya mayar masa tare da cewa.

“Ina kwana Malam ɗazu ka kira ina bacci”.

Ya ida maganar yana shiga ɗakin ɗaya daga cikin matan Malam Arɗo mai suna Hajiya Zainabu domin Malam Arɗo ya ɗauki Moddibo tamkar jika.

 

Wara ido Moddibo yayi yana kallon Hajiya Zainabu yace.

“Hajiya ina kujerun ɗakin?

Indai ba kujera Ni gaskiya bazan zauna ba”.

Sai kuma ya juya tare da kallon Malam Arɗo yace.

“Malam dan Allah asamu kujeru saboda idan sukayi baƙi su samu inda zasu zauna”.

 

Hararansa Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Ba kai bane kake lissafin duk abinda zai cin yemin aljihu kasan yanda gyaran makarantar nan ya cinye min kuɗi kuwa?.

Yanzu ma abu biyune yasa na kira ka na farko motata ta ɓaci zaka kaini Rugar Jauro yaya sannan kuma  muyi magana akan ƙara kudin school fees ɗin yara dan gaskiya saina fanshe kuɗin dana kashe a school fees ɗin forko Aradun Allah.

 

Kai Moddibo ya jujjuya tare da yar kwaffa hana yace.

“Toh ba matsala ai ka’ida iyayen yara.

Yau kuma mai yasami motar ta lalace ne? Ko kuma sa maine bazaka iya ba”.

Yana mai laluben aljihunsa yace.

“Duka biyu, ta lalacen kuma yau du-du-du  da naira ashirin da biyar na tashi”.

Kai Moddibo ya sunkuyar yana mai kallon wayarshi yace.

“Kuma har ina Rugar Jauro Yaya yake da nisa ne!?”.

 

Da sauri Malam Arɗo Yace.

“Koma da nisa  kai zaka kaini dan badan ka matsa min akan gyaran makarantar nan ba da wataƙil in canza mota kuma da ko ban canza a ai bazan rasa kuɗin da mai ba”.

 

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Dama wataƙil ne Malam koba ayi gyaran makaranta ba da wuya ka canza wannan motar.

 

Dariya Hajiya Zainabu tayi tace.

“Aikam Moddibo ka faɗi gaskiya”.

Anutse Moddibo yace.

“Koma dai menene dan Allah Malam ayi ƙoƙari asa musu kujeru dubi fa ba laida ba Capet ba kujere ba tiles sai siminti kawai dan Allah ka daure kasamu tiles da kujeru”.

 

Murmushi Hajiya Zainabu tayi tare da yiwa Moddibo alamar jinjina da hannu kana tace.

“Allah ya maka albarka”.

Tayi maganar yanda Malam Arɗo ba zai jiba.

 

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.

“Naji wuce muje”.

Taɓe baki Moddibo yayi kana suka fita.

Ɗakin Uwar gidan Malam Arɗo suka shiga mai suna Hajiya Ramatu,

Kwance suka same ta akan faranda ta shimfiɗa ta burma.

Gefenta Moddibo ya ɗan zauna bisa dakalin dake mazaunin Mlma Arɗo cikin mutuntaka yace.

“Ina kwana Hajiya ya jikin?”.

 

“Da sauƙi Moddibo ya ƙoƙari?”.

Tace tana mai kallonsa, kauda kansa yayi tare da cewa.

 

“Alhamdulillah”. yana miƙewa.

Yace.

“Ai dole ma sanyi yata kamaku ba Capet ba kujeru asanyin garin nan kam dan Allah Malam asamu kujeru inba haka ba zasu ta cutuwa sanyi zaita kamasu sannan ya batun fitar da ita wajen?”.

 

Tsaresa da Ido Malam Arɗo yayi kafin yace.

“Moddibo! Moddibo!! Moddibo Kafita idona baka iya lissafin komai ba sai lissafin yanda za’a cinye min kuɗina ko”.

 

Shi kuwa Moddibo kai ya karya kana cikin sanyi yace.

“Ai gaskiya ne Malam ita lafiyar nan dole aneme ta”.

Harara ya galla masa tare da faɗin.

“Ai mun gama magana da Basiru na basa kuɗin da zai isa”.

 

Shi kuwa Moddibo kai ya jinjina yace.

Malam munyi magana da Basheer kuɗin ba zai isa ba Malam fita waje fa ba abune mai sauƙi ba”.

Saurin Kallonsa Malam Arɗo yayi yace.

“Na fahimta wato har ƙarana suke kaiwa wajenka to kaiɗin Ubana ne da zaka sani inyi!?”.

 

Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.

“A’a Malam niba Babanka bane ai shawara ce dai”.

 

Shi kuwa Malam Arɗo kai ya gyaɗa yace.

“Toh shikenan naji zanyi”.

Sallama Moddibo yayi wa Hajiya Ramatu sannan suka wuce ɗakin Malam Arɗo.

Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi yace.

“Ya batun ƙara school fees ɗin yaran nan?”.

Shi ma Moddibo Kallonsa yayi kafin yace.

“Malam duk gyaran makarantar nan da akayi a asusun makaranta akayi school fees ɗin yaran yayi dan angyara makaranta baya nufin sai anƙarawa ɗalibai school fees zaka kashe makarantar ida kuɗin yayi yawa”.

 

Baki Malam Arɗo ya cuna har Moddibo ya ida magana sai kuma yace.

“In kashe makaranta fa kace?

Bayan na gyara makaranta sannan kuma ga lafiyayyun malamai masu ilimi yara suna samun wadataccen ilimi ko za’a samu  ilimi abanza ne? zan ƙara school fees Tabbas zan ƙara”.

 

Murmushi Moddibo yayi yace.

“Toh shikenan kamar nawa za’a ƙara?”.

Sai asannan Malam Arɗo yayi Murmushi yace.

“Za’a ƙarawa ko wani ɗalibi dubu Ashirin”.

Wara ido Moddibo yayi yace.

“Innalillahi gaskiya Malam yayi yawa inma za’a ƙara ya kama dole to bazai wuce aƙara dubu biyar biyar za’a ƙara shima saboda za’a ƙara sabbin malamai ne da kuma sabbin tsare-tsare”.

Kai Malam Arɗo ya jinjina yace.

“Toh shikenan tunda ka matsa zan barshi ahaka”.

Zama Moddibo ya gyara yace.

“Akwai kuma maganar tafiya musabaƙa na gasar hadda da za’ayi za’aje Noka”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.

“Wannan ba matsala ashirya komai”.

 

Murmushin gefen baki Moddibo ya kumayi idanunsa akan Malam Arɗo yace.

“Eh badamuwa Malam wato tunda kasan wannan iyayen yarane zasu biya kuɗin motar da sungulla da komai”.

 

Dariya Malam Arɗo yayi yace.

“Atoh ainima dai ina ƙoƙari tunda motoci makarantar nanne ake tafiya dasu ko”.

Kai Moddibo ya jinjina yace.

“Ai Malam, Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”.

 

Cikin sanyi yace.

“Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta’aziyya to kaga motata ta samu matsala”.

 

Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin.

“Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala  muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace.

Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”.

“Amin”. Yace

Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke.

 

Moddibo kuwa ƙira’ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai ɗan nisa sukayi a haka.

 

Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin.

“Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”.

Murmushi Moddibo yayi yace.

“Uhum Masha Allah”.

Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah.

 

Suna dosan Rugar  Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa.

Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace.

“Kai Malam garin nan akwai sanyi”.

Murmushi malam Arɗo yayi yace.

“Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”.

 

Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi.

Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana  yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake.

“Subahanallahi”. Ya furta a hankali sabida tsarin garin yayi matuƙar ratsa shi.

 

Yaya Abba da shigowarsa kenan ya isa garesu tare da miƙawa Moddibo hannu sukayi musabaha kana yace.

“Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?”

 

Kai Moddibo ya gyaɗa da faɗin.

“Alhamdulillah”.

Kallon Malam Arɗo Yaya Abba yayi yace.

“Tsoho mai ran ƙarfe”.

Murmushi Malam Arɗo yayi da faɗin.

“Ya akayi ɗan saurayi”.

Cikin alamun sanayya yayi musu jagora, har cikin ɗakin Malam Liman.

Cike da mutuntaka daddataku Malam Liman yake musu marhabin da zuwa.

“A’a Malam Arɗo kaine tafe, sannu da zuwa, on laleko mon njabɓa ma mon laleko bagare”.

Sai kuma ya juyo ya kalli

Yaya Abba kana yace.

“Jeka kawo musu abin taɓa wa”.

Kai yaya Abba ya gyaɗa sannan ya miƙe ya shiga cikin gida.

Ba jimawa ya dawo hannunsa riƙe da Akwashi guda biyu akan faranti sannan ya koma ya sake ɗauko kofi guda biyu ya buɗe akwashin daya fi girma Gashesh-shen naman ragone da aka masa gashin ruwa ruwa yayin da ɗaya akwashin ke ɗauke da madaran shanu mai ɗumi Yaya Abba yace.

“Bismilla kuci”.

Bai jira jin mai zasu ceba ya miƙe yabar wajen.

 

Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi sakamakon ƙamahin naman daya ratsa hancinsa da kuma yanda gashin yayi kyau a ido da farko baiyi niyyan ciba amma ganin yanda gidan yake atsaftace da kuma masu gidan ga wani irin ƙamshi dake tashi yasa ya fara cin naman cikin nutsuwa tare da zuba madaran sosai yaci dan baƙaramin daɗi naman yayi ba, gashi dama baiyi breakfast ba.

Malam Arɗo ma sosai yaci sannan yasha madaran wanda shi kuwa kirtansa ke hamada ci sai yazo nan yake kashe tsatsan haƙoransa shiyasa ba cika fashin zuwa duk wata yana zuwa sai biyu.

 

Bayan sun kammala ne Malam Liman yashigo ya zauna daga gefen Malam Arɗo ya bashi hannu sukayi musabaha.

Malam Arɗo yace.

“Fatan mun same ku lafiya ya kuma muka ji da ƙarin haƙuri?”.

 

Kai Malam Liman  gyaɗa tare da faɗin.

“Hakuri mungode Allah”.

Malam Arɗo yace.

“Allah ya jiƙansa da rahma da kuma dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

ya amsa.

 

Shima Moddibo cike da girmamawa yace.

“Malam ya mukaji da haƙuri Ubangiji Allah ya jikansa da Rahman Allah ya haskaka makwancinsa”.

Malam Liman ya amsa da.

“Ameen”.

 

Baffa Liman ya kalli Malam Arɗo yace.

“Muje ka gaida Babbar Addarmu wacce take madadin mahaifiyarmu”.

Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.

“Toh ba matsala muje”.

Ya ida Maganar suna miƙewa.

Baffa Liman da malam Arɗo na gaba yayin da Moddibo da yaya Abba ke bayansu Moddibo na ƙarewa yanayin garin kallon sosai garin ya burgesa ko ina ka duba tsaf-tsaf babu alamar ƙazanta ko datti.

 

Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Hajja Nana lokacin tana zaune atsakar gidan kan ta burma.

Baffa Liman ya kalli Hajja Nana yace.

“Ga Yayana kuma ɗalibina yazo zai gaisheki”.

 

Tace.

“Ayyah sannunku da zuwa”.

Sannan ta miƙe ta shimfiɗa musu darduma dake tsaf dashi babu alamar datti ajiki komai na gidanta tsaf babu datti duk da stufanta amma komai nata tsaf yake.

Sosai garin da mutanen garin suka burge Moddibo komai na garin akimtse.

Gaisawa sukayi da Hajja Nana sannan suka yi mata ta’aziyya madara mai ɗumi tasa aka kawo musu. Koda sukace Alhamdulillah fir tace dolefa susha ita baƙo baya zuwa wurinta ya fita baici komaiba.

Madarar kawai Moddibo yasha kasancewar ya ƙoshi agidan malam Liman Aransa kuwa sai yaba karamci da dattakon mutanen yake.

 

 

Aɓangaren Khausar kuwa tana can rafi tare da Dije da Sadik sunje ɗiban ƙwan Zabbi da kuma kayan lambu dake hannun Khausar bayan sun gama suka fito kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace.

“Tunda wayar yaya Abba na hannu na zanje Bishiyar ƙare zancenka in Kira Mommy na”.

Kai suka gyaɗa mata da faɗin.

“Muje toh”.

 

Bayan fitowarsu daga gidan Hajja Nana Moddibo ya ciro wayarsa da niyyar kira sai yaga ba network kallon Yaya Abba yayi yace.

“Baku  da network ne?”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace.

“Eh bamu dashi amma akwai inda zaka samu idan kana da buƙata sai muje in kaika wajen akwai service ta nan nede babu”.

 

Kai Moddibo ya gyaɗa yace.

“Eh inada buƙata gaskiya muje”.

Sai kuma ya juya ya kalli Malam Arɗo da Baffa Liman yace.

“Bari zamuje ya rakani in sami network ina so zanyi kira”.

 

Baffa Liman yayi Murmushi yace.

“Yau ka shigo Rugar Fulanin da basu da network sai anje annema ko?”.

Dan murmushin Moddibo yayi tare da shafa sajensa zuwa gyamunsa daya ƙawata kyawun fuskarsa.

Malam Liman ne yace.

“Abba in kunje  ku karasa  cikin Rafi Modibbo  yayiwa Jauron garin nan ta’aziyya sannan kuce yazo munada boƙo ne”.

Jinjina kai Abba yayi sannan suka fita shi kuma Malam Arɗo da Baffa Liman suka wuce can gida domin ƙara karatu.

 

Suna fita Moddibo ya kalli Yaya Abba yace.

“Kai sanyin garin kun nan yayi yawa bari na ɗauki Jacket nasa”.

Ya faɗa tare da nufar motar ya buɗe ya ɗauki farin Jacket ya ɗaura akan Army green ɗin jallabiyarsa da yayi masifar yi masa kyau.

 

Murmushi Yaya Abba yayi Aransa yana yaba baiwar kyawunsa da kuma iya Dressing ɗin sa.

Ta cikin wata siririyar hanya dake ɗauke da korayen ciyayi masu kyau da ƙamshi suka ratsa.

Sai wani  lumshe  ido Moddibo keyi yana jin kamar ya tabbata awajen saboda yanda garin ya tsaru komai nasu mai kyaune.

Ta Cikin wannan Hanyar suka ɓulla har Rafi Yaya Abba nata yi masa hira shi dai daga Uhm sai Um-um saiko Masha Allah.

kasancewar sa ba mutum nai me surutu ba.

 

Suna shiga cikin Rafin Moddibo ya dunƙule hannunsa waje ɗaya jin sanyin wajen yafi na cikin garin juyawa yayi ya kalli Yaya Abba kana yace.

“Muma muna da sanyi amma sanyin ku yafi namu sosai”.

 

Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace.

“Sosai ma ai tanan kam munfi sanyi”.

Jinjina kai Moddibo yayi yace.

“To ku riƙa rage Bishiyoyi mana sanyin be damun ku?”.

 

Yaya Abba yace.

“Aikuwa mu munajin daɗin sanyin”.

Moddibo yace.

“Masha Allah”.

Acan cikin rafi kuwa Sadik riƙe yake da ƙwan Zabbi mai yawa yayin da Khausar ke riƙe da ma daidaicin kwando ahannunta wanda ke ɗauke da,Inabi,Tuffa, Mangoro,Abarba,Kwakwa, Lemo,da sauran kayan itatuwa yayin da ɗaya hannunta ke riƙe da wayar Yaya Abba tana dannawa Sadik ya juya ya kalleta yace.

“Khausar da kin haƙura da danna wayar nan sai mun tsallake wannan ruwan dake gudu kinga akwai duwatsu aciki”.

Still hankalinta na kan wayar tace.

“Kada ka damu ai ina kallo”.

Kai ya gyaɗa mata  sannan suka cigaba da tafiya.

 

Yaya Abba kuwa yana ƙoƙarin karya kwanar da zai sadasu da Bishiyar ƙare zancenka ya hango Baffa Jauro acikin Rafi juyawa yayi ya kalli Moddibo yace.

Gacan Baffa na Jauron garin nan da Malam yace mubiya kamasa ta’aziyya”.

 

Kai Moddibo ya gyaɗa yace.

“Toh mu ƙara sa”.

Kai Yaya Abba ya gyaɗa sannan suka nufi wajen Moddibo kuwa wayarsa ya ciro a aljihu yana duba ko akwai network ata wajen Dai-dai lokacin da Khausar ta iso wajen baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta nakan wayar tana saka number Mommy.

 

Kallon Dije Yaya Abba yayi wacce tuni ta tsallake ƙoramar ruwan yace.

“Dije har kun ɗebo ƙwoyin?”.

Kai Dije ta gyaɗa masa kana tace.

“Eh Ya Abba”.

Moddibo kuwa sam bai lura da mutum agabansa ba, ya ɗago ƙafarsa na dama zai tsallaka yashiga rafin kenan, ita kuma Khausar ta ɗago ƙafarta na hagu zata tsallaka tafita a rafin ji kake gub  suka bugi juna da ƙafafunsu.

Tagal-tagal Khausar tayi baya zata fadi yayin da shikuma Moddibo da ƙyar ya tsaida kansa daga faduwar da zai yi.

Ita kuwa khausar Atsorace ta saki kwandon kayan Marmarin dake hannunta  tare da kai hannu ta riƙe rigarsa da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke riƙe gam da wayar Yaya Abba.

A kuma lokaci guda ta rumtse idanunta tare da sakin kara.

Shi kuwa Moddibo cikin hanzari yakai hannu ya riƙota sai alokacin idanunsa suka sauƙa akan fuskarta ita.

Ita kuwa Khausar sassayan numfashi ta fesar jin an riƙeta bata faɗiba yasa ta ɗago kan  Idanunta ne suka sauƙa akan fuskar  Moddibo.

 

Lokaci ɗaya jikinta ya ɗauki rawa na tsananin tsoro da firgicin ganinsa kawai sai ta sake hannunsa tare da rintse Idanunta tayi baya zata faɗa cikin ruwan,Cikin zafin nama yasanya Lallausan tafin hannunsa ya riƙo hannunta tare da fisgota ta tsallaka sai yayi wucewarsa batare daya juya ya kalleta ba.

Ita kuwa khausar banda rawa babu abinda jikinta keyi cikin rawan murya tace.

Ka-ka-kayi ha-ƙuri ban gankaba shiyasa, shi kuwa Moddibo ko juyawa baiyi ba bare yaji abinda take faɗa yabar wajen.

Sai alokacin Yaya Abba ya lura da yayan itatuwan ta data zubar yace.

“Ya haka Khausar mai yasa bakya kallon gabanki in kina tafiya?”.

Cikin rawan murya tace.

“Tsautsayine”.

Tafaɗa tare da barin wajen aranta kuwa tunani take yau kuna Moddibo Arugar mu me ya kawo sa? kuma mai ya haɗa sa da yaya Abba? to me ya zoyi? da wannan tunanin ta isa Bishiyar ƙare zancenka tana isa ta hau kan dutse. dake farko ta zauna tare da sa hannunta ta riƙe reshen, kana ta kiran number Mommy.

 

Shi kuwa Moddibo bayan sun karasa wajen Baffa Jauro.

yace.

“Ina yini Baffa fatan mun same ku lafiya ya kuma ƙarin haƙuri?”.

Baffa Jauro kuwa cikin yanayin sauƙin kansa da kuma dattako ya amsa da.

“Haƙuri Alhamdulillah fatan kunzo lafiya?”.

Moddibo ya amsa da. “Lafiya Ubangij Allah yajiƙan sa da rahma idan kuma tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani”.

 

Baffa Jauro ya amsa da.

“Ameen”.

 

Yaya Abba ya kalli Baffa Jauro da faɗin.

“Bari muje na rakasa Bishiyar ƙare zencen ka kuma Baba Yace kaje tare suke da Malam Arɗo”.

Kai Baffa Jauro ya gyaɗa kana yace.

“Adawo lafiya”.

Miƙewa sukayi suka nufi Bishiyar ƙare zancenka tun kafin su isa Moddibo ke jiyo suturatai da dariyar mutane Aransa yace to lafiya dai.

 

Suna ƙarasawa yaga tsoffi,Matasa,maza,da mata kowa maƙale da waya akunnensa ahankali kunnuwansu ke jiyo masa kamar sautin Muryan Khausar da mamaki ya ɗaga kansa gefen yamma idanunsa suka sauƙa akanta saman dutse kana kanta na bisa reshen Bishiyar.

Aransa yace to ashe ga inda ta samo ɗabi’ar hawa bishiya wato garin ne dole sai akan bishiya ake waya wannan shine gado.

 

Ya juya tare da kallon yaya Abba yace.

“Dole sai na hau kan Bishiya zanyi wayar?”.

Girgiza kai Yaya Abba yayi yace.

“A’a ko akan dutsen ma zaka samu network”.

 

Jinjina kai Moddibo yayi yace.

“To ku maida ƙa’ida mana mata su hau kan duwatsu maza su hau kan Bishiya idan ya kama dole ne sai an hau kan Bishiya ko kuma ku maida lokacin yin wayar mata daban lokacin yi. Wayar maza da ban kusa tsari da ƙa’idar musulunci ku dena gwamutsuwa haka”.

Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.

“Gaskiya ne kabamu shawarar data dace Insha Allah za’ayi haka zan faɗawa Baffa Jauro ayi haka”.

 

Moddibo kuwa cewa yayi.

“Ai ya kamata ayi haka yanzu Meye amfanin ga mata asama sannan ga maza aƙasa ko kuma duk suna gwamutse maza da mata ko da duk kan ku ‘yan uwane ai yakamata ayi abu duka bisa tsarin Addini ko ba haka ba bai dace ba duk da cewa yawancin ku ’yan uwane amma akwai auratayya atsakanin wasu”.

 

Cikin jin daɗin Nasiyyar da ya masa da gamsuwa Yaya Abba yace.

“Hakane Insha Allah za’a gyara malam”.

Ita kuwa khausar sam batasan Moddibo sun zo wajen ba.

Bayan sun gama gaisawa da Mommy.

Mommy tace.

“Khausar kwana biyu baki kira ba kuma kinsan ba zai yiwu na kira kiba”.

Araunane Khausar da mutuwar Baffa Umaru ya dawo mata sabo tace.

“Mommy ankashe Baffa Umaru har gida aka kashesa Mommy agaban idanuna aka kashesa!”.

Shi kuwa Moddibo hankalinsa na kan yiwa Yaya Abba magana bai san mai take faɗa ba juyawar da zai yi yaji tana cewa.

“Mommy har anyi sadakan bakwai hankalina ne bai kwanta ba”.

ta faɗa hawaye na zuba daga idanunta.

Shi kuwa Moddibo ido ya zuba mata ganin yanda hawaye ke kwaranya daga idanunta.

Khausar tace.

“Mommy ai zakizo kiyi mana ta’aziyya ko?”.

 

Mommy da mutuwar ya kashe mata jiki tace.

“Insha Allahu zamu zo, nasan idan na faɗawa Abbanki ba zai hana ba, ki shirya idan nazo zamu taho tare, dan Asma’u tazo tayi min magana batun zaku koma makaranta, kishirya kayanki idan muka zo zamu tafi tare idan Hajja Nana ta yarda”.

 

lumshe Idanunta tayi tace.

“Baza ma ta hana ba Insha Allah idan kunzo zamu tafi tare dan dama tace zanje Ɓadamaye wajen Baffa na nacan kuma sunzo ta’aziyya mun haɗu dasu, sannan ma Addata Ikki tazo mun haɗu da ita sai wani lokaci zanje Ɓadamaye nama karɓi number su, suma sunce dan suna sauri ne kuma mun haɗu amma da zasu je su duba ni anma munyi canjin number”.

 

Cikin sanyi Mommy tace.

“Toh shikenan babu damuwa ki shirya idan nazo zamu taho Insha Allah gobe zamu zo ta’aziyya”.

Sallama Mommy ta mata.

Juyawar da zatayi Idanunta suka sauƙa akan Moddibo daya tsareta da ido saida ta kusa faɗuwa saboda tsoron ganinsa.

Da ido ya mata alamar  ta saƙƙo kafin ƙiftawa da Bismillah kuwa ta diro ƙasa.

Kallon Dije dake jiranta tayi tace.

“Mu tafi”

Yaya Abba ya miƙa mata kwandon kayan Marmarin ta data zubar yace.

“Gashi kin zubar dasu na ɗebo miki”.

 

Kamar wacce aka fisgo maganar daga bakinta tace.

“Banaso ka bashi na bashi”.

Sai da ta rufe bakinta asannan ta tuna mai ta faɗa hannu Dije ta fusga tace.

“Mutafi”.

Shi kuwa Yaya Abba gyara riƙon kondon yayi.

 

Shi kuwa Moddibo ɗaya daga cikin duwatsun wajen ya samu ya zauna tare da kiran wayar M Jameel.

M Jameel na ɗagawa Yayi Sallama.

Amsawa Moddibo yayi tare da faɗin.

“Kada kaje kata nemana nasan zaka ne meni bana nan sannan ka kira wayata kaji akashe ina wani ƙauye ne da mukaje da Malam Arɗo amma Insha Allah zamu dawo kafin Azahar”.

M Jameel yace.

“Toh meyasa baka gaya min ba tun ɗazu”.

Cikin yanayin shaƙuwa yace.

“Nima zuwan ba zata ne, kuma lokacin nasan kana bacci”.

Cikin sauƙe numfashi M Jameel yace.

“Toh badamuwa Allah ya dawo daku lafiya”.

 

“Ameen”. Yace tare da katse kiran.

 

Bayan ankira sallan Azahar sun idar kai tsaye wajen motarsu suka nufa Yaya Abba ne ya zo ya miƙa masa kwandon kayan Marmarin da Khausar tace abashi.

 

Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyin murya sa yace.

“A’a Nagode amma ka ajiye awajenka”

Murmushi yaya Abba yayi yace.

“To ai bani ce na baka ba Khausar ce tace abaka”.

Yana gama faɗa ya buɗe bayan motar ya saka masa.

Malam Liman ma ya basu Zabbi Baffa Jauro kuma ya aiko musu da ƙwan Zabbi Hajja Nana kuma ta aiko musu da zuma sannan suka yi musu sallama suka tafi Moddibo kuwa yaba karamci ci halaccin mutanen sukayi.

 

Suna shiga cikin gari ya wuce da Malam Arɗo gidansa ya ajiye sa sannan ya sauke masa ƙwan Zabbin da kuma Zabbin da goran zuma.

 

Malam Arɗo yace.

“Ka ɗauki Zabbin da kuma ƙwoyin mana”.

Kai Moddibo ya girgiza yace.

“A’a wannan zumar ma ya isheni”.

Ya ida maganar tare da jan motar ya fice zuwa gidansa.

 

Acan ɓangaren Mommy kuwa da daren ta samu Lamiɗo ta faɗa masa maganar rasuwar da kuma son zuwanta suyi ta’aziyya, Cikin jimami yace toh Allah ya kaimu gobe zasu zo.

 

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

 

_Ina kuke Ma’aurata masu sha’awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau’ikan sirrin sahihan magungunan ma’aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki…Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba’a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al’khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni’ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni’imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu…Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu’umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba…._  _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan  Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu’uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)…Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji  Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu’uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa ‘yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma’aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba’a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma’aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah ‘yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci…._

 

 

 

🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,

 

Washe gari Da safe suka ɗauki hanya zuwa Rugar Jauro Yaya sukayi ta’aziyya.

Bayan sun gama gaisawa ne Mommy tace.

“Hajja Nana zamu koma da Khausar dan gobe Insha Allah zasu koma makaranta”.

 

Kai Hajja Nana ta gyaɗa dan mutuwar ƙaninnata yasa tayi sanyi baki ɗaya.

Tace.

“Badamuwa ku koma da ita amma idan an kwana biyu ta riƙa zuwa saboda su saba da ‘Yan uwanta”.

Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.

“Badamuwa Insha Allah zata zo”.

 

Kasancewar dama Khausar ta haɗa kayanta tun daren jiya yasa ta dauko jakarta sai kuma ta Rungume Hajja Nana tace.

“Hajja Nana zanyi kewarki ki riƙa zuwa bishiyar ƙare zancenka kina kirana dan Allah”.

 

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.

“Sai kace kin damu dani bayan rashin kunya kike min”.

ƙaramin bakinta ta tura tare da ficewa tana cewa nidai zanyi kewarki.

Baki ɗaya Kakannints suka rakata jikin mota bayan sun haɗa mata tsaraba iri-iri Kama daga, Zabbi, Kaji, Ƙwan Zabbi, Nono jarka-jarka da kuma zuma man shanu.

Kawai sai Khausar ta fashe da kuka cikin raunin murya.

Tace.

“Aranan da nazo kamar haka da Baffa Umaru aka tareni yau kuma gashi babu shi!”.

Hannunta Baffa Garga ya riƙe cikin rauni da zuba hawaye yace.

“Kiyi haƙuri Khausar haka rayuwar take idan kaini yau gobe ba kai bane, kuma in sha Allah zasuga SAKAYYAH”.

 

Hawayenta ta share tare da shiga mota tana ɗaga musu hannu Dije ma kan sosai tasha kukan rabuwa da Khausar.

Fatan sauƙa lafiya suka musu sannan suka ja motar suka tafi.

 

Khausar kuwa motarsu na isa harabar gidan Haiydar, Raudat da Ramadan suka taho da gudu suka rungumeta Ramadan ne yace.

“Addah Khausi nayi missing ɗinki”.

Kansa ta shafa tare da cewa.

“Nima nayi missing naku”.

 

 

“Addah Khausar Barka da dawowa daga zuwanki har gidan yayi haske, amma da bakinan duk saiyayi duhu”.

Cewar Haiydar

Ta wani wara manyan Idanunta tace.

“Kada kayi masu gidan suji”

ta faɗa tare da ɗaukar Ramadan suka shiga ciki afalon suka zube suna ta hiran bayan rabuwa.

Cikin sakin fuska Khausar ta kalli Raudat dake zuzzuɓura baki tace.

“A’a My happiness sis ya akayi ne?”.

Baki Raudat ta kuma turawa tare da cewa.

“Ba wani ai naga kinfi son Ramadan”.

Dariya mai sauti tayi tare da jawota ta ruggumeta.

Kana suka ci gaba da hirar yaushe gama. sallah kaɗai ke ɗagasu.

 

Bayan kwana biyu ya kama yau Asabar zasu koma makaranta kasancewar Asabar ne farkon satinsu Alhamis da juma’a kuma Weekend.

Tun wuri Khausar ta tashi bayan ta idar da sallar asbah tayi Azkharul sabah toilet ta shiga tayi wanka kana ta fito ta zauna gaban dressing mirrow ta shafe jikinta da lotion ɗinta kana ta shafa kajol a manyan Idanunta masu haske sai kuma ta shafa lips dinta Kaɗan tulin sumar kanta dake tsefe ta sanya farin Ribont ta kama ahankali ta buɗe duro ta ɗauki uniform ɗin ta dake goge maroon din wandon ta fara sanya wa sannan tasa ka farin riga sai kuma ta ɗauki farin ɗankwali ta ɗaura kana ta ɗauki maroon din hijab ta Sanya Wanda ya tsaya gwiwarta wani irin kyau tayi na ban mamaki sosai Uniform din ya amshets tamkar dan ita akayi.

A gaban Dressing mirrow ta tsaya ta ɗauki kwalban turare sun kai kala biyar ta feshe ilahirin jikinta dashi sannan ta ɗauki combos Fari ta Sanya tare da ɗaukar school bag ɗinta ta rataya kana ta fito falo.

 

Murmushi Mommy tayi tace.

“Manana kinyi kyau”.

Ta juya manyan Idanunta tace.

“Nogode Mommy na”.

Haiydar kam murmushi yayi yace.

“Yau za’ayi ruwa da ƙanƙara shugaban ’yan letti ta riga kowa shiryawa”.

 

Harara ta maka masa batare da tace komai ba ta shirya Raudat sannan sukayi Breakfast suka shiga mota Amina sai Harara take watsa mata ita kuwa khausar bata ma san tana yiba domin aƙasan ranta tunanin haɗuwarta da Moddibo take da kuma irin hukuncin da zai yanke mata.

 

Suna isa Makarantar lokacin har anfara shiga class cikin sauri sauri Khausar ta riƙe hannun Raudat suka nufi side dinsu Raudat ta ajiyeta a class kana da sauri ta juya, zata fita class ɗin kenan.

Taji Raudat ta saki ƙara tare da kiranta.

Da sauri ta juya tare da kamo Raudat ɗin da taga tana jujjuyawa, tsugunawa tayi tare da cewa.

“Raudat menene ya faru”.

Cikin kuka da yarfa hannu Raudat tace.

“Wayyo idona Adda Khausy ido, borkono”.

Da sauri ta jawota tare da fara hura mata idon.

Sai kuma ta amshi goron ruwar da Antin su ke miƙa mata.

Wonke mata fuskar ta ta farayi tare da murza mata idon.

Cikin Sa’a kuwa ɗan abin da ta shiga idon ya fita.

A hankali ta buɗe idann nata, da tuni yayi jazir.

Cikin sanyi  tace.

“Ayyah Raudy na sannu ko, yanzu dai ya fita ko?”.

Kai ta gyaɗa mata tare da kama hannun Antin nasu.

Ganin hakane yasa Khausar juyawa da sauri ta fito ta nufi harabar makarantar.

 

Shiru ba kowa a tsakiyar harabar alamun  an gama shiga class kenan.

 

Cikin sassarfa ta fito daga side din ’yan nursery.

Kana ta nufi sude ɗinsu.

 

Da sassarfa ta nufi  kan step ɗin.

Dai-dai lokacin kuma  Moddibo ya fito daga class dinsu  ya nufi ƙasa, a hankali yake take steps din yayinda hankalinsa baki ɗaya yana kan….!

 

 

 

 

Ki biya ki karanta, kiji ainin manufar labarin kiyi dariya kiyi shauƙi kibi haushi kiki tausayi kiyi kuka. Kiyi murmushi

 

 

 

 

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button