Harijin Namiji Complete Hausa NovelHausa Novels

Harijin Namiji 1

Sponsored Links

*HARIJIN NAMIJI*
(Bastard b*tch)
1️⃣

By
Oum Aphnanuwa
Hassana Bamalli is a Nurse, a sole proprietor, a teacher ,an activist and a writer ,with several years experience.she specializes in Personal growth, Couple appears and health topics.when she is not working in the hospital or writing a pitch , she is volunteering in the NGOs,she is a believer in using short term goal to achieve big dreams…display her experience to this book will make it baghamm…lolx

___________
Tallah!!!
Magani da kofi☘️
Ana yi ana siyan magungunan Alheri asha magani a burge miji yayi kyautan fisabilillah ,masu son siyan maganin da zaisa ki kece raini wajen mai gida tayi magana ma wannan Number 08139762831
______________
Bissmillahir rahmanir raheem

Kano,Nigeria
Gidan direbobi

Uwale tsabagen dariyar ƙeta har tana burgima a dandaɓaryar ƙasan tsakar gidan ,batareda ta damu da muɗuɗɗukewar da zata daɗa yi cikin dattin turɓayan ba…dafe da cikinta take dariya idonta kace kace da hawayen dariyar ƙeta haka take nuno Hausi da yatsa

“Hehehehe wallahi haka Hausi take barci kamar matacciya har a yankata ai fawanta bata sani ba ”

Hausi marairaice fuska tayi “Wallahi na ɗauka audu ne mijina ya dawo aiki ina barci , saida naji lugiguitan tayi yawa na san audu bazai dinga tanɗeni haka ba Yoo ina ma ya iya! ,shine fa a magagin barci nakai hannu na fara laluben fuskarsa don in tantance ,kawai hannuna sai ya sauka a turgujejen gashin gemun nan nasa,kai da ka gani ba ya tarashi don ɗabbaƙa sunnah bane sai don iskanci.
Shine fa,yina jin na farka ya tsere ,kuma wallahi ko kaffara bazanyi ba Ali ne ya shigo mun ɗaki jiya da daddare🥺”

“Hhhh kai Amma dai Ali anyi bunsuru ya rasa wanda zaibi sai Hausi yina laluben nonon da yara takwas suka jaaa..🤭😁”

Banka mata harara tayi “Yoo a haka dai mazan mu suke zaune da mu suke fake dare”

Saratu dake zaune acan gefen tana saƙan hula da kwarashi ,cikin takaici ta ɗago tanabin taron matan gidan da sukayi dandali ƙarƙashin bishiyar Mangoro da dalbejiyan dake tsakar gidan kusan su goma sha… Kowa tana jinta daƙa daƙa cikin koɗaɗɗun zani ,yaran hannunsu ma haka ,fuska duk kwantsa hanci duk busashen majina,kusan ƙarfe sha biyun rana babu mai aniyar wanke yaronsa bare ya wanke dattin jikinsa sai gulma da tsugudidi in suna cikin hiran wacce ta soma tashi topah za’a dasa gulmar ta .

Cikin takaici saratu ta girgiza kai “Wohoho ni saratu wannan rayuwa ina zaki damu ? Gidan yawa bai yi ba wallahi ….haba gida ga talauci ga ƙazanta ga rashin ibada gamsashiya ga cin naman mutane ta ina za’a cigaba a haka? Basu da aikin yi sai cinikin maganin mata In sun yi dandali komin kiran sallah ba wacce zata miƙe to ta ina zata sa yaranta suyi?”

Muntari yaron hausine da bai wuce shekaru takwas ba ya shigo gidan da gudu yana Gara taya duƙun sauƙin dashi baida banbanci da Almajiri

“Ɓiyyyy ba burki yaseen ba burki” haka ya falfalo da tayan da gudu kafin kace me ? Sai a fuskar saratu . Da azama saratu ta mike tana salati hannunta dafe a kan idonta

“Muntari kai dabbane ?…” yaron motsi da baki ya somayi yina shirin bata haƙuri uwarsa tayi maza ta karɓe zancen

“A’ah ban haifi dabba ba ,kar in sake ji ,gakinan babban dabba . ba cas Ba ass ,a gashe ba Mai a dafe ba Romo ansha Boko har an digiloma (Diploma) an raina mazan Allah da Annabi ,anki aure ana jiran masu jif sukuma ba saoin mai dattin hula bane ba(baban ta) kinga kuwa zaman gida yanzu kika soma kuma dole kici hakurin zama da yarorin mu….aha ki barsu su sakata su wala ga filin tsakar gida nan tata yaro Gara taya wainashi sosai inga ƴar (kaza kazan ) da zata taɓaka” ta ƙare zage zagenta tana dukan zani

Ƙanƙance ido saratu tayi cikin ɓacin rai “Kina nufin goyon bayan ɗan ki ,kikayi ya raina babba?”

Karaf Rashida ta saka masu baki “Yoo waye babban? In Bata goyi bayan danta ba so kike ta zura ƙibla ta bari ki jibgar mata ɗa?…”

Tasalla ma tsalle tayi ta dire a gabanta “To munji ta tare ma danta amma ai muntarin bai ce maki komai ba ,ko yace? Amma ke kuma fa ,sa’ankice ita da kuke misayan miyau?”

Haka gabaɗaya matan gidan sukayi mata caaa kamar zasu daketa,Hayaniyarsu ya fito da baba lantana daga ƙuntataccen ɗakinsu saratu falle ɗaya an sakaye ƙofar da wani irin tattararren labule .

“Yakinan saratu ashe ba na hanaki tanki in tanka da matan gida ba?”

Kasa bata bayani tayi kawai sai ta sunkuyar da kai hawaye na gangara mata a ido ,ba taron dangin da sukayi mata yafi ƙona mata rai ba irin gorin aure! Kwata_kwatana shekarana nawa ne? 22 haba!.

Tausayin saratune ya daɗa narkar mata da zuciya “Kiyi hakuri wata rana sai labari , inshallh bazasu ganki ba ma”

“Sannu kisini! Uwayen kisisina , labarin ma ai baza ayi ba”
Sosai saratu ta sake hassala da maganar Hausi ,abun ya wuce kanta ya kai ma innanta? ,Haɗiye fushinta tayi tazo ta raɓa ta gabanta zata wuce .

Kawai sai Hausi ji tayi an bata tauuuu!

Ƙara ta fashe dashi ta riƙe kuncinta da sauri,jiri na hajijiya da ita, jini na malalo mata ta hanci ,tsabagen zafin marin ya sata zuba wawan haɓo (Epistaxis a likitance/ Nose bleeding)

“Lalalalaaa😯bala’in nan ,yanzu kaurin wuyan naki saratu yakai ki ga marin matan Audu?”

Saratu da har ta gifta su ta juyo a mamakance,jin ƙazafin da ake ƙoƙarin manna mata

“Haba uwale wani irin mari?…” kasa ƙarashe maganarta tayi ganin Hausi cikin mawuyacin hali.

Durƙushewa a ƙasa saratu tayi ta daura hannu aka ta kwantsama ihu “Wayyo Allah na shiga uku Ni yaushe na mareta? Jama’a kunga na mareta wallahi ban mareta ba”

Uwale wani irin kukan kura tayi ta fizgo saratun ta daddage ta ɗauketa da mari ,dummmm! Saratu taji kunnenta ya doɗe na wucin gadi ,idanuwarta sun shafe ta daina gani dasu sai kawai ta soma ganin taurari masu hasken gaske ,a cikin taurarin take hango wasu kujeru masu kama da karagar mulki da wuƙaƙe an crossing⚔️ a daga saman kujerun . Take ta jita a wani halara da batasan inda kanta yake ba ,jijiyoyin idonta a take suka soma mata zugi
Batasan sanda ta canyara wani irin ƙara ba ,da ƙarfi kuma ta wangale idonta .

Daidai nan taga ta dawo da gani tar tar ,saidai tana buɗe idonta taga tsakar gidan kamar an share babu kowa sai uwale a can gefe cikin kwatan wanke wankensu a kwance cikin kwatamin ƙazantar .

“Na shiga uku Baba uwale me ya sameki?” tayi magana tana nufan inda take ,ai da gudu uwale tayi tsalle ta fito daga cikin kwatan kayan jikinta na ɗiga da ruwan kwata tayi ɗaki da gudu ta danƙara saƙata.

Tsaye tayi a tsakargidan kamar bishiya tana mamakin meke faruwa.
Baba lantana da gabaɗaya bata wayi meke faruwa ba itadai taga kamar uwale tayi tuntuɓe da tayan da muntari ya shigo dashine kawai ta hankaɗa kwata ,sukuma mutane ganin hakan ya sasu watsewa a karce harda Hausi mai ganin juwa.

“Saratuna muje ɗaki”
“Me ke faruwa ne inna ina mutanen gidan?”

“Ki ƙyalesu saratu indai sharrine kowa ya haifa wai kece aljanah”

Riƙe baki saratu tayi da sauri “Innanmu Aljana kuma? Ya laɗifu ! Hasbinallahu wani’imal wakeel ,Allah ka kareni daga sharrin wainnan halittun ka kawo mun gauƙan wahalata” cikin kuka ta wuce ɗakinsu ranta na tururi.

***
Nassarawa GRA
Wata ƙosashiyar Hajiya na gani da a ɗebe zata kaiwa shekaru 45 kan wani tanƙasheshen kujera na Alfarma ,a mahaukacin falon dake cikin ƙerarren gidan,waya takeyi a hamshaƙe kamar ba da kudi ake wayarba
Ba sai an fada maka matar sanata bace ba ,gadaranta kaɗai ya isa ya tabbatar maka da babbar macece mai ji da kanta , sunkuye gabanta wani matashine da bazai haura shekaru 29 ba ,ya gama ƙanƙan dakai a ƙasan carpet ɗin tsakiyar falon kamar zai mata sujuda

Ta kwashe kusan minti 40 tana waya har ƙafar matashin ya soma tsami kana ta idasa wayar ,a gajiye kamar wacce tayi gagarumin aiki ta jefa wayar kan ɗayan kujeran gefenta . Tana sane fa da mutum a gabanta amma ta ɗauke kai ta koma ta kwanta akan allon kujeran tana karkaɗa lafcecen farin ƙafarta dayasha jan lalle .

Shikam tunda ya kafe ƴan yatsunta da ido ya kasa ɗagowa saboda tsananin burgeshi da sukayi,ji yake kamar ya jawo ƙafar ya luma babbar yatsan ƙafarta a baki yayi ta tsotsa .

Hajiya Huwaila ƙuluwa iya ƙuluwa tayi ,wato shi yaron nan jira yake tayi masa magana ? Lallai zaiji a salansa.

Ɗaukan wata ƙaramar waya dake gefen hannun kujeranta tayi ,ta lalubo Number ma’aikatanta

“ellow Isiya a fito da mota zaka kaini airport ,baby ta kusa ƙarasowa”

Rass ! Gabansa ya fadi jin tana shirin fitane ma abunta ,A furgice ya ɗago da rikitattun idanuwarsa masu bayyana tsoro ,ya watsa akan fuskarta daidai ta yunƙura zata miƙe

“Ahhhh….Ranki shi daɗe…” katseshi tayi da sauri

“Shishh🤫 kana iya dawowa wani satin ”

Tuni yaji idonsa ya kawo ruwa yaudai jarabansa na kallon mata ya ja masa masifa.

Takawa ta somayi zata bar ɗakin da gudu ya wawuso ƙafarta da hannuwansa cikin ɗimuwa ya ɗago da marayan fuskarsa “Hajiya don Allah ki saurare Ni , Emergency ne”

Hajiya Huwaila da taji kamar an jona mata bâtir kawai kamo ƙafarta da yayi ,wani tsamm taji ,amma haka ta dake tace “In one minute manene sunanka kuma mai kake so?”

Bakinsa na rawa yace “Ali!” zuba masa ido tayi tana admiring fuskarsa mai cike da zallan ƙuruciya lufluf da baƙin gashi .

Ta ɓangaren Ali ganin ta kafesa da ido yasa ya kara furgita

“Eh Ali sunana ranki shi daɗe” yamutsa fuska tayi “And what do you want you are exhausting my time”

“Eh..eh wato dama dama Ni driver ne ,kuma ƙwararre shine nazo don Allah ki taimakeni ki ɗaukeni in Zama drivernki ,wallahi Ni ƙwararrene”

*GARAƁASA!*
*GARAƁASA!!*
*💃GAREKU MASOYANA 🥰,MASOYAN LITTAFAINA😍*

_Kunsan dai masu iya magana na cewa Garin Naji daɗi yafi garin na saba ,kazalika tafiya da gwaninka akwai matuƙar daɗi_
_Takuce uwar afnanuwa data saba nishadantar daku da littafanta,yau zan samu farinciki ta hanyar sauke masu farashi ,a maimakon da da littafan suke a 500₦ ,zasu zama kowani daya 200₦ kacal😉🤗_
Tsakani da Allah ban dagargarza farashi ba?
*_Ga wani ƙarin Armashin in kika siya littafan suka kai shida zuwa sama ,a maimakon duk ɗaya 200 zan bar maki duk ɗaya 100₦_*
Tsakani da Allah ban nuna maku lovayya ba? Kar ku sha’afa ga jerin zafafan littafan 🔥
*1. BAGIDAJIYA* Labarin ƴar ƙauye indo da Umar soja mazan hwama😂 yaya tafiyar takene?
*2. JARABABBEN NAMIJI* Balarabe amma shi mata ƴan Africa kawai yakeso a ganinsa sunfi taste ga bafullatana shatu Yarinyar mai gadinsa ƙaƙa an kayina?
*3.HARIJI* Hariji da harija An haɗune da an dace . abun a murɗe yake matansa sun fito daga ƙabilu mabanbanta dake Nigeria amma fa shiɗin ƙuliyane wato alƙalin alƙalai ,bayan nan mai ya biyo baya?
Karaf sai gata da *4.GIDAN DAƊI* ruguntsumi fada da mai gari ! Sudin dai student Nurses ne,gata balaƙaƙƙiya mai yake faruwa a Hostel din likitocin? Yaya gamonta da Adams ?
*5.GWAURO* Topah har na tuna da waƙoƙin hausawa …gwauro ba mata amma ka iya aikata ta’addanci ba’a baka ajiyar budurwa…lolx gwauro tashi gari ya waye
*6.SUGAR MUMMIES* Ga manyan gwaskayen sun rantse suma sai sunyi ƙara’i dukda shekaru sunja amma sai an dama suma dasu ,me ya biyo baya ne?
*7.BANANA ISLAND* To I’m speechless here,nasan dai mugune ,Sex style ɗin sa na mugunta ne wacece zata iya ma jarabansa?
*8.AKAN DADIRO NA* Wow tsabagen shahara har gasan cin mace sukeyi aga wanda yafi nisan zango,likitane a office ɗinsa yake ƙwaƙule matan mutane ,yaushene dubunsa zata cika?
*9.AUREN SHA’AWA* ƙurunƙus🤭 Alhaji yayi Sex da fatalwa😱
*10.RAMUWAR GAYYA* Fyaɗe ya jama samari uku ƴan jami’a shiga hadari ,me ya faru ne?
*11.INDO MAƘATA* mai aikin yaran ɗan sarki , da rayuwarsu kakaf a turai sukayi shi basu jin Hausa itakuma babu turanci ,fitinannune ko iyayensu sun shafa masu lafiya ,mamansu ƴar gayuce itakam ƴar gargajiya ce,ya zatayi da yaran nan?
*12.QASAITATTUN MATA* Rashin ji ya kare ma student masu lesbians ,rashin ji ya kare ma University girls da tun daga gida basu da tarbiyya ,lallai littafin nan akwai kwamacala.
Hmmm abin da yawa wai maye yaje kasuwa
Ga *13. JININ SARAUTA* Ga *14. SAI NA RAMA* Hmmm ina n’a baro *15.RAYUWAR AFREDARH* An amazing book with lot of dramas all about musayan jarirai *16. BABBAR YARINYA* ƴar Alhaji jikan hajiya ,anya ba ƴar gaba da fatiha bace ba? *17. NAMIJIN KISHI* Hmmm ga kuma *18. LAYLERH*

Hajiya Littafaine fa cunkus a libraryn oum Aphnan ɗin ,karki sake ayi babu ke ,ki hanzarta samun naki garaɓasan na kwanaki uku ne kacal…….daga yau Lahadi 19/02 zuwa Laraba inshaalh

Leave a Reply

Back to top button