Cinikin Rai Book 1Hausa NovelsHausa Novels

Cinikin Rai Book 1 Page 8

Sponsored Links

CINIKIN RAI….8
Beauty and the beast.
Mai_Dambu🌚
<<<<<<<<<<<<|=|>>>>>>>>>>>
Don kar abin ya tsaya a ran yaran, ya mike tana karkad’e jikinshi ya ce musu.
“Babu abin da ya faru, kawai sun min haka ne don ban biya su kudinsu ne, amma nasan babu abin da zai kuma faruwa, In sha Allah.” Ya fada yana kokarin goge bakinsa. Domin baya so su fahimci hakan a matsayin zalunci, baya kaunar zalinci kuma ba zai yarda na kusa da shi yayi ba. Da wannan suka tattara sauran yan kudadensu, suka koma gida.

—–
Malik.
Shigowa wasu kartin maza suka yi, suka tsaya tare da ƙamewa, “Mene ne labari?” “Mun share duk wani shaida da yan sanda zasu yi Investigation akai, babu wani alama domin mun rufe tarihinsu.” Ajiye pen din yayi ya koma da baya, yana me jingina da kujeran da yake kai, yana wani irin murmushi tare da juyawa da kujeranshi.
“How dare zasu bude min wani kasuwanci? Bayan ina nan a raye? Duk wanda zai bude wani kasuwanci dole yazo ya lashe kafata. I’m the only king bana buƙatar gasa da takara. Duk wanda ya taba min dukiyata a aika min shi in da aba dawowa.”
Murmushi bakidaya wannan shine Kasuwancinsu, a kashe ko a raya su suke da ra’ayi da yadda zasu yi, shi yasa daga su har Malik din dukiyarshi yake kara habbaka. Hahawan rashin mutuncin da yake wakana a tsakaninsu da kananun yan kasuwa, ya kara kuntatta mutane. Gashi wani abin takaici duk abin da yake faruwa gwamnati bata da ikon magana, tow ai mutanen da zasu yi magana sune a jikin Malik, akwai wanda ya isa yayi magana ne? Babu kuwa.
—-
Washi gari.
Mutanen Wasim sun sake dawowa, kuma dama wannan shi ne, fatan Zeeno kenan kuma sun dawo din, saman kwanon rumfar shi ta hau idan ka yadda yarinyar nan take makale a jikin rumfar sai tsoro ya kama ka, amma kuma haka bai sakata jin ko dar ba, duwatsun da ta tara a cikin jakar fata, take cirowa a hankali taja dankon ta sake shi da ƙarfi. Sai dai mutum ya ji “Kul!” Tare da ihu me karfi suke sakawa, tsayawa tayi, ganin suna nimanta, sai bata kuma Harbin ba, incredible kawai sai da ta bari sun sake har suna yiwa mutumin farkon fada, kawai yarinyar nan tayi ta sake musu, babu kakkaunatawa. Baki daya ta hana su sakat. Sai da ta buwaye su ta zame musu alakakai kamar, daga sama suke jin al’amarin Harbin, babu shiri suka juya da gudu suka bar bakin ruwan, sai da suka tafi sannan ta sauko daga saman rumfar. “Abba basu kuma dawowa.” Ta fada tana kallon, tana kallon shi, rike da dankon. Karba yayi ya boye. “Zeeno me yasa kika yi haka? Babu kyau kar ki kuma yin haka.” Gyada kai tayi, ganin haka ya rufe shagon suka bar wurin. Ko da isa gida yana shiga suka rufe kofar. “Maman Abbas, kin ga yar nan da zuciya yau kore min mutanen Wasim tayi, yanzu ban san ya zan yi ba.”

“Mun nime Allah ya kawo mana iyakarsu, sai Allah ya bamu ita don haka babu abin da zance sai Alhamdulillahi.” Ta zaunar da Zeeno ta zuba mata abinci. Kadan taci ta tsame hannunta, tana faɗin. “Ina Abbas?” Kallon dakin tayi kafin ta ce mata. “Yana barci” gyada kai tayi. Ta mike ta kai sauran abincin dakin girki. Sannan ta wuce dakin Ammyn Abbas ta kwanta.
Washi gari da suka fito bakin ruwa, sun sami Wasim da mutanen shi. “Wani dan shegiyar ne ya jefi mutane na?” Maida Zeeno baya Alhaji Badaru yayi, zai tura ta gida. “Waye ya daki mutane na?” “Ni ce!” Ta fada da karamin murya. Bud’a mata hanyar aka yi, kanta a kasa, kafarta da babu takalmi tana wasa da ƙasa. “Ke!” Ko gizau bata yi ba, ta maida hannunta baya, tana rike da karfen rodin da ta dauka bayan Alhaji Badaru Daniyal ya maida ta baya, tana wasa da ƙafarta. “Kai dauko min wancan yar hanji!” A yadda ya ganta ya zata irin yaran nan ne masu shegen baki da tsoro, lokacin da ya iso sai da ya duka ya ce mata. “Yarinya wasa kike ko da gaske!” Kamar wacce wani abu ya shiga jikinta, ba tare da ta bude idanu ba, ta kaiwa fuskarshi wani mahaukacin duka da karfen sai da ya cilla can. Hannunta yana rike da rodin ta wani mika shi. Zaka rantse irin yaran cartoon din nan ne, na Avatar ko wonder woman, lokacin tana karama. Yadda tayi dukar hatta Wasim sai da ya sauko a samar motar shi, ya gwalalo idanu waje. “Kai ku min fata-fata da namar yar tsiyakin nan!” Murmushi tayi, tare da jan kasa baya ta ce. “Idan kuka tab’a ni, zan kyale ku salin alin ku yi fata-fata da ni, idan na kararaya kasussuwanku, babu wani shugaba sai Baba na!” Ta fada tana kallon s kou. Idan da wani zai iya bada shaida tow abun da zai fada shi ne tana cikin mutanen da ayi experiment dinta aka yi, nan kuwa babu abin da yake aiki akanta sai wannan harsashin da yake jikin ƙwaƙwalwarta kamarshi. Murmushi tayi ganinsu tika-tika kamar giwaye, hatta gudun da suke kasa tana amsawa kamar zata burma. Da’ira suka mata, yadda zaka fahimci Yarinyar nan hatsabibiya ce, domin wani irin dukar su take babu kakkautawa. Kamar mayunwaciyar xakaya haka take musu duka da karfe ga hannunta baya sab’a abin hari dake akwai karfe rodin sai da ta gama musu dukar kawo wuka, sannan ta tsaya cak, zubewa suka yi. Ta d’ago fuskarta da yayi kaca-kaca da jini da zufa. Ta nufi Wasim kafin yayi wani yunkurin guduwa ta jife shi da karfen sai da ya fadi a ƙasa.

Daukar karfen tayi tana nuna shi da karfen. “Kar na kuma ganinka a nan yankin daga yau, yankin Baba na ne tashi ka. ” Dakyar ya tashi ya ja motar shi, ya kawo yayi ta jigilar kwashe mutanenshi ya zuba su cikin motar. Sannan ya bar wurin.
Damshi da dumi taji a hancinta, a hankali ta d’ago fuskarta zata yi magana, sai zubewa tayi a wurin, da gudu mutanen kasuwar kifi suka rufa mata, tare da daukarta suka nufi asibiti da ita. A lokacin Dr Saddikah ita ta tsaya akanta. Sai bayan awa awa daya ta fito daga kanta, tana kallonsu. “Yarinyar nan rayuwarta tana cikin hatsari, me ya faru?” Shiru sukayi kafin daga baya, suka bata labarin abin da ya faru. Ai idan ranta yayi dubu ya b’aci, yadda take fada kamar zata dake su. Haka yasa suka sunkuyar da kai. “Bamu da zabi ne, ba zamu so fadawarta hatsari ba”
“Gaskiya a kula da rayuwarta!” “In sha Allah!” “Abin da yasa nake magana, a kowani motsa jiki da fushi harsashin kara nutsewa cikin kanta yake. don Allah ku kula da ita.”
Abun tausayi haka suka yi jigun-jigun, sai dare suka bar asibitin. Hmm tashin hankali wanda ba a saka masa rana domin kuwa sabon tashin hankali aka kuma haifarwa. Domin washi gari sai yan daba sun kai mota ashirin, lokacin ta farka domin har asibitin suka biyo ta. Lallai a fito musu da ita, suka fara bibiyar dakuna da aka ki fito da ita, da gudu Dr Saddikah ta nufi dakin tare da rufewa lokacin Ammyn Abbas tana bata abinci. Rufe kofar dakin tayi. “Dr lafiya?” Ammyn Abbas ta tambaye ta, “babu kome” dukar kofar aka yi da karfi, tayi maza ta fisgo hannunta suka fada ban daki.

A hankali ta cire hannun Dr Saddikah, ta ce mata. “Ammyna da Abbas kuma fa?” Fauce hannun tayi ta daki wurin key fita yayi ya cilla cikin dakin daidai shigowar su, sake dukar kofar tayi sai da ta balla. Cire piece na kofar tayi, tana faɗin. “Allah sarki me ya kawo ku?” Ta fada tana fitowa, nufar wurin Ammyn tayi ta shagwab’e ta ce mata. “Ammynay bani naci” jikinta na rawa ta shiga bata abincin tana ci. “Kee!” Yatsar hannunta ta kai baki ta ce mishi. “Dalla yi min shiru, sai na koshi waye ya gaya muku ana magana idan ana cin abinci.” Gyada mata kai suka yi, ta cigaba da cin abincin. Har suka tsaya idan aka ga basu dawo ba, wasu ma zuwa suke kafin kace me sun cika dakin. Tana gamawa ta cewa Ammyn .”Ammyna bari na share musu tantama. Waɗannan suna bukatar kulawa, kai bani abin kunnan nan” mika mata yayi har da radion ta kura karar, sannan ta cewa Ammyn. “ki rufe shi kar ya ga abin da yake faruwa ya fara jin tsoro” a hankali ta juya, “zaku taka min baya ne, ko kuma zan tara muku nauyi ne?” “Mun zo yin dagga-dagga da namarki ne!” Had’a hannun tayi tace musu. “Idan na sake ku da hannu, Ni ce zan yi jinya gara na nime bulalar da zan iya gabatar muku da kaina.” Karfen gadon ta shiga kokarin ɓallawa, sai da ta karyo shi, abin da ya basu tsoro kenan. Suna ganin kamar ba bil adam ba ce. Takowa tayi har gabansu, ta sunkuyar da kanta. Kafin ta d’ago kai sama jini yana zuba. Daga hancinta Idanunta rufe motsin takunsu kawai taji kanta yana sama, gyara rike karfe tayi koda ya iso kafin ya sauke mata,.ta daki mafitsaransa. Durkusawa yayi akan gwiwarsa ya fasa ihu tare da zubewa a gabanta. Take kansa tayi ta tsaya akan shi. “Mu cigaba ne?” Fita suka yi da baya-baya. Har suka isa wajen sai da sukayi kamar kafa goma a tsakaninsu, kafin suka tsaya, karfen wancan mutumin ta dauka hannu bibbiyu. Ta kalle jini na zuba daga hancinta, gogewa tayi tana kiran su, Dr Saddikah kamar ta fasa ihu. Ciwon yana ta’azzara ne. Abin tausayi yarinya ta koma kamar wacce aka kara mata wani abu. Da gudu suka nufeta babu tausayi ko imani balle jin kai. Haka suka rufeta da mugun nufi.
Ihun kartin maza kawai yaƙe tashi a wurin suke da yawa suke da ihu, ba mamaki na mutum ba ce, aljana ce domin a cikin minti arba’in, ta tara su a wurin. Karkarya musu cinyoyi da hakarkari. Masu nisan kwana da lafiya suka yi ta juyawa a guje. Bata kyale su ba haka tayi ta binsu tana kai musu duka. Har suka fito harabar asibitin, da gudu suka yi ta juyawa da motarsu, har suka bar asibitin. D’aga kai sama tayi tana son jinin ya tsaya. Kafin ta yanki jiki ta fadi.
<|=|><|=|>
*Present*
“Me ya faru da har ƙwaƙwalwarta ya kuma tabuwa? Kun manta halin da take ciki ne? Ya kamata a kula da lafiyarta domin kuwa rayuwarta tana cikin hatsari sosai.”
“Babu wanda ya bata mata rai, sai dai a yan kwanakin nan, uzuri ya mata yawa bata hutawa kuma Hutawa tana cikin ka’idodin kula da lafiyarta, amma zamu kula da ita don Allah ayi wani abu!” Inji Ammyn. Tausayi Zeeno ya kuma shiga ransu. “Ita domin wani yayi farinciki ita zata fadi. Ban san yadda zamu yi da Zeenobia ba, mun bar wancan garin ne domin ita, yanzu kuwa rayuwarta ta kuma fadawa matsala!”

“Idan aka ce za a mata aikin cire shi, dole za ayi rasa rayuwarta, amma kuma dole a rabata da shi domin tana kara shekaru lafiyarta zata kassara sama da yanzu, idan muka yi sake zamu rasata.”
“Dr Saddikah ya samu yi?

*Hi……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[8/28, 6:46 AM] Mmn Khaleel: CINIKIN RAI…

Leave a Reply

Back to top button