Bakar Ayah Hausa NovelHausa Novels

Bakar Ayah 3

Sponsored Links

 

 

 

Page 🖤03🖤

 

Saida taje daff da inda su Hajiya Zeena suke tsaye ta riƙe kanta tareda fara layin ƙaryah.
Lylah ce ta kulada ita tace.
“Lubna kema kuwa lafiya,naga sai layi kikeyi?”
“Uhm kaina ne nake jinsa kaman zai fashe,bana jin daɗinsa ko kaɗan”
“Toh ta tafi gida mana,dama waye ya riƙeta,ni nayi mamaki ma danaga tazo wajennan”
Hajiya Zeena ta faɗa tana binta da harara. Itama ta wata fuskar ramawa tayi,tareda yimusu sallama tabar wajen,shikuwa uban gayyar dama yayi fushi da ita jiya. Dan haka ko kallon ta bayyi ba.
Dariyah ƙasa ƙasa Hajiya Lylah tayi,da alama show ɗin yayi mata dadi sosai.
A daddafe tana nishi ta nufi motar ta,hadda tsayawa ta huta kana ta cigaba da tafiyah.
Saida tabar layin asibitin kafin ta saki shewa tareda ciro wayar ta a jaka.
“Kee Dallah ki tsaya nayi magana,nasamo mahaɗin yanzunnan,naji kincemin kinaso kiga yanda zan gama da ita,to ki hanzarta,dan ba’a son tafara naƙuda tukunna,idan ta haihu to aikin bazayyi yiyu ba”
Kashe wayar tayi tareda ƙarawa motar wutah tana waƙa.
Bata ja wani lokaci ba ta isa gida,kasancewar basuda nisa da asibitin.
A bakin ƙofar gidan ta samu motar Yaseerah ƙawarta tana jiranta,bodyguard sun hanata shiga,ta bar ID parmission dinta a gida saboda sauri.
Horn Lubna tayi musu tareda nuna musu motar Yaseerah lokacin da tazo shiga.
Tafiya take tana binta a baya har suka isa apartment ɗinsu.
Direct sashen Lubanan suka wuce cikwda raha da kuma shewa,tamakar tarkon su yakama Toron giwa.
“Wai dagaske kike luby,nifah har yanzu ban yarda ba irin wannanan asirin yana duniyah,kina daganan saiki kasheta hankalinki kwance?”
“Ƙawarai ma kuwa,ki zuba iso kawai kigani,lokacin dana taho bata haihu ba dan haka mu hanzarta”
“Idan ta haihu shikenan bazai aiki ba?”
“Ahah ba aikine bazai yi ba,kawai so nake na haɗa itada abin cikin na kashe,kingane dai koh,tunda kema ƴar garice ai”
Ba’a falo suka zauna ba,saboda tsaro sai suka shige ɗaki.
“Wai lubby har yanzu tsoron Kucakan gidannan kike yi,i think no need,tunda kece kike aikatawa,kuma ma hakan yafi,ta hakanne kaɗai zasu ƙarajin tsoronki su daina aura masa mata,habaa mutum baza a barshi ya wataya da mijinsa ba ya more”
“Hmmm barsu mana,nafisu iya shege ai,kome suke ina daidai dasu, ko nace ma nafisu”
Tana maganar ne tana fitowa da ƴar tsanar daga cikin jakarta,sannan ta ɗauko jinin Hafsa ma a cikin kwalba,zubawa tayi akan ƴar tsanar gefen bakinta yana motsawa tareda bada wani shu’umin murmushi ganin alamun samun nasara a aikinnata.
“Kinga Seerah inaga aikin yayi,saboda jinin ya tsotse a cikin dollyn,yanzu zan fara ƙiran sunanta sau uku sannan saina fara kakkaryah ta”
Tana rufe baki kuwa ta fara aiwatar abinda ta faɗa a aikace.
“Hafsa….hafsaaa…….hafsaaaaa,kwananki ya ƙare ganinan kema gareki!!!!!”
Ƙaƙasss tafara kakkaryah jikin ƴar tsanar,wanda duk sanda tayi hakan sai wata ƙara tafita daga jikin abin,amma hakan ko tsoro bai bata ba bare tausayi,saima wani ƙara ƙwarin gwiwa daya bata tareda nishaɗin matsalarta tana shirin kauwa daga gabanta.
Ta ɗauki kusan minti talatin tana aikin,domin idan ta karyah saita jira kafin tacigaba dayi,badan komai ba sai dan tasake bawa kanta lokacin hakan.
Saida ta gama kafin ta jefar da ƴar tsanar a ƙasa tana maida numfashi,hannunta da kuma jikin tsanar dukka jinin hafsa ya bata.
“Nagama da ita itama seerah,itama ta tafi kaman yanda ɗayar ta tafi,babu wanda zan ƙyale,hakan alƙawari na ne danayi”
Ajiyar zuciya ta saki tareda komawa ta zauna a kusada seerah,kaman wacce tayi aikin daidai.
“Huh ya kike gani seerah,kina ganin ta mutu kaman yanda nake buri”
“Indai har da gaske kin yadda da aikin zulumgum,kuma kin tabbatar kinyi yadda yace,ni ina ga babu wani abin damun kai a lamarin,kinyi yadda ya dace,to yanzu yaya? Zaki kira kiji ko ta mutune ko kuma shuru zakiyi kar ace kece kaman koyaushe”
“Hmm ko nace nice ko kar nace nice dukkansu kowa yasan nice na aikata,abinda yasa kika ga banbar gidannan ba,saboda bahaka nabar mijina ba,duk aikin yasoni tamkar uwargijiyarsa bayyi aikiba,amma namasa aikin da bazai taba sakina ba,har mutuwarsa,saidai idan nice naga damar tafiyar.
Sukuwa bazasu so mutuwar ɗansu dan nabar gidan ba,dan haka a zauna a haka,su cigaba da kawo ƴaƴansu cikin gonata ina murƙushesu kaman ƴaƴan kaji”
“Heee gaskiya bakida dama lubeee,shiyasa fah a Club ɗinmu ke ta dabance,to ni kinga barina tafi,Old lady tana ta ƙirana zanje na ɗora abinci,saikinjini ko sai na jiki”
Daga haka seerah ta ɗau jakarta tayi gaba.

•••••••BACK••••••••

“Innalillahi innalillahi innalillahi……….”.
“To sai salati kike kamawa amma bakya ƙarisawa,nasan yanda kuka shaƙu da hafsa Madeena,amma addu’a zaki mata ita take buƙata a yanzu”
Abdulmaleek ne yafaɗa cikin tausayawa,dan kowa yasan Madeenah batada wata ƙawa bayan Hafsan,kasancewar tare suka tashi,kuma kansu ɗaya.
“Yah Abdul kana gani fah,kalli yanda take shan wahala,jikinta duk ya lanƙwashe,shikenan fah bazata tashi ba”
“Am sorry sis ki dunga yi mata addu’a kinji,ikon Allah sai kiga ta tashi da ƙafafunta,komai nufine na Allah”
Ɗaga kai tayi Alamar taji abinda yace,bayan suɗin babu wanda yake magana a wajen,sai Lylah abu kaɗan taja tsuka ta turo baki,ita a dole an sakata zaman wajen babu yanda zatayi.
Hajiya zeenah ce ta juya ta rafka mata harara,har zatayi magana ko mai ta tuna sai kuma tayi shuru tareda minding nata business din.
Ƙarar ƙofar dakin tiyatar ne ta ankarar da dukkansu,inda kowa ya juya yana kallon waye zai fito daga ɗakin.
Doctor Basheer ɗinne ya fito ɗauke da hankerchip a hannunsa yana share ruwan gaban goshinsa.
Kallon su yayi da alamar bayason faɗamusu abinda yake kan fatar bakinsa.
“Am sorry munyi iya ƙoƙarinmu amma……….”
Abdulmaleek ne ya katseshi tareda cewa.
“Uhm doctor duk wajennan nine namiji,shin ko zamu iyah yin magana dakai a office tukunna,kafin saina faɗamusu,bai kamata ka dunga faɗan magana a waje ba irin wannan ,musamman da iyah a wajen”
Kowa na’am yayi da maganar abdulmaleek din,inda doctor yashige office shima ya bishi.
Ya ɗau kusan miniti talatin kafin ya dawo inda su hajiya zeenah suke,duk da yanda yake ƙoƙarin saita Yanayin fuskarsa,amma kana gani kasan ba ƙaramar magana bace a bakinnasa.
“Am sorry to said,she’s gone,Allah daya fimu sonta ya karbeta Iyah,please dan Allah karki saka damuwa a ranki sosai kinji,ki ɗauka cewar Hakan shine abinda yafi mata Alkhairi akan rayuwar da take ciki.”
Ɗan ja da baya Sayyada tatin tayi ta zauna a akan kujerar da take bayanta,saida ta saita ta kwantar da hankalinnata da taimakon Abdulmaleek kafin ta ɗaga kai ta kalleshi.
“Toh…toh ina yaron naji ance yana da rai kafin ayi mata tiyatar koh?”
“Ahah iyah,an fitar dashi da rai,amma kuma yabi bayanta bayan mintuna da yazo duniyah,saboda shima abin ya shafeshi sosai,bai daɗe ba ya koma ga mahaliccinta”
“Naaaa shiga uku shikenan jinin zainabuna ya ƙare a duniya,wacce nake ganin zata maye min gurbinta itama ta bi bayanta,hadda ɗan dazan riƙe naji daɗi shima ya tafi,yanxu wannan tantiriyar mayya mai yasa zata min haka mai yasa zata lagarta min rayuwar iyali…….yanzu……..”
“Dan yarasulullahi Iyah sayyada ki taimakemu kiyi shuru,Hafsa Addu’a take nema a halin yanxu,naƙira baban su Abdul da kuma Abba ƙarami,dukkan su suna hanyar zuwa inshaaallah”
Hajiya zeena ce tayi maganar tana share ƙwallar da take idonnata,ita ba komai ne yasake girgizata da mutuwar ba sai yanda taga ci taga rashi,burin wannan ɗa yazo duniyah amma sai gashi wata ta kasheshi tun kafin ta ganshi.
Wani tirurine da kuma bakin ciki tareda muradin ɗaukar fansar jikanta suka turnuƙe a cikin ƙirjinta.
Babu abinda take ambata sai sunan Lubnah a zuciyarta.
Suna cikin tsaye xugum zugum Alhaji Abdullahi ne yashigo shida Jabeer,wanda kana ganinsa kasan abun ba ƙaramin dukan ƙirjinsa yayi ba sosai.
Bai taba zaton zai rasa hafsan ba inaga kuma Ɗannasa dayake jinsa tamkar tsoka ɗaya a cikin miya.
Tunda yazo wajen bayyi magana ba,banda rawa babu abinda jikinsa yakeyi,duk yadda Mutanen wajen suka kai ga jin haushinsa saida ya basu tausayi,duk da shi mutum ne mai sanyin rai,amma kuma da wuyah mutum yaga Lagwonsa ya karye kamar haka.
Ɗakin da hafsan take ciki ya nufah jiki a salu’be.
A kwance take akan gadon tiyatar an rufeta da farin kyalle,gefe kuma jinjirinne shima an naɗeshi da farin kyallen.
Kallo ɗaya yayiwa inda jinjirin yake ya ɗauke kansa,dan baya fatan ma ya buɗe yaga menene a ciki,saboda yasan hoton bazai taba barin zuciyarsa da tunaninsa ba,ya dunga farautarsa kenan har ƙarshen rayuwarsa.
Hannunsa yasaka na dama yafara yaye farin kyallen dayake kan hafsan,duk da yanda hannun nasa yake rawa amma yana iya koƙarinsa wajen ganin yayi mata kallon karshe,macen da duk namiji zayyi mafarkin samu a rayuwarsa,hankali,tunani,tausayi,uwa uba sanyi rai da sanin yakamata.
Ko mutum bai taba zama da itaba yasameta yasan sai ya ratsa duniyah kan ya samo irinsu,to inaga shikuma da dama yana cikin duhun rashin sa’ar samun mata,kwatsam lokaci ɗaya hasken yazo masa yafara haska duniyarsa….kashh sai kuma gashi ya ɗauke ya barshi a duhunsa wanda yafi ma na baya,saboda a da bai ɗanɗana hasken yaji ba,yanzu kuwa daya ɗanɗana yaji saiya ke ji tamkar duniyah sun taru sun juya masa baya.
Jajayen fatar bakin sa da suke rawa saboda tashin hankali ya fara motsawa tareda son furta wata kalmar.
“Meyasa meyasa………lokacin da ban shirya ba……”
Ƙwallah ce ta ɗigo daga idonsa zuwa kan goshin matacciyar da take gabansa a kwance.
“Ki jirani nima ina nan zuwa wajenki kinji,banga laifinki ba da kika tafi,domin babu komai a duniyar sai rashin daɗi,kece kika fara nunamin ba yanda na ɗauketa take ba,saidai kuma yanzu dakika tafi nasan babu wanda zai sake nuna min yanda kika nunamin……ALLAH YA JIƘANKI HAFSA”
Yana gama fadin hakan yasaki mayafin yamayar mata kaman yanda ya ganshi,daga nan yafice daga ɗakin yana share hawayen daya taru a idonnasa.
A zaune take tasaka riga rabin ciki,da wando matsatstse,head phone akan ta,da kuma cocumber akan idonta tana jijjiga kai.
Da alama yanayin yanayi mata daɗi sosai.
Bishira ce tashigo falon jikinta har rawa yake domin da isar da saƙon da take ɗauke dashi.
“Hajiya hajiyah hajiya….”
Saida tayi ƙira sunfi biyar kafin Lubnah ta cire cocumber dake kan idonta ta kalleta.
“Menene kuma yanxu kike buƙata kika zo kika durkusamin kaman mai neman gafara,mayu kawai.”
“Uhm hajiya dama …..wani labari naji wai Hajiya hafsa ta rasu a asibiti dazu”
“Oh an faɗi ta mutun,yaya hadda ɗan cikin suka rasu ko ya?”
Abin yaɗan bawa bishira mamaki amma ta danne,dan dama ko karen gidan ma aka tambaya ai yasan itace ta kasheta,to amma wazayyi magana,duk yanda gidan suke ji da taƙama da kuɗi,amma bazasu iya shari’a da lubna ba,saboda baban ta shine Chief private lawyer da abuja take ji dashi,kuma lubna ita kaɗaice ƴar sa mace,zai iya komai dominta.
Musamman daya zamo basuda hujjah bayananniya cewar an ganta ta kasheta,shiyasa take kashesu da boka take cin karenta babu babbaka.
“Eh hajiya naji ance wai harda yaron duk suka mutu,ana tahowa da su gida ma ayimusu sutura a binnesu”
“Huh naji daɗin wannan labarin naki”
Ta faɗa tana murmushi,gefenta ta juyah ta ɗauko dubu biyar ta miƙawa bishiran,dan dama dansu ta kawo mata labarin,duk da zagin data sha bai dameta ba tunda an bata kuɗin.
“Nagode nagode hajiya,zakuwa kijini da wani labarin idan nasamo”
Daga haka taja dabaya ta fita daga falon jikinta har rawa yake don son kuɗi.

 

🖤 Sadi-Sakhna ce🖤
ƴar mutan jama’are

 

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK1_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

 

*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03

*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna

______________****_______________

 

Leave a Reply

Back to top button