Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 59

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

59

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

Tallah !! Tallah !!

 

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce  ta nishadantar daku a littafin ta mai suna *Kanwata* *kaikajawa kanka ,  *Rai daya janzaki*.

 

yau na sake dawowa domin Domin tallata muku Littafaina mai Suna *(RUDANI )* Da kuma *Makauniyar Shari’a*  littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da saura n su basai n’a cika Ku da surutu ba  Hausawa sukace Gani yakori ji.

 

Karku Manta  *Makauniyar Shari’a* sabon littafi ne mai bibiyar Ma’anar sunan sa.

Ya zarce duk littafai na , na baya.

 

RUDANI littafine mai cike da Rudani da ban Al’ajabi , duk wacce kika fi buƙata zaki biya kudin sa Naira ɗari biyar kacal.

 

Farashin kowannen su Naira Dari biyar ne 500 kacal

Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.

Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank

Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

 

 

 

Lokacin daya damƙi nipple ɗin ta akuma dai-dai lokacin itama ta runtse idanunta da masifar ƙarfi jin yanda yasa harshensa yana ɗo bakin nipples ɗin ta ya mata wani irin zuƙa wanda taji tun daga cikin Faratun ƙafarta wani irin abu yana biyowa har bakin nipples ɗin ta.

Macijin kuwa zuƙa ya cigaba da yayi.

Ita kam wani irin zogin azaba take ji duk da cewa bata taɓa Shayarwa ba amma ji take zafin yafi ƙarfin zafin jariri na zuƙan,  baki ɗaya ta kasa motsawa dan duk jikinta ya narke koda ya tsanta ta gagara motsawa bare kuma tayi yunƙurin ceton kanta haka yayita zuƙa tsawon minti biyu da rabi kafin ya zare harshensa.

Sai alokacin ta iya sunkuyar da kanta ƙasa kaɗan ta kalli bakin nipples ɗin ta jini kaɗan ta gani.

Macijin kuwa harshensa yasa ya fara lashar jinin saida ya lasheshi fes.

Tana gani amma ta kasa taɓuka komai har sai daya lashe jinin duka kafin ya maida kansa kan Breast ɗin ta na hagu da ƙarfi ta runtse idanunta jin yanda yaja nippes ɗin ta da ƙarfi yake zuƙa kamar zai tsinkeshi.

Wani irin raɗaɗin azaba take ji tun daga ƙasan farcenta abin yana tattura yana bin jijiyoyi da duk wani magudanan jinin jikinta, wata iriyar fitinenniyar kasala ta fara ji mai masifar yawa bata san lokacin data runtse idanunta can taji ya sake wanda aƙalla taji ya ɗauki kimanin minti ɗaya da rabi kasa buɗe Idanunta tayi sai dai tana jin yanda yake lasar saman nipples ɗin ta wanda shima take zaton jinin kaɗan asama.

Sai kuma taji ya fara zaro kansa zururuuu ya fita daga jikinta lokacin da taji ya fita ajikinta ne ta sauƙe nannauyan numfashi kana ta buɗe Idanunta ahankali ta bisa da kallo ga mamakin ta sai taga ya koma wancan dakin daya fito yaje ya kwanta.

Baki ɗaya taji jikinta ya mutu kasala ya rufe ta wani irin Masifeffen baccin da tunda take bata taɓa jin irinsa ba ne ya rufeta da baya ta koma ta kwanta nan da nan bacci ya ɗauketa awajen…

 

*Morocco*

A kuma dai-dai lokacin Ummi, Hajja Nana, Aunty Ruƙayya, Aunty Hajara,Hajja Ummah, Hajiya Bunayya, Asma’u Asiya Dije Zaune suke a falon Didi bisa alamu sun gama baki ɗaya shirin su tafiya ne yanzu zasuyi.

 

Khausar kuwa zaune take gefen Ummi tana sassayan kuka da shesh-sheƙa tuni. Muryanta har ya dishe dai-dai lokacin kuma Ibraahim da Haiydar suka shigo.

Ahankali Haiydar ya miƙa mata hannu kana cikin sanyi murya yace.

“Zanyi Missing naki Addah Khausy.

Zamu tafi zan barki inda babu kowa namu.

Zanyi missing naki da halayen ki.

Ina ta tunanin idan na koma wazai min faɗa,

Idan na bar datti a falon Momy?”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa hawaye na taruwa a idanunsa cikin sanyi ya cigaba da cewa.

“Wazai yi min masifa idan na buɗe Labule ban gyara ba?.

Wazai min mita idan na ɗauki System ɗin Momy?.

Idan farcena ya taru Addah Khausi Wazai yanke min?”.

Cikin rauni ya ida maganar hawaye na cika kwarmin idanunsa tare da kwaranyowa.

Da sauri ta tashi ta faɗa jikinsa ta rungumesa tare fashewa da kuka tace.

“Wallahi tare zamu tafi Haiydar ni baza Abar ni anan ba tare zamu tafi”.

Ahankali Didi ta jawota tare da cewa.

“Kiyi haƙuri Khausar kinji ko?

Ai bake kaɗai za’a bari ba ba gani ba?

Aini zan zame miki madadin Mommy Sannan ga Rahama zata zame miki madadin Asma’u”.

Sunkuyar da kai Asma’u tayi saboda jin hawaye masu masifar zafi na zubowa a kuncinta tunda suka tashi da Khausar basu taɓa yin wata ɗaya basu haɗu da juna ba tun suna Nasury koda hutu akayi wanda ƙawance shiya zama sanadin Mutuntaka sosai tsakanin Momy da Ummi duk da Ummi ta girmi Momy sosai amma suna mutumtakan da yafi ƙarfin ƙawance.

Jin Kukan Asma’u ne yasa Khausar miƙewa daga jikin Didi ta kifa kanta kan cinyar Asma’u tana kuka.

 

Haka nan Hajja Nana taji rauni ganin za’a tafi abar Khausar ɗin ta agarin da batasan kowa nata ba.

Akuma dai-dai lokacin Dr Jameel da Moddibo suka shigo atare cikin sanyi Modibbo ya rumtse idanunsa sabida jin yadda kukanta ya daki ƙahon zuciyarsa, cikin yin ƙasa da kai ya tsira mata idanu,  tun da gari ya waye yake son ganinta amma ya rasa hanyar da zai bi ya ganta.

Runtse idanunsa yayi jin sautin kukanta Ji yake tunda yake bai taɓa jin wani kuka da yasashi baƙin ciki da ƙunci ba kamar sautin Kukanta Ahankali ya ƙarasa cikin falon tare da zama gefen Ummi dake kan 3sitter wanda ke fuskantar Asma’u da Khausar sai ya zama na yana fuskantar Khausar.

 

Cikin sanyin Murya yace.

“Ummi har kun gama shiri kenan ?”.

Cikin sanyi ta gyaɗa masa kai tare da cewa.

“Mun gama shiri Babana”.

Numfashi ya fesar tare da kallon Khausar dake kuka yace.

“Ummi zamuyi kewar ku”.

Kai ta gyaɗa tare da faɗin.

“Nima zanyi kewar ka Babana Nasan kona koma Gembila, baza taimin daɗi ba tunda ba kai ba Jamelu na”.

Cikin kula Yace.

“In Sha Allah baza mu daɗe ba zamu zo da izinin Ubangiji”.

 

Cikin jin kewarsu tace.

“Toh Babana yan zu dai ga amanar ƴata na bar maka amanar Khausi”.

Shiru yayi tare da sunkuyar da kansa ƙasa haka nan yake ji amanar tayi masa nauyi.

Sai kuma ya ɗago kansa ya kalli Hajja Nana da duk tayi sanyi tana matsar ƙwalla tace.

“To ga dai yarinya Khausar nan mun kawo maka amanar kuma bata da kowa anan sai kai sai kuma Iyayenka wanda su na gamsu da Mutuntakansu, Kararsu, da kuma dattakon su”.

Sai kuma ta share hawayen daya zubo mata ta cigaba da faɗin.

“Nasan su zasu riƙe min Khausar babu haufi kaine dai ban sani ba kana nan kullum fuska babu murmushi bare fara’a gakanan  ga ka nanne ne dai, dan haka ni dai ajihar min da jikata, banda cin zali”.

Kallon ta yayi sai kuma ya sake sunkuyar da kansa bai san wacce kalma zai fada musu ba saboda girman abinda yake ji acikin zuciyarsa ya kuma lura wannan tsohuwar ya rigimace.

 

Dr Jameel kuwa kallon Didi yayi cikin yanayinsa na raha yace.

“Didi dan Allah ki ciwa Khausar ta daina kuka gashi tana samin Matata kuka bana so mu rabu tana kuka, gwara ita tana tare da mijinta Ni kuma zata sa matata ta tafi tana kuka Wazai rarrasa min ita?”.

Baki sake Hajja Nana ke kallonsa kafin ta hararesa da faɗin.

“Oooh Allah Ubangiji ya shirye ku kai kuma wa zai rarrasheta kake tuhuma?Gata da Uwarta kace Wazai rarrasheta?”.

Murmushi yayi tare da langwaɓar da kai yace.

“Wallahi Hajja Nana ko Ummi bazata rarrasa min Asma’u kamar yanda nake so in rarrasheta ba”.

 

Dai-dai lokacin Jakadiya tashigo tare da kallon su Ummi kana tace.

“Toh Bismillah ku fito Mazan baki ɗaya sun fito Sarki yace afaɗa muku ku fito jirginku ya kusa tashi”.

Ummi ce ta fara miƙewa kafin Hajja Nana ta miƙe.

Asanyaye Innayi ta miƙe ta rungume Hajja Nana tare da cewa.

“Allah sarki Ƙawata zanyi kewarki”.

Cikin sanyi Hajja Nana tace.

“Ayyah nima zanyi kewan ki ko yaushe zamu sake haɗuwa”.

Innayi na ɗan raba jikinsu tace.

“In sha Allah bazan daɗe ba zamu zo Auren Asma’u zanzo”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.

“Allah ya kaimu lokacin ya kawo ki lafiya”.

Sai kuma ta kamo hannun Khausar ta sanya cikin na Innayi tare da cewa.

“Toh ni dai ke nafi saninki akan kowa acikin Masarautar nan, dan haka ga amanar Khausar”.

Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin.

“In sha Allah zaku same mu masu riƙe amana da kawaici da kara”.

Da sauri Khausar ta janya hannunta acikin na Innayi ganin Ummi ta nufi ƙofan fita yasa ta faɗa jikinta ta fashe da matsanancin kuka kukan daya sa jikin kowa yayi sanyi cikin rauni take cewa.

“Ummi Ni na fasa mu tafi tare bazan zauna ba,  bani da kowa anan fa Ummi, nikam zan koma wajen Momy na  kaifafa Haiydar mafa tafiya zaiyi”.

Cikin shesh-sheƙan ta cigaba da cewa.

“Ba Momy ba Haiydar ba Raudhat sannan ba Asma’u Ummi abarni ni kaɗai ni na fasa”.

Ummi kuwa cikin ƙoƙarin hana kanta kuka da take ji da sauri ta kauda kai dan raunin Khausar yayi yawa a hankali tace. “Khausar alƙawarin da kika yiwa Yayanki Jameel kenan? Kin fasa cika masa alkawarin kenan?”.

Cikin matsanancin kuka ta gyaɗa mata kai tare da cewa.

“Na fasa Ni na fasa bazan iya ba, Zanyi tayi mishi addu’a kuma Allah ya bashi haƙuri ni bazan zauna da Yah Moddibo ba zaita ta cin zalina”.

Ahankali Rahama ta matsa kusa da ita tare da faɗin.

“Ayyah Addah Khausar ki zauna mana muma muna sonki muna son zama kusa dake kuma zan zame miki madadin Asma’u Didi Madadin Mommy Yah Ibrahim Madadin Haiydar Innayi Madadin Hajja Nana”.

Cikin sauri ta juya ta rungume Haiydar tare da fashewa da matsanancin kuka Haiydar kuwa kasancewar sa Namiji yasa yashiga share mata hawayen ta yana cewa.

“Kiyi shiru Adda Khausy in Sha Allah muna tare dake duk inda kike”.

Ya faɗa hawaye na zubo masa.

 

Ajiyar zuciya Ibraahim ya sauƙe tare da riƙe hannun Haiydar yace.

“Haba Haiydar ya haka?.

Kana Namiji kana Kuka ita kuma ya zatayi?Mu tafi”.

Juyawa Haiydar yayi tare da nufar kofar cikin sauri Khausar ta yunƙura da niyyar bin bayansa tana cewa.

“Ni wallahi na fasa zan koma bazan zauna ba Yah Jameel yayi haƙuri bazan iya cika alkawarin saba ni ban san nan za’a kawoni ba shi yasa”.

Moddibo kuwa wani irin suya da ƙunci yake ji acikin zuciyarsa Kukane da yake saka masa ƙunci azuciyarsa babu wani abu da yaji baya sonji kamar kukanta.

Didi kanta jikinta yayi sanyi saboda yanda Khausar ke kuka.

 

A ɗan raunane Aunty Hajara ta kalleta kana tace.

“Khausar ya za’a yi kiyi haka tun safe kike ta kuka sannan har yanzu ba zaki bari ba zaki sawa kanki zazzaɓi muma haka kike so mu tafi kenan muna kuka?”.

Cikin rauni ta ƙarasa Maganar hawaye na cika mata Ido.

Faɗawa Jikinta Khausar tayi tare da faɗin.

“Yanzu Aunty Hajara sai ku tafi ku barni anan?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“To ai ko wacce mace haka ta saba ,Aɗauketa daga inda ta sani daga wuraren data sani cikin Mutanen ta Yayunta, Ƙannenta Iyayenta”.

Kai Khausar ke girgiza wa tana cigaba da riskar kuka.

Aunty Hajara kuwa cikin sanyi da zubda hawaye ta cigaba da cewa.

“Sannan akaita cikin ƴan Uwan mijinta, Iyeyensa, Yayunsa, Ƙannensa su zauna lafiya da ita su zame mata dangi dan haka kema ki zauna lafiya dasu”.

Sabon kuka ta fashe dashi sai kuma ta kalli Hajja Nana Muryanta na rawa ta kifa kanta kan kafaɗar Hajja Nana tace.

“Yanzu Hajja Nana kema kin yarda zaku tafi ku barni”.

Hawaye na zuba a idonta tace.

“Toh ya zanyi Khausar ke kika ce kina son Moddibo fa ke kikace kina sonshi sannan yanzu an Aura miki shi an kawo ki ki riƙa kuka nima ki sani kuka ba gaki ga masoyinki ba”.

Ta ƙarashe maganar tana share hawaye tare da nufar hanya tana cewa.

“Allah ya ƙaddara saduwarmu Khausar”.

Da gudu Khausar ta zabura zata bita ganin haka yasa Moddibo saurin miƙewa wanda shi kansa baisan lokacin daya miƙe ba.

Hannunta ya kama ya riƙe tare da haɗe tafukan hannunsu wuri ɗaya.

juyawa tayi ta kallesa da fuskanta tayi jazir ga idanunta sun kumbura murya na rawa tace.

“Ka sake ni zan bisu bazan zauna ba”.

Wani irin rawa lips ɗin sa keyi so yake yayi magana amma ya kasa wani irin ƙuna zuciyarsa keyi kukanta na tayar mishi da hankali.

Hajja Nana na fita Ummi tayi saurin bin bayanta ta fita Asma’u ma cikin rauni ta miƙe ta fita haka Dija, Asiya, Aunty Ruƙayya, Hajiya Bunayya suka miƙe cikin tashin hankali ta fashe da sabon kuka idanunta akan hannunta daya riƙe tace.

“Nikam ka sake ni zan bisu”.

Sai kuma ta maida kallon kan Hajiya Bunayya dake ƙoƙarin fita tace.

“Addah Asiya, Dija duk tafiya zakuyi ku barni ba wanda za’a barni ni dashi sai ni kaɗai”.

Jin haka yasa duk sukayi saurin ficewa Didi ma miƙewa tayi tabi bayansu haka Dr Jameel da Rahama duk suka fice domin yi musu Rakiya.

Ganin duk sun fita yasa ya janyo hannunta suka bi ta cikin Corridor da zai sadasu da Side ɗin sa.

 

Tana mai ci gaba da kukan suka haura, suna haurawa kai tsaye Falon shi ya nufa da ita suna shiga ya maida ƙofar ya rufe Falon…

Ahankali ya ajiyeta bisa kujera, ita kuwa Khausar kuka ta kuma fashewa dashi, kukane wanda kasan daga ƙasan zuciyarta yake fitowa.

Cikin sanyi ya janyota jikinsa ya rungumeta hannunsa na dama ya buɗe ya haɗa da nata tare da tsarkake yatsun su, kana ya runtse hannu ya ɗago hannun nata ya manna kan sajensa yana shafawa.

Haka nan yake jin wani ciwom kukan ta yayin da hannunsa daya ke shafa bayanta alamun tayi shiru amma ina kukan ta sai ƙaruwa yake aƙalla sun ɗauki minti biyar ahaka amma Still kukanta ƙaruwa yake bai tsaya ba…

 

Adai dai lokacin kuma tawagar motocin su Hajja Nana ya fita daga cikin Masarautar ya nufi  Saleh Ramat International Airport wanda zai kaisu Adamawa kasancewar Private Jet ne yasa suna tashi daga Morocco kai tsaye Adamawa zasu sauka.

ƙarfe goma dai-dai Jirginsu ya ɗaga daga Rabat Morocco zuwa Adamawa Nigeria…

 

Acan Side ɗin su Moddibo kuwa cikin sanyi yace.

“Kiyi haƙuri ki daina kukan nan”.

Cikin matsanancin kuka take janye hannunta daga cikin nasa tana mutsu-mutsu da jikinta alamun so take ta kwace kanta murya a disashe tace.

“Ni zan tafi”.

Ganin haka ne yasa ya kuma ajiyeta akan kujeran kana ya durƙusa gwiwoyinsa agabanta sai kuma ya riƙe hannayenta tare da buɗa tafin hannunta duka biyu ya daura akan sajensa wanda yake da yaƙinin tana so, idanunsa ya ɗago ya kalleta cikin wata raunatacciyar murya mai cike da rauni da tausasawa yace.

“Kiyi haƙuri kukan yana samun ciwo da ƙuci azuciyata kiyi haƙuri kibar Kukan”.

Ina kukanta ta cigaba dayi tana cewa.

“Ni zan koma bazan zauna anan ba garin da bansan kowa ba!”.

Lumshe idanunsa yayi kana ya buɗesu akanta yace.

“Ba gani ba ai kin sanni Yah Mu’allim ɗinki nefa, ko dai yanzu kin daina son nawa ne”.

Cikin zubda hawaye tace.

“Ni ba mai sona a nan”.

Tafin hannunshi yasa yana sharce mata hawayen tare da cewa.

“Kiyi haƙuri bana so inajin kukan yana tada min hankali yana samin ciwo azuciyata kiyi haƙuri ki daina Kuka *Minha Vidaa* bana son ki daina”.

Sai kuma ya taune lip ɗin sa na ƙasa tare da faɗin.

“Idan har ina jin tsoron da takaicin kukan wani ɗan Adam to Kukan kine Yana min suya da ƙuna azuciyata dan Allah ki daina zubda hawaye ki ki kalleni nine fa Yah Modibbo ɗinki da kikacewa su Lamido shi kikeso, ko dai kin daina Sona ne *Minha Vidaa?*

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Ni dai zan koma gida aikaima ba sona kake ba In banda cin zalina babu abinda kake min tunda muke atsawon rayuwata zalina kake ci, kasa adakeni ka sani kaɗe ɗankwali  ka zalunceni kuma yanzu ma in na zauna mugunta zakai tamin”.

 

Kai ya girgiza cikin fesar da numfashi yace.

“Bazan miki mugunta ba *Minha* niba mugu bane”.

Cikin shesh-sheƙan kuka ta girgiza kai tare da cewa.

“Baka Sona katsaneni su Momy suka yarda suka kawo Ni wajen wanda baya sona ya tsaneni suka tafi suka barni”.

Runtse idanunsa yayi tare da faɗin.

“Nine bana sonki *Minha?*”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh mana baka sona basai mugunta kake tamin ba”.

Kai ya dafe cikin jin zafin hawayenta yace.

“Yaushe nace miki bana sonki, kuma yaushe nai miki mugunta?”.

Cikin tura baki da shesh-sheƙa ta goge fuskarta tace.

“Shekaran jiya da daddare ba mugunta kayi min ba kakusan ka kasheni, kuma sai Allah ya saka min duk muguntar da kake min”.

Cikin taushin lafazi mai cike da kulawa cikin muryar da kashe jiki da zuciya yace.

“Toh kiyi haƙuri ki yafe min ki daina yimin Allah ya isa”.

Hawaye na kwaranya daga idanunta ta maƙe kafaɗarta da cewa.

“Wallahi bazan yafe ba”.

Da damuwa asaman fuskarsa ya motsa laɓɓansa tare da cewa.

“Ya Salam mijinki ne baza ki yafewa ba *Minha* ”.

Kai ta gyaɗa cikin tabbatar wa tace.

“Eg bazan yafe ba tunda zalina kakeci”.

Sai kuma ta kifa kanta ahannun kujera ta cigaba da yin kuka.

Duk rarrashin ta da yake taƙi yin shiru.

 

Ahankali ya miƙe ya nufi bedroom ɗin sa, ganin ya tafine yasa ta yunkura cikin sauri ta miƙe ta nufi ƙofa tana murɗa handle ɗin taji kofar arufe, komawa tayi ta zauna kan kujeran data tashi kana ta fashe da sabon kuka fahimtar ya rufe ta yadda bazata iya buɗewa bane.

 

Moddibo kuwa yana shiga bedroom ya ɗauki wayanta.

Call log yashiga number Momy ya Kira buga ɗaya ana biyu ta ɗauka yana dai-dai bakin ƙofan zai fiti  falo yaji Momy ta ɗauka cikin nutsuwa, girmamawa, Mutumtaka, kara gami da risinar da Kansa ƙasa yace.

“Momy Barka da Safiya”.

 

“Barka dai Moddibo ko?”.

Cewar Momy.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Eh Momy nine”.

Kai ta jinjina tare da cewa.

“Ya gida yasu Khausar suna lafiya?”.

Cikin damuwa da yanda yake jin shesh-sheƙan kukanta yace.

“Momy tana lafiya amma tunda su Hajja Nana suka tafi take ta kuka Momy nayi-nayi ta daina Kukan taƙi”.

Cikin raunin Murya irin na wanda ke gab da zubda hawaye ya ƙarasa Maganar saboda har cikin ransa yake jin kukanta sai kuma ya cigaba da faɗin.

“Momy dan Allah ki rarrasan min ita kukan zai sa mata zazzaɓi Momy ki rarrasheta ki bata haƙuri”.

Cikin sauƙe ajiyar zuciya Momy tace.

“Yanzu ina Khausar ɗin?”.

Ahankali yace.

“Gata nan”.

Dai-dai lokacin kuma ya isa gaban Khausar ɗin durƙusawa yayi agabanta tare da manna mata wayar akunnenta.

 

Momy kuwa ahankali tace.

“Hello Khausar”.

Ta buɗe baki da niyyar cewa na’am Momy kenan kuma kuka ya kufce mata cikin rauni tace.

“Momy sun tafi sun barni basu barmin kowa ba babu wanda na sani”.

Sai kuma tayi shiru sakamakon kuka da yaci ƙarfinta kusan minti biyu ta ɗauka tana kuka still wayan na maƙale kunnenta.

 

Kallonta kawai Moddibo keyi ya rasa me yake masa daɗi suya yake jin zuciyarsa nayi, hannunta ɗaya na riƙe da nashi yana shafa sajensa yana kallonta ji yake kamar ya buɗe ƙahon zuciyarsa ya sata acikin ya rufe kofar koda zata daina kukan.

Ganin yadda hawayenta ke kwaranya ba ƙaƙƙautawane yasashi, ɗan ƙara matsota, tafukan hannunsa yasa ya tallabe fuskanta tare da matso da tashi fuskar a hankali ya zare harshen sa.

Wani irin dogon ajiyar zuciya Khausar taja a lokacin da taji, sanyin tattausan harshensa yana ratsa kumatunta.

Shi kuwa Modibbo cikin yanayi na musamman, ya fara lasan hawayenta tare da hanasu zuba.

Ita kuwa Khausar haka nan taji ta gaza barin kukan.

 

Ganin baza tayi shiru ba yasa Momy cewa.

“Toh yanzu magana zakiyi ko Kuka zakiyi Khausar?”.

Cikin kuka sosai tace.

“A’a Momy”.

Sai kuma ta cigaba da kuka.

 

Cikin ɗaure fuska Momy tace.

“Idan baki daina Kukan nan ba kashe wayar zanyi”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Momy na daina”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauƙe kana tace.

“Wai ni kam Khausar kinyi hauka ne? meyesa baki  da hankali ne? Nace wai  hauka ne a kanki?”.

Cikin ƙoƙarin hana kanta kuka da shesh-sheƙa take girgiza kai.

 

Modibbo kuwa a hankali ya lumshe idanunsa domin yanajin duk abinda Mommy ke faɗa, sai kuma yaci gaba da lasar kumatunta da duk ɗigon hawayen da zai ɗiso.

 

Momy kuwa cikin haɗa fuska tace.

“Waye kika taɓa ganin yayi haka?.

Ke dama kin ɗauka Aure wasa ne?

to ki nutsu ki maida hankalinki cikin jikinki kisan abinda kike yi Aure ba abin wasa bane Aure Sunnar Manzon Allah (S.A.W) kuma Aure unarnine na Allah da Manzonsa sannan kuma keda kanki kikace zaki rayu dashi a ko wanne yanayi.

Dan haka babu yanda za’a yi adawo dake kin taɓa ganin anyi Auren ƴa mace ta koma gidansu?”.

Cikin matsanancin kuka ta girgiza mata kai Momy kuwa cikin nutsuwa ta cigaba da faɗin.

“Hakkine da iko da matsayin miji duk inda yaga dama ya ajiye matarsa ya za’ayi Kice ya dawo dake hauka ne akanki?.

Haka Ummi da muka yi waya take faɗa min Haiydar nata kuka kamar ransa zai fita saboda ya tafi ya barki kina kuka duk hankalinsa ya tashi zaki sa yaro adamuwa kisa ya dawo min da zazzabi shi kansa mijinki kin tayar masa da hankali”.

Cikin faɗa ta cigaba da cewa.

“Har mijinki zai riƙa rarrashinki yana cewa kiyi haƙuri amma ki ƙi kiyita kuka kamar ibada”.

Khausar kam shesh-sheƙa ta cigaba dayi so take ta hana kanta kuka amma kukan yaƙi haɗiyuwa.

 

Cikin damuwa Momy ta cigaba da cewa.

“Ok zakici gaba da kukan kenan?”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“A’a Momy na dainaaa”.

Irin yanda take kukan har numfashinta na yankewa.

 

Momy kuwa cikin damuwa ta cigaba da faɗin.

“Mijinki yaita rarrashin ki ki ƙi rarrashuwa hauka ne akanki, Kiyita kuka kina cewa zaki da kowa ba ganan Maman mijinki ba ai zata zame miki madadina in dai kika mata biyayya zata maye miki gurbina mijinki kuma dole ki masa biyayya sannan ki bishi sau da ƙafa domin shine komai na rayuwar ki a yanzu saɓa mishi kamar saɓa umarnin Allah da Manzonsa ne da suka ce Ayiwa miji biyayya”.

Kuka ta cigaba dayi tana jan ajiyan zuciya.

Moddibo kuwa ganin Momy nayi mata faɗa sannan bata daina kukan ba yasa ahankali yasa hannu ya zaro wayar daga kunnenta kana ya mayar kunnensa cikin sanyi da ƙasƙantar da kai murya a raunace yace.

“Kiyi haƙuri Momy rarrashinta za’a yi ba faɗa za’a yi mata ba”.

Yana maganar kamar zaiyi kuka.

 

Kai Momy ta girgiza kana tace.

“Khausar baza taji rarrashi ba idan ta fara kuka batasan bari ba kafita harƙanta ka barta idan tayi Kukan tagaji da kanta zata bari ka barta na lura Khausar rigima ne da ita”.

Sake ƙasƙantar da muryarsa yayi yace.

“Momy kiyi haƙuri In Sha Allah zan rarrasheta za tayi shiru Mommy bayan iya barinta tana kukaba zai cutar min da ita”.

Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan sai anjina”.

Ahankali ya sanya hannunsa kan kumatunta ya fara share mata hawaye kana cikin sanyi da taushin lafazi yace.

“Kiyi haƙuri ni ba mugu bane bazan miki mugunta ba, nifa Mijinki ne ba kyau kada ki sake cewa mijinki Mugu bakya tsoron Allah ya ƙona kine?”.

Cigaba da kuka tayi wanda yake fitowa daga ƙasan ranta cikin rauni tace.

“Aini ban ce maka mugu ba amma dai kana cin zalina shekaran jiya kusan kasheni kayi kuma Allah zai sa kamin”.

Sake ƙasa da murya yayi cikin taushin lafazi yace.

“Kiyi haƙuri In Sha Allah bazan sake ba ki yafe min kinji ki yafewa Yah Moddibonki Minha”.

Kafaɗa ta maƙale tare da tura baki da juya kumburarrun idanunta tace.

“Ni dai ban yafe ba sai Allah ya saka min daga duniya har kiyama bazan taɓa yafe maka ba”.

Zare idanunsa yayi sai kuma ya langwaɓar da kansa yace.

“Ayyah Khausar am ki yafemin kiyi min duk horon da zaki min amma kiya femin”.

Cikin shesh-sheƙan kukan ta kallesa kana ta tura bakinta tace.

“Da gaske?”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Yess kimin duk hukuncin da kikaga ya dace da laifina, Amman banda kuka kuma banda cewa bana sonki da kuma cewa zaki koma”.

Cikin sauƙe numfashi shesh-sheƙan tace.

“Toh nima yanda kake cin zalina sai na rama ka kaɗe ɗankwali”.

Ba zato yaji murmushi ya sufce masa sabida mgnar tazo mishi a bazata.

Ya kuma lura yadda tayi mgnar kamar hakan shine babban burinta, ɗan ware idanunsa yayi tare da cewa.

“In kaɗe ɗankwali kuma?”.

Cikin tura baki ta gyaɗa kai tace.

“Eh kaima ba haka kake min duk abinda nayi kaima mugunta da kayi min ka kaɗe ɗankwalin kaji abinda nake ji”.

Numfashi ya fesar cikin tsira mata ido yace.

“Idan na kaɗe ɗankwalin zakiyi shiru?”.

Da sauri ta gyaɗa masa kai tare da faɗin.

“Eh”.

Sassayan ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Toh kawo ɗankwalin in kaɗe sau nawa zan kaɗe?”.

Kallonsa tayi ta wani tura bakisai kuma tace.

“Da gaske zaka kaɗe?”.

Girarsa ɗaya ya ɗaga mata.

Cikin jin dadi tace.

“Toh Sau hamsin zaka kaɗe”

 

Ware manyan idanunsa dake narke yayi tare da yarfe hannu da faɗin.

“Wayyo Allah na Ni Aleeyu”.

Sai kuma ya zauna ya kifa kansa akan cinyarta cikin langwaɓar da kai yace.

“To ai zaki kashe mijinkeeh”.

Ya ƙare maganar cikin shu’umar muryar da tasa jukinta mutuwa,

Ƙyafƙyafta idanunta tayi kana tace.

“Ba nima kana sani ina kaɗewa sau 30 ko sau 20 ba?“.

A hankali yace.

“Toh ai ke 50 kikace inyi”.

Cikin sharce hawayenta tace.

“Toh kasan Ai laifin da kayi yafi nawa yawa da zafi ko?”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Toh shikenan kawo ɗankwalin In kaɗe”.

 

Ɗankwalin abayar kanta ta cire ta miƙa masa karɓa yayi yana ɗan buɗawa.

Baki ta tura tare da cewa.

“Ai wannan ma bashi da nauyi bari In ɗauko maka ɗan kwalin Less”.

Saurin riƙo hannunta yayi ganin ta yunƙura yace.

“Ainima wanda nake saki kike kaɗewa bana Less bane kin manta?,Na Uniform ne na Uniform kuma be kai wannan kauri ba”.

Baki ta tura tare da faɗin.

“Toh ka kaɗe”.

Cikin tsira mata idanu yace.

“Ina idan na kaɗe zakiyi shiru?”.

Gira ɗaya ta ɗage cikin jin dadi tace.

“Eh mana kai dai ka kaɗe na gani”.

Murmushi yayi kana yace.

“Toh ki share hawayen ki”.

Ba musu ta sanya hannunta ta share hawayen yayin da take sakin murmushi tana tuna yanda take jin azaba ahannunta idan ta kaɗe sai kuma ta ɗan ɓata fuska da faɗin.

“Toh kaje ka kaɗe mana”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh muje”.

Kallonsa tayi da kumburarrun idanunta tace.

“Ina?”.

“Muje mana kiga yanda zan kaɗe”.

 

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Ok”.

Hannunta ya riƙe suka shiga bedroom ɗin kana suka wuce Bathroom.

 

Bocket ya jawo ya sa ɗankwalin kana yasa ruwa.

Juyawa yayi ya kalleta tana tsaye bakin ƙofa tana murmushi kuma har zuwa lokacin tana sauƙe ajiyar zuciya na kukan da tayi amma kuma fuskarta ɗauke da murmushi ya lura kaɗe ɗankwalin zai sata farin ciki ganin itama yau ta samu ƴanci zata sashi aiki cikin langwaɓar da kai  ya kwaikwayi muryarta yanda take roƙon sa abaya yace.

“Ayyah Yah Mu’allim a kiyi haƙuri mana In cire rigar jikina kar in jiƙe”.

Ka faɗa ta maƙe kana ta tura bakinta tace.

“Ai kaima lokacin da kake sani kaɗewa harda hijabi ma ajikina da kuma Uniform ɗina haka kuma nake kaɗewa”.

Sake langwaɓar da kai yayi tare da narkar da murya yace.

“Kenan yanzu bazan cire Jallabiyar ba?”.

Kai ta gyaɗa tana murmushi tace.

“Yesss Of Course kayi ahakan”.

Ta ƙare maganar tana cilla girarta sama fuska ɗauke da murmushin mugunta.

Kai ya gyaɗa tare da tsugunnawa ya matso ɗankwalin acikin bokitin”.

Cikin sauri ta wani tura baki tace.

“Ai ba’a matse ɗankwalin sosai kaɗan ake matsewa”.

Ta faɗa tana karasa shiga cikin Banɗakin abakin Bathtub ɗin ta zauna shikam cikin wani irin yanayi na musamman ya fara kaɗe ɗankwalin na farko, hammm ya ja numfashi sabida sanyi ruwan daya watsu a jikinshi,

sai kuma ya kaɗe na biyu kana ruwan ya watsu a fuskarsa sake kaɗewa yayi Still ruwan ya sake watsuwa afuskarsa tuni  sajensa ya jiƙe.

 

Ido ta tsirawa Sajensa tana sakin murmushi Allah ya sani sajensa na masifar yi mata kyau musamman yanzu da fuskarsa ta jiƙe da ruwan sai ƙyallin sajen keyi murmushi kawai take tafi kowa sanin yanda zaiji a hannayensa idan ya kaɗe.

Moddibo kuwa sau bakwai ya kaɗe sai kuma ya tsugunna zai mayar cikin Bokitin.

Cikin sauri ta kamo hannunsa tace.

“Wallahi sai ka sake kaɗewa ai bai bushe ba”.

Lumshe idanunsa yayi tun lokacin da hannunta ya sauƙa kan nasa jin tsikan jikinsa na tashi saboda laushi da kuma santsin hannunta haka nan ya tsinci kansa cikin wani irin farin ciki da shauƙi da kuma nishadi ɗan marairaice fuska yayi kana yace.

“Toh shikenan”.

Sai kuma ya ƙara uku kafin ya kalleta yace.

“Toh yayi In tsoma”.

Cikin jin daɗi ta gyaɗa masa kai sake tsomawa yayi ya matse zuwa lokacin baki ɗaya Fuskarsa ta gama jiƙewa har ruwan na ɗiga tal-tal-tal kana gaban Jallabiyarsa ma ya jiƙe ahaka dai har ya tsoma sau biyar ya kaɗe sai kuma ya ajiye ɗankwalin acikin Bokitin ya riƙe ƙugunsa tare da cewa.

“Wayyo Allah ƙuguna”.

Still sajensa na ɗigar da ruwa til-til-til.

Dariya ta ƙyalƙyale dashi harda dafe ciki.

Tsayawa yayi yana kallon yanda dimples ɗin ta ya lotsa da kuma yanda fararen haƙoranta suka bayyana suna sheƙi duk da cewa ga yanda fuskarta yayi ja da kuma idanunta suka kumbura cikin ƙyalƙyala dariyar tace.

“Madallah ka dai ji yadda nake ji. Allah ya ƙara ai nima haka nake ji kuma wallahi saura arba’in da biyar”.

Ta ƙare maganar tana mishi signal ɗin daya sashi jin wani irin fitinenne abu na zirya daga tsakiyar kansa har zuwa tafin sawun shi.

Karya kai yayi tare da langwaɓar da murya yayi kalar tausayi kamar yanda da take masa yace.

“Dan Allah Malama kiyi haƙuri arage min yawansu yayi yawa hannuna ciwo yake”.

Cike da farin ciki ta  kuma fashewa da dariya kana ta miƙe ta riƙe ƙugu tace.

“Haka nake ji kaima kayi”.

Sai kuma ta zuba wa sajensa idanu tana kallon yanda ruwa ke cigaba da ɗiga tal-tal-tal.

A hankali yasa babbar yatsarsa na hannunsa na dama ya kwantar da gashin giransa tare da zira mata idanu.

Ganin ta kifi tafin hannunta kan sanjeshi tana ɗan katse ruwa tare da cewa.

“Bari in gogema maka ruwan”.

Sai kuma ta ƙare maganar da yin murmushin da zuba idanunta kan sajen da kyau.

Ya lura batama sanin lokacin da take kai hannunta kan sajenshi, ganin yadda ya tsira mata idonsa ne yasa tai saurin janye hannunta.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin fitinenne flenings ya ɗan sake matso ɗan kwalin Abayar ya sake kaɗewa dake ta miƙe tsaye tana kusa dashi haka yasa ruwan ya jiƙata.

A tare suka saki ajiyar zuciya.

Ita kuwa gira ta kuma ɗaga mai tare da cewa

“Ya akayi?”.

Cikin fitinenniyar murya can ƙasan maƙoshinsa yace.

“Zaki kasheni“.

Murmushin mugunta tai tare da cewa.

“Ba wani mutuwa sai wuya dai, ci gaba, tunda ban mutuba in sha Allah kaima bazaka mutuba”.

Cikin narke fuska yace.

“Uhmmm bayan wuya kuwa zamsha daɗi ba“. Sai kuma ya sunkuya ya cigaba da kaɗewa har yayi na takwas Kallonta yayi tare da faɗin.

“Wayyo Didi na hannuna ciwo Allah hannuna zogi yake min Minha”.

Dariya ta ƙyalƙyala kana tace.

“Allah ko goma baka yiba kuma sai ka ƙara”.

Juyawa yayi ya fuskanceta kafin yace.

“Kiyi haƙuri ni koma me kike so ki sani amma banda kaɗe ɗankwalin nan yana da wahala”.

 

Ware Idanunta tayi tace.

“Kaima haka kake yimin ba haka kake sani ba dan haka kaima sai kayi,yau kam sai kayi”.

Yana yarfe hannu yace..

“To ai nayi amma arage min kingani kin ninka min yayi yawa ki bari sai gobe In ƙarasa,in yaso yau inyi 25 gobe inyi 25”.

Ɗan shiru tayi kamar mai nazari sai kuma tace.

“Toh kayi 25 ɗin, kayi na yarda”.

Shafa sajensa yayi tare da cewa.

“Kuma nima ai ashirin nake saki”.

Ƙugu ta riƙe kana tace.

“Toh aini laifina kaɗan ne”.

Kwaikwayon maganar ta yayi yace.

“Toh nima ki bari idan na sake miki lefin sai ki sani”.

Da sauri tace.

“Zaka sake laifinma kenan?”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Yess sosai ma kullumma kuwa,bai kema kullum sai kin maimaita laifi dan haka nima banyi alƙawari bazan ƙaraba”.

Cikin kwaɓe fuska tace.

“Wlh komawa zanyi”.

Sai kuma ta kalleshi jin yana cewa.

“Kiyi haƙuri wasafa nake, wanda nayima na tuba ki yafemin”.

Cikin jin dadin cewa yau ita kesa Moddibo irin punishment ɗin da yake sata kuma yanayi harda ƙaramar murya yake mata cikin jin dadi tace.

“Toh ka kaɗe, Ka kaɗe”.

Kai ya gyaɗa kana yasa ita kam dariya ta cigaba dayi yayin da yake jin wani irin farin cikin ganin murmushin ta da kuma yanda idan yace ya gaji take dariya yasa duk kaɗewa ɗaya sai yace.

“Wayyo hannuna”.

Ita kuma sai ta fashe da dariya ahaka dai har akayi ashirin tana ƙyalƙyala dariya kamar ba ita ke kuka ba yanayin yanda ruwan ke sauƙa a fuskarta sai ya zama fuskar ta wanku fes juyawa tayi kan abin alwala ta wanke fuskarta sai ta juya ta kallesa lokacin daya kade na 25 yana ƙoƙarin maida bocket ɗin inda ya dauka tare da sanya ɗankwalin acikin kana yace.

“Wayyo Hannu na ya mutuuuuu”.

Dariya ta sanya tare da faɗin.

“Nima haka nakeji duk randa aka sani kaɗe ɗankwalin nan na koma ko rubutu bana iyawa sai dai Haiydar ya min kaima yau kaji yanda nake ji”.

Juyawa tayi ta nufi hanyar fita.

Da sauri ya tsaya gabanta yace.

“Toh Ni yanzu ko rigana ma bazan iya cirewa ba gashi duk ya jiƙe ki taimaka min ki cire min”.

Kafaɗa ta maƙale tace.

“Um-um nima ai idan ka sani da kaina nake cirewa kacire ka gani kaima idan zaka iya ka dai ji yanda nake ji”.

Cikin langwaɓar da kai yace.

“Toh shikenan”.

Sai kuma ya tsugunna ya kamo ƙasa  Jallabiyar ahankali ya zaro tare da faɗin.

“Wayyo hannuna”.

Cikin sauri Khausar da takai bakin kofa zata fita ta juya jin maganarsa dariya ta ƙyalƙyala dashi.

 

Yana cire Jallabiyar ya saƙale ahanga dake ban ɗakin.

Ita kuwa ahankali ta zubawa sajensa dake ƙyalli ido sai kuma ta maida idanunta kan gashin ƙirjinsa dake kwance luf-luf.

Ahankali ya matsa kusa da ita.

Yayinda ita kam baki ɗaya idanunta na kan ƙirjinsa.

Yana isa jikinta ya janyota kana ya rungumeta aƙirjinsa yana saki wani sanyayyan ajiyar zuciya kanshi ya cusa tsakanin wuyanta da kafaɗarta a hankali ya kai bakinsa saitin kunnenta yace.

*“Minha vidaa* Kin huce ko? Kinji daɗi kinsa mijinki wahala?”.

Kai ta Jinjina tace.

“Eh amma dai zaka ƙarasa saura guda 25”.

Cikin sauƙe numfashi ya shaƙi ƙamshin ta yace.

“In dai zakiyi dariya kaɗewan zai saki farin ciki ko guda dubu kike so zanyi miki *Minha vidaa*”.

Lumshe idanunta tayi.

Shikam ahankali ya riƙa cusa yatsun ƙafansa ƙarƙashin ƙafanta wanda yasa dole ta daura tafin ƙafan ta akan rumfar ƙafansa yana jin haka ya manna kanta da ƙrjinsa ahankali ya fara ɗaga ƙafansa yana takawa har suka fito yana tafiya da ita, ɗin yaja ƙofan ya rufe…

 

Suna shiga tsakiyar bedroom ɗin ya matsa da ita bakin gado akunnenta ya raɗa mata

“Kijifa kema kin jiƙe”.

Baki ta tura cikin kasala tace.

“Uhm toh ba kaine ka jiƙani”.

Yana lumshe idanunsa yace.

“Bake bane kika tsaya kina min dariyar mugunta ba”.

Dariya ta sanya Amma batace komai ba.

Akasalance yace.

“Yanzu ma dariyar kike min ko Minha”.

Cikin lumshe idanu tace.

“Eh mana kaima ba dariyar mugunta kake min ba”.

Yana fesar da numfashi yace.

“Ni na taɓa yi miki dariya ne?”.

Tana tura baki ta ɗan gyara tsayuwar ta akan ƙafarsa tace.

“Baka min dariyar, tunda kasan kayi min Mugunta ai kai kaji daɗi ma nayi maka dariya kai ban taɓa ganin haƙorinka bama”.

Sanyayyan murmushi ya saki tare da cewa.

“Aikam naji daɗi kiyi min dariya nayi farin ciki, kuma ke yanzu ai ba haƙorina bama, ba gashi harda ƙirjina da duka jikinama kike kalloba shekaran jiya har kusan tsinkemin lips nafa kikayi Minha vidaa da kyar na tsira dasu”.

Cikin sauri ta runtse tare da cusa kanta a ƙijinsa.

Sai kuma tayi saurin buɗe idanunta jin ya zuge zip ɗin rigarta yayi ƙasa da ita.

Cikin tura baki tace.

“Sanyi fa”.

Muryansa ashaƙe yace.

“Badole kiji sanyi ba rigar ta jiƙe ki bari In cire miki shi kiji ɗumi”.

Kafaɗa ta maƙale tace.

“Um-um nikam ka barmin rigana”.

 

Numfashi ya fesar yace.

“Zai saki mura Ni kuma bana son abinda zai cutar *Minha* ”.

Shuru tayi jin yanda ya zuge rigar sannan yayi ƙasa da hannunta ya cire acikin rigar runtse idanunta tayi lokacin da taji ya zare ɗaya hannun rigar ya zama ta gaba ne kaɗai ya rage baya yaja kaɗan rigar ya faɗi runtse idanunta tayi.

Cikin sauri da bugawar zuciya ya rumtse Idanunsa jin tudu da taushin Breast ɗin sun sauka kan ƙirjinsa ga sanyi daya ratsa fatar jikinsa wani sanyayyan ajiyar zuciya mai ƙarfi ya saki atake jikinsa ya fara sharking Kamar anjona masa Shorking.

Cikin wani irin sauri tasa hannu ta zagaye ƙugunsa da ƙarfi yayin da take jin wani irin abu yana game jikinta mai cike da shauƙi.

 

Shikam wani irin abune ya tsiga masa tun daga tafin ƙafarsa har ƙwaƙwalwar kansa yayin da idanunsa suka sauya lips ɗin sa suka hau rawa hannunsa dake rawa ya ɗaura akan skintied ɗin ta ya fara murzuwa yana ƙasa dashi.

Da sauri ta tura bakinta ta riƙe kana tace.

“Wayyo Allah ka bari bana so”.

Ahankali ya zauna bakin gado da ita tare da jingina bayansa da jikin gadon ya ɗan ware ƙafafunsa yasata atsakiyar ƙafansa  blanket ɗin ya ware ya rufe su cikin mayatacciyar murya yace.

“Ai kin san ba kyau fa tauye haƙƙin miji, haka zaisa ki faɗa cikin fushin Allah, kina son Allah yayi fushi dake?”.

Cikin sanyi take girgiza mishi kai tare da lafewa a jikinai tana shaƙan.

Wani irin ƙamshin blanket da taushinsa da kuma sanyinsa ɗakin suka haɗu suka sauƙar mata da kasala da mutuwar jiki ahankali ta manna kanta da jikinsa dai-dai kan maransa.

Cikin sauƙe numfashi yasa hannunsa duka biyu ya ɗago ta kana ya manna ƙirjinta da ƙirjinsa ya zamana kanta na dai-dai ƙasan gemunsa yana shinshinan kanta ahankali ya fara shafa bayanta sai kuma ya sauƙe hannunsa kan skintied ɗin ta yana ɗan tura hannunsa kan mazaunanta.

 

Da sauri ta runtse idanunta kana tasa hannunta ta rungumo bayansa ɗaya hannun kuma yana kan sajensa tana shafawa ahankali ya matso da bakinsa kan kunnenta cikin wata kasalalliyar murya yace.

“ *Minha* ”.

Lumshe idanunta tayi zuwa yanzu ta fahimci wani sunane da yake kiranta dashi wanda batasan me manufar saba may be wani abune daban sai wata zuciyar kuma tace waya sani ko ƴar Iska yake nufi tunda yace min Fattanah Rigimammiya yanzu kuma yana ce mata *Minha vidaa* wata ƙil ƴar Iska yake nufi dan yaga yayi abu da ni kuma Allah ya sani nidai ba ƴar Iska bace ta ƙare maganar zucin tana ƙoƙarin tashi.

Da sauri ta koma ta faɗa jikinsa ganin lokacin data tashi yasa hannu ya tallafe ƙirjinta da hannunsa ɗaya kana ya kamo hannunta ɗaya kuma ya ɗaura kan mararsa……

 

 

 

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button