Hausa NovelsHausa NovelsTabarmar Kashi Book 2

Tabarmar Kashi Book 2 Page 11

Sponsored Links

Book 02 Page 11

Wani irin mugun sanyi dukka qafatunsa sukayi,cikin nutsuwa yake takowa gabanta bayan ya sake jaddada sallamarsa kansa a qas,yana jinsa a matsayin wani gagarumin me laifi. Qoqarin zubewa yake a gabanta amma sai ta miga masa dukka hannayenta,baiyi jinkiri ba ya sanya nasa hannuwan a ciki,tayi masa mazauni a gefanta fuskarta dauke da murmushi me hade da hawaye

“Kar kace komai,basai ka nemi gafarata ba,na riga nayi maka dukkan uzuri har a gaban
Allah,na yafe maka kai da dukkan zuri’arka”

majin ta fada tana dauke hawayen fuskarta lokacin da yake zaune a gabanta kansa a qasa har yanzu ya gaza cirashi,yana jin kan nashi yayi masa wani irin nauyi,kunya da nauyinta suna cikashi. Dai dai lokacin hajiya qarama ta hadiyi yawu da gyartaja da baya a hankali ta koma inda ta fito, zuciyarta na wani irin gonewa

“Bani labarin yadda rayuwa ta kasance” ta fada tana sakin murmushi,abinda ya sanyashi daga kansa,ya sauke idanunsa cikin na mahaifiyarsa,wani siririn murmushi ya sauka saman miskilar fuskarsa.

**********K’arfe biyu da rabi na ranar juma’a,babban masallacin juma ar dake iya daukar dubban jama’ar musulmai a wannan ranar a cushe yake da garin baqi daga qasashe daban daban da kuma garuruwan dake QASATA Nigeria domin halartar shaida daurin auren MUHAMMAD TAUFEEQ JARMA da amaryarsa KHADIJA MUHAMMAD
GIREMA,bayan gama daura auren AFIFA
AHMAD da MUHAMMAD SAJJAD a asalin garin mahaifinta da dr mamman yace lallai aje tushenta ayi don karramasu.

Duk yadda takeso taii cikin ranta da jikinta cewa yau din ba wata rana bace ta daban da dukka sauran ranakunta na rayuwa ba,yau din sunanta amarya a karo na biyu dukka taron al’ummar dake gidan da masallacin sunzo ne don su shaida ta zama matar MT JARMA hakan ya faskara,tana gayawa kanta akasin hakan zuciyarta na jaddada mata qarya take fadi,a haka ta dinga jin rauni,raunin da yakai ga zubar hawaye a idanunta masu yawa da zafi.

* MUHAMMAD TOUFEEO RESIDENT *

Kai kawo takeyi cikin dakinta,wanda a qalla ta kusa awanni biyu cur tana yinsa ba tare data zauna ko kuma ta huta ba.
Tashin hankalin da take ciki ya zarta duk yadda hankali zai iya dauka,ya kuma shafe tunanin me tunani. Asara mafi muni tare da faduwa muraran take gani a gabanta,a dai dai lokacin da tafi bugatarsa a dai dai lokacin da mummunar labarin shudewarsa ta sameta?,batasan haka zata faru da ita,batasan haka zata kasance ba,da babu shakka ba zata bashi baya har na tsahon shekarun nan ba.
A nata ganin da hangen bugatarta ta biya,ya kuma tabbatar mata da cewa qulli me dan karen garfi da warwarewarsa ba’a nan kusa ba,nasara biyan bugata da cikar muradi suna ta zuwar mata fiye da yadda tayi zata,hakan ya sake bata qaimin bazama cikin duniya,taci gaba da rayuwarta ta kuma karbeta a yadda tazo mata tana moreta yadda ya kamata.

Knocking qofarta a kayi,a mugun fusace take,don haka har ta buda baki zata tambaya cikin zafi,sai kuma ta tuna,a yanzu gidan yana cikin yanayin da bai kamata ta bari aga alamun matsala ko wata damuwa a tattare da ita ba,wanann yasa ta furzar da iska sannan tayo tattaki ta bude qofar.

Hajiya mansura ce,ita da hajiya qaraman sukayiwa juna kallon kallo,duk mutumin da ya sansu a shekarun baya,a yanzu idan yaga kallon da sukewa juna zai garyata hakan,duba daya kacal zaka yi musu ka tabbatar da abubuwa masu yawa dake qunshe a zukatansu. Abubuwa biyu itama ke neman zame mata barazana,labiba dake neman zauce mata saboda auren toufeeq,ga kuma saukar shifa a nigeria,labari mafi muni ga kunnuwanta. Abune da bata taba kawoshi ga ranta ba,saboda tana da tabbaci daga gurin masu bata tabbaci.
..ita da Nigerian
har abada,tamkar yadda jinjiri yake barin cikin mahaifiyarsa. Ita kadai tasan abinda take gani take kuma karanta daga gurin Dr jarma,bai cancanci shifa ta shigo Nigeria ba ma sam a irin wannan lokacin

“Amarya na dab da shigowa cikin gidan nan,ya kamata a ajiye zafin rashi ko ayi abinda ya dace” sarai ta fahimci mansurar magana take danqara mata,amma sai ta sake mata wani murmushi,saboda ta tabbatar tana wasa ne kawai da wuta me tsananin ruruwa da azabar turiri cikin rashin sani,tayi imani bata gama sanin ita din wacece ba,da tabbas! batayi wasa da ita har haka ba,saidai kuma zata dandana kalarta ta ainihi, wala’alla a nan gaba kome irin sunanta ta gani da gudu zata gusa daga wajen

“Karki wani damu,dama ni nafi cancanta da karbar matar toufeeg” hajiya qarama ta amsawa mansura. Ciki ta juya tana duban suturar jikinta. Girman kanta ne ya motsa,taji tafi gaban fita haka,don haka ta bude makekiyar closet dinta ta fara laluben suturar alfarma.

llahirin jikinta lullube yake da wata irin
suttura da aka yiwa dinki na mussamman da lafiyayyen yadin silki me tsananin tsada da daukar hankali,sannan akabi adon doguwar rigar silk din da wata rigar me zubin alkyabba ta baqin yadin velvet me adon zaren da aka tsomashi cikin ruwan gold. Tun daga nesan nesa da ita hancinka yana iya jiye maka kwantaccen qamshi me tafiya da tunani da takeyi,ba abinda ke fita daga jikinta sai wani irin haske da walwali ke kashe idanu. Babu abinda ake iya gani a jikinta,sakamakon yanayin shigartata daya rufe ko ina nata ruf,rufewar data bata damar yin kuka me yawan gaske ta qasan hular rigar da aka
Tullubeta da ita. Ba abinda ke mata yawo a tsakiyar kanta sai nasihar Dr girema,maama yaa muhyi yaa Saifullahi da yaa zaid,da kuma shaqigan ‘yan uwa sannan masoya irinsu anty farheen anty samreen.

Can cikin jikinta take jin wani yanayi me kashe zuciya, maganganun da sukayi mata sun shiga jikinta sun kashe duk wani karsashi da rashin damuwa da auren,sun dora mata nauyi me yawa, kalaman da suka furta a gareta,banda tana da aminci da afifa zata ce tabbas ta gaya musu manufarta a auren.

Ido ta lumshe tana jin wata
matsananciyar fargaba lokacin dajerin gwanon lafiyayyun motocin dasuka daukota suka fara cusa kai cikin gidan,a baya qaddara ta sanya ta shigo gidan a sunan nanny,a yanzu a karo na biyu qaddarar ta sake dawo da ita d sunan matar aure kuma matar me gidan,abinda ko kadan bata taba tunanin faruwarsa ba.

Wani irin yanayi taji yana bin sassan jikinta lokacin da hannunta ya game da na hajiya qarama da ta karbeta daga hannun yakura yayar Dr girema,zuciyarta ta motsu lokaci guda. Haka kawai takeiin matar kwata kwata bata kwanta mata ba ko kadan. Saidai har suka doshi sassan da ita kanta sãahar batasan wanne bane saboda kanta na lullube tana iya tsintar muryarta fes tana sake marabtar danginta

“Maji tace a wuce da ita sashenta ta huta,ita
‘yar gida ce a gurinta basai an bata wahala ba,kuma ko yaushe zasu kasance tare” sagon da baaba ramatu ta matso ta shaidawa hajiya garama kenan qasa qasa. Kai ta jinjina,a gasan ranta zuciyarta tana bata tabbas akwai dalilin da yasa shifa ta aikata hakan,amma koma meye har yanzu sauran akaloli suna hannunta,kuma ita zata ci daga da yin nasar kamar yadda tayi a baya.

Tunda ta tsoma gafarta a sashen jikinta da hancinta ta TABBATAR mata wani guri ne daya banbanta da kowanne sashe na gidan,guri ne me tsari da koda idanunta suna a lullube amma hakan bai hanata ganin lallausan carfet dan gasar turkey da qafafunta ke nutsewa a ciki ba. Qamshin da wajen ke fiddawa kawai ya isa ya saukarwa da zuciya tare da ruhi salaama,uwa uba dukka hayaniyar gidan sam sam babu ita a nan,bisa alama ma sun baro mutanen dake dauke da hayaniyar a can baya,sai wani irin shuru da sautin muryoyin da basu wuce biyar zuwa shida ba dake magana da sauti mara hayaniya.

Bata gushe ba tana biye da hajiya qarama dake ci gaba da cusa Kai zuwa hallway din da dakunan baccin sashen suke a jere,wanda aka sake narka kudi aka masa mugun gyara na fitar hayyaci,duk kuwa sa cewa babu abinda ya sameshi, amma a yanzun an masa gyaran da zai dace da rayuwar maaurata.

Zuciyarta dake qirjinta takejin kamar ana hurawa wuta saboda ruwan kudin da taga toufeeq din ya barnatarwa gurin,bayan ta samu dukkan bayanai da huijoji masu qarfi daje bayyana mata cewa ba auren soyayya yayi ba,auren sadaukarwa ne ga diyarsa fadeela,a qalla tafi shekara goma batasha maganin hawan jininta ba,amma a yau batajin zata iya kwana ba tare da tasha din ba.

Wasi wasi yaso cika zuciyarta taf,tunda suke mata aiki tsahon shekarun basu taba kawo mata labarin da ba haka yake ba,amma a yau ta shiga tantama,yadda taga komai ya canza,tayi imanin muddin babu son ron taoufeeq bata zaton akwai wanda ya isa ya sakashi yiwa bangaren irin wanna tsarin da kowa zaiyi burin kasancewarsa a ciki.

Bata fahimci cewa babu kowa a tare da ita ba sai bayan shudewar mintuna goma da sumaira ta shigo tana gaya mata yaa Saifullahi ya bada dokar kada wanda ya zauna. Hannun sumaira ta riqe da kyau,qwalla na sauko mata.
A irin wannan gigitaccen yanayin da take ciki inama acw afifanta tana kusa da ita? itace qwarin gwiwarta,saidai kuma inaaa,zagin soyayya ya sanya dukkan wani qarfi nasa ya nesantata da afifan,tana can itama domin fuskantar sabuwar rayuwa, rayuwar da säahar ke mata fatan ta zama me tsananin zaqi,ba me daci ba kamar yadda ta fuskanci tata.

Bude gofar da taji alamun anyi a
karo na biyu ya sanyata kasa kunne. A nutse take takowa zuwa cikin dakin, idanunta akan rufaffiyar fuskar sãahar,zuciya nata yi mata saqe saqen abubuwan da zata iya aiwatarwa a kanta,saidai duk abinda zuciyar ke gaya mata tana ganin bai dace da ya faru a wannan muhallin ba,a kuma dai dai wannan lokacin ba.
[14/09, 7:44 pm] Mimah Yusuf: *HUGUMA*

Leave a Reply

Back to top button