Hausa NovelsHausa NovelsTabarmar Kashi Book 2

Tabarmar Kashi Book 2 Page 13

Sponsored Links

Book 02Page 13

Cikin nutsuwarsa ya gama komai na shirin bacci,saidai gaba days baccin ya gagara zuwa a idanunsa,ganin dazun yayi affecting tunaninsa sosai,abinda bai taba kawowa cikin ransa zai zama wani abu har haka ba. Da kansa ya buda qofar dakinsa ya wuce kitchen ya hada coffee ba tare daya bi takan abincin dake jere a dining ba,aikin jacob kenan, baya wasa da aikinsa,duk wata hidima da ake muddin yana qasar yana kuma gari baya fashin dafa masa abinci,ko a yanzun duk hidimar da akeyi cikin gidan part dinsa baisan anayi ba,shi yasa yakeji da jacob din shi da wanda yake tsaftace masa sashensa.basu da wasa sam a aikinsu

Dakinsa ya dawo,ya buda balcony
din dake manne dashi,duk da cewar dare ne amma bai damu da hakan ba,bacci kawai yake nemawa idanunsa tare da hutu da nutsuwar
ruhi da gangar jiki.

Kurba daya yayi masa kamar lokutan
baya ya ajjiye saman dan qaramin table din dake a gefansa,tun daga waccan ranar daya dandani taste din coffe dinta kowanne ya daina masa dadi a harshensa,saidai yasha Black tea Kawaltunda bava snan madara kwata kwata,ko ya gwada shan madaran da nufin ko zai yi masa irin taste din milk tea dinta
sai yaji gaba daya basu hada hanya ba.

Tafin hannayensa ya hada yana murzawa
guri guda da sauri da sauri,lokaci guda ya dakata yana furzar da iska daga bakinsa,dai dai lokacin da wayarsa tayi qara. Mamakin wanda zai kirashi a dai dai wannan lokacin da sha daya na dare tayi ya kamashi,ya qarasa inda ya aje wayar a hankali ya dauka yana duba me kiran,sai kuma kiran ya katse,sagon da ya gani da number sajjad yaja hankalinsa,yayi sliding ya bude wayar ya shiga saqon

_Duk wani nutsuwa farinciki walwala da kwanciyar hankali yana tattare da diya mace muddin ka dace,ka raya darenka na yau da kyau da soyayya da kawo jituwa da fahimtar juna tsakaninka da iyalinka,zaka fahimci inda maganata ta dosa_ tsaki yaja,sajjad yana bashi ciwon kai,baisan mata bane,amma yana da tabbacin zai dawo daga mararin gardin da yake ganin ya samu. Muddin diya macace tabbas wataran sai ta bashi madacin da zai maye gurbin zaqin zumar data lasa masa a harshensa,duk kuwa da cewa baya taba yiwa wani wannan fatan bare sajjad din da dadi wuya ko tsananin yana tsaye tare dashi.

Kira ne ya shigo wayar tasa lokacin da kwanyarsa ke shirin nutsawa duniyar tunani.
A nutse ya dauki wayar ba tare da tantama shakka ko mamakin kiran da akayi masan a dai dai wannan lokacin ba,saboda waya ce da dukka kiran da zai biyo ta cikinta ya tabbatar kira ne me muhimmanci da ya shafi duk wani makusanci a gareshi.

Cikin lallausar muryarsa da ta gara yin wani irin sanyi saboda yanayin da yakeji yana bibiyar kowace gaba ta jikinsa. Saidai a maimakon amsar sallamar,sai sautin kukanta cikin siriryar muryartan me matugar siranta qwaral ta maye gurbi. Wayar yadan cira yana duba number din ya tabbatar babu wanda zai kirashi da number wannan qasar sai mutum daya wato HASEENA

“Yaa toufeeq wai da gaske ne?,da gaske ne don Allah?, kayi aure?” Tambayar tata ta daure masa kai,meye manufar wannan tambayar? duk da ya jima zuciyarsa da hasashensa suna son kaishi gurin,amma sai ya jaddadawa kansa ba hakan bane,saboda sam baya fatan yarinyar ta jefa kanta shingen da bazata iya samun aminci ba a cikinsa

“Yaa toufeeq,wallahi bazan iya jurewa ba,yaa toufeeq kai na yiwa zuciya tanadi,dukka tsahon shekarun nan,mommy ce takeyimin burki” sai ta sake sakin kukan da yake nuna ciwone daga zuciyarta na gasken gaske yake motsawa. Mamaki gaba daya ya sanyashi kasa cewa komai, yarinyar da yake kallonta bata da maraba da nadeeya a gurinsa saboda rainonsu da hajiya qaraman tayi? ‚bugu da qari sam babu hira da tayi kamanceceniya da wannan a tsakaninsa da ita

“Relax meenal,calm down” ya fada ta sigar lallashi,saboda gaba daya abun nata yana daukarsa ne kamar wani wasan kwaikwayo

“Ta yaya zan iya kwantar da hankalina yaa toufeeq,kasan yadda kake a zuciyata?”

“Are you okay?” Ya samu kansa da tambayarta kai tsaye wannan karon,saboda gaba daya mamaki ya gama cikashi

“I lost what i love most,i can’t keep calm”

“Kisha magani ki kwanta,Allah ya sawwaqe” ya fadi yana sauke wayar a nutse daga kunnensa. Kafin ya kashe yana iya jin yadda take kiran sunansa,ya sake kallon wayar yana sake tabbatarwa kansa kodai akwai abinda tasha,ko kuma lallai dole ya dauki tsattsauran mataki a kanta,muddin dai meenal zata ce tana sonsa,to ba shakka raini ya fara shiga tsakaninsu kenan saboda yadda yake treating nata like nadeeya.

Qarar shigowar tex ya sake sanyashi
waiwayawa ga wayar. Dukka saqon ya gama bayyana saman screen din, kasancewarsa gajeran sago bame tsayi ba
BARKA DA WARHAKA ANGON NANA
KHADIJA,KA MOREWA WANNAN DAREN
TARE D AMARYARKA,AMMA KA SANI
AMEESHA NA NAN DAWOWA CIKIN
RAYUWARKA,SABODA BA ZATA IYA BARWA WATA KAI BA HAVE A NICE NIGHT_ Samun kansa yayi da maimaita karanta saqon,a hankali a hankali wani abu me zafi yana taba zuciyarsa, emotions dinsa marasa dadi sunason motsawa,how and when ameesha ta samu wannan courage din da zata masa saqo haka kai tsaye?,saboda ya daga mata qafa? ya bata damar taje ta rayu ta tuba?. Har ya dauki wayarsa da zummar nusar da ita kuskurenta,sai kalmar

“La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem” ta subuce daga harshensa. A hankali yaji yana komawa daidai dinsa,sai ya maida akalarsa zuwa blocking number tata,sannan ya goge saqon,ya jefa wayar a aljihunsa yana migewa daga gurin,yana ji a zuciyarsa bashi da lokacinta Sam,bama yanzu ba,har abada baya jin zata sake samun lokacinsa,bawai ita kadai ba,dukka wata diya mace ma idan ka debe jininsa dinnan daya zama lazim ya rayu dasu,yake kuma da yaqinin babu cutarwa a tsakaninsu har abada.

Cikin wani yanayi yake fita dag balcony din har ya riski lafiyayyen bedroom din nasa,cikin qanqanin lokaci ya gama shirin kwanciya,ya maida hasken dakin zuwa dim light,idanunsa na lumshe yana jin kewar rashi ganin fadeela saboda cinkoson gidan,yau din tun sassafe da ya fita yabar musu gidan,duk da sashen nasa baisan me cikin gidan ke ciki ba,amma sai yakejin kamar hayaniyar gidan a tsakiyar kansa take. Bacci yake da bugatar yi sosai,to amma yanayin da yake ciki ya tabbatar idan baiyi wasa ba zaici wuya ko ya dade a haka,wannan ya sanya yana daga kwancen ya miqa hannunsa ya jawo wata mp4 me siffar qwallo fara qal ya kunnata,take sautin karatun alqur ani me girma ya karade dakin da muryar sheik mahir almu’aiqaly,karatun ya fara saukar masa da nutsuwa sosai a zuciya ruhi dama gangar jikinsa,sannu a hankali baccin da bai taba zata ba yayi awon gaba dashi.

_sai muce asuba ta gari angon nana kadija_

**********A nutse ta ajiye wayarta data gama karatun qur’ani ta ciki saboda rashin hado mata da qur’aninta da ba’a yiba ta mige tana kallon agogon dake manne a bangon dakin daidai algiblar sallarta. Qarfe shida da mintuna talatin,tana da buqatar ruwan dumin da ta saba sha a kowacce safiya,bata qaunar fita sam sam saboda batason koda tsautsayi yasa su hadu dashi,duk da bata tunanin a dai dai wannan lokacin akwai wanda ya farka cikin gidan. A nutse ta ninke abun sallar tayi masa guri,sannan ta zura lausasan slippers din da suke set da kayan jikinta,wanda couple prayer set ne,ta zari nata ta saka. Blur black ne masu taushi,kala ce ta farare, don haka ta fidda hasken fatarta da kyau wani irin haske dake cakude da amarci da kuma zallar gyaran da tasha daga hannun me gyaran jikin da maii ta ajjiye mata.

Duk yadda taso dauke idanunta daga kallon yadda aka tsara hallway din hakan ya gagareta. Wani irin kyakkyawan tsari aka yiwa gurin wanda hatta weather da qamshin da yanayin iskar dake kai kawo a gurin na musamman ne. Fitilunsa na musamman, kamar yadda kome da akayi amfani dashi wajen qawata gurin ya zama favourite colour dinta ne,zaka rantse da Allah ita ta zauna ta rubuta yadda takeson a shirya komai din. Qafafunta na nutsewa sosai cikin
Tallausan carfet din da aka malale gun dashi har zuwa sanda ta sada kanta da falon.
Hallway din yafi burgeta, amma kuma yadda falon ya tsaru da wasu irin kujeru curtains da carfet carfet sai ta rasa wanne guri ne yafi wani?,nan dinma komai dake dake cikinsa zabin kalolinta ne,kamar tana gurin aka shirya komai. Duk qoqarinta da son ganin abun sam bai burgeta ba hakan ya faskara,ta dinga ratsa falon tana laluben inda kitchen yake,lallausan qamshi me kwantar da zukata yana yawo a hancinta har zuwa zuciyarta. Bata jima ba ta hangi hanyar da zata sadata da falon wanda ke daura da waje na musamman da aka tanada aka kuma qawatashi da dining na alfarma.

Bata fahimci da mutum a ciki ba saboda girman kitchen din har sai data kammala shiga

“Good morning madam” jacob daketa aikin
kintsa kitchen din don shirya abinci na
musamman da zai burge matar ogansa ya fadi
a ladabce.

Turus ta danyi tana dubansa, ya afron
da zungureriyar hular kansa kadai ta isa yi
mata bayanin waye shi,saidai duk da hakan
baiyi qasa a gwiwa ba wajen gabatar mata da
kansa

“‘Sunana Jacob,nine cook din sir,akwai wani
abu da kike bugata ne yanzu?” Mamaki ya
saukar mata,shi komai nasa ya banbanta dana
kowa?,ya kawo qatoton gardi kuma arne ya
ajjiye cikin gidansa yana dafa masa abinci
yana ci?, iyakacin zamanta a gidan ma bata
taba ganinsa ba,ko don ita din bata fiya zurfafa
kanta a lamuran da basu shafeta bane?. Ta
yaya zata zauna itakam wannan qaton yana
mata girki tana ci?.

“Bana buqatar komai, just warm water zan diba,and i can handle it” ta furta tana matsawa sashen da aka jere glass mug cikin tsafta da burgewa ta cire guda daya,ta taka a hankali ta isa ga dispenser ta debi ruwan. Saidai yayi mata zafi da yawa,batason kuma sirkashi, wannan ya sanya ta jingina bayanta da kitchen cabinet tana motsa ruwan a hankali,tana so ya rage zafi tasha tabar masa cup din a wajen.

Cikin kamewa tare da tarin nutsuwar
da sallar asuba ke haifarwa ga zuciya da ruhin kowanne musulmi yayi sallama a kitchen din. Wannan al’adarsa ce,yakan manta da cewa jacob ba musulmi bane,shima Jacob din tsabar sabo da hakan ya sanyashi ya koyi cikakkiyar amsa sallama.

Lallausar muryarsa da bacci yasa ta qara zama husky and deep voice ta ratsa kunnuwanta,idanunsa ya fara sauka a kanta,zagayayyar fuskarta dake tsakiyar hijabi tayi fayau da wani irin haske. Zare idanun nasa yayi daga kanta yaci gaba da takowa ciki a hankali, daura da ita ya tsaya shima yana daukar glass mug din ba tare daya sake duban sashen da take ba

“Good morning sir” jacob ya gaidashi cikin tsantsar girmama

“Morning Jacob”

“Kana bugatar wani abune sir?”

“Warm water” shima ya fadi a taqaice yana sake cirar spoon bayan mug din. Wani mugun kusa taji sunyi ita dashi, duk da kuwa akwai tazara a tsakaninsu,yadda ya ganta a jiya ke dawo mata fes cikin kanta,a hankali haushinsa ya soma sauka saman zuciyarta,tanason ta matsa daga gurin amma ta gaza,wani irin kwarjininsa da bata taba ji ba ya mamayeta. Ta lumshe ido tana kai cup din bakinta duk cikin son nuna bata ganshi a kitchen din ba gaba daya,gefe guda na zuciyarta yana mata bitar abinda afifa ta taba gaya mata

“Aure yana da wata irin daraja,yana garawa namiji kwarjini a idanun macen daya aura din albarkacin wanann igiyoyin guda uku, kibi a sannu bestie, toufeeq ba irin kalar mazan kike kalla bane ba irin adam bane,yadda banbaci da tazara yake a bayyane muraran tsakanin sama da qasa,haka yake tsakanin adamu da toufeed” a lokacin tsaki taja,akwai abinda take son saurara amma gaba daya afifa ta hanata sakat,motsi kadan ta fara mata wa’azin aure

“Kina tsammanin don kawai ya biya sadakina sai yayimin kwarjini afifa?”

“Bestie” bata barta ta gama magana ta dakatar da ita

“Bestie, idan akwai mutumin da ya cancani a duniva nayi masa kara na aureshi ma to mahmud ne,amma saboda har yanzun zucivata bataii akwai wani amintaccen namiji a duniya ba na gwammace na kawoshi,izzarsa dagawa da tsantsar jin kansa ba zasu taba razanani ba,zai kuma ci gaba da tabbata ne a mijin AUREN MANUFA, yayi rayuwarsa nima nayi irin rayuwar da nakeso” a lokacin murmushi afifa tayi ta miqe tana cewa

“Ba zaki gane ba”

“Ke kai ba zaki taba ganewa ba”.
[16/09, 7:18 pm] +234 703 451 7171: *HUGUMA*

* TABARMAR KASHI_*

Leave a Reply

Back to top button