Hausa NovelsTUMFAFIYA Complete Hausa Novel

TUMFAFIYA 26

Sponsored Links

 

 

 

 

 

ZAINAB IDRIS MAKAWA [1/24, 8:34 PM] +234 706 815 1331: 🌱TUMFAFIYA
UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA SIRIN KI     SAI ALLAH
,,,,,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

 2️⃣6️⃣

ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA
DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS
MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA
AMIN,,,,,,,

 

   Ina uwargida da
Amaren gida dama sarakan gida da kowa na gida muna maiba da hakkuri ga kowa dake
jin ana fadan halin matsayin da yake a gida.

   Uwargida sunce an
soki matsayin su an rage masu GP amaren ma sukace ana fa yawan aza masu laifi
hakama uwayen gida sarakan gida sun fadi korafin su.

   To yar uwa rigace
ta zamani abin yayi idan ke hakan ba halinki bane hslin waccan ce ko halin
wanan don abinda yafi yawa a yanzu ne muke fada a fili.

   Uwargida za a karo
kishiya tace shigo zaki sameni ciki ai haka amaryan zamani da danmara a
kwankwason ta take shigowa uwargida yanzu saidai kowa dabaran shi da rikon
Allah ya fitar dashi.

  Bana bayan kowa don
kowa nawane a cikin don haka muyi nishadi mu karu da juna ta wani fannin don
ace zomu zauna zo mu saba Allah yasa mufi karfin zukatan mu muyi kishi daidai
da imanin mu amin nagode nagoda da bin novel dina ko wani lokaci.

    Zufa take karyawa
daga zaunen kafin ta tattaro zuciyan ta wuri daya ta samu natsuwa ta dauki
hakan da sherin mafalkine ba wai zai faru a gaske ba.

    Jin budan kofan
jikan nata har shigan shi dan makewayin su ya fito duk a kunnen Dije da jinsa
ya fito dags bandakin yasata bude kofan ta a lokacin da yai daidai da muryan
Amadin dake fadin waye a wurin nan ne wai tsugune ?

    Dije dake fitowa
ta amsa da ina kuma yace daga barin katangan can kamar mutum yana zaune a wurin
da sauri ta koma dakinta ta dauko toci tana kokarin kunnawa zuwa lokacin har
Amadin ya mike ya kusa kai saitin wurin da lalube don ganin ko waye ?

    A lokacin Dije ta
hasko tocilanta a wurin ja yayi ya tsaya wuri daya yana jan tsuki tare da fadin
ashe dan icen nan nefa yayi girma haka har nake ganin innuwanshi kamar na mutum
a wurin.

    Ya juyo ya koma
inda yake duke da farko da shirin alwala Dije da ta shige bandakin ta fito ta
samu zai fice zuwa masallaci tayi mai a dawo lafiya.

  Ya amsa a gurguje ya
fice daga gidan har cikin lokacin akwai sauran asubahi don haka akwai sauran
duhu sosai gari bai gama washewa ba a lokacin.

    Kai ta dago daga
inda take zaunen ta kalli wurin da Amadin ya kalla abinda yagani ta ganowa
idonta itama don mutum sak ta gani a wajen duke.

    Gaban Dije ne ya fadi dam lokaci guda don
abinda idonta ya gano mata din a lokacin sauri Dije tayi ta mike a daidai
lokacin uwargarke ta saka kuka acikin muryan data kwana biyu batayishi ba a
gidan.

    Tun wanan lokacin
wanan akuyan bata sauta kukanta ba haka take tsaye tana wani irin kuka sauran
dabbobin kuma suna tsaye suna kallon ta yayin da kunnuwan su yake wani irin
dage da alaman wani abin tsoro suka gani lokacin ya gitta.

   Har Amadi ya dawo
daga sallah suna a hakan wurin su ya nufa ya zagaya su ya dan duduba ko maciji
suka gani don suna hakan idan dabbobi sunga wani abin cutarwa garesu.

   Zasu dauki kuka
sosai suna nuna alaman hakan saidai hakan yana da wuya a iya gane hakan idan ba
mutum ya kwarai a kiyo yayi sabo da dabban zai iya fahinta idan ta shiga cikin
bakon yanayi.

   Share wurin yayi ya
debo masu abinci ya canza ruwan shansu ya dan juya zaibar wurin a lokacin
uwargarken ta dona kanta tsakankanin shi zakace tana susan kantane ajikin nasa
a lokacin.

   Kiyi hakkuri
uwargarke kuci wanan dusa yau in sha Allahu zan sayo maku abinci idan zan dawo
kuci wanan din ku koshi kafin na dawo yana dan ture kanta daga jikinshi.

   Buta ya dauka ya
cika da ruwa ya nufi bandaki ya watso ruwa don haka al,adanshi yake bai tsaya
yayi wanka yadda ya kamata sai ranan jumma,a zai tsaya yayi wankan arziki ya
gyara jikinshi ya fito mutum sak sai ko sallah bana da yayi kokari ya dinka
kala biyu koshi da dalilin yin hakan a zuciyarshi.

   Kananan kaya ya
saka a jikin shi ya dauki dan jakkar da yake saka takardun shi ya fito bai
tsaya wani duban ko shigar tasa tayi ba ya fito daga dakin.

   Dakin Dije ya nufa
tun kan ya karaso ya fara kwalawa Dijen kira yana fadin Dije ni zan shiga
school kin san yau zamu koma makaranta .

  Yaka Amadi muyi
magana dije ta fada cikin tausasa murya yace wallahi Dije na makara yau din nan
kinsan yau aka koma daga hutun sallah gani a gida har wanan lokacin zam iya
zuwa na samu har an zauna.

   Saina dawo Dije
muyi maganan koma meye ya fada ya fara tafiya don barin wurin binshi tayi da
kallo dama tasan kota fada mai abinda ke zuciyata din ba lalai bane ya yarda da
ita don kasancewar shi dan boko yaro kuma.

   Hakan ya tafi ya
barta da mamakin shi na rashin tsayawan shi suyi zancen da take son yi dashi
din gaba daya ta kasa gane kanshi cikin kwanakin nan.

    Abubuwa yakeyi
kamar wani abu yana damun rayuwan shi yana boye hakan gareta dkn duk da bai da
hayaniya dama sai miskilanci amma yana dan sakin jiki ya fada mata damuwan shi
a baya.

 Amma yanzu sam baida
lokacin tsayawa yin hakan sai ya nuna ko yaushe kamar a uzurce yake a yanzu
din.

     Har nayi sallama
da ummah na kama hanyar fita daga part din mu muryan ummah ya tsayar dani
lokaci guda na juyo ina fuskantan ummah din.

   Maamah kin dai san
abinda mahaifinku ya fada maki don haka ki kula ki kama kanki a duk inda kikaje
don kimarki itace darajan ki ki kama kanki na fada maki.

 Kwalkwal nayi da
idona don ina jin dacin wanan kalman a zuciya nasan kuma mahaifiyata tafini jin
hakan sosai a ranta dannewa kawai takeyi kada a gane hakan.

   Na iya bude bakina
da kyar nace ummah zan kula in sha Allah nasa kai na fita wurin motana na nufa
saida na tsaya na dan duba motan don hango scratch a jikin motan danayi tun
daga nisa wanda ni bansan dashi ba a lokacin.

   Ban koma ciki ba na
daure na fice hakana zuciya ba dadi har lokacin ga tunanen zancen iyayyena
yanzu kuma na rasa wanda ya gogar min motana.

   To waye yai min
haka da motar nawa don tunda akai sallah ban fito ba lafiya kalau na aje motana
kuma yanzu na samu hakan a jikinta.

   Na shiga school a
kan lokaci don haka na fito ina dan waige waigen satan kallon inda na saba
tarardashi muke haduwa saidai a fakaice nake satan kallon wurin don kada na
gashi kamar yadda muka saba din.

   Nayi mamakin ganin
hakan har na shiga building din mu na zauna a tsarge kowa ka gani aranan yasha
kwalliya a cikin tufafi masu kyau don adon sallah.

   Kaina dukar saman
table din dake gabana ina tuno abubuwa da dama naji an dafa min kafadana na
dago da sauri ina kallon maishi Hannatu ce a tsaye take min murmushi kafin ta zagayo
ta dauke jakkar dana aje a wurin.

   Ta zauna take fadin
wai zahra idon ki ke nan dama wallahi zahra baki da kirki ace wai ayi sallah
bakijini ba kuma baki nemeni ba kinji ko lafiya nake ba.

   Kaina dago ina
murmushi a gajarce nace haba Hannatu ko kallona kikayi ai zaki fahinci bana
cikin dadin rai a tare dani yanzu don jikina na bani cewa har karamin rama
nayi.

   Kallon tsab tayi
min kafin tace gaskine hakan kuma to meke faruwa na kalleta ina hade bakin ciki
a cikina nace sallah nan ciwo nayi saidai bai kaini kwance bane.

   Lectura ne ya shigo
ya katse muna hira  mu kowa ya samu wuri
ya natsu aka fara lecture bamu samu kan mu ba sai karfe daya muka fito don
break da za aje na sallah.

   Hanya na canza
hannatu ta kalloni tana mamaki bata da zabi sai bina da tayi muka isa wurin
sallah baya  mun idar ne wayana ya dauki
karan kira lokaci guda.

    Ban dauka ba don
ganin wanda ke kiran nawa manir ne nasan kuma zancen karatu zai min don ko na
dauka ban san amsan da zan iya bashi ba lokacin don haka naki daukan wayan
karshema daukan wayan nayi na sashi a silent.

 Ganin hakan yasa ya
kira layin hannatu ta dauka tambayanta yayi idan muna tarene tace dashi gamu
cikin mosque.

   Ba zaku fito muje
lesson bane yau ko baku gama hutun sallah bane ku har yanzu don shi dama sarkin
barkwancine ko yaushe.

    Kashe wayan tayi
tana kallona tare da fadin Mayana mufa ake jira akace wurin lesson kada mu bata
masu lokaci.

   Ba zan samu zuwa
lesson ba na bata amsa kai tsaye har yanzu jikin ke damun kine ta tambayeni
nace eh kije kawai zan dan kwanta a nan cikin mosque kafin ku karasa.

    Bataso zuwa ba don
ganin banje ba amma na nuna mata ba komai ga zuwan nata don kada mutaru
duka  bamu je sai ta tashi ta mike ta
fita sai dai da gani tana a cikin kwankwanto a lokacin.

   Fitan ta nakai
kwance kasan kafet din dake malale cikin mosqu din ina lumshe idanuna zaka
dauka ko barci nakeyi a lokacin.

   Tan isa kafin ta
karaso manir yace ina ita kuma yar mulkin ko tana tafe ne mu cigaba ?

   Fuskata ta dan bata
kafin tace ina ganin zahra bata da lafiya don ko a class kusan haka na sameta a
kwance dana shigo let start don nasan dama ba zata zo ba ya fada cikin wani
yanayi.

  Ok master yana da
masaniyar rashin zuwan ta ke nan baidai bashi amsa ba ya fara gaidasu da dawowa
daga sallah kafin su fara darasin.

    Har suka kai
lokacin da muke tashi yayi masu sallama ya tafi a karshe muka koma aji aka
tashi na nufi gida haka muka dinga yi har sati ya shige suka fara fahintar cewa
akwai matsala a tsakanin mune.

  Gashi kuma har ranan
bamu hadu dashi ba kuma ban fasa satab kallon wurin ba duk na iso zanyi kokari
na juya na kalla ko yana wurin saidai ban ganin kowa.

   Sati biyu muna
hakan har kowa ya gama fahintar komai ranan monday bayan mun fito daga daukan
karatune hannatu ta tutsiyeni da tambayan dalilin rashin zuwana group
discussion a yan kwanakin nan ?

   Ba komai kawai na
daina hakan ne don nima na koyi fahinta daga malami da kaina wani irin kallo
tayi min ta sake murmushi tare da fadin.

   Zahra kenan kina
ganin a dan zaman mu tare a school din nan ba zan iya fahintar halinda kike
ciki ba ke bake bafa har su manir da sauran su ina iya fahintar yanayin su suma
maza.

   Nasha zaki fada min
don muga ko za a iya walwale matsalan a cikin sauki duk da daga ke har master
din kuna kokarin boye muna cewa babu komai a tsakanin ku.

   Umhumm hannatu ki
bari kawai wanan zancen ya wuce nake gani don ina kokarin mantawa da komai kan
wanan zancen.

   Zahra kina ganin
cewa ku bata tsakanin ki da master shine mafita a gareki ko me kifa sani irin
su master tsada sukeyi yanzu a cikin maza.

  Ko kin san yawan yan
matan school din nan da suke son kasancewa dashi  amma yaki bada daman hakan,  ni wallahi dama ganin yanayin sa idan badon
naga gidansu ba sai nace shi din dan gidan wasu manyan mutane ne sosai a garin
nan.

   To amma kuma nasan
shi har irin sana,anshi sai hakan ya fara sani a kwankwanto a kanshi kuma yanzu
dai ba wanan nan bama zahra meya kawo matsala a tsakanin ku ?

    Kamar bansan tana
magana ba don hankalina na mayar a wayana ina duba ban dago kai gareta ba naji
tace to shike nan yanzun na fahinci irin zaman da mukeyi da juna dake duk da
kece kika daukeni hakan.

  Don ni tsakanina da
Allah nake zaman arziki dake ba don wani abuba can zarah amma naga ke ba
haka  kika daukeni ba ke har yanzu.

  Nan nake kawo maki
korafin yayata dake tasheni ki bani shawara in kuma je inyi amfani da shawaran
naki yai min amfani a karshe.

   Kaina dago na
kalleta a cikin yanayin tausayin kaina nace hannatu ba hakana bane matsala aka
samu an fadawa Abbana cewa wai soyayya muke da Ahmed shine Abbana yai min
iyakan tsayawa dashi.

   Abba fa har wanan
zancen yakai kunnen Abban ku kai mutane basu da kyau yanzu shiyasa wasu ke
fadin anbar kiwon dabbobi a yanzu an koma kiwon mutane.

   Ba wanan ba hannatu
Abba har Ahmed din ya kira yai mashi iyaka dani ya kumaci zarafin shi a kaina
da wani ido zan kalli Ahmed a yanzu kike gani.

  Ke kanki Hannatu
kinsa Ahmed kadai ke min bayani na fahinci abinda darasi ya kumsa na gane
yanzun kuma Abba yaci mashi mutunci kan haka, har yana fadin cewa Ahmed baida
asali .

  What ta fada da dan
karfi tana kallona kafin tace min kuma shi Ahmed din yasan da wanan zancen
bansan koya fada mashi ba daya kirashi din.

   Zahra ki bar wanan
zancen don Allah mu bari sai mun samu lokaci mu zauna asan yadda za a bullowa
lamarin sai dai ban zaton ya fadi hakan a gaban shi Ahmed din ai.

   Nima shine tsorona
don nasan halin Abba zai iya fadin komai ko a gabanshi idan ranshi ya baci
tunda acewa Abban soyayya mukeyi nida Ahmed din ba karatu ba.

   Amma ke baki ganin
rashin kyautawan ki ga hakan aisai ya zata kema hakan da Abban yai mashi bai
dameki bane kamata yayi mu sameshi mu bashi hakkuri .

  Kinga a nan zamuji
shin Abba ya fada mashi maganganu marasa dadin kamar yadda ya fada maki ni
gaskiya kamar hanyar daya dace ke nan mubi nake gani.

   Hannutu kunyanshi
gaba daya nake ji a yanzu bazan boye maki ba kan wanan maganan wallahi nasa
cewa ba karamin shakuwa ashe mukayi dashi ba.

   Don tun wanan ranan
wallahi Hannatu na nemi farincikina na rashi a tare dani kullun jin kaina a
cikin kinci nake kuma Abba har zai tafi ya kara jadda min cewa duk aka fada mai
cewa angani tare dashi zai dauki mumunan mataki a kaina ranan .

   Wanan yasa nake
matukar tsoron fita har mu hadu din dashi wani dan gulma yaje kuma ya fadawa Abba
kinsan Abba ba zai raga min ba idan har yaji hakan.

  Gaskiyane ki dai
bari gobe idan nayi tunane kan yadds zamu bullowa zancen sai mu san abin yi don
gaskiya ban baki shawaran barin wanan guy din ba zahra.

  Murmushi nayi tare
da fadin wai meyasa mutane ke yawan dauka muna soyayya da Ahmed ne, mutuncine
fa kawai a tsakanin mu kema kin sani.

. Nikan ban yarda da wanan maganan ba ga kowan ku donko
makaho ya laluba yasan gaskiya  kedai
kawai mubar zancen sai gobe in sha Allahu.

    Ina hanya komawa
gida wayana yayi ringing na mika hannu na dauka daga gefena ya musa ne a layin
da murnana na dauki wayan ina gaidashi.

   Zahran mama ke nan
ya fada na lumshe idona don tunawa da wanan sunan da suke kirana dashi shida ya
jafar yace yanzu kin zama busy ko neman mutane bakyayi ki gaidasu.

    No wallahi yaya ba
hakana bane yace to ya ne Allah karatune yanzu yai min yawa sam banda lokacin
kaina ga komai yanzu.

   Saina soyayya da
yan uwanki dalibai ko Zahra Abba ya kawo min karanki yace kin fara soyayya da
wani karamin yaro dan karamin gida a school din ku.

   Wallahi ya ba
hakana bane na fada ina samun wuri na parker motar na kwashe komai daya faru na
fada mashi har mutuncin dake tsakanina da Ahmed din da dan sabon da nayi dashi
fiye da kowa a school din.

  Bayan ya gama
saurarena yace min kin gane zahra ki janye duk wani alaka tsakanin ki da kowa
yanzu kiyi facing din studies din ki kamar yadda Abba yake son kiyi.

 Shawara sosai ya bani
kafin mu kashe waya bayan munyi sallama na tayar da motar na karasa gida ina
tunane don ni abubuwan ma sun min yawa a yanzu nake gani.

    Ranan banyi barcin
kirki ba ina faman tunanen maganganun ya musa dana hannatu a raina sai kullawa
nake ina walwalewa ni kadai a dakin nawa .

   Washegari na tashi
sukuku dani nagama shirin da zanyi na fice a gidan tunda safe na samu malamin
yazo bai shiga ajin ba don haka kusan tare dashi muka shiga.

   Sai bayan gama
lectures din ne hannatu taso muyi maganan jiya din sai ya kasance kaina yana
dan sara min muna fita maimakon mu wuce zuwa mosque sai cewa nayi da hannatun
kaina ke min ciwo zanje gida insha magani in kwanta.

   Kallon mamaki take
min din muna da lecte karfe biyu da rabi ganin da gaske nake yasa ta kyaleni in
tafi din na nufi wurin motana nadan duka ina bude motan naji muryan shi abayana
yana fadin

Leave a Reply

Back to top button