Hausa NovelsTUMFAFIYA Complete Hausa Novel

TUMFAFIYA 66

Sponsored Links

 

ZAINAB IDRIS MAKAWA 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI
,,,,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,

🌱TUMFAFIYA SIRIN KI     SAI ALLAH
,,,,,,,,,,

ZAINAB IDRIS MAKAWA

6️⃣6️⃣

ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA
DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS
MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA
AMIN,,,,,,,

 

Rayuwa ke nan mutuwar yarinyar nan ya taba su mama zakace
wani babban mutum ne ya mutu a lokacin ba yar jariri haka ba mundai isa nida
hannatu munyi gaisuwa inda muka samu ana fama da uwar tayi hakkuri sai faman
kuka take.

   Harda wasu yan abi
yarima asha kida suma suna kukan ita dai mama nasan damuwanta damuwar yartace
Aisha.

  Don Aisha yar gaban
goshin mamace sosai a cikin yayanta koma zata iya yiwa Aisha din a rayuwa idan
tana bukatan abu.

   Ganin yamma yayi
sosai mukai masu sallama muka dawo wurin ummah don mu sallameta bata part din
tana part din daddy lokacin dole muka zauna zaman jiranta kada mu tafi bamu
samu sallama da ita ba asalima bata ina cikin gidan ba a lokacin .

   Uhmmm wai kiji min
sister din nan naki daga Allah ya rabata da wahala ya karbi ran yarinyar a huta
gardama wai shine take kuka haka ?

   Hannatu rayuwace fa
ta rasa dole tayi kuka ai balle da ance shiga ran uwa yakeyi sosai tun yana
ciki kinga ke nan dole ta damu kona dan lokacine.

  Balle ga wahalan
daukan ciki gana haihuwa yaya mutum ba zaiyi kuka ba shiyasa nake ganin karfin
halin irin matan nan masu daukan cikin shege a waje.

   Suyi wahalan daukan
nauyin ciki idan sun haihu kuma kiga mace wai taje ta yarda yaron a bola don
rashin imani da tausayi ko shekaran jiya naji ance an sunci yaro a cikin wani
kwalbati a gidan da mukaje kitso muke jin labarin haka.

   Gidan gulma ke nan
ai in kina neman labarin gari kije gidan kitso kona kumshi a nan zakiji labarin
shege da shegiyan gari ke har kishiyan data gagara zakiji ko namijin da baya
kula da matanshi ke ko wani labari na gidan kitson daya shahara a gari.

   Kai hannatu ashe da
gaskiyane da ake fadin tashin kaka daban suke ko wurin iya tsara maganansu irin
na tsufine ke din nan akwai iya lafazi a bakin nan naki yanzu dai mudake zuwa
gidan kitson mune yan gulman ?

 Kafin tayi magana
ummah ta shigo tana ganin mu mamaki ya kamata take fadin ku kuma yaushe kuka
shigo daga school muka wuto zuwa nan don gobe muna da test ba zan samu shigowa
da wuri ba.

    Aikun kyauta gara
da kukazo yau din nan dan uwa zai gane kana da muhinmanci a wurin shi don baka
sanin ranan dan uwa ko dadinshi sai idan wani abin bakin ciki ya sameka dan uwa
ke tsayawa ya tayaka kukan hakan.

   Ta sake jiki kuwa
Aishan don sunce tun safe da yar ta cika taki cin komai a cikinta har lokacin
da na shiga dazun kara dubata abin ne akwai tausayi ummah ta fada.

  Gaskiya kwance muka
sameta tana kuka da muka shiga saidai tana jin muryan mu ta dago tana fadin
zahra kinga babyn mu tayi tafiyanta ta barmu ko ?

   Murmushi ummah tayi
tace ai haka ta fada dana shiga dazun tace ummah zahra tana son yarinyar nan
sosai jiya bakiga yadda take kafa kafa da itaba kada a dauketa ta wahala ashema
duk hakan bazaiyi ba sai ta mutu.

   Niko naga aita huta
da rikincin su dake kwance kasa tunda ace mijin ma baizo ba har yanzu andaci
karfinshine yayi suna yadda mutane ke fadi agari don akwai wata yar uwanshi a
unguwan mu.

   Kai hannatu aikece
gidan kitso ko wani labari yana bakinki ku tashi dare yayi kuje gida barin kira
Shehu yazo ya saukeku dama yanzu ya dawo kai motan wurin wanki da cewa wani dan
yar uwar Abba daya leke shikuma wurin ummah tun yana karaminshi.

  Mama tayi zagi tayi
koranshi har hjy saida ta saka baki amma yaki barin ummah har gashi mun girma
tun muna Abuja yana karami yake zuwa hutu wurin mu.

  Ta daga waya ta
kirashi dacewa idan ka dawo wanke motan gasu mahmah ka kaisu gida don Allah
yace to gashi nan zuwa lokacin ummah ta kalleni tace ba zakije ku gaisa da
Abban ku ba.

   Wani har nayi da
idanu alaman ban son zuwa tace kuje suna nan falo da hjy karima yanzun na barsu
zaune tare ummah da dai ki bari sai nayi wani zuwan kuma idan yazo.

    Au har yanzu baki
daina wanan sakatcin naki ba ashe ubankine fa kome kikeji a ranki game dashi
gara ki aje donshi ko a jikinshi duk da dai jiya ya tambayeni wai ko kema kina
da cikine yaga kinyi kiba ?

   Ciki kuma nikan
banda komai wallahi idan nayi ciki yanzu ai asirina saiya tono ina gab da zana
jerabawana kuma ciki yazo min dan zugurana hannatu tayi wai na daina maganan a
gaban ummah haka rashin kunyanefa.

    Dole dau muka nufi
wurin Abba yadda ummah din ta fada hakane da hjy karima suna zaune suna hira
mukayi sallama muka shiga falon nasa da ummah din ta gyara tas sai kamshin
turaren shikka yake tashi a cikinsa.

   Suka amsa muna muka
shiga hjy karimace tace a, a  kune ashe
kuji mutuwar yar ke nan nace eh ina school dazun ummah ta kirani tana fada min
daga can shine nazo nan.

    Mijin naki ya
dawone Abba ya tambaya a,a yana can waya mukayi dashi dai OK wanan itace kawar
nan taki lokacin buki ko hjy karima ta tambaya nace eh tare da fadin Abba ya
mukaji da hakkuri kuma ?

   To hakkuri sai
Allah shiya bayar kuma ya karba sai ai fatan lafiya yanzu ga uwar nace hakane
tare da fadin to zamu koma idan kun tafi Allah ya kaiku lafiya.

    Ai muna nan sati
daya zamuyi hjy karima ta fada daga inda take zaune nace Allah sarki tau mun
mike naji yace tunda mijin ki baya gari barin baki wani abu kona shiga school
kya samu.

   Lah Abba da ke Abban naku zai maki alheri kiki
karba eh to ba mamaki kinsan mijinta last donen ne ai matar mai kudin sakaine
Abba ya bada amsa yana miko muna sabbin kudi yan dari biyar.

    Na duka na karba
ina gidiya ya miko wani tare da fadin ke kuma gashi ki rike hannatu tazo da
sauri ta karba tana godiya a lokacin ne hjy karima tace da motarki kikazo ko ?

    Naga dare ya
somayi ga unguwar naku da dan nisa kai na girgiza kafin inyi magana hannatu
tace ai tunda aka karbi motan da bukinta ba a mayar mata dashi ba.

   What kina nufin
motar haya kike hawa kome da ita mukazo hannatun ta kara fadi Alh yaya akai
haka za a barta tana shiga motan haya a gari ita kadai da sauri nace.

   Mommy hakan yafi
min yanzu ma kinga na farko a yanzu ban iya laluran motar kuma gidan kingani
babu inda zan aje motana ai a gidan.

    Dazunma kafin muzo
nan muga wani yana yawo da motan ya kwaso yan mata acikinsa ai kunnena ya
tsinkayi hannatu na fada a bayana.

   Kaji ko motar ma ba
a aje matashi ba wani ke shigarta yanzu wanan son kai gaskiya da yawa yake in
anyi magana kace wai wani abu da sauri na bar falon hannatu ma ta biyoni baya.

   Gaskiya hannatu
bata taba bata min raina irin na wanan ranan ba don har nayi nadaman zuwa da
ita gidan mu din a lokacin .

   Don haka har na kasa
boyeewa saida fuskana ya nuna hakan muna komawa gun ummah na samu shehu ya iso
yana jirab mu a falonta mukai sallama muka nuna mata kudin da Abban ya bamu
tace angode ta mikowa ko wanin mu leda na karba ina godiya muka fito har muka
shiga mota na kama hira da shehu.

  Ita muka fara
saukewa don ina gaba da ita sai ya tafi dani har kofan gida ya kaini na sauka
nayi mai godiya ya tafi ni kuma na shiga cikin gidan.

   Kwananshi biyu a
south Africa na uku ya dawo da safe saidai ya samu ba kowa a gidan hakan yaba
yar aikin daman labarta mai abinda taji daga bakin hjy yabi ranan.

  Ba koma nagode Asabe
ki kara kula yacewa tsohuwar yau din nan matana na biyu zata iso garin nan da
fatan zaki bata hadin kai a zauna lafiya banda tsegumi don Allah a tsakanin su
yarda da aminci yasa na baki amana.

   Tsohuwar ta gyara
tana fadin insha Allahu Alh nakuma gode nima ka fitar dani daga zargin
ubangijina Allah don wanan abin yana damuna shekara da shekaru wallahi bandai
da bakin maganane kawai.

   Sai daya da wani
abu mutanen gidan suka fara dawowa salimace ta farko sai uwarta data dawo a
gajiye lokacin sai bayan ta hutane Asabe ke fada mata ai maigidan ma ya dawo
lokacin.

   Haka kawai taji
lokaci guda gabanta ya fadi akaro na farko da ta taba jin hakan nan a zuciyarta
game dashi ke nan ranan haka ta daure ta mike zuwa wajenshi saidai baya nan
yana masallaci a lokacin.

  Bai fito ba sai
bayan isowan matar nasa amaryan nasa data iso mota biyu ita da yarinyar datake
tayarwa sai kanwata guda datake riko sai yayunta biyu da sukayo mata rakiya da
tsohuwa daya da aka hadosu da ita daga gida.

   Nan aka fara shiga
masu da kayansu cikin gida harsai da aka kusan gamawa sanan taji labari daga
bakin yarta dataga shigowansu lokacin.

   Tashin hankali a
sukwane ta fada dakin uwar nasu tana fadin mommy su wayene sukazo naga wasu
mata na shiga da kaya wanan part din da aka gyara.

    Mata da kaya kuma
ta tambayi yar a cikin mamaki tace eh mummy gasu can suna shiga yanzu haka da
kayansu wallahi.

   Ai a su kwane take
saukowa daga kan gado har tana hadawa da rarafe lokacin haka ta samu ta sauko
daga matakala zuwa falo.

   Ja tayi ta tsaya
wuri daya jin mijin nata yana yaren fulatanci da tsohuwar yana tambayanta
mutanen gida a lokacin nan take fada mai duk suna gaidashi saida daga inda hjy
yabi din take tsaye ba zata iya sheda ko wacece tsohuwar ba alokacin don ko
muryanta ma bata sheda ba..

    Cikin mamaki take
karasowa inda suke yarta Salima tana biye a bayanta who is she daddy Salima din
ta tambaya daga inda take tsaye a bayab uwarta din.

    Jin hakan yasa ya
juyo a lokacin ya dan kallosu kafin yace gwaggonane daga Gembo daga mambila
suke ita da mummy ku na can.

   Wani irin faduwan
gabane ya ziyarci zuciyar hjy yabi lokacin har jiri na neman dibanta zuwa kasa
sai da Allah ya gyara bata kai kasan ba a lokacin wa yan nan fararen yaran
fulanin suka shigo daga waje suna jan akwatinan su zuwa ciki.

    Mamakine karara a
fuskan hjy yabi saliman ta kara tambayan uban da cewa so she now live in Abuja
with us ?

   Yace of course a
nan zata zauna tare damu itama da yaranta ok she is welcome ta juya zuwa cikin
ya bita da kallo kafin uwar dake tsaye kamar gunki tabi bayanta a fusace itama
irin ga mace ta hasala da miji a lokacin.

  Bai tsaya binta
kanta ba ya juya wurin tsohuwar nan suka shiga ciki suna magana dashi.

    Mataimakinta ta
jawo watau waya ta dannawa yarta kira a cikin tashin hankali akai sa a kira
biyu ta dauka tana fadjn yanzu naso kiranki dama sai gashi kin kira.

   Naji gari ya dauka
cewa kishiyar ki ta koma Abuja da zama jiya suka bar garin nan  tace shina kira in fada maki yanzu.

   Yanzu na gane inda
barnan ya fito min yanzu na gano me min bandar kasa ashe nayi sake ina daukanta
sakarai tana min kallon wawiya.

    Tunda har yau Alh
ya iya dawo da ita garin nan kusa damu mu zauna tare a nan da ita yanzu wasan
zai fara a tsakanin mu dama ashe itace ke min saran boye ban farga da hakan ba
?

    Yanzu shi meya
fada maki  yau din nan ya dawo da safe ko
ganinsa banyi ba sai yanzun nan na ganshi a falo suna magana da salima yake
fada mata a nan zasu zauna damu wai.

    To kinji ki natsu
don Allah kada ki yarda harta gane cewa akwai matsala a tsakanin ku yanzu ki
bita da basaja ke inama ruwanki da itane wai kowa yayi harkansa kawai zaifi don
ba wani shiri tsakanin ka da kishiya kowa naciki na cikine a tsakani.

    Ke ni Alh ma ya
ban mamaki wai yau shine harda daukan Murja ya tafi da ita Abuja yarinyar da
abaya yake fadin baisan yadda zai kwanta da itabama.

  Ohh ke kika saura
rakiyan maza ki barshi kawai yanzu nuna masa ba komai a ranki ko zamu samu ta
hakan mu koma daidai dashi inyaso daga baya sai mu san abinyi.

   Anya kuwa zan iya
yau nice na bude ido tare da wata mace a cikin gidan nan da sunan zamu zauna
tare wai ?

    Yanzu dai dole
kibi sannu kamar yadda na fada maki in yaso daga baya sai muyi tunanen abinyi
nan gaba muna can munata zaton ko iyayyen yaron nan nasane ke asiri ashe ga
inda barna yake bamu sani ba.

   Haka dai sukaita
kulla tsiya a tsakaninsu har dai suka gaji suka kashe wayan suna sallama da
juna akan sai ta kirata fada mata halinda ake ciki a gidan.

    Da sallama a
bakina na shiga gidan a waje duk na samesu Dije tana alwala su kuma suna
zazaune nayi sallama tare da gaidasu daga can ban karaso ba.

   Yar nan ina kika
shiga haka har dare hankalin mu duk ya tashi baki dawo lokacin da kika sababa
jin hakan yasa na dan dawo baya ina fadi.

   Ayyah Dije wallahi
naje gidan mu daga makaranta wanan yarinyar da akai suna jiyace Allah ya karbi
abinsa ba dijeba kawai gaba dayansu har inna suka saka salati lokaci guda.

   Inna dince ke fadin
dama bata da lafiyane sai dije ke fadin gashi tana fadan ankaita asibiti ba
wanda yasa rancewa ma zai ai sunan ga jiya amma uwartace ayi kawai.

    Eh to uwar nada
gaskiya aiko banza taiwa uwarta bara kinga da batayi dabaran hakaba da shike
nan ai bata samu gudun mawar data samu a jiyan ba.

  Nikan ina jin ta
fara babatun ta na juya kawai zuwa kofana nasa key na bude na shiga duhu ya
fara don haka na tsaya na lalubo wayata nayi amfani da haskenta na kunna wuta.

    Na saka ki na bude
kofan na shiga don ko,ina ina rufewa idan zan fita don da farko ban rufe part
din amma yanzu dana fahinci ana min barna na fara rufewa idan zan fita din inna
tayi korafin hakan ta gaji ta barni.

    Jakata na wurga
saman kujera na shiga uwar daka har na nufi bayi na tuna da kudin da Abba ya
bani na fito na dauka nakai cikin wardrobe dina na boye.

   Ruwa na watsa a
jikina na dauro alwala na fito na tayar da sallah bandaga ba har akai isha na
gabatar san na  na mike na jawo rigata na
dora sama.

    Zan juya naga
jakar na sake tunawa da kudin na dauko na zauna na kirga dubu darine cif a ciki
wanan ne kyauta na farko da Abba yai min tun bayan aurena da Ahmed din.

   Nayi mamakin hakan
don a gaba yayi warning din kowa akan kada ya bani kudinshi sai gashi yau shiya
bani kudin nasa da kanshi.

  Dubu ashirin na zare
daga ciki don na bawa mutanen gida suma su taba su lakaci arziki kamar yadda na
samu  nima don haka na debewa kowa biyar
biyar na mike na fito da kudin a hannuna zuwa part dinsu.

   Yadda na barsu a
zazaune haka na dawo na samesu sai Dijece ke cikin dakinta lokacin nace to Dije
sallah akeyine har yanzu shin naji tace na sallame dama yanzu nake shirin
fitowa zuwa wurin ki in maki gaisuwa.

   Kai ji dije mutuwar
yarinyace sai kin wani binta kuma kin mata gaisuwa akanshi yarinya ai rayuwa
gareta kuma jinintace ko ta fada tana fitowa daga dakin tana cin karo da kwanon
da suka aje mata a kofa.

   Kai masu wutan nan
Allah ya shirya muna su ace tun jiya ba wuta mutane na zaune cikjn duhu da zafi
haka yanzu dana kara dan dayan kafar mai dan lafiyan.

   Da za a samu wani
ya sayo muna mai da sai mu kara a tayar da injin din nan ko chajin waya mu samu
da sauri Asmau tace indai akwai kudin kawo yanzun nan zanje gangare nasayo
maki.

   Nace to bari inzo a
lokacin ne na mikawa Dije dubu biyar saina nufi wurin inna mai fadin  kullun suna yar mai kudi a gidansu amma har
yau ko kwandala basu taba ciba naji hakan ne a makwabtan mu rana dana shiga
gaidasu tun ranan ban koma shiga ba kuma master ya hana.

    Na mika mata ina
fadin inna gashi jin gashi yasa ta juyo da sauri tana kallon hannun nawa ta
karba Dije ko tana can sai zuba mjn addua takeyi na nufi inda Aisha suke suma
na mkka masu nasu .

  San nan na dago nace
Abban mune ya bani kudi dazun shine na basu ai nan suka shiga godiya inda yaran
ke ihun murnan samun kudin.

   Na juya na dauko
kudi dubu daya naba asmau ta sayo muna mai mu kunna injin din muga haske ta
fita tana godiya bayan ta dawone muka fito da injin din muka zuba mai nika  ba karfi amma haka na gwada don sun gwada sun
kasa tayarwa dole muka kira wabi yaro yazo ya kunna muna gidan ya gauraye da
haske lokaci guda.

Leave a Reply

Back to top button