Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 17

Sponsored Links

17
Kallan kansa yayi a bathroom din yaga yanda ya lalata kansa da kayansa sai a lokacin ya tina da a washing machine ya wanke amma sai tinanin bai zo masa ba sbd kusan haka yake komai nasa na wautan ‘yayan fari wani lokacin duk da ya zama babban mutum hakan ne yasa kusan ko yaushe dd babba a gurinsa koyaushe DD ne a gaba sbd shima yanada zafi da rashin wasa dan haka komai na DD ya masa duk da zafin kan DDn ya wuce gaban nasa sbd shi harda lokacinsa dayake kai na young billionaire sbd dukiyarsa bata Familyn kaantes bace shine ya tara abarsa da businesses nasa wainda ke qara saka dd babba dukan kirji da DD kaante jininsa ne baibar komaiba a halinsaba sak,
Yayi kudi bada kudin familynsa ko iyayensa ba.

Sake kallan kansa yakeyi yaga ko fita bazai iya daga bathroom din a hakan ba ruwa ne sosai a jikinsa dan haka ya zare kayansa kawai ya sakarwa kansa ruwan zafi ya danyi wanka sbd jin kaman yana qarnin wankin ma.

Yana gamawa ya fito ya sanye da Bathrobe mai kauri da girma datai masa yawa sbd Baiyi jikin DD ba,
Shi jikin fulani ne dashi ba girna sosai,shi kuwa DD qaqqarfan jiki ne dashi daya bude sosai sbd Geamin dayake dan haka yanayin jikinsu sam ba daya ba.

Bacci takeyi sosai dan haka ya fice dakin ya nufi bedroom din DD amma a rufe yake kuma baisan codes ne ko key ba ya hana kofan budewa sai kawai ya hakura ya dawo ya koma bathroom ya jefa kayansa a Machine dan wankewa sbd idan yayi ordern sabbin kafin kafin su iso garesa time ya tafi sosai sbd a first gate ma zaa karba delivery din tukuna shima ayo masa aikesensu daga first gate duk taruwa zaayi a qara bata time dinsu.
Yana gama wankewa ya fito ya zauna kan lafiyayyar sofa din dakin yana amsa wayoyinsa a Ahankali.

******qarfe 6 na yamma Benazir ta kammala komai ta fito makarantar ta rasa yanda zatayi tasan Sumayyah na school kokuma ta wuce gida ko tana Asibiti har lokacin.
Batada wayar kira bare ta sani dan haka ta yankara kanta da sumayyah din tikitin Qaddara ta nufi gida tana fatan sumayyar na gida idan ba hakan ba yau suna cikin lissafin kwanan wahala.

Ana sallar magriba ta iso gida bata tadda sumayyah ba take jikinta yayi sanyi ta saddaqar da yau din saita Allah su a hannun Ababa.

Sallah sukayi da Anne ta fito tana wanki hankalinta na kan kofa cikin tsautsayi sai ga Ababa ya riga sumayyahn dawowa yana ganin yanda hankalin Benazir da Annensu ya tashi yasan Sumayyah bata gidan,Hande dake jiran dawowarsa tini tafara fesa masa labarin sumayyah bata iso gida ba har lolacin.

Shiru kawai yayi yana gyada kai idanuwansa akan Benazir zaiyi magana sai Sumayyahn ta shigo jiki a matuqar mace ba qwari zazzabi ne a jikinta sosai ga jiri tana gani komai na jikinta bata jinsa da qyar take daga qafafunta dasukai nauyi tana isowa tsakar gidan ta zube Benazir ta tarota tana jin zafin da jikinta yayi sosai.

Kallansu Ababan keyi cikin tsananin zafi da bacin rai da zallan takaici sbd hakurinsa akansu ya kusa qarewa kwata kwata,
Lissafin kudinsa akansu dayake yi yasa yake hana kansa yi musu dukan da zasu kakkarye ya zubar dasu a bola,
Hijab din jikin sumayyah ya cafko ta wuya yana shaqureta a zafafe yake saukar mata da marika yana tambayar uban me ta tsaya a hanya.

Daqyar ta iya bude baki tace masa batada lafiya tin jiyan shine a hanya ta fadi sai da aka kaita wani qaramin asibiti aka bata taimako.

Bakinta ya hau mari yana sake shawe wuyanta data kasa numfashi tana neman macewa.

Sai data kusa rasa ranta ya saketa yana wurgi da ita tareda qarasa sanya qafa ya rufeta da duka.

Daqyar suka sha bayan ya musu laushi itada benazir saidai Benazir din yan marika ne da basu wuce uku ba nata da sauki sosai sumayyahn ce dai taji jiki sosai.

Daki suka koma Annensu ta gasawa sumayyahn dake rawar sanyin zazzabi sosau jiki ta kwantar da ita tareda rufeta bayan sun bata maganin dasuke dasu yanzu suna boyewa batareda sunsan asalin meyake damunta ba take baccin wahala ya dauketa sbd Acanma saida Wata likita mace tazo ta bata magani da Allurar wani babban lamarin daya samesu.

Koda gari ya waye sbd kawai Sumayyahn ta samu ganin likita a asibiti yasa Benazir da Anne lallabata suka fita makaranta amma kam ko tsayuwa bata iyawa abin harya fara basu tsoro matiqa sbd bata taba zazzabin daya hanata ko iya daga qafafuwanta haka ba.

Suna fitowa ga mamakin Benazir Bilal ne yazo daukansu a qage yake kaman wanda yasan Sumayyahn batada lafiya dan kuwa gabaki daya damuwarsa da rashin sukuninsa a bayyane yake.

Da sauri ya fito motar ya budewa Benazir ta sakata baya ta kwantar ita kuma ta shiga gaba suka wuce.

Ba tambayar komai asibiti ya nufa dasu suna isa dayake likatansa ta jiyan ce sunriga sunyi magana karban sumayyan kawai akai aka daura mata ruwa da allurai dakuma sauran abubuwan dasuka bi baya.

Benazir bata taba ganin damuwa ko rashin sukunin Alh Bilal din ba sai yau duk da ba wani kallan mutane sukeyiba bare su tsaya karantar yanayinsu amma na yau din a bayyane damuwarsa take.

Wani irin tattali da kulawa tareda kauna mai tsananin gaske yake nunawa Sumayyah yana asibitin har ta dan farfado guraren 12 na rana,

Lafiyayyun abinci kala kusan uku aka kawo daga Kaante H&S
Benazir ce ta bawa Sumayyah abincin tasamu taci kadan dr zulfa tasaka wata nurse ta shiga da Sumayyahn toilet ta taimaka tayo mata wasu yan dubarun sai gashi sumayyar ta dan samu qwarin jikinta daga nan tayi sallah tana idarwa Wani baccin ya sake daukanta lokacin jikinta ya dan warware ba laifi.

Anan suka wuni daga ita har Bilal din wanda ya kasa ya tsare bai matsa koina ba saida yamma tayi ya dawo dasu gida kaman ya cinye Sumayyan da idanuwansa masu haske da kaunarta
Ita kuma takasa koda dagowa ta kallesa sbd Halinda zuciyarta da gangar jikinta sike ciki.

A gidan ma haka ta daure tana nuna kuzari da samuwar dan sauki sbd hankalin Anne da sumayyah ya kwanta.

Washe gari Benazir nada wata test dinma dan haka Bilal dake neman dama ya samu shi kadaine yayi jinyarta cikeda so mai tsanani da kauna tareda kulawa kaman ya mayar da ciwon jikinsa.

Dayake iya su biyu ne ranar kuka ta ringa masa zuciyarta cike da qunci saidai shima zuciyar tasa bata cikin dadi sai damuwar amma haka ya ringa lallabata harta dan warware sukai wunin cikin kulawa suka gama da yamma ya biya ya dauki Benazir suka koma gida.

Cikin kwanaki kusan bakwai shine yake jinyarta a sirrance harta warke sosai ta koma lafiya kalau hakama a daidai wannan gabar ya riga ya tabbatarwa da kansa aurenta koda zai dauketa ne subar qasar bada sanin kowa ba amma tabbas sumayyah tasa ce wlh babu me aurar masa ita.

Ita kanta sumayyahn a yanzu da qaddara ta kaisu wani matakin zuciyarta ta sake jarabtuwa dashi,
Yanda suke jin junansu fiyeda tinani cikin ransu.

Kulawarsa akansu ta qaru fiyeda koyaushe hakama yafara shirye shiryen yimusu passports dukkaninsu su ukun.

Sumayyah da benazir aka fara yiwa sbd zuwa lokacin ya sanar musu da manufarsa ta daukesu daga hannun Ababa zasu bar qasar zai kaisu inda zasuyi rayuwa kuma kafin su bar qasar yanason a daura aurensa da sumayyah din dan tini ya tanadi masu daura musu auren manyan malamai na mutunci.

Hoton Annensu akeso da thumbprint amma an rasa mafita saidai daga baya ya bawa Benazir camera a boye cikin dakinsu suka shirya Annen da Hande ta fita da rana sukai mata hoton sai bayan azahar suka tafi makaranta ranar sbd hoton kawai suna fita suka basa kuma cikin saa hotunan sunyi amma sam bazasuyi abinda akeson ba dan haka dole sai anyi dabarar fiddo Anne a gidan.

Anata wannan process din Tafiya ta kamasa dan haka yabar komai ga aje saiya dawo sbd case din DD ne da Dad dinsu sam yaqi dawowa gashi bayan zamansa ‘dan Kaantes business partner dinsu ne sbd ya zuba hannun jarinsa sosai a kamfanoninsu dan haka shares dinsa a kaantes suna dan da kauri kadan duk da suma akwai tarin abar.

*_PHYDOORS FOOD AND MORE_*💯🔥

*_Ina masoya Abincin gayu dana gargajiya da Sea foods? Ga ingantattu kuma tsaftattun kayan Phydoors Sea foods and more da muka tabbatar da dadi, kyau, inganci da tsaftarsu tareda saukinsu._*
*_Uwar gida, Amarya shin kun taba aikin Abinci da kayan Phydoors sea foods and more kuwa?_*
*_Idan baki taba ba ina shawartarki da gwadawa sbd a take zaki gano bambamci da kuma damar Girki masu dadi da ingancin da suka wuce ki._*

_*Phydoors sea foods and more Suna tare daku a koina sbd suna aika kakansu koina a duk Inda kikeso cikin tsari da packaging mai kyau da kulawa hakama ga sauki da Ragusa,Akace siyan na gari maida kudi gida.*_

*_Phydoors food and more is a food branded based in abuja and offered national wide delivery of her items, available food stuffs are stone free crayfish , egusi, palm oil, plantain powder in kg, prawns 🍤 , fried kpomo, some from as low as 2k._*
*_Contact her through this line 08062181151 or DM me let’s do paired order for minna and suleja. She’s based in abuja._*
_*Or visit her instagram handle*_ @ _Phydoors_Food_

 

***Bayan tafiyarsa sai sumayyah tayi sanyi sbd wani irin sabo da shaquwar da sukai kusan kullum saiyazo makaranta ya dubata da kulawarsa,

Ms aysha ma zuwa lokacin ta zama kaman wata uwarsu sbd sosai take hana kebawar Sumayyahn da Bilal dan ganin yanda yake tsananin santa kuma gashi akwai ‘yar rayuwar turai a tare dashi kada barna ta shiga.

Benazir kuwa karatinta takeyi bil haqqi hakama Nasir itama a nata bangaren tana jinsa cikin zuciyarta amma kuma bata taba jin zata iya tsayawa ta kulasa sbd Ababa da sharadinsa tareda gujewa babban masifar da zata biyo bayan ganewarsa Ababan.

Da wayar ms aysha kullum yake samun magana da ita har dai yayi dan busy ya rage kiran sai dare yake samun time kuma lolacin yasan ba lallai tana tareda ms aysha ba dukda time ba daya ba.

****Acikin sati uku zuwa hudu da tafiyarsa ramar sumayyah ta bayyana sbd yanda bata iya cin abinci sai iya na gidansu da ake basu bata iya cin wanda ake kawo musu daga Kaantes,

Gabaki daya tayi sanyi ta dena kuzari,Annensu data ga hakan ta dan ringa lallabata itada benazir a boye ba halin nunawa,
Makarantar daurewa kawai takeyi tana zuwa sbd kawai samun yin magana dashi a wayar ms aysha amma sam ko fita batason yi.

Aikin wahalarsu na gida kuwa kusan akan Benazir ya dawo sbd sumayyahn data fara yanzu rawa jikinta yake dauka sai jiri.

Tin Benazir da Anne basa lura har suka fahimta sosai take hankalinsu ya tashi sbd tsoron idan wani ciwon ne ya shigeta tinda yanzu ta koma yau lafiya gobe ciwo.

Maganin zazzabi da paracetamol suka ringa bata a boye sbd kada ciwon koma wane iri ne yayi mata karfi gwara ta warware kafin Ababa ya sani ya hadasu ya hukunta sbd ta dena aiki sai yakusa dawowa ta fito dan karya gane.

Tin suna boye ciwon Sumayyahn daya fara qarfi sbd koyaushe a zazzabi da jiri take makarantar ma ta dena zuwa har Hande ta gane tayita masifa tana qarawa daga qarshe dole suka ringa saka sumayyahn warewa tayi yan wasu ayyikan sbd kada Ababa yaji ya tsananta mata aiki.
#MAMUH#
#BENAZIR ABABA#DD KAANTE#LITTLE BENA Amnah#HotHot#marriage#love#romance#DBena

ZAFAFA BIYAR🔥

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-FURAR DANKO
Billyn Abdul

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim

Send your Shedan biya Anan👇
09032345899

MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇
09033181070

Zafafa🫶🔥🔥

ZAFIN KAI

Leave a Reply

Back to top button