Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 42

Sponsored Links

42
Ababa Suma ne kawai Bai yiba a inda ya tsaya cak lakacin da kalaman dd babba sukai dirar mikiya cikin kunnuwansa,
Kasa gasgatawa da gasken Abinda yaji yasakashi juyowa ahankali idanuwansa a kafe kan dd babban ya tsaya Yana zaunar da zancen cikin Kansa da zuciyarsa tareda boye shock dinsa.

DD kuwa wuta ya dauke na wasu daqiqun da baisan meyema zaiyi tinani Akai?
Wane qanin Bilal din ake maganar ya auri mahaifiyar ‘yar Dan uwansa?
A saninsa bayan shi akwai qannan dangi dasuke dashi Amma dai koyaushe akace qanin Bilal yasan shi ake nufi duk da a cikin familyn ne kawai ake kiransa qanin Bilal Shima daga mahaifiyarsu sai dad kaante Amma kusan babu kiransa qanin Bilal sbd ganin yafi Bilal din samun cigaban rayuwa ta bangaren dukiya da suna.

Muryar Ababa dake rawa Yana damqeta Dan Hana bayyanarda zalamarsa a natse Yana kallan dd babba yace

“Idan har aurenta zakuyi Banda matsala da Hakan a shirye nake Amma dai Reno ko zuwanta zaman Dan Wani lokacin ne ban yarda dashi kwata kwata sbd babu adalci ahakan.”

Dd babba numfashi ya sauke Kansa na sarawa da hukuncin Daya Yanke din Amma Kuma basuda zabin Daya wuce Hakan a yanzu sbd suna buqatan karban babyn ta dawo hannunsu Kuma rabata da mahaifiyarta kaman yanda Ababa ya fada cutatarwa ne,

Dad kaante ya kalla Wanda Shima dd babban yake Kallo kafin suka Maida kallansu kan DD a tare Wanda shikuma Sam hankalinsa Bai tashi ba sbd baima dauka cewan dashi ake ba akan maganar kawai dai buqatansa ‘daya Daya sani shine ‘yar Bilal ‘yarsa ce a yanzu halak malak da Bilal baya duniya,
Idan akwai wainda ya Isa ya karbi babyn yayi Iko da to shine Dan haka zai karbi babyn kota halin Yaya sbd sanin dayayi babu inda dukiya Bata magana Kuma Bata Aiki.

Dago kyawawan idanuwansa dasuka Dan fada yayi yaga kalar kallan da dd babba da dad kaante suke masa hakama Ababa Shima kallansa yakeyi Yana Jin kaman ya janyosa ya daura masa aure da benazir a lokacin.

Irin kallan da suke masa ya sakasa Sakin Wani gajeran crazy numfashin murmushi cikin zuciyarsa Yana cewa

“Wane crazy tinanin ne yake cikin kan tsoffin Nan”

A fili kuwa Kai tsaye cikin hade fuskarsa daga mamakin tinanin Dayake gudana cikin kansu yace

“You gotta be kidding me,
Ba Abinda nake tinani ba kuke nufi kenan ba right?

Kallan da dd babba ke masa ya tabbatar masa da Abinda suke tinani
Dan haka shi bai iya boye boye ba baya Yi
so tsayuwarsa ya gyara a natse ya Kalli Ababa dake masa kallan mukullin arzkinsa kafin ya dawo da kallansa kansu dd babba ya Bude baki a natse yace

“Babu raayi ko gurin auran mace biyu a rayuwana,
Dayan is ok so bana buqatan Qarin kowanne macen bayan dayan
Please kar ayi complicating things anan,
Maida kallansa yayi akan Ababa dake jiran matsaya Bai masa kallan tsaf ba Kai tsaye yace

“Zan baka blank cheque lissafinka yafara daga naira milayan 100 zuwa sama ka rubuta nawa kakeso ka kawon ‘yata da kanka yau”……

Wani jiri ne ya dibi Ababa ya zubar qasan palon gaban DD din batareda ya sani ba sbd kudin Daya fada shi Koda an auri yar tasa Bai taba lissafin zai samu kudin zasu Kai miliyan darin ba bare zuwa sama.

Zufa ne ya tsatsafo masa ta ko Ina ya karye Yana tsiyayo masa,

Kasa dagowa yayi ya Kalli kowa sbd yaqin dayakeyi da zuciyarsa da hankalinsa dake Neman gushewa akan Jin kudin,
Rawa hannuwansa suka dauka yayi saurin zirasu cikin babbar rigarsa kada a gani asan gushewan hankalin Daya samu na ‘dan lokacin.

Girgiza Kansa ya hau Yi Yana Hana kansa bayyanarda halinda yake ciki
Amma idan har wannan kudin zai iya sakasa haka hakama Idan DD kaante zai iya bayarda wannan kudin kaman ba komai bane to idan ya auri yarsa yaya kenan?
Abinda zai samu zai zama nin ba ninkin wannan???
Hummmnn ya sauke numfashi a boye tareda yaqar zuciyarsa ya dago ya Kalli dd babba da Suma duk suka rasa abin fada sbd Tim farko kowannensu yasan waye Dawood da raayinsa da kalan yanayin rayuwarsa,
To Amma a yanzu dukkaninsu suna buqatan ‘yar dake hannun Ababan Dan haka suna buqatan sacrificing wasu raayoyinsu Dan samun Abinda suke so da buqatan kaman yanda dd babba ya sauke nasa tsananin raayin.

Ganin kaman Basa hayyacin fahimtar Abinda yake fada ya juya yabar palon may be idan Basa ganinsa su kawo Wani tinanin na Abinda zai yiyu.

Yana ficewa Ababa ma Dayake ta yaqi da zuciyarsa gurin Hana kansa karban kudin Dawood kaante din ya fice zuwa gida Yana hada hanya zufa na sake jiqasa.

Bayan barin Dawood da Ababa palon dd babba Kai tsaye Kiran Umme yayi a waya wadda itama take matse da akirata din Jin zuwan Ababa kaantes taji ya aka Kai karshen magana Dan Bata hayyacinta matiqar ba gabanta taga ‘yar Bilal dinta Kuma jikarta ta fari ta dawo ba.

Lokacin da tashigo palon Kallo Daya dd babba yayi mata ya dauke Kai sbd ganin yanda gabaki Daya ta fita hayyacinta sbd ciwon rashin ‘danta,
Kaman wadda take kwance jinyar watanni Takoma idanuwanta kuwa sun kasa hucewa daga munin kumburin da sukai na kukan data kasa denawa har yau din na rashin Bilal da tsananin buqatan ‘yarsa ta dawo gunta.

Cikin nutsuwa da sanyin jiki dd babba ya Bata tabbacin ‘yar zata dawo hannunsu Amma sai idan ta saka Dawood amincewa da auren mahaifiyar babyn wannan shine sharadin Mahaifin maman Babyn idan ba Hakan ba a gobe zai tafuyarsa Subar garin gabaki Daya.

Hawaye masu dumi ne suka gangarowa ummen sbd lalata rayuwar ‘danta da ake magana a maimaikon ‘yar Dan uwansa da suke buqata su dukan,

Auren Sbb dole ne garesa Badan raayinsa ko buqatan Hakan yake ba Amma ya amince sbd ita Dayake son farantawa Amma tasani Wanda bayason hada ko muhalli da kowa har iyayensa ansamu ya aminta zaiyi aure yanzu tin baayi ba ana sake kawo masa Qarin mace ta biyu.,

Yaya Dawood zaiyi da auren mace biyu lokaci Daya?
Tako wane saqo anshiga haqqin rayuwarsa,
Amma Kuma Tayaya suna Kallo zasu rabu da ‘yar Bilal ta tafi tabarsu kaman yanda Bilal ya tafi yabarsu da gibi me girman gaske a zukatansu.

A Karo na biyu zata sake zama uwa Mai son Kai ga Dawood Dan kuwa zata sake shiga rayuwarsa da Qarin wata macen.

Hannu takai ahankali ta share hawayenta tareda jinjina Kai tana Bada tabbacin zata gwada shawo Kansa akan maganar auren.

Miqewa tayi ta fito Kai tsaye part din Bilal da DD din yake ta nufa zuciyarta na karyewa.

Tana Isa a Palo ta taddasa zaune Yana amsa wayar Naseer a hankali Wanda ya kira akan yazo daukansa yau zai koma gidansa.

Jin qarshen wayarsa na tafuyarsa dazaiyi yasaka ummensa kasa riqe hawayenta suka gangaro tayi saurin sharewa da hannunta.

Zaunawa tayi gefensa tareda kasa juyowa ta kallesa sbd kunyar rokon da zata yimasa a Karo na biyu.

Idanuwansa ya dago ahankali ya zuba mata ya karance yanayinta tsaf tsawon mintina kafin ya Dan dauke idanuwansa Yana ajiye wayarsa dake hannunsa gefensa ya kalleta cikin nutsuwa yace

“Umme idan kikace nayi auren Nan Hakan na nufin Zaki janye wancan maganar auren na farko,
Na baki zabin duk Wanda acikinsu kikeso ki zaba Daya zan aura kowace a cikinsu”.

Yana fadan Hakan yayi mata shiru sbd babu Abinda zai qara Akai,
Maganar zasuyita Janta ne har sai waninsu ya samu ciwon Daya shigesa na damuwa da maimaicin Abu Daya Wanda Sam Hakan baya cikin Abinda yake buqata a rayuwarsa.

Shiru ummen tayi tana kallansa da idanuwanta dasukai laushi sbd a cikin Biyun yanzu babu Wanda zata iya zaba tabar Wani.

Ajiyar zuciya tayi ahankali sbd da Bilal dinta na Nan da duk bazasu shiga wannan tsaka me wuyan ba daga ita har Dawood da zaa aurawa mata biyu duka badan Yana sonsu ba.

Miqewa tayi ta fito Bata iya zabar ko Dayaba a zancen ta koma part dinta tana shiga tinani da damuwan Tayaya ma zata iya kallan Dan uwanta da hajiyarsu ta fada musu Dawood bazai auri Sbb ba wata zai aura?

Wannan maganar kadai zata iya shiga tsakaninta da Dan uwanta da hajiyarsu komai ya lalace a zumincinsu.

Dad kaante ma da Kansa yaje yayo magana sosai da Dawood din Amma Sam raayinsa ya kasa sauyuwa Saida dd babba ya rokesa a matsayin shine zaiwa alfarmar Benazir,
Idan ummensa ta rokesa ta zabar masa Sbb shikuma ya rokesa ya zabar masa benazir Dan haka Suka sakasa a tsakiya sbd sune mafi soyuwa a ransa su Biyun sai babyn da ayanzu tin batazo hannunsa ba yake jinta cikin ransa ta maye gurbin da Dan uwansa yabar masa.

Tinda dd babba yake babu Abinda suka taba ganin ya kwantarwa Kai sai wannan buqatan tasa ta auren Benazir wadda ta saka kusan sauran yayansa sanin halinda ake ciki.

DD kuwa daya gama fahimtar babu Abinda zai sauya tinanin su dd babban daga maganar auren dole ya amince sbd yasan auren sbd ‘yar dasuke buqatan karba zaayisa hakama bayajin zai iya kallan matar da Bilal yagama mallaka a matsayin tasa matar,
Bama zai iya saka kalman aurenta cikin Kansa ba sbd Dan uwansa musamman da haihuwa a tsakaninsu.

A cikin Daren zancen yarda da auren isarwa Ababa,
Da farko kasa yarda yayi da Abinda dad kaante ya kirasa ya sanar masa akan zuwansu Neman auren ‘yarsa gobe Saida ya kashe wayar ya sake dubawa yaga tabbas sunan dad kaante ne suka gama magana a lokacin.

Sakin wayar yayi tareda zubewa qasa da sauri yayiwa ubangiji sujjada ya taso ya fito zufa na tsinke masa ya tsaya tsakar gidan ya kwada sunan benazir wadda ke daki zaune tana bawa baby Madara.

Jin Kiran Ababa ya sakata sauke ajiyar zuciya ahankali jikinta sanyi da faduwar gaba ta miqe ta fito kanta a qasa ta tsaya gabansa daga nesa kadan rungume da babyn.

Anne ma dake dake rakube zaune fitowa tayi gabanta na faduwan ta tsaya gefen benazir.

Hande ma da sauri ta fito tana tsoron idan ba mutuwa benazir din tayiba itama yake wannan ihun Dan kuwa benazir na mutuwa wannan Karan zaucewa Ababan zaiyi.

Tinda aka haifesu shekaru masu yawa benazir Bata taba ganin murmushin Ababa akansu ba Dan haka daidai lokacinda ya kalleta ya saki murmushin baya tayi ahankali qafafunta na Neman sarewa da tsananin tsoro da fargaba tana sauke Kanta qasa.

“Benazir kin cika mun burina na shekarun Dana debo Ina wahala daku,.

Kallan yarinyar hannunta yayi yaji zuciyarsa na sake sanyaya da farin cikin ganin wannan ranar
Yace

“Sunan benazir sunan sa’a ta ne a yanzu Dan haka itama na saka mata BENAZIR sbd idan Kuka je Tako ina sa’a tayita fasomin ba kakkautawa,
Aurenki zaa taho nema gobe a satin Nan zaa daura Miki aure.

Anne data ji saukan zancen har cikin zuciyarta ta rintse idanuwanta a hankali tana tilasatawa zuciyarta karban zancen da sanyin farin cikin dole.

Follow me at mamuhgee Arewabooks ko VIP for more pages
09033181070
#MAMUH#
#BENAZIR
#DD KAANTE
#HOT HOT
#MARRIAGE
#LIFE
#DEEP

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button