Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 53

Sponsored Links

53
Amnah ta samu sauki sosai ta warware Dan haka yanzu Bena ta samu nutsuwa da kwanciyar hankalin aikin office Datake Dan leqawa hakama tana samun time sosai yanzu na zaunawa da dd babbanta suna maganganu na businesses sbd kusan matsayin da Bilal ya rasu ya bari ne yake son Maidata Akai sbd Shima Bilal din yanada Saar iya gudanar da kowane irin business ya qulla sai an samu Abinda akeso 100 percent.

Umme Sam batason suje Lagos service nasu Amma Kuma kaman raayi da buqatan dd babba ne suje can din Dan haka dole ta hakura gashi anan zaa bar mata Amnah sai Mummynta ta gama ta dawo Kuma.

Lokacinda tafiyansu ya qarato Amnah harda ciwon kewan mummynta da zatayi ta kwanta daqyar Bena ta iya danne zuciyarta ta tafi tabarta Allah ma ya saka daddynta Yana Nan shi Dan haka kewan da zai ringa debe mata daban ne musamman wasu lokutan gurinsa take kwana sun Saba.

****Sabuwar rayuwar kwanciyar hankali da hutawa suka fara a Lagos sbd Sam ba Wani wahala ko gwagwarmayar dasuke fama da ita sbd tini suka gama komai suka fara bautan qasansu a natse.

Wani 2 bedroom duplex ne dake Ikeja suke ciki na DD Wanda babu Abinda gidan ya rasa na Jin dadi da tsadan rayuwa,

Komai na gidan bisa ga tsari da yanda yake buqata yake hakama komai na a tsare yake kaman gidansa na Zurich da can gida.

Bedroom Daya suke amfani dashi sbd dayan bedroom din nasa ne basuma San Ina key dinsa yake ba bare Yaya yake.

Zeenah datai missing rayuwarta na turai suna zuwa Lagos din ta koma baturiyarta suka goge abinsu suna zuba life daidai yanda tayi musu.

Dayake service din nasu na yayan manya ne akwai ranakun da bama sa zuwa Dan a sati baifi suje so biyu ba gabaki Daya Zeenah ta zarar da Bena wadda itama Daman rayuwarta ta zurfafa sosai a rayuwan hutu da wayewa kawai tanada kawaici ne dakuma kalan rashin sakewanta da mutane sosai Daya zama kaman Wani Jan ajinta ne,

Amma a rayuwar da suka samu Kansu ta garin taji Dadin garin sosai fiye da wasu qasashen turawan Dataje Dan haka ta sake tana rayuwanta hankali kwance.

Kullum tana waya da video call da Amnah matiqar tana gida saidai ranakun Datake gurin daddynta to wannan shine Bata samun ganinta a waya sai ranar data dawo.

Ahakan suka dauki lokaci Dan har suna maganan wata biyu a garin Basu koma gida sbd dd babba yace su zauna su kammala gabaki Daya tukuna tinda a gida suke.

***Yau Zeenah ce kawai ta fita ita kadaice a gida
Itama Bata fita bane sbd yau Bata buqatan fita koina hutawa takesan Yi sbd jiya har dare sosai Basu dawo gida ba.

Baccin Rana tayi sai yamma ta tashi tayi wanka ta fito ta nufi kitchen,
Ruwa tafara Bude fridge ta dauko roba ta Bude Tasha kafin ta nufi kitchen island ta janyo kayan tea dake Kai ta hada warm tea Tasha sbd batasan Abu me zafi sosai ita.

Tana gamawa ta fito tana duba sakonnin wayarta har Dana Zeenah dake sanar da ita zata jima Bata dawoba.

Palo ta zauna tareda janyo laptop ta Bude zata fara Wani Aiki taji ana taba kofan shigowa palonsu.

Juyawa tayi ta Kalli kofar Rabin hankalinta na kan laptop din sbd ta kunna.

Password din kofansu taji ana sakawa Dan haka ta dawo da kanta kan Abinda takeyi sbd tasan bayan ita da Zeenah babu Wanda yasan password nasu so definitely Zeenah ce.

Maida hankalinta kan Abinda takeyi tayi tana Dan Dan girgiza qafanta ahankali.

Harta fara Abinda takeyi taki shiru ba hayaniyan shigowan Zeenah din batareda ta juyoba da muryanta me shegen nutsuwa da Wani aji irin class irin na ‘yayan hutu da wayewa tace

“Zee, kikace you’re not coming back early¿ Ko Zak……. Cak ta tsaya da maganarta tana kasa qarasawa tareda dakawata daga Abinda takeyi bugun zuciyarta ya Dan tsananta sakamakon qamshin Daya shiga hancinta da sauri ta juyo daidai qarasowansa cikin palon sallamansa a makoshi.

Kallansa takeyi batareda tasan tana Hakan ba sbd mamaki da rudewa.

Kallanta dayaji akansa ya sakasa dakatawa ya zuba mata nasa idanuwan dasuka sanyata sake shiga Wani yanayi na bugawan zuciya da sauri.

Kaman daga sama taji muryarsa me wuyan ji

“Kin San ana amsa sallama right?”

Dauke kallanta tayi daga Kansa tareda Bude baki ta amsa sallamansa tana Dan tahowa gurinsa tace

“Barka da zuwa”

Tana tinkarosa ya Dan dauke Kansa daga gefen Yana wucewa zuwa hanyar bedroom dinsa sbd kayan dake jikinta da itama ta manta short free size Balenciaga sweet shirt ne kawai jikinta.

A Palo yabar luggage dinsa wadda Naseer ya ajiye masa bakin kofa ya juya batareda ya shigo ba.

Wucewa yayi yabarta palon tana Dan sauke numfashi kadan tanajin kanta na sarawa ma sbd bazata iya zaman palon bama Kuma.

Laptop dinta ta dauka zata tafi daki sai Kuma ta Tina cajan laptop din Yana palon Kuma Sam Bata taba ciresa bama tinda ta saka sa gurin Dan haka tayi zamanta gashi yariga ya shige tasan ba lallai ya fito yanzu ba Shima.

Zaunawa tayi taci gaba da Abinda takeyi hankalinta kwance cikin nutsuwa.

Wayarta ce tayi ringing a Dan kasalance sbd tafara gajiya ta duba taga Umme ce Kuma vidcall take taji zuciyarta tayi sanyi sbd sanin Amnah ce Dan haka ta dauka tana Sakin kyakyawan murmushin farin ciki tana cewa

“Oh my, ya Akai my baby tasan mummynta is Missing her like crazy da yamman nan?”

Dariyan farin ciki Amnah ta saki har tana kwantawa kan gadon Umme data Bata wayar ta fice duba baqin dake jiranta Palo.

Amnah na tsananin son iyayenta su ringa fada mata yanda suke tsananin sonta shiyasa dukkaninsu dasuka San halinta suke yawan fada mata ire iren Hakan sbd tana nuna Jin dadinta sosai.

Murmushi Bena ta sake saki tana sake cewa

“Baby na tayi missing mummy nata kuwa?
Naga kinyi Wani kumatu bayan mummy duk ta rame sbd kewanki,
Daddynki Yana baki more chocolates right??

Dariya Amnah ta sake Yi tana cewa

“Mummy Nima fa sosai nake missing naki and my daddy ma yayi tafiya yau yace he’s coming to you and…..

Fitowan Daddyn nata ne ya saka Zeenah Dan kallan gefe batareda ta juya ba shikuma luggage dinsa ya fito dauka harya tube daga shi sai black towel daya dauro qugunsa kaman yanda yake daura towelsa kaman zasu Fadi Amma yau din ya daure da kyau sbd sanin akwai Wani gidan bayansa,
Da ire iren wainnan sabon nasa yasaka baya iya hada muhalli da kowa sbd shi mutum ne me tsananin son yin komai nasa yanda yakeso ba takura ko wane kame kame.

Amnah ce idanuwanta suka hango mata shi da qarfi tana tsalle tace

“Daddy,daddy..”

Dakatawa yayi ya Kalli wayar hannun Bena yaga fuskar babynsa tana tsallen murnan ganin iyayenta tare tace

“Zo daddy kaima inata son ganinka Ina kewanka.”

Ta bayan Bena yazo ya tsaya ahankali tareda ranqwafowa Yana kallan Amnah ya saki Wani fitanannen murmushin Daya saka ruwan jikinsa na wanka da Bai goge ba sbd Yana buqatan sabbin towels dazai iya goge jikinsa da bedroom din sun jima aje bazai iya sakawa jikinsa ba.

Ahankali ruwan ya digo kan wuyan Bena ya gangara cikin rigarta
Numfashinta ya kusa tsayawa kafin ta iya janyosa ahankali kirjinta na Dan yin sama Wanda yasashi Dan motsawa sakamakon motsin ruwan ya sake digar mata a wuya wannan Karan rintse idanuwanta tayi ahankali
Amnah data Gani tace

“Daddy ka digawa mummy na ruwan wanka fa Kuma ya mata sanyi tace Kuma ruwa ajikin mutum idan ba wanka zaiyiba ko alwala Yana saka mutum yayi rashin lafiya ka goge mata banason mummyna tayi rashin lafiya.

Maganar Amnah ya saka Bena kallan wayar shikuma ahankali ya juyo idanuwanta kan wuyanta da daidai lokacin wasu suka sake digar mata suka gangarowa ahankali zasuyi cikin rigarta ba tsammani Bena taji saukan tattausan tafin hannunsa kan wuyanta,Saura kadan Numfashinta yabar jikinta ba zato ta Dora hannunta Daya akan nasa ta tsayar hannunsa ta hanasa goge inda ruwan suka bi.

Yanda ta Dafe hannunsa da nata ya sakasa karkato da fuskansa kadan ya zuba mata idanuwansa da suka sake tsananta bugawan kirjinta dake sama yana qasa.

Duk kirjinta yayi sama saiya shafi hannunsa dake kusa da gurin
Ya sake zuba mata lazy eyes nasa zaiyi magana Amnah datake kan waya har lokacin ta kira sunansu da qarfi tana cewa

“Daddy kanata sake zubawa mummy ruwa fa nidai daddy ka goge mata Dan Allah.” Kuka take Neman Yi masa Dan haka a hankali yakai hannunsa Daya ya kife wayan ahankali tareda birkito Bena data kasa motsi yana kallan fatan wuyanta da santsinta ya saka ruwan Yana diga yake gangarawa ya sauko.

Kasa Bude idanuwa Bena tayi tana qanqame hannuwanta sbd kusancin dasuka samu yayi kusa sosai gashi jikinsa babu Riga qamshin shower gel dinsa Mai shegiyar qamshi da tsada sai shiga hancinta yakeyi direct.

Saukan hannunsa kan wuyanta a Karo na biyu ya sakasata sake riqe hannunsa a Karo na biyu itama saidai kafin tayi Wani motsi ya bi ruwan zai goge ba shiri ta qanqame hannunsa tareda Bude idanuwanta ahankali ta dago ta kallesa Shima ita ya zubawa idanuwansa.

Baki takeson budewa tayi magana Amma ta kasa sbd dumin da jikinta ke dauka na shigar zazzabi a take.

Shikuma ahankali ya janye hannunsa data riqe ya gangara da idanuwansa zuwa wuyanta a Karo na biyu ahankali ya Bude baki sbd cikin qaramin sauti me kashe jikin Wanda yake sauraro yace

“Bantaba kasa yiwa Angel Dina Abinda takeso ba.”

Juyawa yayi kaman ba shine yayi maganar ba yaja kayan Daya fito dauka ya koma bedroom dinsa ya shige yabarta tsaye numfashinta na kasa daidaituwa hakama mamaki fal cikin ranta,
Tasan ko me Amnah tace masa tana so Bai taba kasa Yi mata shi ba ko menene,to Amma Bata taba tinanin hadda irin Hakan ba zai iya Dan Amnah ta sakasa Kuma ko ajikinsa.

Silalewa tayi a hankali ta jingina jikin kujeran Datake Kai tana kokarin daidaita nutsuwanta kafin ta dauki wayar Daya kife ga mamakinta har lokacin Amnah na riqe da wayar tana jiransu,tana ganin mummynta ta washe baki tana cewa

“Mummy Ina daddy?”

Kasa amsata Bena tayi saidai da hannu ta nuna mata bayanta alaman Yana daki.

Daqyar ta tattara nutsuwanta suka qarasa firan da Amnah tayi mata sallama ta kashe wayarta tareda miqewa ta nufi bedroom ta sake samun nutsuwa kafin tayi alwala tazo ta tayarda sallar magrib da lokacinta yayi.

Koda ta idar Bata fito ba daki tayi zamanta sai datai ishai kafin ta fito ta nufi kitchen ta dafa tea me Dan zafi Tasha da biscuits bayan ta shafesa da Nutella.

A dining take zaune tana Sha ahankali sai gashi ya fito daga bedroom nasa sanye cikin black guntun three quarter da black free size shirt qafansa da slippers black Suma.

Dining din ya nufo Kai tsaye Yana Dan kallan Abinda take ci murya a hankali yace

“Whats this?

Dan dagowa tayi ahankali ta kallesa Amma Bata Kalli fuskarsa ba ta dawo da kallanta kan Abinda take ci cikin nutsuwa.

“I don’t eat wainnan abubuwan for dinner.” Ya fada fuskarsa ba sakewa Kansa tsaye sbd Yana buqatan abinci and bayada patience na jiran order yanzu sbd inda yakecin abincinsu sunada Nisa da Nan inda yake kafin akawo zai iya kamuwa da ciwon ciki yunwa yakeji sosai.
#MAMUH#
#HOT
#DBENA
#LOVE
#ROMANCE
#MARRIAGE
#SAFNAH.

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button