Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 51

Sponsored Links

51
Cak ta dakata ta tsaya tana kasa juyowa sbd kaman tana Jin idanuwansa akanta Wanda suka hanata motsawa hakama ta kasa juyowa saidai bugun zuciyarta Daya Dan qaru.

Qamshinsa taji ahankali kaman Yana qaruwa a iskan dake shiga hancinta ta tabbatarda tahowa ne sukeyi Dan haka tana Jin takunsa gap da ita sai ta daga qafafunta taci gaba da tafiyarta cikin nutsuwa.

Amnah datakesan jinta tsakiyan iyayen nata hannu ta miqa zata kamo Benazir din tana Kiran sunanta
hannunta Bai Isa gurin Mummyn tata da batasan da ita ba tayi gaba cikin tsautsayi Amnah din ta subuce daga hannunsa tayi qasa
dagashi har Bena dataji ajikinta ta juyo da sauri a tare hannuwansu suka tarota tafin hannunta na sauka kan bayan tattausan hannunsa.

Amnah kuwa qanqame daddynta tareda riqe hannun Bena Daya tana kokarin fasa Kuka a tare suka ambaci sunanta cikin muryoyinsu masu nutsuwa da taushi.

Hannunsa da nata yake Kai ta kama ahankali zatai magana ya dago fararen idanuwansa ya zuba mata Wani Kallon Daya sakata Neman rikicewa tana sake kama hannun batareda tasan hannunsa take kamawa tinaninta na Amnah ne da rudewa tasakata kasa tantance girman hannun sbd taushinsa kaman na baby Amnah din.

Wani kallan ya sake zuba mata lokacinda ta sake damqe hannun da tafin hannunta da itama yakeda laushi,
Wanna Karan hannuwan nasu ya kalla Yana kame fuskarsa da ita firgitata kyawunta da tsananin kwarjininsa keyi..

Sai alokacin ta ankara da sauri Janye hannunta hannuwanta na Dan rawa da sanyin murya mara karfi ta furta  “Sorry” ta juya da sauri tayi gaba a Dan rude ko gabanta Bata Gani Allah yasa flat Hermes shoes ne qafarta shi ya hanata faduwa.

Tana shiga Palo Bata tsaya ba gaida Umme tayi ta wuce dakinta ta shige.

Tana shigewa ya shigo da Amnah fuskarsa freshe as always kananun guntayen kaya ne jikinsa idan dai fitan Shan iska ce zaiyi.

Kallansa Umme tayi cikin farin cikin ganinsa ta miqa masa hannu tana masa sannu da dawowa.

Kama hannunta yayi da hannunsa Daya yana sake mata qayataccen murmushin farin cikin ganinta Shima.

Amnah dake jikinsa ta shafa fuskarsa tana Jan dogon hancinsa tace

“Daddy muje na nuna maka kayan da mummy ta siyo mun data dawo kaji.”

Tashi daddy muje ka Gani please….

Saukowa tayi jikinsa ta tsaya ta kama hannunsa Daya da ‘yan qananun hannuwanta biyu tana jansa.

Kallansa Umme tayi tana dariya tace

“Kaje ka Gani tukuna mayi magana hankali kwance sbd Amnah idan bakaga kayan Nan nata ba bazata bari kowa yayi magana da daddynta ba.

Miqewa tsaye yayi ahankali Yana daukanta batareda tinanin har lokacin dakinta Daya da mummynta ba tinda yasan ko uban siyayya Dayake Aiko mata dashi dakin ta ma bazai daukaba sai ana rage wasu bare ace daki Daya take da mummynta da itama tanada kayanta Dan haka ya dosa dakin Datake nuna masan suje.

Bude dakin yayi Kai tsaye suka shigo ya tura kofar ya rufe Yana juyowa ya tsaya cak Yana kallan dakin dake cike da qamshin Mummynta Daya gama kama dakin da sanyin Acn Daya dada sanyayasa.

White clovia bra dinta dake yashe kan lafiyayyan gadon dakin idanuwansa suka sauka ya dauke idanuwansa daga gefen Yana juyawa zai fice Amnah ta taresa da cewa

“Ga mummy Nan ma ta fito ta dauko ma ka Gani Daddy.”

Benazir data fito Kai tsaye daga toilet daga ita sai short sleeveless gown me kwantawa ajiki wanka ta shiga Yi Amma ta kasa sbd Jin ana Kiran sallah sai tayi sallah tukuna Dan haka alwala tayo ta fito Daman ta cire doguwan rigarta da bra Daya dameta.

Maganar Amnah ta ankarar da ita suna dakin da sauri ta dago tana dubo gurin kofar daidai Yana dauke Kansa daga kallan fuskansa a fuske yaso juyawa Amnah ta hanasa shikuma Daman bazai batawa Amnah din ba Dan haka kaman baima San da wanzuwarta ba a dakin suka nufi kujera ya zaunar da Amnah din kafin yayi magana Benazir tini Takoma cikin toilet din tana Jin Amnah nata kiranta tayi kaman bataji ba.

Jansa Amnah takuma Yi har kan gadonsu ta ringa dauko masa duk Abinda takeson ya Gani Yana sauraranta kawai batareda ya iya magana me tsayi ba Daman sauraran surutun kawai Yana Basa nutsuwa da farin ciki.

Da kanta ta gaji Amnah din suka fito ba Dan Hakan ba shi zai iya zama taita masa surutun har kowane lokacin zasu Kai ba damuwansa bane.

Suna fita Benazir ta fito Dan tini tayi wankan data fasa.

Sallah tayi Shima lokacin an tada sallah tini ya fice zuwa masallaci.

Tana idar da sallah ta dauki wayarta tana duba sakonnin emails na yan ayyukan da dd babba yasa aka fara Bata Dan gwada zurfin hankalin ilimin data yo akan harkan business gashi akwai acct sosai cikin kanta kaman me.

Aje wayan tayi ta miqe tareda zare abayan sallarta ta fito jikinta sanye da Celine English straight gown da Hula mara nauyi akanta riqe da hannun Amnah Da itama tai mata wanka ta shiryata cikin black pyjamas na Yara masu tsantsi tana hammar bacci gashi Bataci abincin dare ba.

Gurin su Umme dake Palo zaune ta barta ta nufi kitchen da kanta Dan hado mata tea Dan yawanci idan taci abinci me nauyi da dare baya Bata lafiya sosai shiyasa da daddare an sabar mata baa Bata Abu me nauyi se light.

Chocolate custard ta damo mata da kanta ta zuba madaran sosai aciki Bata saka sugar ba ta fito riqe da cup din tana Dan juyawa a hankali ta dawo.

Zaunawa tayi gefen Zeenah tana sake juyawa sbd ya huce.

Sallamarsa ta sanyata kasa dagowa taci gaba da hurawa se gashi baima zauna ba yayiwa ummensa goodnight ya fice.

Tana gama bawa Amnah custard din ta kira Nafisat ta dauketa ta tafi sake gyarata Ta Kwantar da ita sukuma suka nufi dining cin abinci.

Tana gamawa taje ta Sako babbar jallabiya akan rigarta ta nufi gurin dd babba kaman yanda ta Saba duk dare kafin shigewa saita je ta gansa.

Bata Wani jima ba kaman yanda ta Dan Saba jimawa har dai idan takai masa abincinsa da kanta ne sbd mafi yawan lokutan idan tana gida itace ke masa girkinsa na musamman me qara lafiya da inganci.

Tana dawowa babu Bata time ta kwanta take bacci ya dauketa itama.

Washe gari zata fara zuwa office ganin Wani aikin da dd babba yasakata duk da bawai bar mata aikin yayi ba gabaki Daya ya sakata joining fahat kaante ne babban yayan Siyam din Mum Khadija.

Dayake da ‘yar gaban goshin dd babba akafi saninta Dan haka ta samu tarba da respect sosai daga wainda suka samun ganinta Dan company din nada girman da kowa Yana can gurin sabgar gabansa ba kowa zai ganka ba harka tafi ka Gamo ka fito.

Fahat kaante yaji Dadin ideas dinta da wasu suggestions data Bada tareda Yaba nata ilimin Dan haka sosai yaji Dadin Aiki da ita a wunin sai yamma suka fito tare ta wuce kaantes Shima Yana biye da ita suna isowa shi ta gate din baya Wanda acan nasu bangaren yake ita Kuma ta shigo ta gate din gaba a Dan gajiye.

Tin a gurin parking taga Rolls-Royce black haraban gidan ta fahimci Daddyn Amnah na gidan Dan haka ta shigo a Dan natse cikin sa’a baya part dinsu Dan haka Kai tsaye ta wuce bedroom dinta.

Ko da tashiga tana waya Dan haka tana shiga Bata Kalli inda gadanta yake ba ta nufi closet tana ajiye handbag nata da key na mota tafara zuge zip din gaban doguwar jallabiyanta.

Rufe kofar dakin taji a juyo tana kallan kofar tana kashe wayarta cikin mamaki,

Bata ga kowa ba Kuma tabbas rufe kofar taji anyi,
Dawo da kallanta kan gadonta tayi ga mamakinta sai taga Amnah kwance tana bacci.

To waye ya bude dakin?
Shigowa Akai ko fita?

Numfashi ta sauke ta koma ta qarasa tubewa ta shige toilet kawai.

Bayan tayi wanka gajiyanta ya sake tayi sallah ta tashi ta nufi Amnah zata tada ita sbd baccin magrib zaisa ta kasa baccin dare.

Tana taba ta taji jikinta da zafi sosai
da sauri ta Kalli fuskatarta tana sake taba wuyanta zuwa goban kanta taji zafi sosai.

Mummunan faduwa gabanta yayi ta janyota jikinta tana Kiran sunanta ahankali cikin tsananin damuwa da kulawa tace

“Meya samu my baby.”

Motsawa Amnah din tayi ahankali tareda Dan Bude idanuwanta tana ganin mummynta ta sake shigewa jikinta tana lafewa ahankali tareda Dan Kiran sunan Mummyn.

Rungumeta Bena tayi tana cewa

“Baby zazzabi kikeyi?
“Meyake Miki ciwo?
“Kinsha ruwan sanyi sosai kokuma qasan ruwa right?

Numfashi ta sauke tareda saukowa gadon ta mayar da Amnah din ta Kwantar ta fito Kai tsaye kitchen ta nufa inda maganinsu suke cikin Wani Dan qaramin fridge Daya da aka ware a kitchen kawai sbd saka maganin Amnah.

Paracetamol ta dauko ta Kalli Nafisat dake kokarin jera kayan da aka wanke tace ta hadowa Amnah white indomie ta kawo mata.

Daki ta koma tana shiga ta zauna bakin gadon tareda janyo Amnah jikinta ta rungume duk ranta na dagulewa sbd Amnah itace kuzari da farin cikinta bayan Annenta,.
Hankalinta ba qaramin tashi yake ba idan Amnah tafara zazzabi sbd komai qanqantar ciwo jigatar da ita yakeyi sosai taita wahala Dan haka hankalinta ke Neman tashi.

Maganin ta bata cikin kulawa da lallabawa kafin ta goge mata fuskarta da tissue tana ajiyewa sai ga Nafisat ta kawo mata Abinda tace din.

Zaunar da ita tayi jikinta cikin lallabawa da kulawa ta fara Bata indomie din Nafisat kuwa ta tattara kayan maganin da tissue zata fita dasu.

Kawar da Kai Amnah din keyi tana girgizawa tace

“No mummy banaso na koshi.”

No please sweety kici kadan ok???

Sake girgiza Kai tayi tana lafewa jikinta tace “No I don’t want”

Kallan Nafisat tayi ta miqa mata plate din jiki ba qwari tace

“Ki hado mata tea mara zafi sosai”

Karba Nafisat tayi tana cewa to ta fice da sauri.

Bayan fitan Nafisat shafa kanta Bena tayi cikin kulawa kaman zata hadiyeta tace

“Sweetyn mummy me kikeson kici to?
Zaki Sha warm yoghurt?

Girgiza Kai Amnah tayi a hankali

Bena tace “but baby you have to take or eat something before going to bed ga Kuma magani kinsha”

Kuka Amnah ta fashe dashi ahankali tana cewa

“No mummy ni banason abinci,bana Jin yunwa.”

Numfashi me dumi Bena ta sauke tana rarrashinta zuciyarta ba dadi.

Nafisat ce ta kawo tea din ta karba ta saka Amnah Shan nasa dole cikin tausasawa Yana gama shiga tafara Amai sukai toilet.

Aman datayi ya saka Dan kuzarinta tafiya tareda tsananta zazzabin ta fara Kuka daqyar Bena tai mata wanka da ruwa me zafi ta dawo da ita ta shirya ta Kwantar tini Nafisat Daman ta sake gyara dakin ta sauya zanin gado sabo duk da aman be taba ba Amma sbd tsafta da kiyayewa.

Rage sanyin Acn tayi sosai kafin ta fice daga dakin.

Itama Bena din Saida ta sake wanka tea kawai Nafisat ta kawo mata Tasha ta kwanta Batama iya fitowa ba.
##MAMUH#
#HOT
#DBENA
#ROMANCE
#DEEP

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button