Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 79

Sponsored Links

79
*****
Momy ce tafara Bude baki ta gaidasa cikin
Dan kamewa sbd ganin kallan Dayake mata,
Sam bayason baqi kowanne suna shigowa gidansa sbd baya San kowa na sakawa rayuwar Dayake gudanarwa cikin gidansa Ido.
Amsa gaisuwanta yayi Yana kallan hande yace tayi ciki da Anne
Fizgarta Anne tayi tana cewa
“Muie ni wannan masifa har Ina da tsufana anbarni da aikin kulawa da mahaukaciya,
‘yarki na can cikin daula tana hutawa da ‘yarta tabarni da aikin kulan mara da mahaukaciyar uwa ayi magana su miqawa Ababa kudi yace na Dena damunsa da zancen Ina dawainiva da mahaukaciyar.

Daki hande taja Anne suna shigewa momy ta juyo ahankali tareda sauke numfashi me dumi da ajiyan zuciya ta Kalli Ababa suka sake gaisawa Kai tsaye ya tambayeta daga ita ba walwala a fuskarsa.
Numfashi ta sake saukewa tareda Dan gyara tsayuwa ta Bude baki tace
“Magana ce me mahimmanci da girma ta kawoni…
Akan me kenan??”Ababa ya katseta sbd bayasan kwana kwana ko batawa Kai lokaci matiqar ba garkar samunsa bace.
Sake kallansa momy tayi itama Kai tsaye tace “Akan halinda kake ciki muma muke ciki,a taqaice dai akan safnah ‘yarka dakaji mahaifiyarta na fada…
Wani mummunan matsiyacin kallai ya dago idanuwansa yayiwa momy sauran annurin fuskarsa na daukewa gaba Daya ya juyo da kyau ya kalleta zaiyi magana ta Bude bakin
Jakarta nuna masa daurin kudaden dollar dake sama kafin na nairas a qasa.
Kudin ya kalla da kyau ya ga Basu kama da fake ba Dan haka ya dauke kallansa akansu ya dawo dashi kan momy suka Kalli juna ta gyada masa Kai alamar zasu iya magana yanzu.
Wani numfashi ya sauke sbd mamakin matar datasan kudi sune Abinda ke karkatasa ga wata lanqwasar,
To Amma idan Safnah data ambata tana nufin safnan data gudu daga gidansa ce tsawon shekaru masu yawa wh wannan kudin bazai fidda ita daga hannunsa ba.

Ta dawo da kanta ne a daidai lokacin da yake
Neman ‘ya ko ta sata ce ya migawa yan drugs din Daya ci kudadensu sama da miliyoya
Dan haka babu Abinda zai hanasa hukunta rayuwarta mafi munin hukunci kuwa.
Palonsa suka garasa Yana gaba taba bayansa har cikin palon ya zauna a natse tareda Nuna mata guri ta zauna itama a natse tareda ajiye
Jakarta gefenta.
Numfashi ta sake saukewa a Karo na uku da ajiyan zuciya kafin ta kallesa dakyau ta tattara hankali da tinaninta guri Daya tafara da cewa
“Sunana hai Nuratu matar Alh basheer bulama,.
Kallanta Ababa ya sake Yi da sauri sbd baya mantuwa ga duk Abinda yakeso ko ya tsana ko lissafinsa ya sauka Akai,

Alh basheer bulama shine ‘yarsa ta auri DD kaante Rana Daya da Benazir.
Wani tinani ne kawai yafara zuwa Kansa a take kafin ta qarasa bayanin na kishin ‘yarsu ya kawosu akan tasa ‘yar Amma zai gama Jin Abinda taxo dashi da inda sunan Safnah ya shiga bakinta.
Ci gaba da bayani momy tayi da cewa
“Nice momy din matar Dawood kaante Daya wadda aka daura masa aure da ita Rana Daya da Bena Kuma nice marigiyar ‘yarka Safnah data bar gida a baya.
Shiru Ababa yayi Kansa na daukan caji da maganganun data fada din.

Kallanta yayi da kyau Yana Dan gyara zama yace
“Bangane marigiyar ‘yata ba Kuma mahaifiyar
Matar Dawood?
Ke menene sunan Taki yar matar Dawood din??
“Safnah basheer bulama” ta fada Kai tsaye.
Ni tawa yar Datake hannunki da wane sunan take amfani yanzu?
“Safnah basheer bulama” ta sake fada Kai tsaye.
Shiru Ababa yayi ahankali ahankali zafin kansa na tashi sbd Jin sabon zancen kaman bana hankali ba, Safnah basheer bulama har so biyu a gida
Daya??
Zare hular Kansa yayi ya ajiye gefe sbd zufan da Kansa ya a Dan fara hadawa ya kalleta yace
“I dan sunan yarki Safnah bulama,tawa ma
Safnah bulama a cikinsu da waye aka daurawa
DD aure da ita??
Sake sauke numfashi momy tayi tareda gyara zama Dan Yi masa gwari gwarin zancen Dalla
Dalla tace
“Safnah ‘yarka da ita aka daurawa DD kaante aure,Kuma Nima itace ‘yar tawa ‘yar Alh basheer bulama.,
Bayan barinta gida nice na tsinceta Kuma nice na bayyanar da ita ga Alh basheer bulama a matsayin ‘yar Dana Haifa masa,
Safnah ‘yarka itace ‘yar basheer bulama..
Shiru Ababa yayi zuwa lokacin zafin kansa sosai yake ci ya Bude baki cikin tsananin mamaki da tiririn Kai yace
“Benazir da Safnah miji Daya suke aure kenan?
Safnan tawa yar itace Kuma ta koma ‘yar Alh basheer bulama wadda aketa ikirarin babu
Abinda yakeso Sama da ita,
Auren mi Daya a tsakanin ‘yaya biyu to na waye ya haramta acikinsu yanzu??
Momy da Nan takeson Akai tace
“Aurensa da Safnah ya Riga ya haramta sbd
Bena yanzu haka tana Asibiti kwance ita ya fara mayarwa matarsa.”

Sai alokacin Ababa ya dago ya Kalli momy
Yana share zufansa sbd tsaka me wuyan da zasu sakasa idan akace na Bena ne zai haramta Dan kuwa shi ita Kai tsaye yake bugata a Kaantes,
Ko sumayyah ta dawo duniya yanzu akace ya zabi wadda zata zauna aciki Bena zai tsaya ta zaunu a ciki sbd itace saarsa.
Kai tsaye momy ya kalla Yace “Ina Safnah?
Girgiza masa Kai tayi tace
Ka nutsu kaji asalin Abinda ya kawoni.
Wani mugun Kallo yayi mata sbd a yanzu
Safnah yake buqatan Gani gabansa kawai yaga inda ta samu zarra da qarfin zuciyan iya barin Wani ya tinkaresa da zancensa bayan tana kusa dasu Ashe.

Zafi zuciyarsa ta dauka sosai sbd gabaki Daya zancen tafasa jininsa yayi duk Wani zafin kansa da zafin zuciyarsa suka taso.
Momy data ga yanda lamarin zai lalace batareda sunyi maganar datazo da ita ba ta fidda wayarta kawai ta Nemo recording din maganar Anne ta kunna masa tareda ajiyewa gabansa muryan Anne na fita cikin kyakyawan sauti tana fadan vanda Ababan yayi komai da yanda ya canja Bena da sumayyah dakuma gaskiyar sumayyah ce ta haifi Amnah da yanda ta fadawa dd babba komai da alqawarin da dd babba yayi make na ganin qarshen
Ababa.
Tsit palon yayi har recording din yagama playing bayan numfashinsa dake fita babu
Abinda yake motsawa a jikin Ababa, Sake kunnawa yayi ya sake saurara,Yana qarewa ya sake kunnawa har so hudu ya tabbatarda muryan Anne ce da kanta take maganar,
daidai Nan Kuma Safnah ta shigo palon Kai tsaye ta kofar waje dake kawoka cikin palon direct.
491 a
1 101
Daqyar take iya daga kowane takunta tana garasowa cikin tsakiyar palon.
Bugawan zuciyarta har ta saman kayanta ake ganinsa sbd tsananin tsoro da firgicin Dayake cikinta,
Tsayawa tayi a inda take gafafuwanta da hannuwanta na rawa ta dame hannuwanta sbd rawarsu ta tsananta.
Bata iya dagowa ta Kalli Ababa sbd Shima Wani horo ne da har abada Kila bazasu iya denawa ba saidai Nan gaba Kila idan ya shiga
cikinsu.
Tinda ta shigo ta tsaya Kallo Daya Ababa yayi mata da idanuwansa dasuka kada sukai jajir lokaci Daya da Wani irin mummunan tashin hankali bagin ciki tafasar jini da zuciya.
2 PA
Sharkaf ya jige da zufan da baimasan meyake akai Dan Adam keda irin wannan ruwan me yawa cikin jikinsa sbd har Wani tsiyaya yakeyi.
A tsawon shekarunsa baa taba Yi masa
Abinda ya jijiga duniyarsa da tinaninsa irin wannanba,
• A tsawon shekarun Nan Ashe kallansa ake tsaf Angama sanin komai gameda shirinsa,
Tarko aka hada masa mummunan da baisaniba Bai zataba saidai kawai yajisa aciki,
Duk wahala da gararin Daya ringa yi Yana kashe Kansa da lissafi da tinanin ya gama samun Abinda yakeso ranar kawai yake jira
Ashe babu ranar zuwan wanna ranar bare ya
Gani.
Lallai Anne ta demo Abinda kanta bazai iya dauka ba,
Benazir ma ta debo Abinda kanta bazai dauki nata ba bare na uwarta.
Safnah datake tsaye ya dago itama ya sake kalla da jajayen idanuwansa ya miqe tsaye ya nufeta
Take rawar hannuwanta tsananta sbd dukkaninsu da uwarsu wIh babu Wanda zai fita Basu he gasa tare ba.
Tsayuwarsa gabanta ya sakata dagowa ahankali tana fidda Wani irin zufa ta kallesa ko gama sauke idanuwanta akansa bataiba ya sauke mata Wani mummunan Marin bayan hannun Daya sakata zubewa qasa gefen bakinta Yana zubarda jini
Qafa ya saka yayi mata mugun Harbin data gangara gefe tana Dafe cikinta hannuwanta na tsananta rawa Kuma har lokacin ta kasa Bude baki tayi ihu ko Kuka, Jajir kawai idanuwanta sukai Wanda yake nuna tabbacin taurin zuciyar Datake dashi da bushewa ya saka qafarsa Daya ya take wuyanta daidai magoshinta tini tafara Shure
Shure tana Neman rasa ranta ga bakinta lokacin ya sake zubarda jini sosai sbd ba qaramin muni Marin Daya saukar mata yayi ba.
Momy dataga masifar rashin Imani Dayake
Neman daidai da nata koma fin nata sbd su a tsorace cikin rawar jiki suke komai Ababa kuwa hankalinsa kwance yake Neman kasheta har lahira babu toro ko rawar iiki a tareda shi.
Da sauri tazo gabansa tana kokarin cire
Safnah daga garqashin kafafunsa tana rokan ya saketa zata mutu.
Bai saurara Saida ya Bude baki yace

“Idan ma ta mutu ke kinada bagin ciki ne?
Tafi kowa sanin waye ni Amma har ta lya dawowa bayan ta gudu daga gareni tazo ta tsaya gabana Kuna tinanin na amsheta hannu biyu ne?
Somewa Safnah tai sai alokacin ya dauke kafarsa daga wuyanta zuciyarsa na tafasa da tsananin zafi da jininsa dake quna ya nufi cikin gida Kai tsaye dakin Anne ya nufa hande na ganin wucewarsa ta fito daga dakinta tana tambayar lafiya.
Yana shiga dakin wuyanta ya fara shagowa Bai tsaya komaiba ya janyota kaman ba mutum ba ya fito da ita har cikin palonsa ya jefar da ita gasa sai alokacin idanuwanta suka Bude cikin wahala ta Kalli gabanta tayi arba da fuskar Safnah kwance a some itama bakinta na zubar da jini.

Rufe idanuwa Anne tayi jikinta mace ta Bude ahankali ta sake dubawa dakyau taga Safnah dinta ce,
Wani nauyi zuciyarta yayi sbd idan har lafiyanta kalau ba cikin hali ne na hauka take ba idanuwanta ke nuna mata Safnah to tabbas
‘yarta ce take Gani gabanta.
Kokarin tashi tayi Dan sake Gani dakyau
Amma Ababa ya shaqota tareda fizgo wayar momy ya kunna make a maganarta taji.
Tinda tafara sauraran recording din ta fahimci itace Kuma shikenan Ababa yasan Abinda komai zai iva lalacewa Bena dinta.
Duk Abinda ya shafi Bena a yanzu kaman rayuwarta yake Dan haka jikinta ya dauki rawa idanuwanta suka fara sauyawa zuwa ia sbd
Abinda ya taso daga zuciyarta na tsananin fargaba da tashin hankali.
#MAMUH#

Leave a Reply

Back to top button