Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 80

Sponsored Links

80

Rawa bakin Anne keyi kaman yanda duka jikinta ya dauki rawa ta Bude baki zatayi magana ya dauketa lafiyayyan Marin bayan hannun daya sakar mata habo itama a take.
Bata damu da jinin dake zubo mata ba ta sake dagowa zatai magana ya shagota cikin Kansa dake Neman juyewa sbd bagin ciki da masifar dake cin jininsa da Kansa.
Hande data shigo tana sake ihun tambayar lafiya kan Safnah idanuwanta suka fara sauka ta tsaya ta duba dakyau dakyau ta tabbatarda
Safnah ce sbd kamannin Basu sauyaba duk da girma da sauyin rayuwar data samu.
Bata bi takan Anne dake Neman mutuwa hannun Ababa ba tayi kan Safnah da momy ke Neman ruwan zuba mata ta farfado a rikice take cewa “Waye wannan kamar baqar ‘yar can Safnah data tsallake uwarta ta gudu ta fada duniya.”
Ababa kuwa baimasan me hande ke fada ba
Jin yake baqin cikinsa na ninkin ninkuwa akan
Anne da duka Abinda ta Haifa masa babu
Abinda suka qaresa dashi sai baqin ciki da asara kan asara.
Wato ita yanxu Nan acikin hauka harta samu
Daman ganin dd babba tafada masa komai bayan algawarin dayayi na hallaka duk Wanda ya fitarda zancen Nan har Abada,
Wato shi wahalar banza ma yakeyi ya sharewa
Bena guri ya samar mata gun shiga da zama a
Kaantes qarshensa kawai suke Jira.
Tabbas da Badan Anne dake hannunsa ba da tini sun Dade da aikasa inda Bai taba tinaniba. Wane babban balai da masifar ne wannan?
Sannan yanzu wannan shedaniyar da sabuwar uwarta suna Karanto masa zancen miji Daya
Bena da safnan ke aure kenan dai a daidai Nan kowa alalensa ta kwabe masa,
Idan har tasa Alalan ta kwabe to wlh ta kowama kwabewa zatayi ta Hakan zai samu tasa mafitar fita da wannan zagayen da Akai masa sbd a yanzu kam zagaye yake baida tudin tsira.
Sakin Anne yayi tareda jefar da ita gefe ta zube tana kasa sakin ko tarin azaba sbd wahala ko fita bayayi.
Magana hande ta hau Yi tana tsinewa Safnah da gudunta da dawowanta Wanda yake sake qular da zuciyar Ababa ya kasa rige Kansa ya hada da Annen da Safnah yayi musu shegen duka Yana fatan ace Bena na gurin ya hada da ita Dan kuwa a yanzu dukkaninsu babu me amfani a gurinsa rayuwarsu da mutuwarsu duka Daya ce a gunsa Amma ko ta halin yayane sai ya samar da amfanin garshe daga gurinsu kafin gamawa da rayuwarsu.
Momy tin Datake Bata taba shiga mamaki da tsoron ganin me aikata barna irin haka babu ko shakka bare tsoro a tareda shi kaman
Ababa ba,
Su tsautsayi ne ma ya sakasu kisa Amma sun
– kasa samun kwanciyar hankali tin ranar har yau din Amma ga Ababa Yana taka wuyan mutane kaman dabbobi ko ajikinsa idanma zasu mutu rufesu zaiyi babu Wanda zai sani
Kuma yaci gaba da rayuwarsa hankali kwance.
Hande ce ta janyo Anne da kanta ya juye ta fito da ita tsakar gidan ta wucewarta dakinta,
Itama momy jiki na rawa da tashin hankali da toro ta fito da Safnah tsakar gidan ta debo ruwa daga Anne har Safnah din ta ringa zubawa a tare kowannensu na sauke ajiyan zuciya suna motsawa ahankali.

Tana ganin sun farfado tayi kan Safnah dake tashi zaune ahankali tana kasa iya juyowa ta
Kalli mahaifiyarta dake Jin jiki sbd bazata iya hada Ido da itaba.
Anne da Bata hankalinta batama tsaya kallan su Safnah din ba ta tashi zaune tana Sosa bakinta Daya fashe ta nufi dakinta Dayake a hargitse kaman na mahaukaciya ta shigewarta tana shiga ta zauna tana qanqame jikinta sunan Bena kawai take kira.
Safnah kuwa momy kamata tayi hande na zaginsu da tambayar gidan ubanwa ita
Safnah zata koma Kuma?Amma ko kallanta momy bataiba sbd Jin takeyi kaman ta fasa kan shegiyar tsohuwar da garamar pistol din
Jakarta.
A bayan mota ta saka Safnah dake Jin Wani radadin zuciya da zafi,
Ko radadin jikinta bataji saina zuciyarta dake tafasa,
Wih bazata ci wannan dukan a banza ba batareda sun samu Abinda takeso ba,
Idan har ta rasa DD to sai Bena ta rasa DD itama.
Koda suka Isa gida ko dressing din ciwonta gin bari tayi a kira likita yayi mata zafi sosai zuciyarta ke mata tanajin qunci.
Momy kuwa Jin tayi lamarin Ababa ya Bata toro sbd wannan ko su zai iya kashewa akan zafin zuciyarsa da nasa buqatan.
Har dare yayi zuciyar Safnah Bata Dena radadi ba gashi tanason zuwa Asibiti gurin DD Amma ba Daman zuwa sbd raunikan dukan Ababa da zaa fahimci duka ne take bare tace accident.
Dan haka dole karya tayiwa Umme cewan batada lafiya sosai itama a kwance take sai gobe zata sake dawowa Asibitin.

****Familyn kaantes kuwa duk inda hankalinsu yake ya tashi suna cikin mummunan tsaka me wuya da tashin hankali da damuwa,
DD dai Yana cikin Wani mummunan hali Dan kuwa Bai farfado ba Kuma an rasa Abinda ya hanasa farfadowa,ko motsi babu Abinda keyi a jikinsa,haka sai Wani irin fayau yakeyi sosal kaman Wanda ake zuge jininsa kullum.
Ba Umme da zeeyba ko Bena da ake boyewa tini ta fahimci ahalinsa ake ciki sbd rashin ganinsa dakuma Kuka da damuwan Umme da
Zeenah Daya kasa boyuwa.
Taji sauki ita sai Dan Abinda bazaa rasa ba na dinkinta da Bai warkeba sai zazzabin Dayake sakar make idan tayi kaida kawo,
Ita kanta gabaki Daya zuciyarta cikin mummunan hali take game da Abinda babu
Wanda yasan meya samesa.

Ko data lallaba har dakin Dayake ta dubosa hawayen dakeson tsiyayo mata ta danne sbd su Umme da dad kaante zuciyarta suka koma tareda Kona duk Wani nutsuwa da kwanciyar hankalinta.
Tana dawowa dakinta Bata zaunaba a sanyaye ta shiga toilet ta rufo kofar tareda Sako wasu hawaye masu tsananin zafi.
Ta jima aciki kafin ta fito idanuwanta jajir
Amma taqi yadda su Umme su Gane ta dawo kan gadonta takwanta ahankali tareda rufe jikinta.
Da daddare harta kwanta Amma batai bacci ba Zeenah na zaune kan sofar dake dakin me laushi tana waya da Naseer Daya kirata Dan sune suke jinyar a tare,shi na DD ita Kuma ta
Bena.

Dd babba ne ya shigo dakin Abbakar na bayansa.
Zeenah kashe wayarta tayi tareda gaidasu tanawa dd babban sannu barka da zuwa.
Amsawa yayi tareda Maida hankalinsa kan
Bena data Bude idanuwanta Jin shigowansa tana kokarin tashi zaune.
Zeenah datasan da babba idan zaiyi magana da Wainda yake ji dasu baya bugatan kowa ta miqe ta fice daga dakin zuwa na DD gurin
Naseer.
Kallanta dd babba yayi cikin kulawa ya tambaya Yaya jikin nata.

Amsawa tayi cikin sanyin jiki sbd ganinsa ya sakata sakin kukanta Datake ta riqewa.
Yasan Daman tana bugatan Wanda zata fasa kukan ciwon ranta gabansa shiyasa ya kawo ziyarar dakuma abubuwan Dayake son ji daga gareta.
Sai datai kukan ta gaji dd babba ya kalleta bayan yasa Abbakar ya miqa mata tissue ta goge idanuwanta yace
“Bena,fadamun meya faru bayan zuwanki highbridge,
Da kikaje wa kika tarar?
Dago idanuwanta dasukai laushi tayi ta kallesa tareda Dan girgiza Kai ahankali tace

“Babu Wanda na tarar”
Shiru yayi kafin yace
“Bayan kin Isa matarsa Safnah Bata zo ba?
Sake girgiza Kai tayi ahankali tace
“Aa”
Dan sake kallanta yay yace
“To Amma securities sun tabbatarda bayan shigarsa baiyi baqi ko Daya Ba sai ku Biyun daga ke sai matarsa data dawo gidan har so biyu.”

Shiru Bena tayi tana sake tabbatarda tinaninta na ranar babu Wanda yazo bayan zuwanta.
Abbakar ya kalla Yace “kasa su tura maka footage na Time da Safnah ta shiga da fitarta ita da mahaifiyarta ko zata Tina Wani abin Kila shock ko ciwo yasa kin manta.”
Banason bincike me girma sosai akan case din sbd kada media su sani inason komai a sirrance sbd son sanin ya Akai aka samu irin wannan mugayen qwayoyin masu iya kashe mutum ma a jikin DD.
Gayada Kai Abbakar yayi Yana cewa
“Inshallah”
Shiru Bena tayi sbd Bata fahimci me dd babba ke nufi ba da maganar qwayoyi a tareda D.

Sallama sukai suka fice suka barta cikin shiga tinani da mamaki harma da tsoron me Hakan ke nufi,
Ana nufin drugs ne na maye masu muni D yasha ko me?
Cikin tinani da fargaba tareda rashin nutsuwan zuciya ta kwana itama Wanda ta kasa tantance na menene Amma zuciyarta Wani nauyi tayi mata da rashin sukuni.
Yawanci irin wannan yanayin tana jinsane a duk lokacinda Annenta zata kasance cikin matsala ko tsananin Neman agaji,
Jin tayi hankalinta ya sake tashi akan Wanda take ciki Dan haka ko rintsawa bataiba yanda taga dare haka taga safiya cikin tinani da radadin zuciya.

****Yanda Bena ta kwana haka Safnah da
momy suka kwana hakama Kaantes suka
kwana,
Ababa ma a zaune ya kwana har safe ko
ringinginawa baiyiba,
Dagyar yaga saflyar ta waye masa sbd tinani
da lissafin rayuwar Daya samu Kansa a ciki
lokaci Daya ba shiri,
Tako wane bangaren ya duba yaga mafitarsa
tana kunshe da rige kowannensu a tafin
hannunsa ne,
Bashida Rabo a Kaantes dai ta tabbata to Dan
haka Shima idan Yana son mafita da tsira to
dole ya samarwa Kansa hanyar bullewa Shima
kafin DD kaante ya farfado kaantes su dawo
hayyacinsu.
Ko sun dawo hayyacinsu idan yanason tsira
da mummunan Shirin dd babba da baisan
ya yake ba to dole. ya batar da Wainda zasu bayarda tabbacin gaskiyar magana akansa wato Bena da Anne,
Idan bazai ci dukiyar kaantes ba bayan duk gama wahala da gwagwarmayar dayayi akan shigarsa cikinsu to Bena ma wlh bazataci ba hakama uwarta,
Shima dd babba bazai samu yanda yakeso ba kaman yanda Suma su Safnah bazasu samu yanda sukeso ba bayan ya karbi dukkanin
Abinda suka Tara prison ze aikasu Dan dole a wannan masifar mutum Daya ne zai tsira Dan haka gwara shi ya tsira tinda yaga hanyar.
##MAMUH#
#KAANTES
#ABABA
* Arewabooks@Mamuhgee.

Leave a Reply

Back to top button