Bakar Ayah Book 2Hausa Novels

Bakar Ayah Book 2 Page 31-32

Sponsored Links

Page 🖤31••32🖤

 

 

“Shigo Maleekah ki zauna,tunda kinji abinda muka faɗa banida zabi illah na sakaki cikin plan ɗinmu.
Saidai idan kika kuskura nasamu wani naƙasu a ciki,please don’t imagine mai zai biyo baya”
“Karki damu anty maryam,matuƙar abinda zakiyi bazai cutar da ahalina ba zan baki haɗin kai”
“Bazai cutar da ahalinki ba saima taimakonsu,domin yayanki na daf da faɗawa siradin plan ɗin wasu.
Badan ceton yayanki nake wannan aikinba,saidai kuma yin aikina zai taimaki yayanki”
“Dan Allah menene aikin,suwaye suke ƙoƙarin cutar dashi,dan allah Anty maryam kada ki barsu su cutar dashi,a shirye nake dana taimaka sosai”
“Ohk tunda kin yarda zaki taimaka abu ɗaya nake so kiyimin,idan ina buƙatar taimakonsa inason shiga rayuwarsa sosai,inaso kiyi iya ƙoƙarinki kada Mahaifiyar ku ta gano mai yake faruwa,inada dama ma ki dunga bata fake information akai.
Inkinyi hakan shikenan aikinki”
“Iya wannan kawai,dan Allah to shin zan iya sanin mai yake wakana”
“Abunda zan iya sanar dake a ciki shine,Mahaifin Matar yayanki wato Lubnah,yana ƙoƙarin lallai sai ya ƙarbi kujerar CEO na company JAAN daga ahalinku,ba iya shikaɗai ba harda ƙanin mahaifinku da matarsa Lylah,koƙarin jefah ɗan uwanki Prison suke akan wani Gurbataccen file,rannan nayi nasarar karba file din na wargazashi.
Suna aikine da Gen abdu manga,a tunanin su yana taimaka musune su karbi kujera,saidai basu san yana amfani dasu bane shi ya karbi share dake wajen Alhaji Abdullahi,wannan share ita kaɗaice damarsa ta ƙarshe dazata bashi lasisin ƙarbar Companyn”
Lokacin da Maleekah taji wannan bayanin jikinta rawa yafarayi kar kar.
Faɗawa jikin Bombee tayi ta kankameta.
“Innalillahi ,nake rokon ki taimaki yayana ashe kin daɗe dafara taimakonsa,tabbas ke Alkhairi ce a rayuwarsa,maƙiya sunyi masa hawa,a kowanne lokaci ƙaruwa sukeyi,sai gashi lokaci guda allah ya kawoki Anty maryam nagode nagode miki,abba zayyi farinciki idan yasan abinda kikayi,mafarkinsa ne Yah Jabeer ya zauna akan wannan kujera,bansan yazaiji ba idan yagane cin amanar da Baban Hanif yayi masa”
“Baisaniba amma inkin faɗamasa a surutunki zai sani,kuma saunawa zan faɗamiki cewar ba dan yayanki na taimakeshi ba saidan kaina”
Ƙarisa maganar tayi tareda ture Maleekah a jikinta tana haɗe rai.
“Nidai kodan wa kikayi bai dameni ba,amma nasan idan kika matsa kusada rayuwar ya Jabeer zakiga abubuwa dayawa wanda mu bamu ganiba a gameda shi,shi mutumne abin a tausayawa masa”
“Uhm to naji zan duba nagani,yanzu dai ki tafi aikinki shine ki saka mana ido akan Hajiya zeenah da kuma Lylah da ƙanin babanki”
“Amma mai yakawo mommah a cikin lamarin kuma?”
“Saboda itama bata tsiraba,Hajiya rabi mahaifiyar Jawaheer so take tayi amfani da ita irinna ahalin Lubnah,zatayi shuru taji ƴarta ta haihu,idan wata a cikin matansa tarigata haihuwa,ko kuma bata haihuba to ki sani zata bi wata hanyarne da karbar companyn tabawa babban ɗanta itama,musamman da companyn su na shirin komawa ƙarƙashin JAAN bayan aurensu da Jawaheer”
“Tabb badaƙala,ashe abubuwane ke faruwa boye da mungun yawa kenan,karki damu anty Maryam,zanyi koƙarin kawomiki rahoto yanda ya kamata,sannan inda hali zanyi ƙoƙarin kawomiki Takardun share na Abban hanif,inaga in muka samesu zamu iyah tsada gudun plan ɗinsu”
“Deal kinshiga Cikin member,akwai meeting da zanyi a guest palour na,4:00 pm naganku a wajen”
Dariyah Maleekah tayi tareda rungume Hilyaan
“Ƙawas finally zanyi wani abun dazai taimaki Yah Jabeer,da banida power yin hakan,amma yanzu na samu”

A tsaye take a gaban dining tana goge kan table ɗin bayan ta ajiye abincin.
Taji ƙarar buɗewar ƙofar,amma bata dagoba,duk da cewar tayi mamakin dawowarsa da wurin.
Idonsa kam ya haɗe da nata lokacin daya shigo,jiya bata kawo masa abinci ba amma yau ta kawomasa,da alama kenan ta yarda da neman taimakon daya nema a wajenta?,na idan ya nemi taimako a wajenta ta taimaka masa,shikuma ya amince bazai bincike ba ballantana yasan wacece itah.
Rigace fara a cikinta armless,saidai ta alama ta adoce ba simple gown ba,kawai adonta ne yazo a haka.
Dauke kanta tayi daga kansa taci gaba da abinda takeyi,tana jinsa har ya ƙaraso kusada itah,zazzafan numfashinsa maicikeda abubuwa dayawa,gajiyah,kaɗaici,buƙata ds yana sauƙa kan wuyanta.
“Nagode”
Shine abinda yafaɗamata a hankali,inda bata kusada shi bazataji ma ya faɗa ba.
“Dana mefah?”
“Dana shigo sashen atleast naga wani mutum aciki,kuma ya haɗamin abinci.
Godiya ta biyu kuma da kika ƙarbi roƙona gareki,it mean alot to me.
Zanahiga nacire kayan,please zan iya fitowa naganki a falon baki tafi ba”
“Um”
Murmushi yayi,duk da batayi magana ba,amma kuma hakan ya tabbatar masa ta yarda kenan.
Sai bayan ya shiga ɗakinsa ta buga kanta tareda cize yatsa.
“Kutt Bombee yaushe kika zama haka,dagaske wai um kika ce masa,you need to see a doctor”
Tunda ta yarda batada zabi,dan haka ta zauna a kujera tana jiransa.
Bai dade ba yafito saboda yana tsoron kada ta sanja ra’ayi ta tafi,ba har cikin ransa ba yasan yake jinta,duk da yayi ƙarya yace baya jinta.
Inaga rashin Jaleelah ne a kusada shi yasakashi son kasancewa da maryam.
A zaune take tasaka aljazeerah Ana labarai na harin yaƙin da aka kai wata ƙasa.
Gabaɗaya hankalin ta yatafi ga akwatin talebijin ɗin,ko motsin fitowarsa bata jiba.
“Maryam!!!”
Karon farko a rayuwarta yaƙira sunanta,wani lokacin har mantawa dake da sunanta kenan,tsikar jikinta ce ta zuba lokacin dataji Haruffan sun fito daga bakinsa.
Saurin juyowa tayi tasauƙe idanuwanta akan sa.
“Na’am”
“Am nace shin zaki taimakeni da saka abinci?”
“Ohk toh”
Gani tayi batareda musu ba taje ta zuba masa abincin,duk motsin datake yana zaune yana kallonta,har taje fridge ta ɗakko masa lemo,a cikin wanda taga yafison irinsa,dan dama ranar farko sunyi kala kala ne dansu ga wanne yafiso.
“Gashinan na gama nizan tafi.”
Juyawa tayi zata bar wajen taji ya riƙo hannunta na dama.
Jimm tayi kaman saƙago tana jira taji ta inda jinin sai cigaba da bugawa a zuciyarta,bayan ɗaukewar dayayi na wucin gadi.
“Stay with me please,ina buƙatar wani numfashin mutum a kusadani a yanzu”
A zuciye ta fisge hannunta tareda cewa.
“Wai ancemaka ni mutum ce ne,ko yaushe zai zance kake kana addressing ɗina da mutum”
Kallonta yake da mamakin sanjawarta,wanda hakan yabashi dariyah amma ya cije.
“Uhm..uhm ke mecece to idan ba mutum ba”
“Mutanen dukka jinsi iri ɗaya akayisu,miye banbancina dakai”
“Ohhh to ina buƙatar jin mace a kusada ni”
“Halinku ɗaya ai”
Tafaɗa a hankali yanda bazaiji ba
“Kikace me?”
“Babu abinda nace,ka gama cin abincin na hutama da dawowa na ɗauki kwanuka”
A zuciye ta zauna akan kujerar gefensa tana kallon wani waje daban.
Yayinda shikuma yafara cin abincin idonsa yana kanta har ya gama.

A bakin ƙofah ta tsaya tana kallonsu,domin taga sun cika koda saura,khamees,Maleekah,Inayah,Hilyaan saikuma ita tabiyar kenan.
“Barkanku da zuwa”
“Yawwa barka”
Suka faɗa a tare.
Bayan ta zauna maida kallonta tayi kan Inayah,wacce ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tana kakkaɗawa,wani kallo Bombee ta watsa mata,da sauri ta maida ƙafarta tareda cewa
“Sorry ogah”
“Da alama zuwanki chadi yasa kin manta hanyar dana sakaki koh,wannan karon ki maida hankalin ki banason rawar kai,dafatan ƴar uwarki da faɗamiki mai zakiyi koh?”
“Eh tafaɗamin Anty maryam,kuma bazan baki kunya ba nayi alƙwari,koda yake kin fi kowa sanin hakan ai my ogah”
Tafaɗa tana sanja magana tareda kanne ido ɗayah,Hilyaan ce ta zungureta yayinda Bombee kuma ta jijjiga kai.
Mai hali baya fasawa,tafaɗa a ranta.
Jin Maleekah tayi shuru itada khamees yasa ta kalli inda suke.
Gabadaya basusan mai ake ba,sun bige da aikawa junasu satar kallo.
Gyaran murya tayi mai ƙarfi wanda ya jawo hankalin su.
“Mr romeo business ɗinku yajira a waje,yanzu muna buƙatar hankalin ku a nan”
Murmushi mai dauke da ma’anoni khamees yayi,yayinda ita kuma Maleekah tayi ƙasa dakai tana ƙikkifta ido.
“Mai nayi miss haka?”
“Hilyaan!!!!”
“Ahh sorry zan tambaya an jima”
Bayan sun gama abinda zasuyi kowa yasan aikinsa,ita Maleekah a lokacin aikinta zai fara,yayinda ita kuma Hilyaan zata jira sai anyi approve na komawarta aiki,itakuma Inayah sai Brr Na’imah ta dauketa tukunna.
A taiƙace dai sun shirya komai yanda sati komai zai fara aiki.

Bayan wani lokaci…….

Tafara yanke farce kenan taji kukan haidar,dan yanzu yayi wata shida,ta daina bashi mama,madara kawai yake sha,kuma yaron yayi wayo sosai,gashi fulele irin yaran madarar,sai fitina sosai.
A wannan wata biyun da Bombee tayi ita kadai a gida,ji take kaman tayi ƙaramar hauka,ga haidar ya dameta ga kuma Jabeer,tunda yasamu lagonta nayi masa hidima shikenan ya maidata baiwa a ganinta.
Dan yanzu ko bata kai masa abinci ba zuwa yake ya ɗauka a sashenta.
Ga plan ɗinsu yanzu yafara zafi,dan ma Maleekah tadamu damar ɗakkomusu takardun Share na Alhaji Abdullahi,suna jinsa yana nema kaman zayyi hauka amma suka yi miƙis.
Maleekah ta dauke musu hankalin Hajiya zeenah,wanda suke da tabbacin harda na hajiya rabi,kodayake ita dama ta auren ƴar take wacce za’a ɗaura nan da sati biyu.
A cikin wata biyun inayah tasamu yardar brr Na’imah,yayinda ita kuma Hilyaan tasamu shiga Division ɗin gen abdu manga,tana yiwa Gen Sameerah aiki,saidai bata ganeta ba saboda Badda kama da tayi.
Duk bayan sati guda sukeyin meeting a gidan da innayi suke itada inna Danejo,wacce take samun kulawa sosai a wajen su Hilyaan da innayin.
Kowa a lokacinne yake bada record ɗin daya samu mai muhimmanci.
Yatsa uku ta samu damar yankewa ta tsaya da abinda take,saboda wayar ta datake ƙara da kuma kukan Haidar.
Mr annoying taga yafito akan fuskar wayar,aikuwa nan da nan ta cune baki sama.
“Kai kai…..ƙaramin fitinnanne yana kuka,can kuma ga babban yana ƙira,waya taba tunanin kamar captain Bombee zata kare a gida tsawon wata biyu tana yiwa wasu hidima”
Jefar da nail cutter tayi ta dau wayar.
“Am Boss nace ba……”
“Faɗi kanka tsaye kawai,mai kake buƙata kuma?”
Dariyah yayi saboda jin mai tace.
“Uhm idan kinzo zaki gani ai,dan allah hurry up minti biyar”
Tun kafin yasake cewa wani abin ta suri haidar tayi part ɗinnasa”
Ko ƙwanƙwasa ƙofar dakin batayiba ta shiga,yana kwance akan gado yafito da kayansa dayawa akan gadon yana danne danne a waya.
Tsayawa tayi batace komai ba har saida ya dago ya kalleta,kanne mata ido yayi tayi saurin dauke kanta tana zazzare ido.
“Uhm nayi zaton za’a bar wannan bawan Allah yana ta jira,dama kaya zaki zabamin nayin Sati ɗayah a tafiya irinna wancan watan please,tunda nake bantaba saka kayan dazasu dace da tafiyah ba irin wanda kikayi min,naji dadinsu sosai”
“Wancan ma ai bakai ka sakani ba nina ga damar haɗawa koh………ohh nayiwa kaina,wannan bai san ayimasa gwaninta sau ɗayaba”
Taƙarisa maganar can ƙasa kasa.
“”Mekikace banjiba””
“Basai kajiba mr CEO kawai cewa nace sannu.
Naji zan haɗamaka amma hungo riƙemin ɗana,kuma idan ka bari yayi kuka daga Lokacin ba haɗa kaya…..clear”
Tana gama faɗin haka ta ɗora masa haidar akan cinyarsa,tareda zaddada masa da idonta.
Wajen kayansa tace tana nazarta su ɗaya bayan ɗaya.
“Ohhhh wai meyasa inna nemi kiyimin abu saiki bani riƙon,ina ƴar aikinki ta tafine wacce nake gani da”
“Ba ƴar aiki bace ta koma bakin aikinta,nikadai nake kulada shi,idan har kasakani yimaka wani abu wazai rikeminshi.
To shikenan bani ɗana ka haɗa kayanka da kanka mallam”
“Ahah barshi zan riƙeshi,inda sabo ai yakamata na saba,hadamin kayan barinaje falor kanki gama,kona zauna,yafada yana ƙwaƙume yaron saboda karta fasa,shima yaron a ɗan lokacin har ya sanshi sosai.
“Kayimin me,yawwa wacce ƙasa ne zakaje?”
“Ukarain ne,za’a yi meeting ne na wanda suke da share companyn mu a can”
“Mutun nawa ne masu share a can”
Bombee tafaɗa da sauri.
“Uhm mutum biyar ne,saikuma sauran masu share duk zamuyi meeting dai kawai,meyasa kika tambaya amma”
“Ahhh……uhm bakomai kawai na tambaya ne. Gen abdu yana cikin wanda zaku haalrci meeting ɗin?”
“Eh yana ciki,kin sanshi ne”
“Ahah ba har can ba,mahaifin Lubnah ne tana faɗar yanada share na companyn shiyasa na sani”
Shuru Jabeer yayi da zancen,amma daga yanda yaga fusakarta yasan ba iya hakane yasaka shiga yanayin ba..
Tana hadamasa kayan tana nazari har ta gama.
Tunkafin tafito falon taji kaman muryar mace,
“Hmmm yanzu abinda kake kana kyautawa kenan honey,kwana shida kenan baka ƙwana a sashena ba ,kana zuwa ko awa guda bakayi kake fita,yanzu nina biyo naga ya kake kawai na ganka kana zaune hankalin ka kwance,riƙeda ɗan shagen matarka”
“Oh Lubnah yanzu duk zamana dake da abinda kikayi min duk yana a bana kyautamiki,kada ki manta fah rabonda ki sauƙemin nauyina dayake kanki anyi wata uku kusan,amma duk da haka ban kyauta ba koh.
Da kike faɗan bana kwana a sashenki idan na kwana zakiyi min maganin abinda yake damuna ne,tun ina tunanin bakida lafiya yanzu na gano da gangan kikayi hakan.
Amma ki zuba ido idan har nasake kawo mata biyu gidannan zanga yanda zaki yim rowar kanki.
Da kike faɗar na riƙe yaro kuma,ina abinda yafi yarone ma zan riƙe,saboda tafiye min ke itada shagen ɗannata da kike faɗa”
Kuttt akan ta kakemin Wannan tujarar JJ?.
Barina haɗu da ita munfukar Allah sai nayi maganinta”
“Gatanan basai kinsha wahalar nemanta kinyi maganinta ba”
Ɗaga ido tayi ta kalli Bombee wacce tayi maganar,Lokaci guda ta maida fuskar rashin wasa.
Takowa tayi har gaban Lubnah ido cikin ido.
“Meyasa kika kasa maganina Lubnah,wai a hakan har kika samu damar zuwa kiyi burga a gaban miji,nifah ko a namiji bana ganinki ballanta na kuma mace”
“Hehehe dadinta ma kema ba mace bace a gabansa face Robot mai yimasa aiki,saboda nasan har yanzu bai sanki a mace ba.
Koda yake wazai saka jikinsa a inda wani gardin ya huda babu aure,harda sakamakon ɗa na shege,shine aka zo ana mannawa mijina ɗan domin ya samu shiga.
Rashin haihuwar ai ba hauka yasakashi ba dazai ƙarbi ɗan shage a matsayin nasa”
“Ahahah mai kikeci nabaka na zuba Hajiya Lubnah,niban cusa masa ɗana domin yasamu shiga ba,hasalima aikin raino kawai na sakashi,tunda naga ita matarsa tsawon rayuwarta kashi kawai ta iya haifa,bata taba bashi dan da zayyi raino ba. Bashi nake ya koya kafin wanda ake ƙira mata suzo su haifamasa nasa,tunda wannan kazar ita batada gurbin ƙwai saina kashi Juyace”
Idon Lubnah ne yayi ja saboda bacin rai,hannun ta ɗaga zata kifawa Bombee mari.
Cikin zafin nama kuwa ta riƙe hannun tamm a nata tareda natseshi saida ta sau ƙarar wahala.
“Kull nasake ganin hannunki kusada fuskata ,idan kika kuskura kika aikata hakan kuwa,…..to a ranar hannunki ba hannunki bane ba,domin ko ubanki gen abu manga bilahillazi bai isa hanani cireshi daga jikinki ba a garinnan.
Shidama baki inyasan mai zai faɗa bai san mai za’a maida masa ba.
Kibi a sannu baki gama sanin ni wacece ba,zaifi miki ki dunga taka tsantsan dashiga layin dana shata.
Kullum ina faɗamiki,kuma shizan faɗawa masu zuwa ma.
Bombee babu ruwanta da shirginku harkar gabanta take,amma duk wanda yashiga jan layin data shata……..hmmm don’t imagine the consequences”
Saki hannun tayi yayi jawur abinka da fatar data sha mayuka babu ƙarfi,Lubnah ji tayi kaman ta saki fitsari a wando.
“Kaima bani ɗana nabar wajennan,damuwarka zata sakani ciwon kan da ban sababa”
Sakoko yake kallonta,itafah ta gama rigimar amma kuma wai shine ma zai sakamata ciwon kai,haidar daya fara bacci firgit ya tashi saboda hayaniyar su,amma ji abinda tace.
“See this woman”
Yafaɗa a kasanlance.

Can cikin dare kaman a mafarki taji wayarta tana ƙara.
Ɗagowa tayi taga ƙarfe shabiyu,kuma Jabeer ne.
Mamaki abin yabata,shin mai zaice mata kuma,dan rabonta dashi tun da yamma lokacin da suka rabo ta karbi ɗanta.
Ɗaukar wayar tayi cikin muryar bacci tafara magana.
“Hello lafiyah na…..”
Bata ƙarisaba taji maganar sa daƙyar cikin nishi.
“Am sorry but please zaki iya gareni yanzu,ina buƙatar taimakonki ne”
“Taimakona kuma mai yafaru haka”
“Zafi jikina zafi sosai,kuma…..”
Wayarne tafaɗi daga hannunsa tafaɗa ƙasa.
Da sauri Bombee tayaye bargon dayake jikinta da saka slipper tafita da sauri.
A kudundune tasameshi a bargo yana rawar ɗari kaman an jona masa shocking.
Yayewa bargon tayi tareda taba kumatunsa,kaman ta taba garwashi.
Hasbunallah garin ya haka yaushe zazzabi yayi maka wannan kamun.
“Uhmm dama inaji tun jiya haka,amma baiyyi yawaba sai ɗazu,ki miƙomin magani a cikin drawer can”
Drawer daya nuna mata ta zata buɗe.
“Ahh karki buɗe am…..”
Kafin ya gama magana har Bombee ta buɗe drawer.
Jada baya tayi tareda zaro ido tana kallon abinda yake cikin drawer a kiɗime.
“Menene wannan Jabeer nake gani haka uhm?.
Koyaushe drawer nan na kulle,dama abinda yake cikinta kenan”
Kallon ta yake da idanuwansa wanda sukayi narai narai saboda zafin zazzabi,yama gagara furta mata komai.

*sadi-sakhna ce*

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK 2_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

Anshiga Sashen na Kuɗi,in kasan baka biya ba karka karantamin littafi,Ka ɗau hakkina bisa kanka tamm!!!

Makarantan Arewabook ku danna zai kaiku cikin littafin

https://arewabooks.com/book?id=62d939a19904b02ce6fa2b31

Masu karatu ta whatsapp kuwa,zaku biyah Naira 300 kacal ne.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Shaida tanan
09035784150

Masu saka katin wayah zaku turo katin 300 na MTN tanan layin..
09035784150
No VTU

Mutanen niger kuma zaku biyah kuɗinku tanan
300f
+227 97 21 16 15
Shaida tanan
09035784150

______________****_______________

 

Leave a Reply

Back to top button