Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 18

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

18

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

Spjt. Rungume juna sukayu tamkar zasu shige cikin jikin junansu, yayin da ruwan sama kuwa ke cigaba da sauƙa tamkar da bakin ƙwarya, kana ga walƙiya da tsawa dake cigaba da sauƙa.

Moddibo shi kam baki ɗaya ya burkice ya rasa tunaninsa, na wushin gadi, gaba ɗaya jinshi yake a wata duniya ta da ban,

ga wani matsanancin tsoro daya lulluɓe sa kana ga wani baƙon yanayi da yake ji yana yawo agaba ɗaya ilahirin ajikinsa, wani irin rawa lips ɗin sa keyi tamkar mai jin tsananin sanyi, ga kuma wani irin azabebben buguwan da zuciyarsa keyi da masifaffen ƙarfi yana bada sautin  dib-dab-dib-dab.

 

Haka zalika Khausar dake rungume dashi, itama haka zuciyarta ke bugawa,

sake ƙanƙamesa tayi da ƙarfi tana mai tura kanta afaffaɗan ƙirjinsa da bottle din gaban rigar suka buɗe, hakan ya bawa fuskarta damar mannewa farar afaffaɗan ƙirjinsa dake ƙawace da tattausan gashi baƙi mai sulɓi.

Wani irin fusga numfashinta keyi saboda tsananin tsoro da firgici da tashin hankali, haka yasa idan taja numfashin sai ta ɗauki sekon talatin Kafin ya dawo.

Ko kaɗan Moddibo bai da wani kataɓus sabida yanayin da suka kasance a ciki, sake rungumeta yayi tare da cusa kansa atsakanin wuyanta da kafaɗarta.

Daga can bayansa yake jiyo sautin ƙaran mota tana danna masa ɗiyyyyttt-ɗiyyyytttt, yasan shi akeyiwa hon ɗin, amman sam baya jin zai iya koda kwakwaran motsine.

Shi kuwa mai motar dake bayansa, ganin shiru bai motsa bane, yasa ya ɗan ratsa ta gefensu ya fuce yana dan leƙawa ganin ko lafiya kasancewar. Atsakiyar titin suke ganin babu wani alamun hatsari ko damuwa yasa ya wuce.

 

Moddibo kuwa da ƙyar ya iya buɗe Idanunsa tare da ɗago kansa still ruwan ake sheƙawa zuwa yanzu harda  ƙanƙara yana jin yanda sautin ƙanƙarar ke sauka asaman motarsa fat-fat-fat ko kaɗan baya kallon komai duk da kuwa gashi idanunnasa abuɗe suke, amman ina ganinsa ya ɗauke makanta ta meye gurbin ganinsa, ya zama sam baya gani, kana ji yake jikinsa kamar shanyeyye.

Daƙyar ya iya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa da yake jin wani irin jiri na fizgarsa tare da sarawa, da sauri ya sake sunkuyar da kansa akan wuyanta kana ya sake rungumeta da ƙarfi baki ɗaya ya rasa wani irin yanayi yake ciki.

 

Khausar kam sam batama san wani irin yanayi take ciki ba sam bata cikin hayyacinsa, hakan yasa ta sake rungume Moddibo da ƙarfi,

Jin yadda take liƙewa a jikinsa ne, yasa shima ya saƙe yi mata wani irin amintaccen rugguma tare da fesar da wani irin raunataccen numfashin yana mai shaƙan ƙamshin jikinta.

Itama sake rungumesa tayi cikin mawuyacin hali tana neman numfashi domin numfashinta na ƙoƙarin ɗauke wa gaba daya tsananin tsoro da tashin hankali ya bayyana asaman fuskarta, duk da sanyi garin da kuma yanda ake tsuga ruwa amma goshinta na na tsastsafo da zufa kana jikinta ya ɗauki ɗumi.

 

Cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa da ficewar hayyaci Moddibo ya sake rungumeta yana jin ɗumin jikinta kana yana mai furta.

“Hasbullahu wani’imal wakin, Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n La’ilaha Illah anta subhanaka Inni ukuntu Minal Zhalimin, Allahumma Ajirni fii musibati wa’ahlifli khairan minha”,Kana ya cigaba da karo to duk wata addu’a da tazo bakinsa cikin fitar hayyaci, Allah ya sani kuma shine shaidarsa ya rasa yanayin da yake ciki shin mutuwa zaiyi ne, koko kuma sumewa yake shirin yi,

domin jinsa yakeyi  tamkar yana tafiya cikin sararin samaniya ne bisa gajumare,

ji yake tamkar fuka-fuki garesa ya kasa tantance shin mafarki yake ko kuma azahirance ne kana yakasa tantance shin a sumen yake ko kuma amace yake, cikin rashin sanin madafa ya cigaba da karanto duk wata addu’a da tazo bakinsa.

Yayin da numfashi Khausar ke cigaba da fusga,

adduo’i ya cigaba dayi cikin ikon Allah Albarkanci Adduo’i da yake da kuma zuciyar namiji dake da dakiya yasa yafara dawowa hayyacinsa amma still Idanunsa basa gani mai kyau.

 

Ganinta kwance ajikinsa tana fuzgar numfashi yasanya shi sa. Lallausan tafin hannunsa ya tallabo fuskarta tare buɗe manyan idanunsa da ƙyar dan har yanzu dishi-dushi yake gani, idanu ya tsirawa kan goshinta daya tsats-tsafo da zufa, sai kuma ya rumtse idanun da karfi kana ya buɗesu tare da zura ido na daƙiƙu bakwai sai kuma ya juya idanun zuwa kan wuyan hijabinta daya zame daga kanta zuwa kafaɗarta yalwataccen sumar kanta mai tsayi da ƙamshi ya zuba agadon bayanta, yayinda saura kuma ya zuba asaman fuskarta, kallonsa ya mayar kan fuskarta jin, yanda numfashinta ke fusga. Idanunsa ya mayar kan ƙirjinta da sauri ya lumshe idanun sai kuma ya buɗesu, ganin yanda numfashinta ke hawa da sauka alamun zata sume a ko wanne lokacin.

 

Ganin tana gab da sumewane ya sanyashi sun kuyar da kansa kaɗan, zuwa kan fuskarta kana ya ɗaura lips ɗin da suke masifar  rawan sanyi akan karan hancinta, lumshe manyan idanunsa da suka sauya launi zuwa ja yayi, tare da fesa mata sanyayyan numfashinsa domin dai-dai ta mata nata numfashin, domin  duk da tsoron da kuma firgicin da yake ciki hakan, bai sanya numfashinsa ɗauke wa ba, kana yana kallon fuskarta wanda akowani lokaci zata iya suma, sai kuma ya sanya hannu ya toshe hancinta tare da ɗaura sanyayyan lips ɗin sa akan nata ya riƙa hura mata iskar bakinsa mai ɗumi da kamshi ceto rayuwa zuwa gareta,

Wani irin dogon numfashi taja mai nauyi tare da fesar dashi da ƙarfi, cikin daƙiƙu kaɗan numfashinta ya soma dawowa dai-dai kana duk abinda ke faruwa idanunta na lumshe.

Sannan har zuwa lokacin hannunta na kan mararsa, saman yatsarta na kan hudan cibiyarsa, sannu ahankali numfashinta ya dai-dai ta sai dai har zuwa lokacin bata dawo hayyacinta ba,  still kuma ruwan ake cigaba dayi tamkar da bakin ƙwarya ita ko sai wani irin sakewa tayi tare da lafewa a jikinsa tana shaƙar ƙamshinsa.

Shi kuwa Moddibo sannu ahankali ya fara dawowa hayyacinsa da nitsuwarsa.

Sake lafewa Khausar tayi ajikinsa tare da lumshe Idanunta domin ganin abun take kamar mafarki, ko kuma mutuwa tayi tsaban masifar tsoron rugugin da take.

 

Shi kuwa Moddibo sannu ahankali cikin ikon Allah ya dawo hayyacinsa, kana har zuwa yanzu tsikar jikinsa na tashi yayin da kansa ke juyawa jiri na ɗibarsa.

Ahankali ya sauƙe idanunsa akanta data manna a ƙirjinsa, yayinda  tattausan suman kanta ya baje aƙirjinsa, kallonta yakeyi kamar ya samu sabuwar halitta, kana aƙasan ransa ke mgnar zuci,

Wai yaya haka ne? Mekw faruwa? Wai ma waye ni?

Ya tambayi kansa da kansa,

Kaine Moddibo, sannan wannan Khausar ce kwance ajikika tana rungume dakai cikin yanayin da ma’aurata ne kaɗai ya halatta su kasance ciki.

Wani sashi na zuciyarsa ya bashi amsa.

Lokaci ɗaya kuma jikinsa ya sake ɗaukar rawa far-far tamkar wanda ake sheƙa masa ruwan ƙanƙara lips inshi kuwa, wani irin masifeffen tsuma sukeyi,

lumshe idanunsa yayi jin jikinsa babu kuzari kona misƙala zarratin, ji yake tamkar an zare masa lakar jikinsa cikin sanyi da rashin kuzari dake tare dashi.

A hankali ya sake birkitota tare da ɗago kanta ya ɓanɓareta daga jikinsa gani yayi Idanunta alumshe.

 

Ita kuwa Khausar ji take tamkar cikin bacci take, ko kuma suma ta kasa fahimtar kalar yanayin

da dai take ciki,

Shi kuwa Modibbo kanta ya tallabe da hannunsa ɗaya yayin da ɗaya hannu yake ɗan marin  fuskar yana faɗin.

“Ke! Keh!!”.

Shiru bata motsaba, hakan yasa ya sake ɗan fizgo muryasa tare da faɗin.

“Khausar! Khausar!!”.

har zuwa lokacin tana rungume jikinsa

For the first time arayuwarsa da bakinsa yafara kiran sunanta.

 

Fuskarta yake ɗan yiwa ƙananan maruka ahankali kana cikin wata Sanyayyar murya mai cike da tattausan lafazin yake fadin.

“Khausar!, Khausar!! Khausaaaar!!!”.

Lumshe idanunsa yayi shi kansa bai san yana da irin wannan raunataccen muryar ba, ya rasa taƙamemmen yana yin da yake ciki, yayin da aƙasan ransa so yake ya mata faɗa da tsawa da masifar ta sauƙa jikinsa, amma ya kasa kasancewar har zuwa lokacin bai gama dawowa cikin ainihin nutsuwarsa ba.

Kumatunta ya cigaba  da ɗan mara yana faɗin.

“Khausar!, Khausar!!”.

A hankali kanta ya zame  daga hannunsa ya tafi gefe luuuh kamar sumammiya.

Lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga da ƙarfin gaske tare da jin tsinkewar zuciya ganin yanda Kanta yayi kamar ta mutu!.

 

Cikin ɗaga sautin murya ya sake ɗan marin kuncinta tare da cewa.

“Khausar, *Lelewal*”.

Khausar kuwa still Idanunta na lumshe take Jin sautin muryar Moddibo na kiran sunanta kamar amafarki ko kuma daga can sama.

Sai kuma ta sake jiyo sautin muryarsa da alamun kiɗima yake  cewa.

“Ya salam Lelewal meya faru? me ya sameki?”.

 

Ahankali ya sanya hannunsa tare da ture hijabinta kana ya sanya hannunsa aƙirjinta wanda har yana iya jin tudun caɓɓullen ta ahannunsa ji yayi ƙirjinta na bugawa da ƙarfi-ƙarfi.

Hannunsa ya cire tare da sunkuyar da kansa har suna shaƙar numfashi bakin juna, bakishin yakai kan kunnenta kamar meyu mata raɗa yake faɗin.

“Lelewal tashi! Lelewal buɗe idonki!! Lelewal kalleni”.

Lumshe Idanunsa yayi akaro na barkatai tare da kai bakinsa cikin kunnenta kana cikin Sanyayyar murya mai taushi yace.

*“Fattanah!”.*

Dogon numfashi taja tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya tare da buɗe Idanunta sai kuma ta sake runtsesu da sauri gani take tamkar har yanzu rugugin akeyi kana walƙiyar zai iya kashe mata Idanu.

Bayan kamar daƙiƙa ɗaya ta sake buɗe Idanunta still yana ronƙofe akanta yana shaƙar ƙamshin numfashin dana gashinta dake baje.

Yayin da har zuwa yanzu hannunta ke cikin sa yatsunta guda uku nakan cibiyarsa tafin hannunta da sauran yatsu biyun nakan ainihin mararsa ta danne.

Cikin wata sanyayyar murya ya tsira mata idanu tare da faɗin.

“Lelewal”,Ya faɗa still yana tallafe da kanta.

Buɗe Idanunta tayi sai kuma ta sake rufewa,

Akuma dai-dai lokacin Moddibo da itan duk suka gama dawowa cikin hayyacinsu tare da nutsuwar.

Cikin sauri tare da fushi

Moddibo ya kalleta a tsawace yace.

“Keee!!! Tafi can Mage uwar fitina tashi akaina ko in kakkaryaki”.

Ya dire mgnar cike da tsawa tare da yarfa mata mari da bayan hannunsa.

Shi kansa jin maganar yayi ta fito daga zuciyarsa kai tsaye kamar an fisgo a bakinsa.

 

Azabure Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe tare da janye jikinta daga nasa amma still hannunta na kan cikinsa tana murza cibiyarsa.

Wani mugun kallo mai cike tarin kufula, takaici, tsuyan zuciya, da tarin ƙunci ya watsa mata firgitaccen kallo. Ta da ɗaga hannunsa cikin wani irin masifeffen rawan jiki da gigitan yanayi yasanya tafin hannunsa ya finciko hannunta dake kan cikin sa da masifar ƙarfi ya yarfa hannun nata har saida ta saki ƙara, dan ji tayi kamar zai ɓalla mata hannun.

Shi kuwa a take kuma tsikar jikinsa ta mimmiki ta tashi.

 

Cikin tsananin tsoro da firgici Khausar ta janye jikinta kana ta koma ta mannu da jikin kujera tare da rungume kanta a can gefen jikin kujeran motar tana mai jin raɗaɗin marin.

Moddibo kuwa da ƙarfi ya rumtse idanunsa sabida  wani irin masifaffen har bawa da yaji zuciysrsa nayi da masifar ƙarfi, lokaci ɗaya wani azabebben zufa ya wanke sa kana rawan da lips ɗinsa keyi ya tsananta karkarwa yayin da har hakoransa ke rawa har suna bugun juna saboda wani masifaffen abu da yaji yana yawo cikin kwanyar kansa, wani irin baƙon yanayi yaji ya taso masa da azaban ƙarfi, abinda bai taɓa jiba atsawon shekaru.

Cike da dauriya da kuma fushi ya figi motar da gudu yayin da zuciyarsa ke wani irin azalzala idanunsa kuwa har yanzu dishi-dishi suke gani sanna, sai wani irin rawa jikinsa da lips inda keyi, cikin mintunan da basu gaza goma ba taji yayi Parking aƙofar gidansu.

 

Cikin tsananin tsoro da ruɗu ta buɗe murfin motar, cikin sauri ta fice batare data lura da ɗan kwalinta da kuma hankief ɗin ta dake kan cinyar Moddibo ba.

Da ƙarfi yafi gi motar cikin mintuna kaɗan ya isa gidan yana parking ya fito.

Lokacin ɗaya ya jiƙe jikib saboda ruwan da ake cigaba dayi kamar da bakin ƙwarya.

Cak ya tsaya Atsakiyar gidan nasu, ruwan na sauƙa atsakiyar kansa saboda masifeffiyar baƙon yanayi  da yake ji ga kuma suya da raɗaɗin da zuciyarsa keyi, na firgicin saɓawa Ubangiji da yayi, tsoron Allah da tarin damuwa ne ya sanya idanunsa fara zubda wasu irin zafafan hawaye masu ƙuna.

Rumtse idanun da yayi tare da furta.

“Astagfirullah wa,atubu ilaik, Ya Allah kaine mafi sanin zuciyata, Yah Allah ka gafarta min ya Allah ka shafe min wannan zunubi, ya rabbi kada ka sake bani damar sake saɓa maka Yah Allah ka sani ban taɓa aikata makamancin hakaba,”. Gaba ɗaya muryarshi rawa takeyi, yayinda idanunsa ke kwaranyar da hawaye.

Duk da ruwan na dukansa amma ko kaɗan baiga alamar zaiji sauƙin abinda ke damunsa ba. ji yayi tamkar ya ɗora hannunsa a ka ya rinƙa ihu da kururuwa. Duk da dauriyarsa kuwa, bai san sanda kuka ya kubce masa, domin duk sauƙan ruwan akansa ji yake kamar ana  ƙara rurumashi wutar fitina a jikinsa,  ga kuma ƙuncin zaciya da yake ji,

Har lau  haƙoran sake dukan juna suke nusa bada sautin Ƙat-ƙat-ƙat baki ɗaya jikinsa rawa yake tamkar mazari ahankali ya sunkuyar da kansa gani yayi yadda muhallin sa ya sake masifar nuna zalamarsa.

 

Cikin mawuyacin hali ya dafe kansa da hannunsa na hagu murya narawa yace.

“Wannan wace irin masiface? shin wannan wani irin abune mai wuyar jurewa me yake yafaru dani ne wai? Shegiyar yarinya mai fitintinun al’amura, ya Allah ka isarmin da cutar dani da tayi, Yah Allah kaga ita ta riskeni kaine shaida ni ban nufetaba, Allah ka isarmin kan wannan muguwar yarinya mai jikin zalumci Astagfurullah”.

Ya ida maganar tare da fashewa da kuka, still dai yana tsaye acikin ruwan yana cigaba da dukansa, ganin sam kuma abin nasa yaƙi nitsuwa ne yasa ya nufi hanyar sashensa domin sakarwa da kansa ruwan ɗumi koda zaiji sauƙin abinda ke damunsa, abakin faradan Falon sa ya tsaya tare da zare rigar dake jikinsa kana ya zame wandon ya shanya ya rage daga shi sai boxer Kai tsaye toilet ɗin sa dake cikin Bedroom ɗinsa ya nufa yana shiga ya sakarwa da kansa ruwan ɗumi batare daya cire boxer ba yana tsaye ruwan ɗumin ya cigaba da zuba akansa amma babu abinda ke yawo a idanunsa kamar lokacin daya rungumi yarinyar ga wani masifaffen ƙamshinta da yake ji ajikinsa da ƙarfi ya matse jikinsa waje ɗaya kana cikin tsanananin tsoron Allah ya ci gaba istigfari.

“Astagfurullah wa’atubu Ilaik ³ ya Allah na tuba kayafe min wannan abin da nayi. Ya Ubangijina na tuba”.

Kai kawai yake girgiza wa cike da tashin hankali mara misaltuwa daya rufe idanunsa babu abinda yake hange face yanayin da suka kasance amota.

 

Acan ɓangaren Khausar kuwa da gudu ta shiga gida tare da wucewa Falon su.

Tsaye ta samu Mommyn ta cikin yanayin damuwa da tashin hankalin.

Mommy na ganinta ta saki ajiyar zuciya mai nauyi tare da cewa.

“Alhamdulillah Khausar kin dawo, gaba ɗaya hankalina ya tashi na kasa zaune na kasa tsaye, tunda Haiydar ya dawo ya faɗa min yanda ku kayi da Amina!”.

Ida mgnar taba kallon yadda jikin Khausar ke ɗigar da ruwa ga wani rawa da jikinta keyi cikin  jin ƙai da tausayawa tace.

“Amina bata kyauta min ba. Wallahi Allah Amina bata taɓa yimin abinda ya ɓata min rai irin na yau ba, ya za’a yi cikin wannan hadarin cikin wannan yanayin ta baro min ke a makaranta.

Yanzu waya dawo dake?”.

Cikin karkarwa na tsoro da sanyi  ga kuma zogin mari tace.

“Uhhhmmm”.

Ita kuwa Mommyn cikin sanyi tace.

“Yanzun nan dama Abbanku nake jira? ya dawo dan baya nan na faɗa masa kina cikin makaranta. Yanzu yana dawowa ne akan zai ɗaukeni muje can ɗin”.

 

Cikin sanyi da yanayin tsoro da kuma ruɗu Khausar ta dubi Mommy yayinda, jikinta ke rawa kamar zata faɗi.

Kallonta Mommy tayi cike da tausayinta ta girgiza kai kana tace.

“Gashi na sani Khausar yanda kike rikicewa idan kikaji rugugi kike fita hayyacinki idan kika ga walƙiya bare kuma kiji tsawa!.

Gashi yau kuma ruwan yazo da wasu irin tswawwaki masu ban tsoro.

 

Cikin rawan jiki ta sanya hannunta dake ta karkarwa ta janye Hijabinta kana ta kalli Mommyn Muryanta na rawa tace.

“Yah Jameel ne ya kawo ni”.

Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.

“Kai Ubangiji Allah yayi masa albarka. Allah ya saka masa da mafi kyawun sakamakon”.

Kai Khausar ta gyaɗa still jikinta na tsuma tace.

“Ameen Mommy bari in cire kayana”.

Ta ida mgnar tare da wucewa Bedroom ɗin ta tana shiga ta kalli hannunta lokaci ɗaya ta sake shiga sabon tashin hankali, cike da damuwa ta yarfe hannunta kana tace.

“Nashiga uku Ni Faɗimatuzzahara  ina nasanya hannu na! Ni Batula?”.

Duk da cewa tana cikin tsoro amma tana sane da inda  ya zaro hannunta kai tsaye toilet ta Wuce tare da cire kayan jikinta ta sakarwa kanta ruwan ɗumi sabulu ta ɗauka ta mulke hannunta dashi kana ta shiga gogawa ajikin tiles dake jikin bangon tana Girgiza Kai kana tana mai Furta.

“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n Astagfirullah wa’atubu ilaik Subhanallah ya Salam Allah na tuba”.

Da ƙyar ta iya yin wankan ta fito bayan ta ɗaura alawalan tare da buɗe Siff ta ɗauki dogon riga na roba baƙi ta sanya har zuwa lokacin jikinta na ƙamshin tularensa Sallaya ta shimfiɗa ta gabatar da Sallah kana ta riƙe carbi tana hawaye da Istigfari.

 

Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan ya gama wanka al’wala ya ɗaura tare da fitowa har zuwa lokacin zuciyar sa na tsaye alamar zai samu nitsuwa Siff ya buɗe tare da ɗaukar Boxes ya sa sai kuma ya tsaya yana kallon kansa, ya tabbata idan yasa Jallabiya mutane zasu iya fahimtar halin da yake ciki wani dogon tsaki yaja.

“Mitsssssssss!!! Yar iskar yarinya”.

tare da sanya hannunsa ya matse muhallinsa da ƙarfi wai ko zai masa biyayya cikin yanayin tashin hankali ya kalli kuma sunkuyar da kansa tare da faɗin.

“Wai wannan wacce iriyar Masifa ce!?”.

Sake buɗe sabbin boxers ɗin sa dake cikin leda yayi ya ciro wani ƙarami wanda yake zaton zai masa kaɗan shiyasa ma bai taba sakasu ba,

Cikin yamutsa fuska ya sanyashi,

sosai ya matsesa sai dai har zuwa lokacin al’amarin  azimunne.

 

Wani boyel baƙi mai kyau ya ɗauka ya sanya kana ya feshe jikinsa da turarukansa cikin sanyin jiki ya fita zuwa Masallaci ya gabatar da sallah Azahar.

A wunin wannan ranan dai baki ɗaya haka yayita agigice.

 

Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Bunayya ce zaune akan 3sitter yayin da Amina ke gefenta riƙe da kofin shayi yana tururi.

Anutse Hajiya Bunayya ta juya tare da kallon Amina data kai kofin shayin bakinta kana tace.

“Amina yanzu ya kuke da Malam Jameel ne? nifa nagaji da wannan al’amarin kullum sai munga Abu kamar yaci sai kuma kiga abu ya sake ta ɓarɓarewa!”.

Gyara zama Amina tayi tare da ajiye Cup ɗin tea kana tace.

“Hmmm ba gwara ma muba akan Samira Sani, sufa duk abinda suke kamar anshuka dusa shi Moddibo na nan kamar Waliyyi baya fahimtar karatunta shu’umanci bare ya ratsasa kamar kurma baya ma sauraronta bare kuma ya sake mata fuska”.

Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tana cigaba da sauraren Amina.

Amina ta cigaba da cewa.

“Amma kinga gwara Ni dama Malam Jameel Yana da sauƙin kai sannan yanzu ya daina shash-shareni idan na gaishesa yana Amsawa cikin sakin fuska da mutunci mun koma kamar da duk da dai dama haka halinsa yake ga kowa”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“Kawai dai abinda nake gani Ummah kawai Abbah ya masa magana idan Abba ya masa magana kan cewa Ina son sa bazai ƙini ba, saboda yana da kirki yana da mutunci da kawaici ko ba komai kuma gidan dala yake domin nifa kuɗin mahaifinsa nafiso, badon kuɗin da suke da shiba, nafi son miji irin Modibbo mishkili, ba sake fuska dan sunfi iya soyayya”.

 

Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauke tare da gyara riƙon wayarta kana tace.

“Anya Amina za’ayi hana kuwa? Ai gwara dai mujawo hankalinsa zaifi, kuma batun kuɗi yoh dama ai shi mukewa bauta domin duk abinda nake kashewa a wurin boka ina lissafawa kina shiga daga ciki zaku biyani”.

Kwaɓe Fuska Amina tayi kana tace.

“Kayya Ummah tun yaushe mukeyi amma abin baya wani kamasu  gwara ma Malam Jameel Idan munyi munga Abu ya kama kwana biyu sai kuma ya dawo baya kula har kata! anata ƙara lissafin kuɗin da zan biya”.

Kai Ummah ta gyaɗa kana tace.

“Gaskiya dai kam in dai hakan zaiyi sai in faɗawa Mafaifinku yafi min kwanciyar hankali ma amma ko. Abbanku baza mu fuskance sa kai tsaye haka ba dole sai anja hankalinsa akan maganar”.

Ta gumi Amina tayi tare da cewa.

“Toh Ummah acanza wani boka mana?”.

Saurin Kallonta Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Wani boka muke dashi da yafi wannan?,Duk aikin sai yace ana wasa dashi sannan aikin kuɗi yake buƙata sosai kuma kinga Yanzu bani da kuɗi sosai Amina, kuma ai tunda muka canza boka Zurau wannan duk aikin da yake min yana ci”.

Taɓe baki tayi tare da cewa.

“Gaskiya Ummah asamu ayi aikin nan idan muka samu nashiga gidansu zamu fanshe duk kuɗin da muka kashe!”.

Jinjina kai Ummah tayi kana tace.

“Zanyi ƙoƙarin hakan in Allah ya yarda”.

 

Acan ɓangaren su M Jameel kuwa bayan ya shiga gida ya sauya kayansa zuwa blue jeans da farin t-shirt mai dogon hannu kana ya gabatar da Sallah Azahar Yana idarwa ya nufi sashen Mahaifinsa zuwa lokacin ruwa ya tsaya bakinsa ɗauke da sallama ya shiga kana ya zauna kusa da Abbansa.

Kallonsa Abba yayi bayan sun gaisa yayi gyaran murya tare da cewa.

“Dama batun Company Adamawa ne acikin kayayyakin da aka kawo muga ya yanayin ingancinsu akwai atomfofi,

Gyaleluwa da kuma sauran kayayyakin ya kamata kaje”.

Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba yaushe ne tafiyar”.

Kallonsa Abbah yayi kana yace.

“Insha Allah tafiyar zai kasance idan kun gama jarrabawar ɗaliban ku da zasu gama makarantar bana nasan zuwa lokacin hankalinka ya kwanta Asma’u da Bashir sun kammala Secondary School”.

M Jameel kuwa jingina kansa da jikin kujeran yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Hakane kam Alhamdulillah yanzu kam na gama  sun gullarsu Asma’u”.

Dai-dai lokacin da Hajiya Karima ta shigo falon Abba na cewa.

“Kaga yanzu shikenan tun da kagama da wannan shungullan gaba ɗaya duk abinda ya shafi shungullana da kuma harƙoƙina, kasuwancina duk zan danƙasu ahannunka Babana.

Domin ni girma ya fara zuwa Inason hutu”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba babu damuwa duk abinda kace shi za ayi da izinin Ubangiji”.

Murmushi Abba yayi har cikin ransa yake jin ƙaunar ɗan nasa saboda yanda yake masa biyayya ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.

“Toh Nagode Allah yayi maka Albarka”.

Duk abinda suka tattauna Hajiya Karima na rakuɓe tana jin tattaunawar su Amaryan Abban Jameel Hajia Turai ta shigo ganin Hajiya Karima atsaye yasa ta faɗin.

“A’a Lafiya kike tsaye anan Hajiya Karima?”.

Cikin sauri ta juya, sai asannan Abba da M Jameel suka juya suka ganta tsaye.

Murmushin da bai wuce saman laɓɓabanta ba tayi kana tace.

“Yanzu na iso ina gyara labule nai”.

Ita dai Hajiya Turai batace komai ba ta ƙarasa shiga falon kana Hajiya Karima tabi yo bayan suka cigaba da hira.

 

Washe gari.

Cikin sanyin jiki da damuwa Khausar ta shirya cikin Uniform ɗin ta dake haska fatarta  baki daya ta kasa sakewa da zaran ta tuna inda ta sanya hannunta sai taji tashiga matsanancin tashin hankali.

Cikin sanyin jiki ta fita tare da nufar inda motarsu ke fake Amina ce tafito hannunta riƙe da   lunchbox ɗin Aminu dai-dai lokacin da Lamiɗo ya fito daga sashen Gimbiya Dadu da  fuska a tsuke ya kalli Amina tare da cewa.

“Banaso Amina kada ki sake yi min abinda kikayi jiya banaso haka ki kiyayeni! Ki kiyayeni!”.

Ƙasa tayi da kanta kana tace.

“Toh Abba kayi haƙuri”.

Sannan ta juya ta  shiga, kana su Khausar ma suka shiga mota ko acikin mota Khausar jingina bayanta da jikin kujera tayi tare da damƙe hannunta ahaka har suka isa makarantar.

 

Anutse ta fito ta tashiga hall da suke Exam kai tsaye bencin da number ta ke kai ta nufa tare da zama kana ta dafe kanta ba jimawa Malam Isa ya shigo ya fara raba musu Booklet da questions na Economics.

Kallon Khausar data dafe kanta da hannu biyu yayi kana yace.

“Lelewal meke damunki?”.

Da sauri ta ɗago kanta ta kallesa sai kuma ta girgiza kanta cikin sanyin murya tace.

“Ba komai Malam”.

Question peper ya ajiye mata kana ya cigaba da rabawa sauran.

Cikin mutuwar jiki Khausar ta riƙa yin amsarin Questions ɗin tun kafin a miƙa wa wasu Questions pepar tuni ta gama Amsawa kwantar da kanta akan deks ɗin tayi tana godewa Allah daya sa basu da Exam din Moddibo da batasan da idon da zata iya kallon sa ba.

 

Moddibo kuwa tunda yashigo makarantar ya wuce office ɗin su ya zauna cikin zullumi da damuwa.

Ahankali M Jameel ya fito daga class da yake teaching hannunsa riƙe da booklet ya nufi Office ɗinsu bakinsa ɗauke da Sallama yashiga zaune ya samu Moddibo idanunsa na rufe kana lips ɗin sa na rawan sanyi ahankali.

Booklet ɗin ya ajiye tare da zama gefensa kana yace.

“A.J meke damunka?”.

A hankali Moddibon Ya jujjuya idanunsa dake lunshe yayi kana ya Girgiza masa kai tare da cewa.

“Bakomai”.

Kallonsa M Jameel Yayi kana yace.

“Ya zaka ce min bakomai A.J ke faɗa min meke damunka ko dai baka da lafiya ne?”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da gyaɗa masa kai.

 

Cikin damuwa M Jameel yace.

“Toh meke damunka?,Ka faɗa min abinda ke damunka mana”.

Sai asannan Moddibo ya buɗe Idanunsa cikin raunin murya tamkar mai shirin fashewa da kuka yace.

“I don’t know J I really don’t know what’s wrong with me WLH BAN SANIBA, BANSAN MEKE DAMUNA BA J”.

Da Mamaki M Jameel ya kallesa kana yace.

“How A.J kamar ya bakasan meke da munka ba”.

Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin yanayin damuwa da tashin hankali ya kalli M Jameel daya tsaresa da ido ya sauƙe Idanunsa ƙasa kana yace.

“Bansani ba J bansan meke damuna ba Na dai san bana jina dai-dai ina cikin ɗimuwa”.

Ya ida maganar yana mai lumshe idanunsa sam ya rasa taya zai fara faɗawa M Jameel yanayin da yake ji ajikinsa.

 

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace.

“To ko dai zazzaɓi ne?”.

Girgiza kai Moddibo yayi still cikin raunin murya yace.

“A’a”.

Ahankali M Jameel ya sake cewa.

“Toh ko Kanka ke ciwo?”.

Still Kai Moddibo ya sake Girgiza masa alamar a’a.

Numfashi M Jameel ya fesar kana yace.

“Toh ko dai cikin kane?”.

Nan ma kai Moddibo ya Girgiza kamar zai fashe da kuka.

Tagumin M Jameel Yayi kana yace.

“Toh meke damunka?”.

Lumshe idanu Moddibo yayi cikin sanyin murya mai rauni ya buɗe idanunsa tare da kallon M Jameel daya tsaresa da Ido kana yace.

“J bana jina dai-dai ina jin kamar akwai wani abu da nake buƙata amma bansan menene ba”.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Toh me kake buƙata?”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da buɗe hannunsa kana cikin sanyin murya yace.

“Idont know J nima ban sani ba bansan me nake so ba amma inaji kamar akwai wani abu da ɗan Adam yake buƙata acikin rayuwarsa wanda nima nake buƙatarsa kusa sani, daga jiya zuwa yau amma bansan menene bane”.

 

Kallonsa M Jameel Yayi tare da kallon yanda idanunsa suka sauya launi zuwa Ja tun safe da suka zo ya lura da hakan tamkar mai mayen bacci kana ya lura da yanda lips ɗin sa ke rawa sannan ya lura da yanda bini-bini yake matse ƙafafunsa.

M Jameel na cikin Kallonsa. Moddibo yayi miƙa tare da matse ƙafafunsa kana lips ɗin sa suka shiga rawa sai kuma ya runtse Idanunsa.

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“J kodai kana jin kana ɓuƙatar mace akusa da kai ne?”.

Lokaci ɗaya Moddibo yaji zuciyarsa ya tsinke da masifar ƙarfi ajiyar zuciya ya saki tare da kallon M Jameel ji yake tamkar ya fashe da kuka ko zaiji sauƙin abinda ke damunsa  sunkuyar da kai ƙasa yayi cikin wata raunan’niyar murya mai sanyi yace.

“Ban sani ba J”.

M Jameel yace.

“Toh mutafi gida mana tunda na gama abinda nake kai kuma naga kamar baka da komai”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana ya miƙe tare da yin miƙa da ayau ya zame masa jiki domin baya minti goma mai kyau sai yayi miƙa.

Kallonsa M Jameel yayi dan yanda yaga Modibbonsa ya tashi ta saman rigar duk da kuwa boxes biyu ya saka duk dan ya suturta jikinsa ɗagowa M Jameel yayi tare da kallon fuskarsa yayi Murmushi.

Fita Moddibo yayi M Jameel yabi bayansa dai-dai lokacin da aka kira sallar Azahar acikin masallacin dake makarantar.

bayan sun Idar suka fito suka shiga mota M Jameel ke driving yayin da Moddibo ke gefen mai zaman banza idanunsa alumshe duk abin duniya ya Ishesa.

 

Suna isa gida M Jameel yayi Parking ya fita kai tsaye sashen Innayi ya wuce ya karɓa musu abinci Moddibo kuwa cikin mutuwar jiki ya wuce sashen sa ya kwanta.

Ba jimawa M Jameel ya dawo hannunsa riƙe da Warmers da kuma Plate kwance ya samu Moddibo akan 3sitter yayi rub da ciki idanunsa akan ƙofar falon.

Ƙarasa shiga falon M Jameel Yayi tare da zama aƙasa kana ya kalli Moddibo da faɗin.

“Saƙƙo muci abinci idan muka gama sai muje kaga Dr”.

Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyayyar Murya yace.

“Bana jin yunwa bana son cin komai”.

Buɗe Warmer M Jameel Yayi tare da cewa.

“Toh Meyesa haka J?”.

Cike da raunin murya tamkar wanda ke shirin fashewa da kuka yace.

“Ban saniba nima”.

Dariya mara sauti M Jameel Yayi kana yace.

“A.J Na fahimceka fa kamar *Mace* kake buƙata acikin rayuwarka!”.

Cikin sauri Moddibo ya lumshe idanunsa jin suna tsats-tsafo wa da hawaye, miƙewa yayi tare da wucewa Bedroom ɗin sa yana shiga yasa key ya rufe.

 

M Jameel kuwa jingina bayansa da jikin kujera yayi tare da fashewa da dariya harda riƙe ciki.

Moddibo kuwa yana kulle ƙofar ya juya ya kwanta ruf da ciki tare da lumshe idanunsa yayin da ƙwaƙwalwar sa ta shiga tariyo masa moment da suka kasance acikin mota lokaci ɗaya Muhalinsa ya shiga harbawa da ƙarfi tamkar zai fisge ya fito, yayin da lips ɗin sa suka shiga rawa har haƙoransa na haɗuwa kar-kar-kar.

Batare daya shirya ba yaji hawaye suna bin kuncinsa shi kansa baisan meyake so ba bai san meke faruwa dashi ba yakasa sanin yana yin da yake ciki ji yayi kawai yana kuka hawaye na bin kuncinsa yana sheshsheƙa.

Miƙewa yayi cikin rashin sanin madafa shin ya zaiyi da wannan jarabar tun jiya yake fama da zaran ya rufe Idanunsa yanayin da suka kasance da yarinyar ne yake gani.

 

M Jameel kuwa dambun shin kafa dayaji vegetables da soyayyen naman kaza dake tashin ƙamahi ya zuba a Plate ya fara ci yana cikin ci ne wayarsa dake gefensa ya hau ruri.

Ahankali ya sanya hannunsa ya ɗauka Turkey Kawai ya gani babu Number.

Picking yayi tare da kaiwa kunnensa yana dariya yace.

“Yaushe kaje Turkey?”.

Murmushi Jalaludeen yayi kana yace.

“Na kusa kwana biyar acan ai”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Lallai dai kam yayi kyau ya gida”.

Gyaran murya Jalaludeen yayi tare da cewa.

“Lafiya wai meyasamu Aliyu ne”.

M Jameel na ajiye cokalin hannunsa yace.

“Nima kaina ban sani ba”.

Dariya Jalaludeen yayi kana yace.

“Mace ta fara shiga rayuwarsa kenan.

Aure fa yake da buƙata yana da ƙaƙƙarfan sha’awar da tuntuni na kwantar masa da shi”.

Zare Ido M Jameel Yayi kana yace.

“Auuu Jalaludeen kenan kaine ka maida mu waliyan dole?”.

Cikin sauri Jalaludeen yace.

“A’a Ni ban mayar daku mata ba, amma dai kawai nasan Aliyu nada ƙarfin sha’awa na masifa idan har aka bar shi da wannan sha’awar zai iya zame masa masifa kana zai iya jefashi acikin damuwa gashi naga burinsa a lokacin yayi ilimi mai zurfi, kuma in ka tuna a lokacin yana yawan fama da ciwon ciki”.

Dafe kunci M Jameel Yayi yana saurarensa.

Murmushi Jalaludeen Yayi kana ya cigaba da cewa.

“Tun haɗuwar mu na farko kafin ku fahimci wanene ni kafin ku fahimci komai akaina, kana tun kafin afahimci wanene ni asan komai akaina na bashi abinda yasha wanda ya karyar masa da ƙarfin sha’awarsa har yake ji kamar baya buƙatar mace acikin rayuwarsa”.

M Jameel ya gyara zamansa tare da cewa.

“Ikon Allah”.

 

Jalaludeen kuwa cikin yanayin su na can yaci gaba da cewa.

“Toh ajiya akwai abinda yafaru ko dai mace tashiga rayuwarsa ko dai akwai macen data kama jikinsa wannan dalili yasa gaba ɗaya takarya alƙadarin abinda ke jikinsa!”.

Ajiyar zuciya M Jameel ya saki kana yace.

“Toh fa”.

Murmushi Jalaludeen yayi tare da faɗin.

“Kai kuma kwaɗayin ka ne ya kaika dana bashi maganin yana cikin sha kawai ka amshi kofin kasha shiyasa kuka kasance atare haka amman ai kai naka ba kamar nashi bane ”.

 

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Amma dai gaskiya Jalaludeen baka da mutunci”.

Dariya Jalaludeen yayi kana yace.

“Nifa bance komai ba gaba ɗaya abinku lafiya lau yake kawai dai sha’awar ce na kwantar”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“Toh yanzu shi kuma wannan ya za’ayi dashi dan yanzu wallahi ya tashi ya tafi ɗaki kamar zaiyi kuka”.

Murmushi Jalaludeen yayi kana yace.

“Kukan ma yakeyi yanzu”.

Ware ido M Jameel Yayi kana yace.

“Lallai dai kam maza sun gamu da aiki kenan”.

Jinjina kai Jalaludeen yayi tare da cewa.

“Gaskiya yanayin daya ke ciki ne awahale yake haka ya wuni jiya still haka ya kwana gashi kuma yau ma ya wuni haka”.

Cike da tausayawa M Jameel yace.

“Toh yanzu ya za’ayi ?”.

Girgiza kai Jalaludeen yayi tare da cewa.

“Gaskiya ban sani ba dan bani da yanda zan mishi kawai abune daya zo masa babu yanda za’ayi haka zaita rayuwa mafita ɗaya ne kawai yayi ƙoƙari yayi aure”.

 

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da cewa.

“Ok zamu yi ƙoƙari muga mai ya dace tunda gashi dama duk abinda ya dace mun gama”.

Jinjina kai Jalaludeen yayi kana yace.

“Masha Allah amma yanzu ka samu ruwan ɗumi kasa masa laimun tsami yaji kana ka sanya zuma yaji sai ka bashi yasha zai ɗan ji sauƙi”.

Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan ba matsala mun gode”.

Sallama sukayi tare da katse kira.

Miƙewa M Jameel Yayi yashiga cikin kichen dake falon ya buɗe Flaks dake ɗauke da ruwan tea ya zuba a Cup lemun tsami ya duba yaga babu rufe Cup ɗin yayi ya nufi cikin gadin ɗin gidan ya tsunko guda biyar sannan ya dawo ya wanke tare da matse su duka acikin shayin kana ya buɗe kofin roban zuma yasa.

Fita yayi a kichen ɗin ya nufi Bedroom din Moddibo yayi Knowking ƙofar.

 

Dai-dai lokacin da Moddibo ya cire kayan jikinsa ka ya zura Jallabiya kasancewar boxers ya takure masa jiki har yana jin mallakinsa na yimasa ciwo saboda yanda ya takuresa ya hanasa miƙewa cikin gajiyawa ya mike ya cire boxes ɗin tare da cewa.

“Bari naga iya inda zaka tsaya uban ƴan zalamammu”.

Yayi maganar yana kallon jikin nasa daya miƙe ya tsaya acikin Jallabiyar.

Muryar M Jameel yaji yana cewa.

“A.J ka buɗe min ƙofar mana in baka magani”.

Daga ciki Moddibo ya buɗe masa ƙofar.

Kallonsa M Jameel Yayi sai kuma ya kalli yanda  ya ɗaga rigar kawar da kai gefe yayi yana jin dariya na neman kufce masa.

Kofin dake riƙe ahannunsu ya miƙa masa.

Cikin Sanyayyar muryarsa yace.

“J Me wannan?”.

M Jameel ya Kalli kofin kana yace.

“Kasha mana zaka ji sauƙin abinda ke damunka na fahimci meke damunka A.J”.

 

Moddibo bai sake cewa komai ba ya amshi Cup ɗin ya koma bakin gado ya zauna tare da kafa kansa ya shanye tass kana ya ajiye kofin, cikin ikon Allah lokaci ɗaya yaji zufa ya fara sauƙa masa Atake yafara jin abinda ke damunsa na sauƙa kaɗan-kaɗan amma still jikinai ɗin na nan amiƙe ahankali yaji lips ɗin sa ya daina rawan zamewa yayi ya kwanta akan gadon yana sakin ajiyar zuciya akai-akai.

 

Acan gidansu Khausar kuwa zaune suke afalon  Mommy suna cikin hira ka jiyo sallama.

Cikin sauri Haiydar ya ɗago kansa tare da cewa.

“Laaaaah….!

 

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki yar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group na ɗin da zanke posting. Ko kinga littafin SAKAYYAH a waje na satane*

 

 

 

 

 

*By*

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button