Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 33

Sponsored Links

33
Acan bangaren Familyn kaantes tini Dd babba ya sanar da ‘yayansa yayiwa Bilal matar aure Kuma ba lokaci zaa dauka ba zaa daura musu aure kawai ba buqatan wani biki ko wata bidiar kawai daurin auren alfarma zaa daura musu shikenan.

Da mamaki kowa yake son sani ‘yar waye aka nemowa Bilal aurenta haka har cikin qanqanin lokaci zaa Ce zaa daura auren?
Dad Kaante yaso sanin ‘yar gidan wace Amma Dd babba sam Yaqi barin tambayoyinsu da zancen ya zurfafa har su fahimci auren na manufa ne da akwai dalilin yinsa,

A yanda yakeso kada kowa ya fahimta ko yasani sai ‘yar ta shigo hannunsu sai su taru su rufe zancen cikin gida bame sani sai an shakara da auren a bari duniya tasanta dacewa ‘yarsu Bilal din Ce ta yanda ba kowane zai tsaya lissafin yaushe Akai auren yaushe aka haihuba.

Umminsa da zancen auren Bilal ya risketa kaman zata shide Dan farin ciki Mai tsananin gaske sbd matar aurensa Ce kawai zata iya Saka mata Bilal dinta cikin farin ciki su taru su goge masa tareda maye masa gurbin so da kaunar dayake rasawa a cikin familynsa.

Zancen auren Bilal Babu abinda ya qara mata sai tsanani na buqatan Shima Dawood yayi auren sbd tini Shima anan din tai masa matar datake tsananin so itama.

Qaninta ‘dan kawunta daya jima da yin nasa arzikin Shima tin tsawon shekaru Ashirin har da yan kai daya Rabu da matarsa ta fari baya tayi barin ciki kafin rabuwarsu
yayi aure har so biyu Amma Bai taba samun haihuwa ba ko barin baa taba sake samu gidansa ba gashi Shima yafara manyanta Amma ba ‘yaya ga tarin arziki ya Tara Babu magada.

Daga ita ummen har hajiya Mahaifiyarsu suna cikin damuwar hakan da tausaya masa shiyasa aketa sake auro masa wasu Matan ko Allah zai basa wata ran idan akwai Rabon samun.
A wannan yanayin ne suna cikin fata da adduoi koyaushe da sadaka da komai sai gashi Allah ya share musu kukansu ta hanyar dawowar tsohuwar matarsa da ‘yar qaramar budurwar ‘yar da Bata Gaza shekaru Sha uku zuwa Sha hudu ba Ashe cikin daya bare kafin rabuwarsu Yananan Bai qarasa zubewa ta haifi ‘yar harta girma.

Duk da basa kaunar tsohuwar matar tasa daga ita har hajiya Mahaifiyarsu sbd son Rai da kwadayi tareda rashin girmamawa Harma da iya yin komai akan kudi da rashin godiyar Allah yasa suka rabun dakuma a lokacin Yana talakansa ne baida komai.

Amma dai tinda Allah yasa takawo musu Rabo na haihuwar da suke fata take suka manta komai suka hau tsananin farin ciki da nunawa ‘yar so mai tsanani.

Da farko hajiya dashi Kansa hankalinsu bai wani kwanta ba Saida akayo DNA Wanda a asibitin qanin tsohuwar matar tasa Akai komai Kuma suka samu sakamako na tabbacin ‘yarsa Ce jininsa Ce Dan haka tini suka hau farin ciki da murnar da bazasu iya kwatantawa ba.

Shi kansa Alh Basheer bulama a wannan lokacin tsananin so da kaunar ‘yarsa ya shigesa fiyeda komai da kowa,
Kauna da soyayyar da ake nuna mata tareda halaye da tarbiyar da mahaifiyarta take Dora yarinyar yasa cikin qanqanin lokaci ta sauya daga wuya da talaucin dasuka fito da uwar na rayuwarsu duka ta baya su biyun suka fara kokarin shimfida rayuwar da sukeso ta yanda sukai raayi.

A lokacin matansa biyu ya Rabu da sauran Dan haka ba ja ‘yarsa tasa ya sake daura aure da mommynta cikin shekarun da Basu Gaza biyar Ba da auren suka sauyawa Hajiyarsa da yan uwansa shi bayaji baya gani idan akan lamarin ‘yarsa ita Kuma ‘yar komai mommynta take sakawa Yana yiwa sbd ita Kuma mommyn da ‘yar take amfani tana rayuwarta yanda takeso a cikin dukiyarsa.

Har wannan lokacin hajiya da ummin kaante kaman yanda take Kiran yayar mahaifin nata haj Fatima kaante suma basu taba Jin so da kaunar ta ya Sauka a ransu ba dan haka Tako Ina yarinyar ta samu gatan daya lalatata kusan gabaki daya dan kuwa tini ta rufe kowane Babi da ake cewa babin Tina baya.

Da karatun SS 1 ta fara bayan dawowansu hannun Daddynta tana gama secondary school ta fara karatun jamia a Lagos Amma shekara daya kawai tayi dad dinta ya cireta ya maidata Malaysia dayake Daman mummynta itama tai bokon Sosai tare suka koma can da zama itada mummyn dan bazata iya barin ‘yar tata ita daya ba  can tinda ita din Bata komai a Nigeria din Kuma ‘yar tamkar mukullin juya rayuwar Alh basheer ce a hannunta shiyasa Bata wasa ko nesa da ita.

SBB shine sunan da ake kiranta tinda ta waye rayuwarta ta sauya gabaki daya,ita din ‘yar gatace a yanzu gaba da baya, ‘yar masu tarin arziki Ce,
Babu abinda take nema ta rasa Daddynta Bai mata shi ba,
ta gama karatunta ta sake fadawa wani Dan zurfafawa, tsawon shekarun da Sukai a qasar ta waje tini suka bar Malaysia Takoma Zurich mommynta kuwa Takoma Nigeria Amma kusan Akai Akai tana zuwa Dan akwai shaquwa da kauna Mai tsananin gaske tsakaninta da mummyn.

Wayewarta tayi yawan da yawanci acan gida Nigeria idan tazo sauran dangi na mata kallan mara tarbiya kokuma tashin turai da bayan rayuwarsu Bata iya rayuwar ‘yayan Nan.  Shekarunta a yanzu sun haura Ashirin da biyar zuwa da shida ko da bakwai ma Amma gata da rayuwar Datake yasa koyaushe a yarinya sharaf iyayenta ke kallanta.

Bata taba sanin DD kaante ‘dan ummen kaante ba duk tsawon shekarun Saida ummen tazo qasar ranar data je gurinta a ranar idanuwanta da zuciyarta sukai kyakyawan Gamo dashi,

idan tace tafada soyayya to ta ragewa zancen karfin gaske Dan haka ba soyayya ta fada ba Kai tsaye ta kamu da mahaukaciyar soyayyar da zata iya yadda ta mutu ba aure matiqar ba Dawood Dayyab dauda kaante zata samu ba.

Bata kula kowane namiji a rayuwarta da sunan soyayya sbd Sam ita tama manta da ana tsayawa Ayi soyayya da aure gaba,
Tin a Malaysia datai wani saurayi Dan qasar yaso aurenta Amma yanaso su ringa qwanciya tare taqi sai hakan ya lalata soyayyar tasu duk da suna son juna Amma shi yafi buqatan ta dawo gidansa da zama.

Soyayyar DD kaante a rayuwarta tasan abu ne Mai wuya kafin ta samu Amma tinda umme na sonta kaman yanda take son Zeenah yasa Bata boye ba Dan batasan wata kunya ba a yanzu ta bayyanar da soyayyarta a Fili Kuma ta samu Goyan baya tareda bayyanarda farin ciki sosai da amincewa daga ummen.

Hakan yasaka kusan kullum tana gidan Akai Akai danma taso dawowa gidan gabaki daya Amma qa’idar DD ce bayason mutane a gidansa baya iya rayuwa da wasu a guri daya,su ummen ma Dan mahaifiyarsa Ce Bai hadata da kowa ba sai qanwarsa dayake jinta cikin tsakiyar ransa itama Bai hadata da komaiba dan haka su baida damuwan zamansu a gidansa duk da ummen tasan Dan Yana son su fiyeda komai ya barsu Amma ba wai dan Yana sakewa da hakan bane ta sani.

DD a rayuwarsa bayan baturiyar budurwarsa lizz Shima Bai taba soyayya da kowace mace ba sbd bama zai iya Tina wace macen bace yayiwa kallan tsaf da har zai iya soyayyar da ita

Zuwan ummensa Zurich ta rabasa da Lizz dan tsoran kada ‘dan nata ya fada Zina sbd ganin yanda Lizz din ke maqale da hannunsa ko yaushe Idan tazo gidan batareda damuwa da ita uwarsa tana gidan ba.

Babban Saa da Daman da Sbb ta samu shine maganar ummensa kaman yankan wuqa ne Bai taba musawa ba Dan haka tana rabasa da Lizz ta fara Saka masa zancen yai aure tinda zaman a haka ya Isa.  Bai taba tinanin aure a yanzu ba Amma sbd bayason ana maimaita magana a rayuwarsa yasa ya barwa ummen zabin komai Dan tasan kalar matar da bazata taba binsa tadamesa ba zata zabar masa.

Sbb na ganin zancenta da DD ya tabbata yasata Jin duniyarta ta sake sauyawa gabaki daya, ita ‘yar  millionaire zata auri ‘dan billionaires Shima Kansa billionaire.

Daga lokacin tafara Jin kanta qarasa juyewa gabaki daya a sonsa Bata Ji Bata gani Bata ganewa duk zancen da babu sunan DD kaante dinta aciki.

Duk wannan bidirin Bai taba tsayawa ma yasan asalin kamannintaba bare tantance muryarta sbd Bai taba maganar data wuce ta minti daya zuwa biyu Ba da ita Amma a hakan taji tagani ta amince.

********
Zancen maganar auren Bilal ya sanya umme ta yiwa Dad kaante magana dan a hade auren Dana DD tinda tare zasu dawo,
Shima Dad kaanten yanason dawowar DD din da zamansa anan Dan haka wannan shawarar tai masa daidai dan haka da kansa ya samu Dd babba da maganar dayake Alh Basheer bulama nasu ne babban mutum ne sosai Shima gashi akwai sanayya Dan haka aka yanke shawarar  Neman auren kawai a hade Dan kuwa Dd babban Yana buqatan dawowar DD a kusa dashi suna buqatansa.

Da wannan Shirin aka fara Shirin auren DD da Bilal lokaci Daya.

******Benazir zuwa yanzu rayuwar ta sake matse musu babu sauki sai a gurin ubangiji,

Sumayyah lafiya tafara qaranci sbd rashin Cima Mai lafiya isassa da yawa aikin wahala.

Anne ma depression ya fara tayar mata da ciwonta itama yau lafiya gobe sai ahankali Dan haka benazir ta ‘daidaice Takoma abin tausayi,

Sumayyahn ma nata ciwon Yi yakeyi Yana kokarin tashi ga cikin jikinta yayi girma sosai kaman me cikin ‘yan biyu.

Tashin hankalin benazir a yanzu shine yanda zata iya karban haihuwar sumayyahn sbd da alama Anne sai ahankali,
Hande Kuma ko sumayyahn zata yage gurin haihuwa bazata taimaka musu ba a yanda ta tsani cikin da su gabaki Daya akansa.

Ta bangare Daya ga karatunta suna kokarin fara exams a satin.

Abinci ta koshi ta manta rabonta da Hakan sbd kullum barwa sumayyahn dake dauke da juna Biyu sukeyi saita koshi suci sauran Wanda itama sumayyahn bawai cin takeyi ta koshi ba tana Dan ci zata ce ta koshi sbd tabar musu itama su samu suci.

Lokacinda benazir suka fara exam lokacin tini depression Mai tsanani yafara kokarin juyar mata da Kai itama sbd Anne da ciwonta ya tashi sai tayi fiyeda kwana nawa kafin ta dawo daidai
Hakama sumayyah sai ahankali itama Dan haka hankalinta ya rarrabe cikin damuwa da rashin sanin madafa,
Bata iya karatun Daya kamata,
Ga aikin gida ga wankin shagon Ababa Idan ankawo wuni takeyi ta raba dare tanayi harda guga,
Ga kula da Anne da sumayyahn wadda a yanzu cikin takejin kaman zai kasheta sbd numfashi ma gagararta Yi daidai yake sbd cikin.
#MAMUH#
#MARRIAGE#
#BABYMAMAH
#LOVE
#HOTHOT
#ROMANCE
#DD KAANTE/BENA ABABA
*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button