Cinikin Rai Book 1Hausa NovelsHausa Novels

Cinikin Rai Book 1 Page 1

Sponsored Links

BOOK ONE
001
Keivroto city.
Sau dayawa mutane suna amfana ne da abin da yake, zuwa gare su ba abin da suke tsammani ba, wani lokaci abin da aka samu shi ake iya ado da shi domin lullube wata rauni. Raunin da zata durkusar da mai shi zuwa faƙiri ba ƙaramar rauni ce ba. “Xnooooooooo!” Shi ne sunan da gungun matasa marasa ji irin ta suke kiranta da shi. Bude idanu tayi tana kallon silifin dakin. “Wayyo Allah na, bakin na rayu kamar Cinderella ba, ko na rayu kamar wata Barbe Queen, amma yau na kare a sansanin jagaliyawa.”cizon lips dinta tayi tana buɗe window ɗakinta. “Wani dan iskan ne ya min kiran mafarauta? Zanci uban mutum idan na fito ku watse kafin na fito” “Allah ya huci zuciyar ki Yar kunama.” Lumshe idanunta tayi, tana me rufe window din ɗakinta, ta nufi hanyar da zai sadata da cikin gidan. Daidai ana buga kofar. “Zenobia! Please open the door!” “Ke ba jiya Babanki ya ce kar ya kuma ganin ki da ni ba?” Ta fada a tsawace. “Mtseeeeeew abinci na kawo miki ” “ko ba abinci ba, uban abinci.” Ta wuce gefen drower ɗinta, ya dauko toothpaste da brush dinta. Kasancewar gidan Babban gidan hayace kuma irin me dauke da dakuna rututu ne, har da gidan sama. Ita tana hawa na uku ne. Ta fito daure da towel a saman kanta, domin Allah ya mata baiwar gashi. A hankali idanunta ya sauka kan Kawarta. “Xno ina jiran ki” dauke kai tayi tana tafiya abin ta, ita kuma ta shige dakin ta fara gyara mata, ƙasan gidan kamar kasuwa kabilu ne mabanbanta daga kowacce kusurwa na garin ƙasar *Gista*, tun daga hawa na biyu idanun jama’a ya fara hango musu Yar kunama take suka fara watsewa, ita din kamar zakanya ce bata tab’a yarda ta haɗa kanta da sauran, wasu mata biyu dattijai ne suka shiga wanke ban dakin tare da saka garin kumfa da maganin kashe ƙwayoyin cuta. Sannan suka dauraye ban dakin, koda ta iso. Amsar bokitinta wasu matasan yan mata suka yi aka zubo mata ruwan zafi, aka surka sannan aka wuce da shi ban daki. Shiga ban dakin tayi, tana kallon shi. ” Inna ki rubuta abin da babu a gidan nan kafin nan da an jima.” “An gama yar albarka.” Ta fada tana juyawa, yau ya dace ta fara aiki amma sam bata jin aikin a kanta. Sai dai Alfarman da Mr Amjad yayi mata ya isa kome ya kuma isa ya saka ta fahimtar rayuwar ta zata juya, murmushi tayi tana kallon kanta, yo dakyar ta gama secondary school, bayan ta gama ta shiga college shima dakyar ta samu damar yin diploma a fannin Kasuwanci. Sai da Inna ta kuma karfafa mata gwiwa ta shima wai gudun kar a rena ta duk da haka bai hana ka fahimci, yadda take cin Uwar uban turanci ba. Idan.kana niman me tozarta turanci. Ba shakka Zeenobia ita ce za a fara bawa Award shi yasa ta kare mai da hankalinta kan dabancinta, jama’a dayawa na masifar tsoronta a waje, amma cikin gidan ita ke bin mutane da luma. Domin sune ita, sune rayuwarta, daidai da rana daya bata fatan ta nisance su. Ita tasan darajar su, shi yasa ko mutuwa zata yi bata fatan ya dauke ta akan idanunsu. Wanka ta fara ta fara jin ihun mutane, bata fasa ba sai da ta gama sannan ta fito. Kallon wani matashi tayi fuskar shi ya b’aci da jini alamar duka aka mishi. “Wani dan shegiyar ne ya dake ka Abbas?” Ta tambaya duk da tana can baya ne, darewa aka yi aka bata wuri. Juyawa yayi ya kuma juyawa. alamar irin dolo ne. “Abbashena waye ya dake ka?” “Wai… Wai … Wai” takowa tayi ta rike hannunsa. “Gaya min!” “Wai don na dauki madara na bawa Hibba shi ne yan uwanta suka dake ni!” Ya fada hawaye yana zubo mishi. Mahaifiyar sa kan bata iya magana ba, sai share hawayen take. “Gaskiya basu kyauta ba, ai kowa yasan yadda yake son Hibba bai dace a ci zarafinsa ba. ” Rike hannunsa tayi ta ce. “me kake so nayi musu?” “Ki gaya musu su daina duka na” rike hannun damansa tayi har dakin Mamarsa da take kuka. “Ammiy kuka kike ne? Na zata zaki daina kuka ai tunda Allah ya bashi rai da lafiya, kuma babban engeering ne, manyan kamfanonin suna niman sa amma ganin sa a haka suke tsammanin ba zai iya ba, sai dai ki sani ke ce kike karya mishi kwarin gwiwa. Daga yau Abbashena babu shegen da zai kuma dukanka” ta fada tana barin dakin. Kallon shi uwar tayi a raunane. “Mahaifinka ya ja maka wannan rayuwar, da bau cusa kansa cikin wancan rayuwar ba babu me cutar da kai.” Cak Xno ta tsaya. “Me kike nufi Ammiy?” “Ba kome Zenobia” lumshe idanu tayi ta wuce abinta. Tana jin babu dadi amma na yau yafi na kullum yawa, tana shiga dakinta ya rufe tare da sake towel din. “Ke dai baki da hali haka kawai sai kin sakawa,mutane talauci hankalinki zai kwanta.” Murmushi tayi ta cigaba da shirin ta, bata damu da Hafsah Ameen da take dakin ba. Yankar da yake kwance a gefen kafad’ar ta, take shafawa ta ce. “Hafsy? A ranar da kuka tsince ni, haka kuka same ni da wannan tabon?” “Eh da wannan oscar din muka same miki.” “Hmm!” Shiryawa tayi tsaf sanye da riga da skit na American suit, dark green, sannan ta kwaso wasu kaca na sarkoki ta zuba a wuyarta, hannun ta kuwa kai kace wani gasar nuna zobuna ake, sannan ta dauko wani mahaukaciyar takalmin me bakin tsawo ta saka. “Xno! Office din zaki fara zuwa da wannan shigar kamar kunce hauka?”. Kallon kanta tayi a madubi ta ce, “nafi tunanin daga turu nake madadin kuncen hauka.” Ba a bin ta
bashin bakar magana ko kai uban waye. Gefe guda kuwa Xno bata da damu da ado ba, ko da yake ai ba laifinta ba ne, rayuwar dabanci ya fi mata armashi sama da wani paint a fuskarta. Tozali da farar hoda ta shafa a fuskarta, sai lipglow da ta goga. A hankali ta kalli kanta. “Ina girmama namijin da zai.” Juyawa tayi ta watsawa hafsy kallon banza. “Zanci mutuncinki” ta fada ba tare da ta bari ta karasa zancen ta ba. “Allah ya huci zuciyar Yar kunama!” Murmusawa tayi, sannan ta nufi hanyar waje. Itama Hafsy ya fito tana take mata baya. “Don Allah kar a takalo rigima, kwana biyu bani da kudin biyan beli.” Juyawa tayi ta kalli aminiyarta ta ce mata. “Bani jakata” mika mata jakar tayi tana faɗin. “Allah ya bada sa’a first time in office!” Murmushin gefen baki tayi, tana faɗin. “Ba ni da lokacinki” ta nufi hanyar sauka kasa, riga da wando ne a jikinta, rigar palazzo pants grey colour sai shirt shima grey top din rigar black, sai sarkokin da ta saka a wuyarta. Asalin halittar gashin kanta, nad’e shi tayi bayan ta daure da ribom, sannan ta daura black turb akanta, wanda ya mata masifar kyau. A hankali take sauka a stairs din. “Ina kwana Aunty.” “Lafiya lau, yan makaranta.” “Barka da safiya Yar kunama” “Barka dai Mr Umar!” Har ta iso kasa, juyawa tayi tana kallon ilahirin gidan. “Yau ba wani abu ne sabo?” Da sauri kowa ya tawo in da take, suna me son duba sabon abin da take buƙatar son sani. “Babu Zenobia!” Lumshe idanunta tayi tana faɗin. “Ina Abbas?” “Yana daki” murmushi tayi ta ce mata. “Mami ki kula da shi!” Sannan ta ce musu. “Babu kome kuka ce?” “Babu kome Yarnan” “shi kenan, ku min addu’a yau zan fara aiki.” Ta fada tana nufar wurin motarta, da wasu gungun matasa suke tsaye a jikinsa. Irin motar nan ce mara koda ko murfi caterpillar, ta shiga mutane hudu uku suka shiga baya, suka tsaya. Gefen drive ne yana jan motar. “Kai ni kofar gidan su Hibba!” “An gama!” Wucewa da ita yayi kofar gidan da babu tazara da tasu. “Amma Uwardakina akwai son rai, kin san dai Abbas ba lafiya ne da shi ba.” Juyawa tayi tana kallonsa. “Sai aka yi yaya?” Shiru yayi bai ce kome ba. “Na zata kai me tausaya mishi ne? Ubansa ya gina wannan gidan ne domin saka haya, yadda zai tallafi rayuwar d’ansa daya tal, kasrshe ya mutu ba a san mene ne sanadi ba, ya kuma rabta sunan al’umma a cikin takardan gidan, kasan wahalar da muka sha kafin gidan ya zama mallakarsa? Kuma kana cikin gidan kana raye nawa kake biya a wata? Son of bitch?” Ta fada kamar zata kifa masa mari. Dai-dai isarsu kofar gidansu Hibba kenan. Ajiye jakarta tayi da yake kan cinyarta. Sannan ta nufi bayan motar ta, sauka daya daga cikin matasan yayi yana dadin. “Uwardakina me zan baki?” Kwagiri. “Mika mata driven yayi, bata amsa ba ta juya tare da nufar inda matasan suke. Mikewa matasan suka yi, tare da cewa. “Idan don wancan mahaukacin kika zo, tow maza ki juya.” Jinjina kai tayi sannan ta ce musu. “Wani dan iska ne ya dake shi?” “Ai mune muka dake shi bakidayan mu!” “Kunyi kuskuren dukansa, bani kwagirin nan Dondurus!” Ai kuwa yaci sunansa domin irin labtaceccen kato ne na bugawa a mujalla. Ya mika mata kwagirin, cire top din rigar ta tayi ta mika mishi. “Uwardakina wannan aikin na mune!” Inji daya daga cikin matasan. “Black bari naci ubansu.” Yes sunanshi ya dace da shi, idan muka yi al’akari da yadda ya kasance baki sosai, “hahhhh! Wai ita zata iya damu ne, an dake shi kiyi abin da zaki yi.” “Uwardakina ki kyale su, baki san yana yin kwarewar su ba.” Inji driven,Juyawa tayi ta watsa mishi kallon banza ta ce mishi. “Duk abin da na kasa a gabana bana jin tsoronsa, sai dai ban saka a raina ba. Paul!” Ta kira asalin sunansà0pa. Tana rike da bulalan, tana juya shi yadda zaka san ranta ya kai kololuwar b’acin, nufarsu yayi cikin zafin nama, ta shiga tsakiyar su. “Ke yar jagaliya, ki tafi idan ba haka ba zamu zane ki, mu miki tumbur.” “Na yarda idan daya kanku yayi nasarar ko kwarzanar jikina, zan bari ku min duk abin da kuke so, idan kuma kuka sake sai na bulale muku, mazauninku.” Ta fada tana kallonsu, tabbas sun san zata aikata amma abin kunya ce a gare su ana bada labarin kanwarsu tana soyayya da dolo irin Abbas. “kin ga Zeeno kin san.” Zuba mishi kwagirin tayi a cinyarsa, tsalle yayi yana fadin “Amma da kin saurare mu ko, sai mu miki bayani” bata yi magana ba ta cigaba da zane shi, ganin yadda take watsar mishi da jikimarsa. “Zenobia don Allah ki kyale mu, ki shiga ki samu megida shi ya saka mu.” Yarda bulalar tayi ta shiga cikin gidan, dattijo ne zaune, sai wasu kartin maza uku. “Yallabai barka da safiya.” D’agi kai yayi ya zuba mata ido, kafin ya ce mata. “Kece Zeenobia!” “Eh yallabai nice Zeeno, Xnoo, Yar kunama.” “Me yake tafe dake.” Ya tambaye ta, cikin sanyin murya ta ce. “Ban zo nan da wata manufa ba, sai dai nazo na gaya maka cewa. Yarka tana son Abbas kuma shima yana sonta, Yallabai ina kaunar Abbas tun daga ranar da na fara ganinsa, amma sai akayi dace Abbas baya sona kasan abin da ake nufi da son maso wani karshen wahala. Amma ita Hibba yana sonta ne da dukkan zuciyarsa. Ko Mahaifiyarsa bata san yana son Hibba ba, amma ni ya gaya min, Yallabai duk da yana da lalura wallahi zai bawa Yarka duj wani farincikin rayuwa. Kaf kudin hayar da ake biya a cikin al’umma charity House nashi ce, a ƙalla ana biyan bera miliyan goma duk shekara. Idan luxury rayuwa kake so zai saya mata expensive stuff amma abu daya nake son gaya maka, idan kace ba zaka bashi ita ba wani abu bane, amma ka da a kuma aikata kuskuren dukansa.” “Idan an dake shi me zaki yi?” Cikin fushi da dauki kofin jug din kwalba ta daki fuskarsa da ita, sai da yaji kamar yayi karo da bango ne, ta nuna mishi yatsa. “Ba da kai nake yi ba, wannan family issues ne.” Sannan ta juya ga dattijon. “yau ranar sa’ata ce zan tafi wurin aiki, Yallabai xan tafi shawara daya xan baka shi ne, ka bashi Yarka ko kuma ka shafa kaji ba tattara su, sun fecce ” sannan ta mike, ta bar falon. “Baba me yasa ka barta?” “Kasan yadda mutum yake ji idan abin da yake so ya rabu da shi? Exactly haka take ji, sannan akwai abin da na hango a kwayar idanunta, zata iya kome domin Yaron, tayi alƙawarin haka da zuciyarta. Ku kira min hibba ”
••°°••
Tana fita ta mika mata rigarta black yayi, ta saka sannan ta zauna a motar. Daukar glass tayi ta saka, tana me cuno baki tana fitto wato feduwa. Suna isa trafficking jam, aka tsayar da motarsu. “Yan majalisar dokokin Keivroto suke wucewa a guje, sai da suka gama wucewa aka sake su. “Uwardakina ga motar Mr Amjad can.” Kallon motar tayi, ta tab’e baki tana cewa. “Su suka sani” haka suka nufi Queen Elizabeth road. Kai tsaye wani katafaren Company suka nufa, sai hada hada ake kamar ana cin kasuwa a kofar Company. A hankali suka sulalle cikin compound na cikin kamfanin, suka yi parking a inda ake ajiye motoci. Sauka tayi Black ya mika mata jakarta Charles & Keith, a hankali ta maka a kafad’arta, tana tafiya ana bin ta da idanun. Saman building na kamfanin an rubuta, S….. digital art, tana isa bakin kofar aka bude mata kofar a hankali ta cusa kanta cikin building ɗin. Ware idanunta da suka sha tozali tayi tana kallon around na building. “Miss Zeenobia Nasr Hadejia!” Gyada kai tayi tana murmushi. “Kizo tare da ni ” gyada kai tayi, sannan ta bi bayan matar da take sanye da dangalallen skirt iya gwiwanta. Elevator suka shiga ita da matar tana mata murmushi. Tana ganin matar ta danna number 9, a hankali yake walking around, tsayawa yayi aka bude shi, wasu yan mata ne suma ma’aikatan kamfanin. “Good morning Mss Mary!” “Morning helima morning Faither!” “Mss Mary an kawo sabuwar employee ce?” “Yes!” Dake babu wasa a fuskar Mss Mary yasa basu fadi abin da yake ransu ba, but sun kagu da su yi gulmarta domin azabar kyan diri da cikar halittar Zeenobia Nasr Hadejia wani abu ne da dole sai kaji a ranka. Infact there never met mace irinta ba. Suna isa floor dinsu suka fita, “sai an jima Mss Mary” tab’a juna suka yi bayan fitar su. “Ke she look familiar?” Inji Helima, zaro idanu Faither tayi tana faɗin. “Really?” “Eh na santa, but na manta inda na san fuskarta but na santa.” Floor 9 suka isa, a hankali kofar ta bude, suka fito rights side suka nufa, tare da Mss Mary. A hankali suka isa wani kofa, Ciro card ɗinta tayi ta manna a jikin security door din ya bude, “waw” ta fada a kasa makoshinta, wani azazzben Office ne me masifar kyau da ɗaukar idanu. “Good morning Sir.” D’ago kai yayi, ya amsa da “morning Mss Mary! Zeeno barka da zuwa ” ya fada yana jin zuciyarsa da ransa ya biya da siffar yarinyar da take tsaye a gabansa, “moni sa” inji Zeeno, murmusawa yayi ya ce. “Mss Mary zaki iya tafiya ki turo min Mr Salim” “okay sir” mikewa mutumin yayi, yana faɗin. “Zeeno zauna, coffee ko caffeine ko tea?” “Coffee mara sugar!” Ta fada tana kallonsa. “Waw baki son kiba ko?” Murmushi tayi tana kallon office din.”muna farincikin zuwarki wannan kamfanin me albarka, wanda muka bude ta kasa da mako shida. Sai dai har yau tana nan a yadda muka bude ta.” Ya mika mata coffee ɗin, kallonsa tayi irin like how, ya ce mata.”tunda muka bude ta muna bukatar masu daukar nauyin da wasu tallace-tallace kana da masu zuba hannun jari.” Bude kofar aka yi wani kyakyawar matashi me tsawo da cikar halittar irinta maza ya shigo, ya ce musu. “Barkan ku.” “Barkar dai Salim, ga Zeenobia Nasr Hadejia, Zeeno Xnoo Yar kunama ko?” Murmushi tayi ta daura daya a kan daya. “kwarai da gaske!” “Nice to meet you!” Inji Salim yana mika mata hannu. Itama mika mishi hannu hannu tayi, sannan suka sake hannun junansu. “Zauna Salim.” Sauke numfashi MD na kamfanin yayi ya ce mata. “Mr Amjad ya bani labarinki, shi yasa muka ga dacewar mu baki matsayin me mu’amala da bakin mu da gayyato mana su, ta fuskar Kasuwancinmu.” Hàdiye yawun tayi ya ce. “Ni kuma ya gaya min cewa, zaku bani aiki ta ɓangaren security service, domin shi ya dace da ni.” “Haba Xno ba zamu dauke ki a matsayin wacce zata yi harkan tsaro ba, domin muna son kamfanin mu yayi achieve successful abubuwa Bama fatan wani abu mara dadi ya faru da mu, i hope you understand what I mean?” Tana jin abin da ya fada da turanci amma ita da ta tsani turanci taya zata iya rayuwa da abin da bata iya ba, babu boye -boye ta ce mishi. tace, “ba laifi idan kun bani shugaban security service. Hatta bera ba zan bar shi yayi shigo kamfanin nan ba, amma wend kuke ce min meka sifiki Ingilishi yu get rong idia, bikus na tsani Ingilishi ani mo!” Ta fada tana daukar jakarta. “Zeeno You can did it, zauna.” “Sa kake ko saniya nace bana jin Ingilishi, i sa i no Ingilishi meye sai ma zauna da ku dole? Dalla ku bani wuri.” “Idan baki amsa ba, zan kira Mr Amjad na gaya mishi, sannan zamu sauya miki damar haka, ko baki son rayuwar mutanen cikin al’umma charity House ya sauya ne? Zamu baku fili a gina muku makaranta da Asibitin da zai na kula da ku, sannan zamu dauki Abbas aiki a bangaren software!” Duk wanda ya zauna da Zeenobia Nasr Hadejia yasan Al’umma charity House da Abbas sune weakpoint, shi yasa suka kara tab’a inda take da yakinin aka. “zamu sauya miki rayuwa ki karbi aikin mu…”
*Barka dai Ya kuke ya kwana dayawa! Gamu nan Top-notch mun dawo i hope zaku amshe mu hannu bibbiyu*
#Zeeno
#Beauty
#Beast
#RomanceS
#Tycoon
#WeatherMan
#Top-notch
#Jelousy
#Cursed
#Mai_Dambu
[8/28, 2:22 AM] Maman Sadiq Da Khadijah: *CINIKIN RAI….*

Leave a Reply

Back to top button