Cinikin Rai Book 1Hausa NovelsHausa Novels

Cinikin Rai Book 1 Page 15

Sponsored Links

CINIKIN RAI….15
Beauty and the beast.
Mai_Dambu🌚
Maniyyata sun fara payment! Jiran me kike?
<<<<<<<<<<<<<<|=|>>>>>>>>>>>>>>>>>
Baki daya suka juya suna kallonta, idan ka gansu, karti ne na bugawa a mujalla, Murd’ad’an Giants. “Waye Malik Menk Jordan?” “Timmmmmm!” Aka bugata da kasa, sai da taji kamar kashin bayanta ya rugurguje. Domin buguwar irinta a kai ka lahira ne babu notice. Ganin yadda suka bugata da kasa, bata tashi ba suka juya abin su suna cigaba da aikinsu. “Boss me hannu daya,waye Malik Menk Jordan?” Sake surarta aka yi aka maka da tsohuwar motar da take wurin, “wash Allah na!” Ta furta dakyar domin ta bugu asalin buguwa, tashi tayi tana nishi dakyar.
“Last warning ka gaya min waye Malik Menk Jordan!” Da wani irin gudu, mutumin yayi kanta, kafin ya isa ta gyara tsayuwarta, kafin ya idda nufinshi akanta, ta saita shi tare da dukan wuyar shi sai, ya cilla kafin ya fadi sosai a kasa, juya wuyarta tayi ya bada wani irin sauti. Sannan ta ce. “waye Malik Menk Jordan!” Da gudu kartin mazan nan suka nufeta, karfe ta dauka a kasa kafin su isa wurinta, ta isa, gare su ta shiga musu wani irin jahilin duka, idan baka tsayar da tunaninka ba, zata zaka yi ganga ake bugawa cikin wani irin zafin na’ma. Duk abin da yake faruwa Idanunta a rufe. Sai da suka zube baki daya. Sannan ta bude idanunta hancinta yana zubda jini. D’aga kai tayi sama, sautin takunshi taji kawai ta kara rike karfen hannunta, kafin ya yi tunanin kai hannunshi jikinta tuni ta kai mishi wani irin bugu a gefen kanshi. Sannan ta kalle shi ya fadi a sume.

“Waye Malik Menk Jordan?”
“Hmmm yaushe aka haife ki? Yaushe aka reni ki da zaki gwada kwanji da Malik Menk Jordan, kin san waye shi? Shi din Mayor ne birnin nan bakidaya, a shekara sau uku ake ganin Malik Menk Jordan, sunan shi kad’a hantar fusatattun maza yake, balle kuma muryan shi firgita mace me juna biyu yake. Shi karfin da shi daya daidai yake da na kartin maza ɗari, kasuwancin sa yana sama da Ibadar shi da ki tab’a Mishi Kasuwancin sa gara ki kona garin nan ba zai tab’a kula ki ba, Yarinya Malik Menk Jordan ba kanwar lasa bane koma gida kiyi hakuri, idan wani abu ne a tsakaninku tabbas ba zaki iya ba!” Wani irin duka ta kaiwa kofar da yake tsaye, sai da kofar ta karye.
“Farautar shi na fito a daren nan babu makawa sai na sami abinda ya kawo ni, idan kuma aka ki bani, zan ta karya maka mutanenka ne!” Ta fada tana goge jinin da yake gefen bakinta.

“Zan gaya miki, amma ki sani sanin Malik ba abu me sauki ba ne, kinyi yi yarinya da son sanin wani waye shi. Zauns na baki labarin Malik Menk Jordan! Dan kazar da Uwarsa ta kasa, Allah keci da abinsa. Giwa babbar dabba, Zaki baka cin bakin wasu sai dai kaci ka rage.”
————
Kasancewar Hausawa sun yad’u ta hanyar fatauci da kasuwanci, yasa duk inda suka samu matukar wurin akwai kasuwanci basu tab’a barin wurin.
Mahaifin Malik ya taso tun daga Birnin Kano, ya sauka a garin Keivroto, mutum ne da yake da nasibi da Kasuwancin, sannan yana da matukar wadata. Domin daga yadda yake shiga ta Alfarma, gashi yana da gogewa a kasuwanci. Izuwa lokacin da ya iso garin babu wani bakin fata da yake da damar yin kasuwanci, domin turawa mulkin mallaka sun mamaye ƙasar da kasuwanci. Kuma wani abin damuwa anan yadda baki daya aka hana wasu yan kasuwan sai fararren fata da larabawa.
Masu mulkin garin babu abin da suka sani sai cin hanci, idan ka sakar musu kudi, zasu baka garin kayi yadda kake so, shi kuma kasuwanci yazo yi. Don haka ya sake musu bakin aljuhun. Suka yi yadda suke so, a lokacin akwai wani tantirin dan kasuwa Mr Jahid Khan kaf Keivroto kowa yasan halinshi.

Sonkai, son zuciya, bakinciki da keta,
mugun da zalunci, mutum ne da baya bukatar kishiya, duk abin da za a gani daga gare shi ake gani, shi yasa ya k’amk’ame sauran jahohin baki daya. Menk Jordan yana da mata da Yaronsu, baturiya ce tana Demark, asalin ƙasar ce mahaifinta babban malamin katolika ne, tunda ta ga Menk Jordan tace bata da miji sai shi, Menk Malik Jordan, Jordan ya samu asali ne daga kakanshi wanda suka yi tafiyar kasuwanci har aka haifi Menk, lokaci kakan da Uban basu nan, Malam Abdul Malik yana zuwa, ya saka mishi Menk domin mahaifinshi ya rasu a jordan. Shi yasa da ya girma yaji tarihin mahaifinshi a inda ya rasu ya kara Jordan a sunansu, domin Jordan yake kiran Kakanshi, sai ya zama mana Jordan ya fito as family din su.

Menk Malik Jordan ya fara bin kakanshi fatauci har zuwa lokacin da ya fara zuwa da kanshi. A wani tafiyar da yayi ya dawo ya samu labarin mutuwar kakanshi, haka yasa shi bazama, duniya niman kudi, sai yar Uwar.

Bayan tafiyar da yayi ya kai karo har Demark anan ya hadu da Diana, wacce tayi ruwa tayi tsaki, tace sai Menk Malik Jordan. Ubanta da yake yana sonta, ya barta ta aure shi, da cewa ba zata yi musulunci ba, baki daya sun gina rayuwarsu ne a Demark, har suka samu cikin Malik, haka suka yi ta tarerayar cikin har aka haife shi lafiya kalau. Kafin ya tafi Kano ya dauko yar uwar shi. Suka zauna da matar shi, duk wani kulawa Qudussiyah ta musu,

Wani abokinshi ya bashi shawaran su tafi, Keivroto kasuwanci, babu karya Malik da danginshi kasuwanci a jininsu take, domin duk abinda suka tab’a tana yad’o da yabanyayya.
A bangaren Keivroto kuwa, tunda Jahid Khan ya ga Menk ya fara samun jama’a sai kishi da bakin ciki ya fara kama shi, haka yasa shi fara turawa ana lalata duniyar Menk, wanda har ta kai an mishi wani irin taron dangi, amma mutumin bai yarda yayi give up ba, haka shi da matar shi suka kara hada karfi da karfe suka kara habbaka Kasuwancinsu. Abin mamaki sai gashi kasuwancin yafi nada albarka.

Bayan shekaru goma, lokacin Malik yana da shekaru goma sha bakwai, wannan iftila’in ya faru da su, shine na farko konewar Kamfanin Menk Jordan house, kamfanin yin takalmi da jaka, abin tausayi wannan itace mafi girman asarar da yayi a lokacin. Domin Diana tsabar kuka sai da ta daina gani, ana cikin wannan yanayin wasu daga cikin abokanshi suka saka shi zuwa amsar bashin duk da baya so, haka suka tilasta shi amsa, yana amso kudin barayi na biyo bayanshi, suka amshe kudin tare da mishi shegen duka.

Ko kwana ɗaya baa yi ba masu kudi, suka shiga mishi sallama, last dai abin da ya faru shine wasu sun zo gidan sun mishi kashedi. Daga haka sai tsintar gawar shi aka yi ya rataye kanshi, duk da masu binciken gawa sun tabbatar da ba kashe kai bane, kisan kai ne. Haka ya d’aga hankalin Diana wacce bata kawo haka Aranta ba, sai da ta kusan zarewa, kafin Allah ya nufeta da dawowa dai-dai, karshe bayan rasuwar shi ta musulunta, ta koma Salsabilah,. Abin haushi suna wannan rayuwar aka kwace musu kome nasu, hatta passport da zai fitar dasu kasar an kwace haka yasa Malik ya shiga tashin hankali, ga Mamanshi da bata da lafiya. Haka wata rana ana ruwan sama, ta fara rawan dari yaron nan ya rasa yadda zai da ita, dole ya shiga niman wanda zai taya shi su kai Mamar asibiti be samu ba. Dole haka ya dawo, sai a wani tsohon wheelbarrow ya dauka ya sakata suka tafi asibitin, yadda zaka san an shirya kashe su domin da ya kaita babu wanda ya damu ya duba ta, sai ya ajiye kudi haka suka barta a dandaryar kasa, ya fita yana yawo kwararo-kwararo. Kafin a hanya motar Jahid Khan ya buge shi, bai damu da buguwar ba, ya tashi…..duk da ba yawa managing…..
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[28/08, 7:47 pm] usmanlauratu71:

Leave a Reply

Back to top button