Hausa NovelsInda Rai Hausa Novel

Inda rai 2

Sponsored Links

*INDA RAI*……..

*By*.

*MARYAM ABDULLAH*
(Oum shaheed)

*Mikiya writer’s association*

Page 02

 

_______Yau garin Abuja an tashi da sanyi sosai kasancewar an kwana ana zabga ruwan sama, anguwar asokoro ta yi shiru,, babu komi sai kukan karnuka, wata haɗaɗɗiyar mota ce ƙirar BMW, Baƙace wuluk sai ɗauke idanu ta keyi, ta yi Horn a kofar wani tangamemen gate me kalar jikin damisa, buɗe gate a kayi motar tasa kai cikin salon tuƙinsa da salo yake sarrafa motar.”Barka da zuwa sawon giwa, ranka shi daɗe, cewar gate Man ɗin yana me rusunawa. zuge glass ɗin motar wani had’ad’d’en guy yayi, Allah ya masa hallita da ko waccebudurwa zata so ace wannan mijintane, kalar fatarsa chocolate color wadda hutu dajin ɗadi ya kara maidata wata kalar daban, gashin kansa a kwance luf yasha gyara,Yanada manyan idanu masu kashewa mace jiki sosai gayen ya haɗu, “zaro kuɗi ya yi daga cikin aljihun motar ya mika wa gate Man ɗin cikin husky voice ɗinsa ya ce “gashi Baba, kasaiwa yara alawa,”sa hannun Baba me gadin ya yi ya karba, zai fara godiya b Barrister Sudais ya yi gaba, cikin iya salon sarrafa mota yaje parking lot ya yi, kafun yafito a motar saida yaɗauki lokaci sannan ya fito, kai tsaye bangaran Mahaifin nasa Alhaji Auwal Ambassador na ƙasa ya nufa, “assalamu alaikum.” da gudu ya ji an rumgume sa ta baya,”well come ya Ajmal, “juyo da ita ya yi yaja karan hancinta ya ce, “Hi my bloody, ya ki ke? “I’m fine ya Ajmal, “to ai saiki sake shi tunda nine na ne mesa ba ke ba, cewar Alhaji Auwal” daga bayan su Ammy da ke shigowa matashiyar mata me kamanin shekaru sittin a D duniya ta ce “kai wai harka iso?” Yes mommy naji kira na sani ko gidan su Samha za muje neman iri? “Ja’irin yaro, wai kaikan ba kada kunya ne? “Murmushi ya yi ya janye little Sahla ya zauna kusa da mahaifin nasa cikin girmamawa ya gaidasu Sahla ta gaida sa ta yi waje domin basu waje.

“Abunda yasa kaji na maka kiran gaggawa to nima hakance tasameni, Kakanku ya kira ni akan an fitar da gonaki a can R rugar, kuma ana son sayarwa cikin hanzari, naso ace ɗan uwanka yananan, to amma har yanzun ya ki maido hankalinsa gida, bansan dalili baa, “yanzu de ka shirya zuwa gobe zamu ta fi, kuma shigar wuri na keso muyi, dan inada meeting a goben.” Ajiyar zuciya Ajmal ya sauke jin ƙirjinsa ya masa nauyi, da ga jin maganar zuwa ruga mafi soyuwa a ransa,”Allah yakaimu goben lafiya zan kasance a shirye cikin lokaci in sha Allah.

Birnin New Delhi

Wajan shaƙatawar yau ya fi kullum cika, kasancewar Imran ya saye duk wani kayan mayen gurin, a rabawa kowa kyauta, ƴammata da samari cikin shiga mara tsafta su ke chashewarsu, kamar a nce ba zasu mutuba,”yakamata ka tashi mutafi hakanan Boss, kalli time an kusa kiran sallah. “Mtswww Imran ya ja dugun tsaki ya kalli abokin nasa me suna Bhu Ali cikin muryar maye ya ce cikin yaran Hindu, Ina zan ganta? Ya sake lunshe idanu kafun ya kara buɗewa da sauri ya ce tashi muje yau banyi dream din taba, oh God,” cikin sauri Bhu Ali ya ce kwantar da hankalinka, zaka ganta soon amma kafun nan tashi muje gida kar daddy ya kira ka kana wannan wajan cike da kiɗa. Miƙewa ya yi ya na tangaɗ, “Bhu Ali ya kamasa har in da su ka yi parking suka ɗau hanyar gidan da Ya kama musu.

Ruga

Jin sauƙar ruwa me sanyi a fuskarta zu wa jikinta shiya ya dawo da ita cikin duniyar da ba ta so, kuma tayi D da na sanin dawo war tata cikin ta, mai zatayi a cikin wannan duniyar babu innar ta aciki? maiyasa Innar Rabi ba ta bari tabi Innar taba? innanillahi wa’inna ilehirra’ji un, cikin fitar hayyaci ta ke sanbatu, babu a lamar tasan me ta ke cewa,”ganin halinda ta ke ƙoƙarin sa ke shiga bayan yau kwanan Innar ta biyu da amsa kiran Ubangijinta, sai yau Maryam ta dawo hayyacinta, gashi ta na ƙoƙarin komawa,”ddu’ah Innar Rabi ta ci gaba da tofa mata duk ta ruɗe, gani ta keyi Maryam za tabi mahaifiyarta. “Babu kunya bare tsoron Allah haka Malam Bukar ya tsallake tsirarun matan dasu kayi saura zuwa ɗakin da su Maryam ɗin suke, yauwa ta farka ko? “kisanar mata gobe ɗaurin auranta, gara ta tashi tafara kintsawa koda kitso ne a
a fara mata ko.?” cikin muguwar mamaki Innar Rabi ta kallesa, cike da tsana me ƙarfi ta ce, haba Malam, A ai zaka bari ko sadakar bakwai ce a yi kafunnan itama yarinyar ta dawo hayyacinta ko kaɗanne. “da kata, ya katseta cikin haɗe fuska,”mutuwa ce an riga da anyi aure kuma gobe babu fashi….

Writing by oum shaheed💔💔

Leave a Reply

Back to top button