Hausa NovelsMusabbabi Book 2

Musabbabi Book 2 Page 5

Sponsored Links

MUSABBABI BOOK 2
NA
HABIBA ABUBAKAR IMAM
(Mrs Aliyu Mayere)

Page 5

Likitan ya cigaba da cewa “ko wane ɗan adam yana da ƙoda guda biyu a jikinsa, sai dai mutum zai iya rayuwa da ƙoda guda ɗaya, hakan yasa ko da ɗaya ta samu matsala to ɗaya zata iya riƙe shi ya cigaba da rayuwa, to a zahirin gaskiya duk a gwaje gwaje da binciken da mu kayi, mun gano cewa Afrah tana fama da ciwon ƙoda”, Inna Halima da Mallam Mahmud suka fiddo da idanu waje cike da kaɗuwa gami da tashin hankali, suka haɗa baki gaba ɗaya su ka maimaita, “ ciwon ƙoda likita”.
Shi kam musaddiƙ takardar hannunsa kawai ya ke cigaba da juyawa yana kuma jin zuciyarsa na matuƙar bugawa, likita ya gyaɗa kai yace “Eh, kuma wani abin mamakin shine bakasafai ƙoda guda biyu ke kamuwa da ciwo lokaci ɗaya ba, amma ta Afrah gaba ɗaya guda biyun duk sun harbu sun kamu da ciwo, sai dai ɗaya tafi ɗaya lafiya”. Sai alokacin musaddiƙ ya runtse idanunsa a hankali ya ji hawaye ya fara ƙoƙarin fita masa, sai dai baya son hakan ta kasance a gaban su Inna Halima, domin yasan zai iya karyar musu da guiwa.
Mallam Mahmud ya matso gaban likitan sosai yace cikin rawar murya “ yanzu likita meye abinyi? Wane taimako zaku iya ba ta domin samun lafiyarta?”.
Likita ya ɗan dubi musaddiƙ, duk da baiyi magana ba, ya fahimci irin tashin hankalin da yake ciki.
Yace “ ka kwantar da hankalinka, ko nace duk ku kwantar da hankalinku, a yanzu zamu ɗorata akan magunguna da kuma shawarwari, amma ku sani, a duk lokacin da ƙodojinta biyu suka daina aiki, to ya zama dole sai anyi mata dashen ƙoda”,
A hankali mallam mahmud ya lalubi kujera ya zauna domin ji ya yi yana neman faɗuwa, Inna Halima kuwa baki ta rufe ta shiga kuka.
Musaddiƙ ya ɗago ya dubi likita lokaci ɗaya yana ƙoƙarin tsaida hawayensa, yace cikin wata irin murya, “ Dashen ƙoda? Zuwa tsawon wane lokaci za’a ɗauka kafin hakan ya kasance?” Likita ya gyara zamansa yace, “ Eh to gaskiya bazan iya cewa ga lokaci ba domin ya danganta da yadda ciwon ke tasiri a cikin jikinta, zai yuwu zuwa watanni ko shekaru kai koma kwanaki, sai dai ka sani nata ciwon ya yi tsanani, don da alama ya daɗe yana cin jikinta ba tare da kun an kara ba, ko kuma rashin sanin alamomin cutar”.
Duka shuru su kayi na wani dogon lokaci kafin likita ya gama rubutunsa ya miƙa ma musaddiƙ yace “ A samo waɗannan maguungunan, sannan a tabbatar ta na shan ruwa sosai, kada kuma ta dinga matse fitsari ba tare da ta yi ba, wannan maganin kuma akwai nurse da zata zo ta dinga bata bisa ƙa’ida”.
Ya amshi takardar lokaci ɗaya ya tashi cikin ƙarfafa guiwa ya dubi su mallam mahmud ya ce “ kawu mu je”, ya riga su fita daga ofishin, bai koma ɗakin da Afrah take ba ya wuce ya tafi sayo maganin cikin matuƙar tashin hankali mara misaltuwa, yana tafe yana sharar hawaye tamkar wani ƙaramin yaro.

Hankula fa gaba ɗaya sun tashi, jinya sosai Afrah take yi,a yayinda gaba ɗaya musaddiƙ ya tare a asibitin shi ne yake jinyarta, duk da ga Inna Halima, amma baya yarda ya je ko nan da can, yana manne da Afrah, duk da ta fara samun sauƙi ta kuma san irin ciwon da ke damunta, a hakan ma itace ke ba musaddiƙ haƙuri a duk lokacin da ta ga ya faɗa cikin damuwa da tunani. Ita tuni ta fauwalama Allah komai domin tasan shine me yin yadda ya so, kuma ta ɗauki wannan ciwon a matsayin kaffara a gareta.
Zuwan Mama Hauwa biyu asibitin tana dubata, duk da babu wata damuwa a tare da ita na halin da Afran take ciki.
Haka zalika itama Haj kilishi direba ya kawota ita da Haj Rakiya sun dubata, sosai Haj kilishi ta nuna damuwarta, sai dai ko sisinta bata bayar ba don a cigaba da duba Afrah, duk da tasan musaddiƙ ɗin ba wani abu ya aje ba, haka su Mallam Mahmud.
Don ma Allah ya rufa asiri duk kuɗin da ake kashewa musaddiƙ ke badawa bai taɓa gazawa ba, tunda duk irin kuɗaɗen da Haj Hudah take bashi baya almubazzaranci, yana ajewa don yana tsoron buƙata ta taso musamman buƙatar Afrah ace bashi da yadda zaiyi.
Ranar da Haj kilishi ta je asibitin har suka kai gida cike take da farinciki yadda taga Afrah haka take son ta cigaba da kasancewa, ita kam Haj Rakiya a zuciyarta tausayin Afrah take ji amma a zahiri sai ƙara ƙarfafa aikin Tsiduhu take tana ƙara tabbatarma da Haj kilishi cewa duk aikinsa ne, tunda dama yace zai sa mata ciwo mai wuya ne, to gashi nan ya haɗata da ciwon ƙoda.Haj kilishi fa ranta ya yi mata fes ta ƙara gasgata duk abinda Haj Rakiya ta faɗa mata.
Taɓangaran Haj Hudah kuwa damuwa ce ta addabi ruhinta, ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta kuma rasa dukkan farincikinta, a dalilin rashin zuwan musaddiƙ aiki, domin da kansa ya kirata ya sanar da ita cewar bazai iya dinga zuwa wajen aiki ba saboda yana jinyar matarsa.
Haj Hudah bata jin zata iya jure rashin ganinsa, haka zalika ta rasa wane irin muhimmanci da so musaddiƙ yake ma matarsa da baya iya ganin kowa sai ita.
Adalilin hakan ta shirya ta tafi asibitin domin ta duba jikin Afrah, idanunta kuma su yi mata tozali da abinda suke son gani. Wannan shine karo na farko da tayi ido biyu da Afrah, ta zauna a gefen gadon tana ƙare mata kallo, duk yadda take fasalta Afrah a cikin zuciyarta ta fi haka, Afrah kyakkyawa ce sosai bata da wata makusa, wani irin kishi ne yake ta cika zuciyarta, ko yaya ta dubi Afrah sai ta ji kamar damuwa zata yi ajalinta.
Bata ƙara jin damuwa mai tsanani ba sai da ta ga yadda musaddiƙ ya rame duk ya fita hayyacinsa, tamkar shine baida lafiyar, ga shi sai tsuma yake da rawar jiki akan Afrah, hankalinsa baya kan kowa sai kan Afrah, ko ita bata jin ya dubeta sau biyu, ji tayi gaba ɗaya ba zata iya zaman asibitin ba. Don haka ta tabbatar ma da musaddiƙ cewar ta ɗauki nauyin duk hidimar asibitin, sannan kuma ta aje musu kuɗi masu yawa wanda musaddiƙ zai riƙe a hannunsa ko da wani abu zai ta so. Kwarai matuƙa Mallam Mahmud da Inna Halima sun yi ma Haj Hudah godiya mara misaltuwa, kimarta ta ƙara yawa a zuƙatansu.
Shi kansa musaddiƙ ya ji daɗin wannan karamci da gudunmawayar da Haj Hudah ta ba su, domin duk yan kuɗaɗen nasa sun tasarma ƙarewa, dama don farincikinsa ta yi ganin kuma farincikin nasa kaɗai ya wadatar da ita. Haka ta dawo gida cikin wani irin yanayi, tunda kuma ta dawo gidan take zaune a falo ta kasa shiga ɗaki, duk kuma irin abinci da kayan marmarin da hadimanta suka jera a gabanta, babu abu ɗaya da Haj Hudah tasa a bakinta, damuwa ta bayyana sosai a tattare da ita. Dai dai lokacin Alh yusuf sanda ya shigo falon yana gyara zaman babbar rigar da ke jikinsa, tsayawa ya yi ya zuba mata ido, ya daɗe yana kallonta kafin ya yi ɗan murmushin da ya zama tamkar ɗabi’ar rayuwarsa ne, sannan ya gyaɗa kai ya ƙaraaa cikin falon, amma har ya zauna Haj Hudah bata san da shigowarsa ba.
Shi ma kuma bai damu da tasan ya shigo ɗin ba, domin yadda ya miƙa hannu ya ɗauki tufar dake cikin farantin kayan marmarin da ke gabanta, ya shiga sha hankali kwance, haka nan ya zubama fuskarta ido, ko kaɗan baya neman sanin duniyar tunanin da ta faɗa. Karar da wayarsa ta carke da shi ne ya dawo da Haj Hudah duniyar tunanin da ta faɗa, nan da nan ta gyara zamanta tana tunanin iya tsawon wane lokaci ya ɗauka da shigowa falon, domin ko kaɗan ba zata so ya ganta cikin yanayin da take ciki ba. Hankalinsa kwance yake waya, maganar kasuwanci yake yi har suka gama idonta na kansa.
Ya aje wayar yana kallonta yace “ kin dawo kenan”, ta ɗan gyara zamanta tana jin nutsuwar rashin tsintar wani abu mai kama da zargi a muryar Alh yusuf sanda, tace “ Na dawo tun ɗazu, ai ban daɗe ba”, ya ƙara miƙa hannu ya ɗauki ayaba ya cigaba da ci, yace “ ya me jikin”, tace “ Ta ji sauƙi, ta dai sami ciwo mai wahala ne”, ya ɗan dubeta yace “ me ke damunta?”, ta ɗan yamutsa fuska tace “ ciwon ƙoda take, kuma duka biyun”, ya girgiza kai yace “ Lalle kuwa ciwo mai wahala Allah ya bata lafiya”, Hakanan ya ƙara zuba mata ido yana wani irin nazari, lokaci ɗaya ya maida bayansa ya kwantar akan kujerar, gami da girgiza ƙafafunsa zaman shurun duk ya damu Haj Hudah don haka ta miƙe ta shige ɗaki yayinda ya bita da wani rikitaccen kallo cikin murmushi.
Tun daga wannan ranar Haj Hudah ta kafama kanta zuwa asibiti duba Afrah, ba don wai ta damu da ciwon nata ba a’a sai don kawai ta samu ta dinga ganin musaddiƙ tunda yaƙi dawowa bakin aikinsa, idanunta kuma ba zasu juri rashin ganinsa ba. Haka ta dinga kashe lokacinta tana zuwa asibitin duk da tana da abubuwan yi , har zuwa lokacin da Afrah ta sami sauƙi aka sallameta, tare da magunguna da kuma shawarwarin yadda zata taimaki kanta,
Ko bayan da aka sallami Afrah, musaddiƙ kin fara zuwa aiki ya yi, ya zauna a gida yana cigaba da kulawa da matarsa.Daƙer Afrah ta shawo kansa ya fara zuwa wajen aiki, tunda ita kanta ta ji sauƙi sosai, don har tana tunanin fara zuwa makaranta. Afrah tana da matuƙar tawakkali shi yasa bata sama kanta damuwa ba sam agame da lalurar da Allah ya ɗora mata.

Damuwa mai yawa ta shiga mallam Mahmud, duk da yana ƙoƙarin boyewa, domin duk abinda zai taɓa Afrah baya ƙaunarsa, Mama Hauwa dai babu yabo ba fallasa, ma’ana bata jin tausayin Afrah haka zalika kuma bata jin daɗin abinda ya sameta.
A ranar da Afrah ta fara zuwa makaranta kuwa Haj kilishi ji ta yi kamar ta yi hauka saboda damuwa, ko kaɗan bata so samun sauƙin Afrah ba, duk da itama jikin nata ya matsa mata kwana biyu, zafin zuciya da raɗaɗin jiki da matsanancin ciwon kai mai tsanani, sai uwa uba yanzu ƙafarta da ciwon ya ci uban na da, don yanzu saboda tsabar ciwo da azabar zafi da take yi mata ko tana zaune sai dai asa ruwa me sanyi a baho ta sanya ƙafarta ciki wanda kafin wasu yan mintoci ruwan yakan koma tamkar ruwan zafi, saboda azabar zafin ƙafar, ko yaya ne kuma bata taɓa iya rufe ƙafarta saboda azabar zafi hakanan zaka ga ƙafar tana zufa.
Likitan da ke dubata babu gwajin da baisa ta yi ba amma har yanzu babu abinda su kayi nasarar gani domin komai lafiya ake nuna masa, ga azaba tana ciki amma ba’a san ta ina za’a fara ba, dole sai dai pain reliver suke bata wato maganin da ke lafar da ciwo, wanda shi kansa shan zai iya zamar mata illa zuwa gaba.
Kuɗi take kashewa sosai wajen nemo lafiyarta amma babu biyan buƙata kamar yadda take ta narkar da kuɗin wajen malamai da bokaye domin ganin bayan musaddiƙ da Afrah, amma har yanzu babu wani cigaba, ance zara bata barin dami sannan taken masu bin bokaye ne yin asarar komai da rasa komai duk abinda suka tara sukan rasa hakance ta fara faruwa ga Haj kilishi, domin dai duk yawan kuɗin da ta tara na cuta da na ta yanzu komai ya fara kakkaɓewa, hankalinta ya ƙara tashi matuƙa, domin dai rayuwa tafiya take tana da burika da yawa amma ta fara karaya, tunaninta ya ƙara nisa.
Wanda take son ganin tashin hankali da tagayyararsa shine kullum yake cigaba a gaban idonta, mu’amalar da musaddiƙ ya yanke da mutanan kirki duk ya dawo da su, domin dai tare ya ke yawo da Murtala da zaran ya tashi aiki to gunsa yake wucewa, shaye shayensa ya yi baya sosai, don a yanzu ma tun fara ciwon Afrah yake matuƙar taka tsan tsan da duk abinda zai tada hankalinta, ga azkar da kansa yanzu yake yi ko da Afrah bata sa shi ba.
Idan Haj kilishi tace tana cikin natsuwa to ta yi ƙarya, ita kanta Haj Rakiya yadda take sintirin zuwa gidanta da yanzu ta rage, idan ba aikenta zata yi gurin malamai ba bata zuwa.
Sai dai abinda bata sani ba, Haj Rakiya tuni ta dawo daga rakiyarta lokaci kawai take jira, ta buga wasanta na ƙarshe.

Alh yusuf sanda yau laraba jirginsa ya tashi zuwa paris, domin shigo da wasu kaya masu muhimmanci na maƙudan kuɗaɗe.
Washegarin alhamis kuwa Haj Hudah cike take da zumuɗi domin tana da taro har biyu a Abuja, so samu ne ta kwana ko da biyu ne a can, amma ƙwaɗayin tafiya tare da musaddiƙ yasa ta haƙura da kwanan ta gwammace su je da wuri su dawo ranar, tunda tasan babu yadda za’ayi musaddiƙ ya yarda ya kwana don ƙa’idarsa ce hakan.
Duk sammakon da musaddiƙ ya yi sai da ya tabbatar da Afrah ba zata sami damuwa ba wajen zuwa makaranta kasancewar sun fara jarabawa, baya son tana wahala duk da tana cikin lafiya amma lallaɓata yake yi sosai. Murtala ya kira ya roƙe shi ya zo ya ɗauki Afrah zuwa makaranta idan lokacin zuwanta ya yi, ya kuma taimake shi ya dawo da ita idan ta kammala zana jarabawar. Murtala ya tabbatar masa bashi da wata damuwa zaiyi duk abinda ya buƙata. Hakan yasa musaddiƙ ya sami ƙarfin guiwar tafiya, bayan ya sanar da Afrah inda zasu tafi tare da Haj Hudah.
Har kullum irin ƙaunar da musaddiƙ ke nunama Afrah, gami da damuwa da ita ya fi komai faranta ran murtala, domin dai shi kansa yasan musaddiƙ ɗin ya yi dacen mata.

Cikin gigita Haj Kilishi ke faɗin “ Duk abinda ki ke yi ki barshi, ki taho yanzu ina son ganinki”, Haj Rakiya ta taɓe baki tace “ Lafiya dai ko Haj” ta girgiza kai tace “ Maganar bata waya bace, ki dai taho yanzu”, tana gama faɗin haka ta kashe wayar. Haj Rakiya ta saki tsaki ta juyo ga Dillali Babaye, ta miƙa hannu ta amshi takardar tace “ Zansa hannu idan na dawo zan kiraka, sai mu ƙarasa” Dillali Babaye ya girgiza kai yace “ Haj gidan nan akwai masu so da yawa, duk da kin bada kuɗi fin rabi gaskiya idan baki cika kuɗinki yanzu ba ana iya samun matsala, gara koma meye ki cika kuɗin duk wani sa hannu ai mai sauƙi ne”. Haj Rakiya ta girgiza kai babu abinda ta tsana da ya wuce a furta cewa tana iya rasa gidan da ta ƙallafama rai, irin gidan yan gayu da take mafarkin shiga.
Tace “ Daina wannan maganar Babaye idan na rasa wannan gidan ai an sami matsala, ina zuwa”, ta miƙe da sauri ta shiga ɗaki, ƙasan katifa ta ɗaga ta ciro ƙuɗi da ta baza a ƙasan katifar, ta yi zaman dirshan ta gama ƙirga kuɗin, bata tashi da ko sisi ba, duk sun shige cikin kuɗin da zata cika, sai dai da ta tuna inda kuɗin zasu tafi da abinda zata mallaka bayan sun tafin sai ta ji wani sanyi ya cika zuciyarta.
Ta maida kuɗin cikar baƙar leda ta ƙulle sannan ta fito ta miƙama Babaye ya amsa yana kallonta yace “ zan je na yi musu balance, kisa hannu a takardar da zaran kin dawo sai ki kira ni”, ta jinjina kai gami da yi masa godiya.
Bayan fitarsa, ta yi dariya tace a fili “ kilishi na kusa fita daga ƙangin bautar ki, domin na dawo daga rakiyarki yau itace rana ta ƙarshe da zan saurari kokenki ko na yi miki aiki, domin duk abinda nake nema na riga na samu, zan tuba zan kuma cire musaddiƙ daga sauran masifar da ki ka sa shi ciki, karshe ma idan ba kiyi wasa ba zan tona asirinki a wajen kowa”. Ta ƙara yin dariya, lokaci ɗaya ta janyo gyalenta ta yafa, sannan ta ɗakko waya ta kira maigidanta Tasi’u wayar bata daɗe tana kuka ba ya ɗaga, ya yi mamakin yadda yau ya ji muryarta cikin mutunci da mutuntawa tana kuma wai tambayarsa izinin fita, Tasi’ u ya gyara zamansa a gaban sabuwar amaryarsa da bai wuce makonni biyu da aurota ba, ba tare da sanin Haj Rakiya ba, yace “ ikon Allah yau kuma kece ke neman uzinin fita Rakiya, lafiya kuwa?” .
Ta yi ɗan murmushi tace “ Lafiya ƙalau mallam, ina dai neman izini don Allah”, cike da tsantsar mamaki yace “ Na baki izinin Allah ya dawo da ke lafiya”, tace “ Amin” lokaci ɗaya ta kashe wayar ta fice.
Tasi’ u ya wangame baki yana kallon amaryarsa,lokaci ɗaya yana tunanin idan ma nadama Haj Rakiya ta yi to ta makara, yadda ya zauna ya haɗiye zama da ita ba girma ba arziƙi duk da duk yayan da ta haifa masa sun rasu, ta hana masa ƙara aure, yau kadarinta ya karye , tunda gashi nan ya ƙara aurensa yana zaune da matarsa cikin kulawa da mutuntawa ba tare ma da ta ko sani ba, idan tana ganin itace ta hana masa ƙara aure, to lokaci ne kawai baiyi ba, domin da Allah ya kawo lokacin gashi ya yi. Gaba ɗaya Haj Rakiya ta daɗe da fice masa a rai, kawai dai yana zama da ita na dole ne.

Isarta gidan Haj kilishi, ta taddata cikin wani irin gigita da ƙaɗuwa, haɗe da tsoro, Haj Rakiya ta zauna kusa da ita tace “ Haj lafiya kuwa ko jikin ne?” Ta girgiza kai ido jajir tace “Eh akwai jikin ma amma ina cikin damuwa ne sosai”, ta ɗan matsa kusa da ita tace “ Damuwar me?”.
Ta ɗora mata ido sannan tace “ wani irin mummunan mafarki na yi da boka mai Rakwacam yana gaya min na jefa shi cikin masifa, Haj ina kallo wuta ke cinsa yana kuma faɗin saura ni, sannan kuma duk ranar da aka tone tukunyar ƙasan kuka to tawa ta ƙare,”, Haj Rakiya ta numfasa tace “ kai Haj yanzu saboda mafarki ƙarya shi ne ki ka gigice haka, wannan ai shirme ne irin na mafarki”.
Ta girgiza kai tace “ Bana jin hakan a jikina komai ya bayyana a gare ni ne tamkar idona biyu, babu bambanci da gaskiya”.
Cikin ƙosawa da maganar tace “ To shikenan, yanzu me ki ke so ayi miki kika kira ni”.
Tace cikin rawar murya, “ Bazan iya tuƙi ba, ba kuma zan iya tafiya da direba saboda sirri, saboda haka ki kira mai taxi ɗinki ya zo ya kaimu rugar mai Rakwacam lalle ina son na ga halinda yake ciki”. Gaban Haj Rakiya ya fadi sosai, ko kaɗan bata son Haj kilishi tace zata je domin idan har yana cikin wannan halin to ba ta son ta gan shi a haka, don tabbas tasan zata iya sa zargi da zato a cikin zuciyarta.sai dai duk yadda ta so ta dakushe tafiyar to fa Haj kilishi ta ƙi yarda ta dage dole sai sun tafi, Bata son ta cigaba da yi mata musu, don tasan shegen kafiya irin na ta don haka waya kawai ta ciro ta kira direban ta gaya masa inda zai taddata.
Wanda ba’a ɗauki wani dogon lokaci ba direban ya iso.
Haj Rakiya da kanta ta riƙe Haj kilishi har cikin motar, yayinda Baba maigadi ya bita da sannu don a tunaninsa ma ko asibiti zasu tafi.
Sun kai Rugar da wuri domin mai taxi ɗin ya yi gudu sosai.
Sun tadda Boka mai Rakwacam a inda aka saba aje shi, wannan karon ma babu kowa a tare da shi, alamar kowa ya gaji da lamarinsa. Idanun Haj kilishi suka buɗe sosai, tunda ya faɗa wannan masifar bata taɓa ganinsa ba sai yau, ita kanta Haj Rakiya da yake tun zuwan da ta yi bata ƙara zuwa ba, ko Haj kilishi ta aiketa bata zuwa, tunda ta fahimci hatta wayarsa ta daina aiki balle Haj kilishi ta kira shi ta gane inda ta dosa.
Hakan yasa itama taga mai Rakwacam ya ƙara rakwacamewa, babu abinda ya ƙara tada hankalin Haj kilishi sai irin yadda ta ga duk jikin mai Rakwacam a ƙone yake duk ya sabule sai tashin wari kawai yake yi, wani farin gurɓataccen ruwa ya na fita daga ko’ina a cikin jikinsa.
Cikin rawar jiki da murya Haj kilishi ta riƙo Haj Rakiya tace “ Dama haka mai Rakwacam ya koma amma ki ka ce wai kunyar rashin samun nasara a ayyukan da yake min ne ya sa shi cewa baida lafiya, ki dubi jikinsa irin wutar da naga tana cin sa a jikinsa a cikin mafarkina ce, haka jikinsa ya koma ko a mafarkin nawa, dagaske ne mafarkina, na shiga uku, saura ni ……”, jikin Haj Rakiya itama ya yi sanyi, a sanyaye tace “ Me ki ka gani a game da ni a cikin mafarkin na ki…” Haj kilishi ta yi mata kallon tsaf, wasu tarin tambayoyi da wani abu mai kama da zargi Haj Rakiya ta gani kwance a cikin idanunta, tayi saurin ɗauke kanta, sannan Haj kilishi tace “ Kada ki damu banga komai a game da ke ba, amma ki sani duk abinda ya ci doma ba ya barin awai”.
Shuru Haj Rakiya ta yi ba ta son ta cigaba da furta duk wani abu da zai dasa zarginta a ran Haj kilishi.
A haka suka baro rugar ba tare da ko sau ɗaya sunga mai Rakwacam ya yi motsi ba, kamar yadda har suka bar rugar ko matarsa basu gani ba a matsayin me kula da shi, lalle wannan duniyar shirme ce, shin ina bokancin nasa? Ina taimakon da yake ba mutane? Me yasa bazai iya tsinanama kansa komai ba bayan a yanzu babu wanda ya kaishi neman taimakon?.
Irin tambayoyin da Haj kilishi ke yi ma kanta kenan. Lokaci ɗaya kuma tana kashe Haj Rakiya da wani irin kallo wanda ke haddasama Haj Rakiya kaɗuwa, hakan yasa tun daga Rugar har cikin gari babu wanda ya yi ma wani magana, suna shiga gari Haj Rakiya tace “ Ina jin zan sauka anan, akwai uzirin da nake son yi”, Haj kilishi ta girgiza kai tace “ A’a ki jira mu je gida tukuna, akwai tambayoyin da nake son na yi miki”.
Cikin Haj Rakiya ya shiga ƙugi, tsoro ya bayyana akan fuskarta,
Haj kilishi ta ɗauke idonta daga kallon fuskarta ta da ta gama bayyanar da rashin gaskiyarta, hakan yasa gaba ɗaya motar ta ƙara yin tsit, ko ƙwaƙƙwaran motsi Haj Rakiya ba ta yi don ji take kamar idan ta yi motsi Haj Kilishi zata faɗo wata maganar da zata ƙara dugunzumata.
Hakanan a daddafe su ka kai gida, Haj kilishi ta sallami me motar. Sannan ta shiga dafa bango domin shiga cikin gidan, Haj Rakiya na ƙoƙarin riƙeta ita kuma tana ƙoƙarin tafiya.
Baba maigadi bai fahimci komai ba a tsakaninsu, sai sannu da yake cigaba loda yi mata, irin tashin hankalin da ya gani a tare da Haj kilishi zahiri bai taɓa ganinsa a tare da ita ba. Haka ya bisu da kallo har suka ɓacema ganinsa.

Suna shiga falo Haj kilishi ta zauna daƙer tana aje ajiyar zuciya me ƙarfi, sannan ta dubi Haj Rakiya wacce ta zauna a kujerar da ke kusa da ita sai dai ta kasa haɗa ido da ita kamar yadda zuciyarta ke bugawa tana addu’ar Allah yasa ba ganota Haj kilishi ta yi ba, wani abin ban takaici kuma shine yadda ta zuba mata ido ba tare da ta ce mata uffan ba.
Dai dai lokacin murtala ya sauke Afrah a ƙofar gida daga makaranta, ta yi masa godiya sannan su kayi sallama, tana tura kai cikin gidan, Baba maigadi ya tareta da sannu da zuwa, cikin mutuntawa ta amsa masa har ta nufi ɓangarenta, magamar Baba maigadi ta dakatar da ita, “ Jikin Haj fa ina tunanin ya matsa, don basu daɗe da dawowa daga asibiti ba, kuma ko da suka dawo na fahimci ta fi yadda suka tafi ƙara galabaita, ta wahala sosai”, Afrah ta dan yi jim sannan tace “ Allah ya bata lafiya, bari na shiga na dubata kafin na shige gida”, yace “ Eh hakan ma na da kyau”.
Ta juya ta nufi ɓangaren Haj kilishi, amma hakanan sai ta sami kanta da jin faɗuwar gaba, mai tsanani, ta ji tana neman ta rikice, duk da haka dai haka ta cigaba da tafiya harta isa cikin gidan, muryar Haj kilishi da Afrah ta ji cikin ƙaraji da fusata ya tilasta mata tsayawa jikin windo,
“Ina tambayarki duk irin kuɗin da kike ƙarɓa a cewar boka mai Rakwacam ne ya ce a bayar, gidan uban wa ki ke kaiwa, bayan da shi da matacce basu da wani bambanci………………..

 

Yar gidan Imam✍️

Leave a Reply

Back to top button