Hausa NovelsTUMFAFIYA Complete Hausa Novel

TUMFAFIYA 54

Sponsored Links

 

🌱TUMFAFIYA SIRIN KI     SAI ALLAH
,,,,,,,,,,

5️⃣4️⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA
DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS
MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA
AMIN,,,,,,,

 

Sannu a hankali wani irin shakuwa da sabo yake shiga
tsakanin mu wanda hakan ya kara kwantar min da hankali a gidan matsalata dayane
zuwa biyu shine irin matsalan dake tsakanina da uwar Ahmed da kannen sa har ma
dai ita karamar tafi shiga min ido sosai.

  Don dayan ba zance
ga wani matsalan daya taba hadani da ita ba saidai kawai ba sakin fuskane itama
daga wajen ta kamar yadda uwar da yar uwan keyi min.

   Sai tsohuwar gidan
ce mai sake min fuska don ina zaune zanganta a parrt dina ta shigo mu danyi
hira ta kuma ta ban hakkuri na daure da yanayin dana tsunci kaina a ciki wata
rana sai labari.

    Nakanyi mata godiya idan ina da abu na dan
bata ko nayi dafuwa in saka mata da dan yawa duk da nasan bata iya cinyewa ita
daya .

   Don su din na kula
da sunyi fushi kan zancen abincin da master yace a daina sakawa dasu din gashi
koni din bako yaushe yake bari inyi girki ba a part din mu din.

  Saidai idan zai dawo
ya sayo dan wani abu mu danci harda ma yan cikin gida wanan sallon kuma yasa
mahaifiyar shi saka ido ga hakan da yakeyi din .

  Tana fada ranan a
gabana cewa wanan ai salon kashe mata dane aka dauko wai ace mace ba zata girka
abinci suci ba sai an fita an sayo abin kwalan a kasuwa taci.

   Da Dije taji fadan
yayi yawane ta fito tana fadin kai kai Rashida baki biyo halina ba wallahi baki
da godiyan ubangijo ko kadan dake watace sai ki godewa Allah daya hada danki da
yarinyar nan a yanzu.

   Koda yake ba abin
mamaki bane don kinyi hakan a yanzu don baki san irin wahalan da muka fito a
cikiba a baya har zuwa ranan da Allah ya hada dan naki da yarinyar nan abubuwa
suka fara bude mashi.

   Fadin hakan da
tsohuwar tayi sai naji maman ta saka kuka tana fadin Dije ko baki min gori ba
nasan na tafi na barku a cikin wahala shekara da shekaru nima kuma hakan ai ba
laifina bane tunda aure nabi.

    A,  toh ni dai na fada in kina cire ido ga yaran
nan ki cire don arzikin su yazo data idan kinyiwa dan ki sawal, walin tsiya
kuma ya rabu da yarinyar nan wanan kuma kinwa kanki don dai ki sani.

   Shine kwana biyu
naji shiru ta daina shiga harkan mu tama dauko fita in tabar gidan tun safe sai
yamma zata dawo.

   Da yan kushin
abubuwan irin su rake yalo karas lemu mangoro ayyah da sauran su a nan zasu
baje saman tabarma da yaranta suci sai wata rana wata rana akan debo min akawo
min dan kadan.

   Saidai Allah bai
sako min kwadayin irin kayan nan ba wata rana in karba in aje idan ya shigo shi
zaici wata ran kuma ba zan karba nace a mayar nagode.

    Sai su cinye
abinsu ko wanda ake kawo min din ma ita yar babban yar nata Aishan ce kecewa a
diba min sai karamar ta yatsune baki tace abinda baida yawa zatace wai sai an
dibamin shi.

 Haka dai zasuyi ta
fada a tsakanin su har ta kawo min ruwa kuma koda sanina koba da sanina ba haka
zasu shigo su bude fridge su dauka susha saidai wanan bai dameni ba kamar yadda
sukanyiwa fridge kamar da gaiya zakaji an rufe shi da karmi har sai mutum yaji
shi har cikin ranshi .

   Irin hakan wata
rana ya faru yana gidan Asmau tazo ta dauki ruwa ta buga marfin saida duk muka
zabura lokaci guda.

   Ya mike yana fadin
meye hakan da kyar na iya dago kai na bashi amsa da frige ne aka buga wata kila
wanine ya dauki ruwa a ciki.

   Ya juya ya fita a
hasale ya samu yarinyar Asmaun daice ma lokacin yayi mata tas saiga uwar ta
fito tana fadin don ruwan da nace ta dauko min din shine zaka zo kana kokarin
fadawa mutane maganan banza.

   Ke karbi ashirin ki
karbo ruwan ki mayar masu don Allah kuma daga yau kada wanda naga ya koma shiga
sashesu da sunan dauko wani abu.

    Innan mu bafa
fadan an dauki ruwa yakeyi ba yadda asmau ke buga masu marfin fridge dine yayan
mu ke magana a kan shi.

   Wani tsawa ta dakawa
yar nata da saida ta kadu lokaci guda ta koma ta rakube a bayan Dije tana ci
gaba da sauraron uwartasu dake sake magana.

   Inna nifa ba ruwa
nace meyasa ta dauko ba yadda take rufewa yarinyar nan fridge ne bai mun ba don
Allah ai mata magana ta bari.

    Yana fadin hakan ya juya ya tafi ya dawo
dakin yana cicika kafin muji muryan Asmau tana sallama tare da fadin ga ruwanan
ance in kawo.

    Ya mike ya fito da
sauri yabi bayanta yana kiran tazo ta dauke ruwan ko ya saba mata abin taron
kurciya dukansu sai ya kwasa ya bita da gudu ita kuma ta koma bayan uwar dake
hasale ta boye tana leken shi a inda yake tsaye yana wa uwar kallon mamaki.

    Dake fada tana
fadin don ruwa kawai zaka taso min ya a gaba zaka doketa ina dai don ruwan kake
wanan hasalan gashi kuma na sayo na mayar maka da abinka.

   Mama don me nake
sayen ruwan ba don asha bane nake sayowa ni magana nake mata cewa ta dinga kula
mata da kaya kada a bata matashi.

   To ai shina nace
mun daina tabawa ruwan kuma dana dauka nasha gashi nan mun biya koba shike nan
ba ta fada tana mai wani irin kallo na tsana.

    Kai Amadi maza
koma ka zauna in fita zakayi kuma tai zuwa inda zaka ke kuma in dai radhin
kunya abin yine ki   biyewa uwarki gara
ita takamanta a yanzu na haihuwan shi da tayine keko fa ?

   Ina shi din daine
gatan ku garin nan don in kun iya ko abinci sai ku daina cin wanda yake sayowa
kunaci din karewan dai ke nan ke yar banza ko mutum daya kun gani gidan nan da
sunan dangin uban ku halan ?

   Zaki biyewa uwarku
da bata san ciwon kanta ba kunawa yaro iya shige iri iri idan yai magana uwarku
ta tare maku tundai ke Asmaun nan ba ma,un arziki kike ba wallahi don duk wani
iskanci da iya shige kece ummul,abasin shi a gidan nan yanzu.

    Ko shekaran jiya
in kula dake da kika gama wanki yarinyar nan tana shigowa kika dauki ruwan
wankin nan kika watsa mata da kadan a jikinta in ba Allah ya gyara ba.

   Ido waje yace kin
gani ba kingani ba Dije ni idan zasu takurawa yarinyar nan ne gaskiya saidai
nabar gidan nan mu koma haya da ita don ba zan dauki hakan ba a rayuwata tunda
yan uwanta ni basu raina min ba don me ni nawa zasu dunga wullakanta min ita ?

    Jeka ai abin
baikai na barin gida ba yar banza maganin shegiya mara kunya zanyi gidan nan
tun kan aika ga hakan asirin mu ya tonu idan ka bar gidan nan yanzu da dan Amo
ya gwajesu yaran banza kawai.

   Ya juya ya tafi har
ya shigo part din kuma yasa kai ya fita zuwa wajen dabbobinsu a nan Aisha din
kanwarshi ta bishi tana fadin.

  Yayan mu kaiyi
hakkuri nima ynzu na gane gaskiya abinda akai wa amarya ba a kyautawa ko ranan
ni nishigarwa maganan da Dije ka hwadi dazun da niyi magana innan mu ta dawo
Asmau ta kwashi karya da gaskiya ta hwada mata.

  Kije ai ba komai duk
abinda mutum yayi don kaine don kuma baku san irin gidan da zaku hwada ba ai ga
amre don Allah yayan mu kayi hakkuri damu da innan mu.

    Ya duka yana gyara
wurin dabbobin yana fadin ki tahiyar ki ai komai ya wuce garan nikan bandai
yadda a rainawa matana da wayo don na aurota gidanga shin hakan laifina ?

  To in abin yayi min
yawa daukan mata zanyi mubar garin in koma gidan ubana mu zauna don su can basu
gudun mu duk wanan abin na kula cewa dani innan ku ke adawa kiyayyana ne ya
shafi Zahra yanzu itama.

  Yarinyar tayi shiru
na dan lokaci kafin ta furta don Allah kayi hakkuri ta juya ta tafi dama ya
fadi hakan ne don yasan sako ya bata zai isa kunnen mahaifiyar nasu.

    Yasan kuma ba zasu
taba yarda dacewa ya koma gun mahaifin nasa ba a yanzu don irin yadda suka
kulla shi a ransu irin yadda suke ganin yayi banza dasu a baya sai yanzu da
yaro ya fara tasowa zaice zai koma garai.

    Tana shiga ta samu
suna maganan tsakanin Djje da innar tasu nan ta samu wuri ta zauna tana
sauraren su kafin a kawo inda ta tsoma baki tana fadin.

   Ai yayan yace
tahiyatai zaiyi gidan ubanai wane uban ne ubanai uwar ta tambaya a hasale tana
kallon yar nata.

   Lokaci daya suke
kara tambayan junan su da cewa wane uba kuma to ai yanzu kin gani kinji
hukuncin da dan naki ke kokarin yankewa zuciyarshi yanzu akan halin da kika
dauko mashi a yanzu.

    Sai in bani raye hakan
zai faru mutymin da yai tahiya tai bai ko taba tunawa da muwa ba a duniya sai
shi da rashin zuciya ya daukeshi ya kaishi inda yake .

   Yan uwanai sunka
taho nan da barazana waisu ga dangi wagganshi ko yasan inda yake yanzu maganar
banza da wofi kawai.

   Ki dai natsu kada
wani abu yaja maki bacin rai daga baya wanda ba maganin hakan a gareki yanzun
dai kekin ka rage da shawaran da zai fusheki inba haka ba kina kallo danki ya
gujeki saboda halinki na banza.

  Shiru tayi har
tsohuwar tagama ta naji tayi shiru tana nazarin zancen tafiya gidan ubanshi da
kanwar nasa ta fada masu lokacin.

   Ina kwance ina
karatun handout a hannuna don abin ya dan shige min duhu shi kuma baida lokacin
zama ya koya min karatu yanzu sosai.

    Sallama nake ji a
kofa yasa na aje takardan na mike zuwa falon din don ganin wace ke min sallaman
Tani ce mai aikin ummah bansan lokacin dana sako fara,a a fuskana ba lokaci
guda ina fadin.

   Tani kece da yamman
nan ta karaso ciki tana fadin wallahi uwar dakina yau dai nace barin lekoki
muji lafiyan ki kwana biyu shiru koda yake hjy tace min ai kuna gaisa.

    Tani ai nayi fushi
rabon ki da gidan nan har na manta na dauka kema ke manta dani ai yanzu takai
zaune inda taga alaman nake nufin ta zauna don ganin na cire filon dake wajen .

  Uwardakina aure kan
ya karbe ki kinga yadda kika koma kinyi kiba hasken ki ya karu ai kan zaijewa
hjy dake cikin damuwa akanki da wanan labarin mai dadi wallahi.

   Kin kyauta da kika
rufawa kanki da mahaifiyar ki asiri inyi hakan ne garuku dan a cutawa rayuwan
ku kekan alheri wanan aure ya zama maki yanzu.

   Ba irin auren yan
uwanki ba da yanzu ya komawa iyayyen ciki kullun ana gida tare da uwa shiyasa
nake fadawa hjy cewa hakan yafi maku in anyi da sunan kuntata maku yanzu ya
zama alheri a wajem ku.

   Don ga zahiri na
gani nikan walle hjy zataji dadin labarin nan nawa dama damuwanta shine ba
komai kike iyaci ba a rayuwanki.

    Banda matsalan
abinci ko abunsha don gaskiya ina samu iya karfin shi Tani ba laifi yana iya
kokarinshi dani alaman jin dadin hakan dana fada ya baiyana a fuskanta dkn
bakin danaga ta kara washewa lokaci daya tana fadin.

    Haka akeso ka
godewa Allah da mai maka idan har yana maka ko da kadan ne watarana idan ya
samu zai maka wanda yafi hakan ai.

    Ki kara hakkuri
sosai sama da wanda kikeyi din yanzu insha Allahu zuciyana tana bani cewa kinyi
dace da miji nagari wanda kowa keson samun irinsa nan gaba.

    Don nasan baki
sani ba duk jumma,a yanzu zaije gidan ku ya kwashi kannen ki yaje masalaci dasu
idan zasu dawo kuma ya hadosu da tarkacen makulashe ya dawo dasu.

    Haka duk ranan
talata yakan zo ya gaida mahaifiyar ki har yayi kokarin masu alheri hjy taso
hana hakan amma nayi mata magana ta daina kinga kuwa ko hakan abin alfaharine
gareta yanzu.

   Aiko kinga bai taba
nuna min yana zuwa gidan mu ba fa koda wasa bai nuna min hakan ba yakan dai
kira waya ya bani mu gaisa idan yana gida wanan kawai nasani ni.

    Na fada maki hakan
ne don ki kara rike mijin ki da zuciya daya kamar yadda shima ya rikeki har
cikin ranshi.

    Muka dan taba hira
wanda taso ta fada min halin da Aisha da Rukkaiya ke ciki a gidajen auren su
nayi saurin tarewa da fadin Allah ya kyauta yasa su gane gaskiya su rikesu
amana ta amsa da Amin.

   Da zata tafi na
hado mata clean da sabulun wanka da yan tarkace harda soyayyen nama tana ta
godiya muka fito na rakata ta gaidasu Dije munyi sa,a inna ta dawo har ita suka
gaisa tana ta kallon ledan dana rikowa Tani din tana son tantace abinda ke
cikin ledan lokacin.

   Bayan na dawo daga
rakiyanta din zan koma part din mu naji muryan Dije tana kirana da yaki nan
amarya nazo take fadin.

  Nace matar nan ya
kuke da itane wai na dan sake murmushi ina fadin mai aikin muce ita keyiwa
mamata aiki ai.

   Bana fada maki
basuda alaka ba dama wanan yar garita sosai yar unguwan tudun wadace ai
shinagani haka kawai mace ta mayar da kanta baya taje tanawa wata katuwa aiki
kamarta.

   Uwar Ahmed ta fada
hakan yasa na dan daga kai na kalli gefen da take take naji raina ya baci har
yanayina ya canza taci gaba da fasin baki fini ba don kwadai kina kwance da
yayan ki ni ina maki wahala.

  Muryan Dije naji
tana bata amsa da fadin yafi mata alheri don hakan yafi mata yawon tallan gida
gida wai kayan mata ana daukan ta yar iska mara kamun kai .

   Inno tallan nawa
shine na kika kira da iskanci ta fada cikin tashin hankali sai tsohuwar tace
aikin nemam na kai da rufin asiri ma an zageshi mai zai hana masu yawon talla
kica kica suna gogaiya da maza ba a zagesu ba.

   Nan ta soma cewa ni
dai waga sana,an bari nai nikai gara inyi zama hakan tunda ya zama illa garan
yanzu kuma .

   Nidai na wuce da
mamakin su a raina ina mai jin zafin irin yadda uwar mijin nawa takan jefeni da
kalamai haka masu zafi kai tsaye.

  Ban taba fadawa
Ahmed ba saidai idan shi yaji ko yagani idan yana gari ya dauki matakin hakan
don yakan dan debi kwanaki yana school zaria inda yake hada masters din shi
yanzu.

  Yayin da ni kuma
nake nan gusau ina hada nawa digree din wanda a lissafina saura shekara daya da
yan watani na hada karatun nawa lokacin.

    Tani kuwa ta koma
da labari mai dadi wurin ummah wanda hakan yasa ummah farin ciki tayiwa Allah
godiya don ko tani bata raga komai da taji ko tagani ba a ziyaran data kai min
din harma da kari.

  Ba abinda yaiwa
ummah dadi a cikin labarin sai jin da tayi nayi kyau daki sosai a bakin mutane
ga kuma karatuna yana tafiya daidai haka kuma ina zaune lafiya da kowa a gidan.

    Dama damuwanta ke
nan dani idan ta tuna cewa bana son yawan mu,amula da mutane sosai a rayuwana
gashi kuma Allah ya jefani gidan yawa yanzu.

    Satin shi biyu a can
zaria din ya dawo ya dubamu ya samemu lafiya saidai ya samu wai kayan abincin
su ya kare dole ranan ya fada kasuwa yayo masu sayayya ya kawo masu dan ledan
semo da kubewa danye ya riko muna jin karan ledan yasa uwar kyala idonta akan
roban tana son sanin meya dauko a ciki a zaton ta wani abin dadine ya sayo min.

    Aisha ki dauki
ledan nan ki kaiwa Zahra ta tuka muna shi don naga nata ya kare ya fada don
kawar da wani zargi a zuciyar mahaifiyar nasa lokacin.

    Da sauri yarinyar
ta dauko ledan zuwa part dina ta sameni a dan kitchen dina na dora ruwa don
ranan nasan yana gari zan girka muna abincin dare ke nan ranan.

   Don in baya nan
saidai nasha tea ko complain in kwanta ban damu da girka komai ba tunda ni
kadaine kuma abincin bai dameni ba ni .

    Amarya yayan mu
yace in kawo maki ki girka ta fada tana miko min ledan dake hannunta din na
juyo ina kallon ledan kafin nace me kuma ya kawo yanzu har na dora ruwan zafi
zan zuba shimkafa a wuta ?

   A gaban ta na bude
komai ta gani tace na bata kubewan taje ta gyara min sai hakan yai min dadi
sosai don dama shine abu mai wuya ga aikin nake gani gashi kuma ta taimaka min
da gyaran shi.

   Don haka na hada na
wanke da kyau na miko mata tare da abinda zata gurje min shi ta tafi wurin su
dashi ni kuma naci gaba da aikina.

  Duk daba saurin
aikin nake dashi ba amma ina kwantar da hankalina na girkashi da kyau yayi dadi
saida saurin aikin da bandashi kawai ne matsalana.

    Sai gani nayi
Aishan ta dawo min da kubewan data fara gurza ranta kuma bace tana fadin anty
kiyi hakkuri ban kai ga gamawa ba innan tace in dora girkin mu.

   Na mika hannu na
karba ina fadin aiba komai ko hakanma nagode ai saura kadan ki gama min ba zan
dade ba zan gyara shi yanzu.

  Tace bari dai in
tsaya nan in karasa maki kafin na koma ita innan mu bansan abinda ke damunta ba
haka wallahi dan wanan zatace din me na karbo maki aiki in tayaki bayan ga namu
nan har na dora tukawa kawai zanyi yanzu ida
na gama.

    Muna magana tana
gurza da sauri tana kallon hanyan shigowa part din namu saura kwara uku ta kare
nina juya ina kokarin yin talgi mukaji muryan mahaifiyar nasu a bayan mu tana
fadin.

   Kekan anyi mara
wayau  da rashin sanin ciwon kai na
rasama me zan kiraki dashi naji sanyi yanzu kece don rashin sanin ciwon kai
zaki dawo nan kina kamawa wata aiki kin bar na uwarki can yana konewa ?

   Kiyi hakkuri mama
don Allah na fada daga inda nake tsaye nasha jinin jikina don banson wani abu
ya hadani da matar nan ko kadan don ban hango kaunata ba a zuciyar ta.

   Don Allah ki rufa
min baki idan ba lalaci ba wanan dan girkin ne za ace sai an kama makishi ko me
ko idan kin dafa damu zakuci ?

   Naga yar nata ta
kallota da sauri tace ke kuma munafuka kallon me kike min don na fadi gaskiya
tasan ba zata iya kula dashi ba tayi auren ko an fada mata yar aikina haifa
matane tunda sun saba kwanciya ana girka masu suna ci ko ?

    Ke Aisha fito ki
koma cikin gida ki daina zuwa kama mata aiki tunda tana iyawa inma bata iyawa
ai gani saiki fada min abinda zan kama maki kiyi ba sai anje ga haka ba.

     Daga dan tsakar
wurin mu ya tsaya yanawa kanwar tashi magana a fakaice ta aje abin kubewan ta
juya ta fita sai naji uwar tayi kwaba tana binshi da kallo ta juya ta tafi.

   Jikinane yayi sanyi
saiga hawaye na silalo min a fuskana ya karaso ciki bayan fitan ta yana fadin
kema princess meyasa zaki basu aiki bayan kinsan halin inna ?

   Dago kai nayi da
niyar in fada mai yadda zancen yake sai na kasa sai hawayen dake bin fuskana ya
dauki roban ya daga yaga saura kwara uku a ciki wanda bata goge ba yace aima ta
gama ashe akwai wani abinda zan kama makine dashi ?

  Na girgiza kai na
samu na bude baki da kyar nace komai na hada sai wanan din ya rage min dama
kuma Aisha din ta gyara min shi ai.

    Ya danyi shiru
yana kallon yanayina kafin ya juya zuwa ciki ya koma ya kwanta yana duban
laptop din shi da yanzu yake aiki a cikinsa har na gama girki ana gab da
magariba na wuce shi na fada bandaki nayi wanka tare da dauro alwala.

 

Leave a Reply

Back to top button