Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 34

Sponsored Links

34
Dd babba dukkanin tsare tsarensa na jiran haihuwar ya gama,
Shirin Daya tanadarwa Ababa ana haihuwar zai saka a batar masa da hankali yanda babu me iya Tina komai sai Abinda zaa Dora a Nan gaba Dan haka ya sanarwa Ababa lokacin haihuwa na zuwa a sanar masa ya turo mota akaita asibiti haihuwa.

Ababa komai yakeyi Yana tsayawa ya Kalli lamari Dalla Dalla kada ta kwabe masa Dan haka Sam ya kasa yarda da maganar Wani Kai sumayyah asibiti haihuwa sbd komai ma zaa iya yiwa cikin a kashesa gurin haihuwa a rufe zancen Dan haka bazai taba yarda ba a gida zata haihu idan an maqale da Kansa ze kaita Asibitin Daya yarda a haifo masa Dan a Basa a hannunsa yaga me kashesa bayan Wanda ya Basa Rai ya aikosa duniya.

Shi Kansa yanzu ya rage fita sosai koyaushe Yana gida tinda cikin zo gangar haihuwa Dan bayason ma baya kusa haihuwar ta taso ayi masa katsalandan kaita Asibiti.

Benazir azabarsa duka akanta yake qarewa sbd ganin itace yanzu mara amfani a gurinsa,
Duka asarar duniya ganin yakeyi ta qare akanta batada amfani komai gurinsa a yanzu,
Jiran ma yakeyi a gama auren sumayyah ya samu su shiga kaantes ya miqawa yan dilar qwayar dayayi alqawari benazir din Dan bama zai iya cigaba da biyan nata karatun ba tazo ta debo masa Wani abin maganar Dan kuwa ita binneta zeyi da Rai idan tayo masa Hakan sbd babu wasu sauran masu kudi a idonsa bayan kaantes.

***Rayuwa tayiwa benazir tsananin da ko ruwa ta saka bakinta ‘dacinsu takeji,
Babu Daren da Anne da sumayyah Basa kukan tausayinta sbd a kanta wahalar kacokan take yanzu.

Exam dinta dasuka fara kullum zuwa kawai takeyi ta rubuto ta dawo Badan tana Gane komai ba ko karatun komai din.

Qwaqwalwarta datafi ta kowa lafiya a kaf gidan har Ababa da hande
Itama tafara samun rauni sbd a yanzu itama kusan magana takeji kaman anayi mata cikin kan saidai Sam qarfin zuciyarta ya Hana kowa Gane halinda take ciki.

Ranar da suka gama exam tana dawowa gida ta tadda ayyukan dake jiranta
Sallah kawai tayi ta fito tafara aikin
Sai dare ta kammala ta shigo dakinsu ta Kalli sumayyah dake zaune shiru tayi Nisa a tinani cikin mutuwar jiki da tausayin kansu Dana Annensu dake gefe zaune shiru itama batama San tinanin datakeyi ba.

Ajiyar zuciya benazir ta sauke ahankali tareda zaunawa itama Bata iya cewa komaiba zuciyarta na Wani irin rawa sbd ta Kai zuciyarta tagama tsotsewan da babu komai a cikinta sai iska da fili.

Zuba mata idanuwan dasuka gama fadawa sbd rama sumayyah tayi tanajin cikinta na motsawa a hankali.

Benazir batasan kallan da sumayyah ke mata ba na tsananin tausayinta da tsanar kanta akan sakasu cikin wannan halin datai Amma itama ba itace ta zabarwa kanta qaddarar haihuwa a yanzu ba,

Hawayene suka gangaro mata masu tsananin zafi Daya Sanya benazir juyowa ta Kalli sumayyahn zatai magana jikinta amace itama
Sumayyah ta fashe da Wani irin Kuka mara sauti tana sunkuyar da Kai Dan kuwa komai Basu samu a wannan rayuwar ta duniya ba face tarin jarabawa da darasi,
Samirah jarabawarta ta qare da wuri ta tafi ta huta hakama Safnah,
itama tana fatan a daidai wannan gabar Allah ya Yanke mata wahalar ta tafiyarta tabar duniyar ta huta
Benazir ma ta samu sassaucin ukubar.

Benazir data San tinanin da sumayyah takeyi take idanuwanta dasuka Fi kwanaki a bushe Bata iya Kuka sbd azaba idan tai yawa Kukama baya zuwa,
A hankali Idanuwanta suka fara Tara ruwan hawaye masu dumin dasuka fara gangarowa fuskarta.

Hawayenta yasaka Anne kasa riqe nata kukan itama sbd kukan benazir Yana karyar da duk Wani kuzarinsu Dan itace qwarin gwiwarsu Kuma karfinsu.

Kukan Anne yasaka benazir kokarin Hana hawayenta cigaba da sauka Amma sun kasa tsayuwa hakama Wani sheshekan kukan Mai tsananin ciwo da nauyi ya taho mata ta rufe bakinta da hannuwanta biyu tana cusa kanta cikin qafafunta sbd nata quncin yafi nasu Dan su suna Mata Kuka su bayyanarda radadinsu
Ita Kuma batada inda zatai kukan ta bayyanarda damuwarta sbd sune nata Rabin jikinta Amma basuda lafiya ko hankalin fahimtar nata quncin bayan ma ta sake gigitasu da nata kukan shiyasa duk tsanani take dannewa ta riqe komai ta barwa zuciyarta.

Wani irin Kuka suka rufu a dakin suka Taya benazir sbd tayi kukan sosai ko zata samu sassaucin Abinda take dannewa tana riqewa a zuciyarta batareda fitarwa taji sauki ba.

Suna cikin kukan marar sumayyah tayi Wani irin riqewa ta daure ta kasa nunawa saidai kaman bazata iya dannewar ba Dan haka ta Dan dago jajayen idanuwanta ta Kalli Annensu kafin ta Maida kallanta kan benazir ahankali ta Bude baki tace

“Zanje bandaki”

Hawaye benazir ta share da tafin hannuwanta kafin ta janye daga jikin Anne data rungumeta Dan rarrashinta ta miqe tsaye tana sake goge fuskarta kada a Gane kukan da sukai Hande ta hau Wani fadan Kuma.

Daman sumayyahn ba kasafai take iya komai ba da kanta a yanzu sai an taimaka mata sbd ko kuzarin tsayuwa da kanta batada shi sbd wahala da yunwa.

Kamata tayi suka fito tana riqe da ita suka je bandakin tayo Abinda zatayi suka dawo suna isowa inda zata ajiye butar ta Dan saki sumayyahn da ajiye butar Ashe Bata tsayu daidaiba sai Jin tayi sumayyahn ta zube qasa.

Faduwarta yayi daidai da fitowar hande da Anne a kusan tare suka saki ihun tashin hankalin Daya saka Ababa fitowa da rigarsa a hannu dagashi sai dogon wando da singlet.

Rawa jikin benazir ya dauka cikin tsananin tashin hankali ta durqusa tana kamo sumayyahn data fara Wani wahalallan Nishin da bama na faduwar bane na halinda take ciki ne kafin faduwar.

Azabar datafi Wanda suke ciki tsawon shekaru ne sumayyah taji Wanda yasaka kasa motsawa tafara Jan numfashin wahala jikinta na daukan rawa take.

Salati me karfin gaske hande ta saki tana cewa

“Mun shiga uku benazir kin tado mata nakuda lokaci baiyiba
Wannan ‘da dai Allah yasa rabo ne”…

Kalmar hande ta saka Ababa Jin zufa da tashin hankali Mai tsanani rufesa
Ya Kalli benazir daketa rawar jikin taimakawa sumayyahn ta tashi Amma ta kasa.

Fizgota yayi kafin ta motsa ya sauke mata wasu Marika biyu a Jere da suka dauke mata jinta na daqiqu
Gefen bakinta take ya Dan fashe.

Cikin tsananin zafin zuciya da masifa yace

“Wlh kiyi adduar a haihu lafiya na dauki ‘dan da hannun idan ba haka ba kece kika kashe cikin Nan Kuma wlh bazai dauki asarar Rai ba miqa ki zanyi hannun yan sandan gidan yari”.

Hande kuwa gabaki Daya dagawa kowa hankali tayi da ihun ai an kashe babyn tin baizo duniya ba shikenan.

Wannan kalaman nata suka haukatar da Ababa Kansa na Neman kuncewa.

Anne ma duk da ciwonta take lafiyanta ta dawo ganin zata rasa sumayyah,
Benazir duk da jinta daya dauke tana Jin hayaniyarsu sama sama haka ta taso Bata ko Gani sosai ta nufo sumayyahn suka kamata zuwa daki ita kanta sumayyahn lokacin ciwon yayi mata tsanani Amma ahakan ta qanqame hannun benazir tanajin ita tafi buqata a yanzu fiye da kowa Dan a hannunta takeson haihuwar koma me zata Haifa,
Tana son Abinda zata haifa Yana fadowa duniya ya fado hannun benazir dinta sbd Anne ko an bar mata shi bata Gane kanta wasu lokutan bare Abinda zaa bar mata.

Suna shiga daki da ita Anne da jikinta ke rawa haka kawai ta Kalli sumayyahn dake hada Wani zufan gaske tanason tayi magana ta kasa.

Hande shigowa dakin tayi ta koma kofar dakinta ta zauna tana jiran haihuwar itama Ido awaje.

Ababa kuwa rigar Daya fito da ita Bai iya sakawa ba haka ya tsaya tsakar gidan Yana kaida kawo zuciyarsa na tsalle da fargaba da tashin hankali harma da tsoro Mai tsanani sbd ayau ne ranar da zai karbi mukullin shigarsa kaantes,
Wannan haihuwar ta sumayyah itace tabbacin makomarsa da matsayarsa a babin gaba.

Naquda sumayyah ta fara gadan gadan cikin tsananin azaba da wahalar data fara qarar mata da karfin da Daman batada dashi,

Anne da benazir Basu taba shiga matsanancin halin fargaba da tashin hankalin wannan Daren ba,

Tin tanada karfin iya motsawa da numfasawa daidai harta rasa dukkanin karfinta.

Ababa a tsakar gidan kuwa wutar ruwan zafi ya kunna da Kansa ya ringa tura itatuwa suna cinyewa Yana saka wasu sbd idan ya tsaya guri Daya zai iya kasa riqe Kansa ya fada dakin.

Shi Kansa tinda yake a duniya Bai taba shiga hali na fargaba da tsoron wannan Daren ba gashi haihuwar na Neman zuwa da gardama Dan kuwa Tim suna Jin Nishi da kukan sumayyahn harsun Dena ji.

Sumayyah data cire daga rayuwa gabaki Dayanta tini jini ya fara tsinke mata Bata iya ganin fuskokin Anne da benazir dake kanta dishi dishi take ganinsu tana kokarin Hana kanta sarewa Amma Kuma numfashinta baa hannunta yake ba da zata iya daidaitasa.

Babban fatanta idan gurin haihuwar Allah zai dauki ranta ya dauki ranta da Abinda zata haifa Shima ya bita sbd ta tafi da masifar da zata qarawa benazir da Anne,
Bazasu iya renan jariri a wannan wannan matsin rayuwar da suke ciki ba.

Har Akai sallar Asuba sumayyah Bata haihu ba tagama ficewa hayyacinta.

********
A safiyar ranar karfe 6 na safe jirgin da DD kaante ya sauka a Nigeria tareda ummensa da Zeenah,

Motar Bilal kaante ce tazo daukansu,
Sai Amintaccen DD na tintini wato Naseer Wanda baida kaman DD din Shima Dan kuwa DD ne ya dauke nauyin karatunsa tin secondary har gama jamiarsa daya gama last year,
Abinda yasaka Bai bi DD ba acan sbd akwai wasu ayyukan DD din dashine yake kulawa dasu ta Wani bangaren Kuma soyayyar wadda takasa yardama ko sakewa dashi tayi harya bar makarantar Dan haka yake Jin bazai iya tafiya koina batareda ya sameta ba.

Shi Bilal da Naseer suka fara hangowa a tafe cikin kalar kayansa da baya sauyawa sai Dace wato black.

Michael kors Black sweatshirt ce jikinsa da black Balmain jean,
Qafarsa ma black BV saldals ne da suke bayyanarda hasken kafarsa dake kaman bada ita yake tafiya ba a rayuwarsa.

Hannunsa na dama a cikin aljihun wandonsa yake dayan hannun kuwa hannun ummensa ne a cikin nasa suna tafe gabaki Daya baka iya ganin fuskarsa daga gefen fuskarsa da bayan wuyansa da farar fatarsa ke bayyane sbd facemask din dake rufe da fuskarsa da tsadaddiyar luxury black Fcap din flexfit dake Kansa.

Idanuwan Naseer Daya jima baiga maigidan nasa a fili ba kusan kasa dauke idonsa yayi akansa sbd gabaki Daya wannan dake doso sa shi ake nufi da Asalin kaantes Dan kuwa babu kamarsa Kai tsaye a harka indai acikin familyn ne.

Kafin isowarsu Naseer ya nufosa da sauri Yana Isa DD ya dago fararen idanuwansa dasuka saka Ba Naseer ba hatta Bilal Jin jikinsa ya mutu da kwarjinsa take ya zaro hannunsa daga aljihun wandonsa ya ware ahankali ya rungume Bilal din Wanda ganinsu su ukun ya saka sa Jin Kansa kaman qaramin yaro gabansu yanaso tsiyayo da hawayen quncin dake damunsa a Rai na tsawon lokacin da basa Nan Dama Abinda yake damunsa kwanakin.
#MAMUH#
#MARRIAGE
#CRAZY IN LOVE
#DD
#BENA
#ZAFIN KAI

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button