Bakar Ayah Book 2Hausa Novels

Bakar Ayah Book 2 Page 59-60

Sponsored Links

Page 🖤 59••60

Fitowa tayi daga motar ta zagaya ɗaya bangaren ma ta buɗewa Jabeer.
A hankali yafito daga motar,kana ganin jikinsa kasan sauƙi yasamu,amma duk da haka bai ware sosai ba.
Kallon harabar kotun yake wacce take cikeda mutane,saboda shari’ar daza’a gabatar.
Hannun bombee yakama wanda ta miƙomasa tana murmushi,riƙewa yayi ya ɗam bada ƙarfinsa a jikinta suna tafiyah.
“Sai yanzu dana fito waje na san cewa lallai nadaɗe a zaune a gida,amma yakike ganin shari’ar zata ƙare”
“Yanda ake tsammani,kowa abinda ya shuka zai girba a yanzun,zai fi kyau ka daina surutunnan haka muƙarisa ka zauna”
“Hmm ke kike ganin haka,naji ƙarfin jikina fah sosai,tuƙin motar ma dan kinƙi banine”
“Hhhh nasan dalilin dayasa kake son tuƙin ai,dan ka nunamin ne saboda yau karn hanaka abinda kake tasonyi…….”
“Karma kifara dan kince sai angama komai kowa ya karbi hukuncinsa dama zaki bani damar shiga rayuwarki,dan haka babu fashi yaune”
Dariyah bombee tacigaba dayiwa Jabeer suna tafiya,har suka iso bakin ƙofar shiga kotun,dan dama tuni an fara shari’ar,bayan sati guda dasu Lailah sukayi a hannun ƴan sanda sai yau za’a zartar musu da hukuncinsu.
Kotun tacika sosai da mutane,Lailah,Hajiyah rabi,lubnah,brr na’imah dakuma sameera.
Dukkan su suna wajen tsayuwa guda,duk wanda yaga fuskarsu da kuma halinda suke ciki,dolene zai tausaya musu.
Musamman ma lubnah wadda ta moje ta yamushe,abinda duniya ya isheta,ita kamma tasan nata lokacin ne yakusa,tunda an tabbatar mata a asibiti cewar cancer mahaifane da ita saboda abinda ta cuccusa.
A ɗaya bangaren kuma alhj Abdu manga ne da kuma su daamus.
Kasancewar akwai cikakkun shaidu,kowa kuma ya amsa lainfin sa,yasa basu bawa mutane wahala ba..
Dukkansu a laifinsu akwai kisa ko kuma yunƙirin aikata hakan,hakanne yasakasu zaman gidan yari tsawon rayuwarsu.
Hajiya Lailah kuma da mijinta zasu biya alhj Aliyu tarar kuɗi mai yawa na farmakin dasuka amsa sun kaimasa,sai brr na’imah da kuma lubnah zasu biya diyyar kashe kishiyoyin lubnah,yayinda zasu haɗa su biya diyyar haidar kuma harda sameerah.
Shikuma Gen abdu manga bincike yanuna cewar baya cikin hankalin sa lokacin da abubuwan suka faru,dan haka kotu ta yanke masa yin wata shida a gidan yari daga nna yakuma inya fito za’a wankeshi daga zargi.
Hayaniya ce ta kaure kotun,kowa yana faɗin albarkacin bakinsa.
Ganin yanda wajen ya hargitsene yasaka Jabeer ƙanƙame hannun bombee kaman an liƙa su da gum,da haka suka fito daga cikin harbar kotun,zuciyar su fari tass,musamman bombee sai yau taji nauyin daya hau kanta ya sauƙa na ɗaukawa Hidar fansar abinda yayi mata.
Magana taji anayi mata bayan sun fito daga cikin kotun.
Waigawa tayi ta kalli nu’aimah itada Hajiyah Zulaiha,Gabaɗaya nauyin ganinnasu ne yakamata sosai,rabonta dayin tozali dasu tun Ranar dasuka rabu akan ita ta kashe haidar.
Hannunta take ƙoƙarin zarewa na haidar domin nufarsu.
“Mr. CEO kabar Mrs.CEO taje ga mutane ana ƙiranta”
“Uhm kinsanfah bazan iya jure tsayawa na dogon lokaci koh?”
“Nikuwa nake da tabbacin haka,yanzu zan dawo ka jirani a mota yanzunnan”
Sakin hannunnata yayi yana haɗe fuska,ita in yana wani abun kwanannan har dariya yake bata,babu dama ya waiga bai ganta ba saidai taji ƙiran wayarsa ko kuma aike.
Su maleekah har dariyah suke masa amma bai dameshi ba,shikansa baisan yanada wannan halin ba sai yanzu daya gamu da soyayyar gaskiya..
Indai suna zaune a falo to kuwa kansa yana cinyarta ko kuma ya jingina da ita,babu kunyah haka zasuyi da faɗa da haidar idan ya sauƙeshi akan cinyar shiya kwanta.

Ƙarisawa inda su Hajiyah Zulaiha tayi cikin sanyin jiki,tunkafin tayi magana ta jawota ta rungumeta a jikinta,kuka tasake tana magana a hakan.
“Kiyafemin ɗiyata kiyafemin,koda kowa yagaza fahimtarki nibai dace nayi hakan ba,ban tashi sanin gurbinki cikin Ahalinmu ba saida kika tafi haidar ma ya tafi,a nanne nafara tunanin tabbas ba lallai kece kika aikata abinda aka zargeki ba.
Yanzu da komai yafito fili har kunyar kaina nakeyi da abinda nayi miki bombee.”
Ƙanƙame Hajiyah Zulaiha tayi wadda itama takejinta a matsayin Mahaifiyarta har cikin ranta.
“Karkice haka mommy,kidaina zargin kanki dayawa,kowacce uwa a lokacin iya abinda zatayi kenan,dan haka ki bar komai ya wuce kaman bai faruba,tunda a yanzu kowa yasan mai yafaru sannan wanda suka aikata kuma sun karbi hukuncinsu daidai laifinsu”
Sakin juna sukayi bombee tana share mata hawaye,a lokacinne Gen Muhammad bello ya iso wajen shiga ƙanin haidar.
Har ƙasa bombee ta tsugunna ta gaisheshi,shima haƙurin yafara bawa bombee saida ta katseshi tukunna yayi shuru.
“Uhm mommy barina tafi Yana jirana a mota,har yanzu bai warkeba bayada cikykykyiyar lafiya”
“Oh haka fah ai munji duk labarin abinda yafaru,Ƙaramin haidar ma na ganshi a wajen hilyan dakuma ƙanwar mijinnaki,sukamma basu fito ba har yanzu,kinsan abin zai fi tabasu fiyeda kowki saisun taho daga baya.
Karki damu momy zanzomuku inshaallah idan komai ya lafah”
“To shikenan Bombee,nima zanzo naga ɗakinki,nagode dakika bar komai ya wuce,idan nazo zanji girkinki shin ya ƙaru kokuma yana nan tun wanda nakoya miki”
Dariyah bombee tayiwa Hajiyah Zulaiha,saboda tunowa rayuwar ta a gabannata.
Kafaɗar nu’aimah ya tafah tareda cewa.
“To kema saikinzo min ina jiranki,duk da nadaɗe ina duba yanayin shigarki makaranta da kuma tafiyar gida,saboda kar har sannan basu daina kulla abinsu akanku ba.
Uhm naga saurayinnaki nan,shima nayi bincike akan sa,kicemasa antynki tace yayi mata”
“Wow really anty Bombee kinsan mai nake?”
Tafaɗa a kunyace tana sunkuyar dakai bayan sun haɗa ido da Hajiyah Zulaiha.
“Ohh mai kike nufi,yanzu nice kaɗai antynki dan haka ki kula sosai hmm?”
“Ehh zan kula amma irin wannan zancen ki barshi sai mu biyu tukunna”
Dariya sukayi a tare Hajiyah Zulaiha tana kallon su cikeda sha’awar sake ganin hirar tasu bayan tsawon lokaci.

Lokacin da bombee tashiga mota Jabeer ɗauke kansa yayi.
“Hubby bazaka min magana ba wai,ban daɗe ba fah nadawo baka ganine”
“Hakanne baki daɗe ba,tun ɗazu fah nake jiranki nikaɗai,gashi can naga su maleekah sun fitoma,yanzu nasan da sun haɗu dake bazaki dawo ba yanzu.”
“Nifah nayi mamaki wai bazakayiwa lubnah bankwana bane,ku wuce gidan amarennaka suma kayi musu”
“Hmmm bazawarai dai,tun yaushe na sakesu,maima yakawo maganar su yanzune,inaga in wanine yake maganar su zaki ce yabari kafin naji”
“Hhhhh to in ita baka mata bankwana ba,Babannaka fah shida matarsa,ga surukarka ma duk a wajen”
“Kai dan Allah Ummu haidar kibar zancennan haka,ni yanzu mu tafi gida ke nafi buƙatar gani a sirrance basu ba,banda kindamu ma nida bazan zo ba,dan ba daura ɗamarar zubar da rayuwar baya na fuskanci ta gaba yafimin”
Hannun ta yakama ya acikinnasa yafara tuƙa motar.
“What mai kake nufi,wai kai zaka tuƙa motar?”
“Menene to a ciki,nida zan tuƙaki in anjima mota ai ba komai bace”
“Naji naji kabar zancen toh”
Dariyah yayi ganin yadda lokaci ɗaya kumatunta yayi ja.
Ƙutt taja bakinta tayi shuru tana kallon ɗaya windown,danta kula surutunnasa marar burki yazo shi.

Shiga cikin gidan sukayi,maimakon yakama hanyar sashensu sai kuma taga yanufi wani wajen daban.
Batace komai ba har suka isa wani sabon sashe da akeyi a cikin estate ɗin.
Gininsa akeyi a lokacin,saidai kana gani kasan aiki yayi nisa sosai.
Ƙoƙarin fita Jabeer yake daga motar,hakanne yasa bombee kasa tsuke bakinta har zuwa sannan hakan yasakata tayi magana.
“Abban Haidar inane nan kuma muka zo kafin gida,naji kacemin ka gaji sosai”
“Uhm nagaji amma ba har can ba,zo muje na nuna miki wani abu”
Fitowa tayi daga ɗaya bangaren ta riƙe hannunsa suka nufi wajen ginin.
Sashe biyune a cikin wajen,amma suna nesa da juna sosai.
Kowanne ciki da falone da kitchen da kuma ɗakuna biyu a ciki.
Kallon Jabeer bombee takeyi domin yayi mata bayanin ginin wanene,tunda taga yanda ya damu da nuna mata ya yake.
“Nagode da zuwanki rayuwata,wanda ƙaddara ta daɗe da shigowa dake tun kafin nasani.
Kinga abubuwa dayawa a cikin ta amma hakan bai saka kin juya baya ba,saima jajircewa dakikayi kika tsaya gefena.
Masu iya magana suna cewa a kowacce nasara da namiji zai samu,takan kasancewa ne idan ta jajirtacciyar mace a gefensa,niba iya jajirtacciya kawai nasamu,nasamu jaruma tsayayyiya a gefena,shin wanne abu kuma zan sake nema Allah yabani indai a wajen abokiyar zamane.

Wannan gidan part ɗin dayake farko na Umar ne wanda zai auri khadija,munyi maganar dama baba kece baki sani ba,zan sama masa aiki a Company tunda yayi karatu.
Ɗaya side ɗin kuma nasu inna ne zasu dawo nan da zama. San…….”
Tun kafin yagama magana bombee ta rungumeshi tama manta da cewar jikinsa har sannan babu ƙarfi.
“Duk da cewar zan ce maiyasa kayi haka,nasiya musu gida tunda daɗewa,amma kuma hakan bashine zai daƙushe farincikina na abinda kayi min mahaɗin rayuwata,nima ka zamemin tsagi na gangar jikin rayuwata,wadda rashinka cikinta bansan taya zanyi tunanin cigaba da rayuwar ba ma?”
“Kiyi Addu’a da fatan Allah yabarmu tare kawai,danni kinyimin abinda komai nayimiki ma anan gaba Basai kinyimin godiya ba,domin kin daɗe da biyana.
Badan nagaji ba da mun je kinga yanda aka raba sashena ba na da,wato nasu Abdulmaleek tunda shi wancan likitan yace shima bazai koma indian ba anan zai zauna”
“Ohh hmm ya zancen maganar su da waɗancan ƴan biyunne,nidai naji suna cemin jiya wai sunyi wa baba magana(malam Ahmadu) kan cewar suna son su hilyan,shine yace su bari zayyi magana da Abbah”
“Uhm sunyi maganar jiyan da daddare,zakusha bikifah wajen shida inaga,tunda akwai nasu Maleekah da Madeenah ma,naji sunce wai duk tare za’a haɗa tunda na gidane”
“Uhm Aidama tunda naga yakoma bakin aikinsa nasan shiri yakeyi,wayaga maleekah matar gen Khmees,gakuma amaryar Khaleel ma.
Hmmm gaskiya kam za’a sha biki,gashi duk nice mai shirya komai ba”
Da sauran lokaci ai tunda ko tsaida rana ma ba’ayiba.
Komawa cikin motar sukayi suna ƴar hirarsu har suka ƙarisa sashensu.
Tun daga bakin ƙofar shiga sashennasu ta kula yanda yake aika mata wani kallo mai cikeda ma’anoni.
Bata so biyeshi ba lokacinma,saidai yanayin yanda yake ciki tasan yayi ƙoƙari sosai,dan haka bata hanashi miƙa saƙonsa zuwa gareta ba,saima taimaka masa tadayi wajen ƙarfafa saƙon yatafi yanda ake so.
Dan ita kanta idan tace bata buƙatar mijinnata da kuma jin tsagwaron kasancewa dashi to tayi ƙarya.
Wannan dalilin ne yasa ta bada kai bore ya hau,suka taka mataki na gaba ba zama abu guda a zamannasu,cikeda soyayya da kuma annashuwa.
A ranar farinciki a wajen Jabeer baya misaltuwa,dan yaune ya amsa sunansa na angon Amaryar tasa bombee,wacce akayi auren da daɗewa amma cikin gwargwamaya sai yau akai ga cimma buri na zaman taren.

**** ****

*Bayan wata bakwai*

“Ahh serious fah dagaske cikin juyawa yake Abban haidar tunda na tashi dasafe”
A zaune take akan doguwar kujera ta mimmiƙe ƙafafu wanda Jabeer yake mammatsa mata saboda kumburin dasukayi.
“Wai dagaske kike dama,hmmm saida nacemiki ki rabu dasu da wani bikinsu ki huta saboda yanayin dakike ciki,yanzu gashinan kimgama bawa kanki wahala su kowa ya ɗauke amaryarsa sun lula basama ƙasar.
Suna shirin sakaki haihuwa tun lokaci bayyi ba,ai idan har wata matsala tafaru dukkansu saisun dawo ƙasar nan a yau”
Masifah Jabeer yake har cikin ransa,yana matsa mata ƙafar cikeda kulawa.
Dariyah bombee tayi tana kama gefen ciki.
“Easy mana my man,bana tunanin haihuwa…….”
“Ohh inaga fah itace ɗakko ɗakko min zani na saka akan kujerar nan,naji abu yana zubowa ba tsayawa”
Cikin azama jikinsa har rawa yake ya ɗakko mata zanin,zuwa lokacin tana ƙoƙarin miƙewa,amma abu yagagara saboda riƙewar da mararta tayi sosai.
Zanin yasaka mata ta bayanta,tun kafim tayi magana ya kinkimeta zuwa cikin mota,a hanya yaƙira Hajiyah Zeenah ya faɗamata itada Su inna.
Direct asibitin su ƙawarta ya nufah wato dr. Rahama,dan haka tun kafin su isa ma har an shirya komai.
Suna zuwa babu bata lokaci aka shiga da ita labour,har ta galabaita sosai,banda jijjiga kai babu abinta take.
Saida suka shiga ɗakin kafin Jabeer ya dawo wajen dazai zauna ya jirasu,yana nan tsaye yana safa da marwa su inna suka iso itada Hajiyah Zeenah.
“Jabeer yaya jikinnata dai”
“Hmm wlh mommah bikinnan da akayi nasu Abdulmaleek gabaɗaya bata samu da zauna ta huta ba har aka gama,tun jiya dama take cewa jikinta yayi nauyi sosai,sannan abin cikinta baya motsi sosai,nayi tunanin gajiyace nasaka ta yin wanka da ruwan zafi ta kwanta.
To dasafe kuma sai tatashi da ciwon mara,kafin wani lokaci haihuwa tazo”
“Tabb yo ina aka san wanann lamari,kaga fah ranar yininnan sau kusan uku ina ƙiranta ta zauna ta huta a sashena,amma abu kaɗan saikaga sun turo a ƙirata,nayi faɗan har gaji,ƙarshema saina daina ganinsu.
Yanzu gashi sun jawo mata haihuwa a wata bakwai su kuma suna shan shagali koh.
Maza ka ƙirasu kace su dawo to”
“Ahah haba Hajiyah ayi haka,kibarsu suci lokacinsu,ita kuma muyi mata fatan allah yaraba lafiya kawai”
Haka Hajiyah Zeenah tacigaba da sababi innna Danejo tana dannarta,ba ita tayi shuru ba saida Dr. Rahma tafito tana murmushi tukunna.
“To Alhamdulillah ta haihu hajiya,tasamu ƴaƴa biyu mata,amma daga ita har su suna hutu,kasancewar dama jikinta a gajiye yake,sukuma yaron ƴan bakwaine basuda ƙarfi sosai,sai an basu kulawa ta musamman”
Sauran bayananta iyah Jabeer ne kawai ya nutsu yajishi,sukam tunda aka ce babu matsala murna ce kawai tabiyo baya.

*Paris*

A hotel guda suka zauna,saidai kowa da nasa ɗakin.
Dukkansu shiryawa suka yi dasafen zuwa jaga gari.
A zaune suke a irin grass field ɗinnan suna karyawa,kowa matarsa tana gefensa,sunyi sharr dasu cikeda nishaɗi.
Wayar Abdulmaleek ce tayi ƙara hilyan ta miƙamasa.
“Honey big bro yana ƙiranka”
“Da sanyin safiyar nan,yanzu kam tunda mun basu waje suma ai saisuyi cin amarci na biyu”
Dariya suka saka kafin ya ɗora wayar a kunne.
“Sannun ku newly wed,ya kuke ya kowa da kowa”
“Ahh sannu big bro kowa ƙalau yake,muna tarene muna karyawa ma”
“Uhm to inkun gama karyawar saiku juyo ku dawo,kun gajiyarmin da mata gashinan Ta haihu lokaci bayyi ba”
Saurin tashi tsaye Abdulmaleek yayi tareda zare jikinsa daga na hilyan.
Suma sauran wanda kowa ke bawa tasa matar abinci a baki kallon sa sukayi.
“Hasbunnallah garin yaya haka?”
“Kai kaga is nothing worse ta haihu lafiya ta samu ƴan biyu mata,dukkansu suna cikin ƙoshin lafiyah,amma dai dr. Rahama zata riƙesu su huta na kwana ɗaya,saboda yaran basuda ƙarfi sosai”
Wata ajiyar zuciya Abdulmaleek yayi tareda komawa ya zauna.
“Ahh thank god,da daɗi tunda ba’a samu matsala,ai abu kam hardamu yasashafa kam,wanne honeymoon zamu cigaba nephews na jiran a gida,muna nan dawowa”
Sauƙe wayar yayi yana kallon idanuwa suna jiran yayi musu bayani..
“Congratulation!!!! Anty maryam ta haihu twin yanzunnan,komawa gida kenan ya kamamu dan uban gayya yana cewa mune muka saka matarsa naƙuda da wuri,dan haka yanzu saimu koma mu kuma muyi shirin yimata bikin suna”
“Ahh Lallai bro ,indai wanann ne ai ba matsala bace,nihar na matsuma mukoma na gansu,i think yanzu can zaifi interesting akan nan,koya kuka ce”
Maleekah tafaɗa cikeda murnar jin labarin.

A kwance take akan gadon asibitin,an saka mata bargo rabin cikinta.
Bacci take kana gani kasan na hutune.
A hankali ya zauna a bakin gadonnata tareda saka hannunsa a nata.
Idonsa ya cire daga kanta ya mayar wajen jinjiran,wanda aka lullubesu da kaya masu laushi,ɗan motsin su kawai kake gani.
“Har sun ɗauke maka hankali dakaina koh?”
Tafaɗa a hankali tana tsuke baki,itama wajen da yaran suke take kallo.
“Wanene ni na isa idona ya ɗauke daga kan gimbiyata,ya jikinnaki toh?”
“Jiki Alhamdulillah kawai karfin jikinne har yanzu da saura,ya yaran lafiyarsu kalau?”
“Mommah na da inna tah lafiyarsu ƙalau,maman su suke jira da gama samun sauƙi mu tafi gida”
“Haka kasaka musu?”
“Uhm haka nasaka musu inafatan yayi miki koh?”
“Sosai Allah ya albarkacesu ya rayasu,ina fatan dai baka faɗawa su Maleekah ba koh”
“Tun ɗazu ma na faɗamusu ai dole su dawo suma suji”
“Ohh dear dabaka faɗamusu ba atleast sai ana jibi suna”
“Ahah gwanda su dawo suyi komai abinda za’ayi ranar sunan,dan daga nan har ranar hutawa zakiyi tayi”
Murmushi tayi tareda ɗaga masa kai,dan ita wani lokacin har mamakin soyayyar da mijinnata yake mata take,wanda tayi imani daga Allah ne hakan yafaru.

Babu abinda zatace sai Allah yabarta da ahalinnata,kuma yabata ikon tsayawa akan su dabada dukkan taimakonta wajen ganin sun dawwama cikin farinciki.
“Nagode”
Ɗagowa yayi daga kallon yaran ya kalleta tareda sake matse hannunsa a nata.
“Shin mai nayi miki dana cancanci wannan godiyar?,nine mai godiya gareki da kika bani Ahali maryam,a lokacin dana yanke tsammanin samunsu,ke haskece da Allah ya turomin bayan tsawon lokacin danayi a duhu.Nagode miki har fiyeda da yanda baki ba zai iya furtawa ba,fatana faranta miki da kuma kyauta muku keda Ahalina gabaki ɗaya”
Yunƙurawa bombee tayi ta tashi tareda sako hannunta a kafaɗarsa..
Sunkuyowa yayi kaɗan ta kanƙameshi a jikinta,hakan ba ƙaramin bashi dariya yayi ba.
“Karka ce komai,bansan taya zan maida maka martanin maganarka ba sai iya ta haka.
Koda ban mayar maka ba amma dolene nace

“ALHAMDULILLAH”
Da kyautar dayayimin.

Nima anan na datse alƙalamina tareda cewa Alhamdulillah.

*AFUWAN*
Kuyimin afuwa masu karatu na takure labari a kusan ƙarshe,buƙatar hakan ce ta taso saboda banida ishashshen lokaci,inaga dana tsaya ban ƙarisa ba,gwanda na taƙaiƙata labarin ya tsaya iya haka.
Nagode da nuna ƙaunarku ga littafina.
Zanyi muku sallama saikuma in Allah da ikonsa yasake haɗamu a wani littafin inshaallah.

Wassalamu Alaikum

Ga number wayata inda mai ƙarin bayani,godiya ko kuma ƙorafi duk ƙofata a buɗe take.
09035784150

_*SADI-SAKHNA CE*_

 

Leave a Reply

Back to top button