Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 61

Sponsored Links

61

*_HAMMAK KITCHEN UTENSILS

*_INA MAABOTA GAYU DA SON BURGE BAQI DA ME GIDA?_*
*_SHIN KUNSAN HAMMAK KITCHEN UTENSILS SUNA DA QAYATACCIN KAYAN KITCHEN MASU KUDI DA MASU ARHA NA WAJE DANA GIDA NIGERIA_*

*_BA IYA ZUWA SHAGO KADAI KU SIYO BA HARDA AIKAWA SUNAYI KOINA HAKAMA SUNA ADASHEN KAYAN KITCHEN MANYA DA QANANA,MASU SAUKI DA MASU TSADA,NA WAJE DANA GIDA NIGERIA,_*

*_ZAKIYI ZUBINKI A HANKALI KI KWASHI DUK ABINDA KIKESO A AIKA MIKI ABINKI CIKIN SAUKI DA AMANA DAN HAKA SISTERS KARKU BARI AYI BAKU MUN SANI MUN SHEDAR HAMMAK KITCHEN UTENSILS SUNE THE BEST👍_*

@hammakkitchenutensil
Tarauni market Abba hamisu plaza block A shop no 8
or dorayi sabon titi before gidan man b i
Wa.me/+2348067376035

 

******
Tinda suka kama hanyar zuwa gidan nasa tayi shiru Bata sake magana ba saidai idan Zeenah tayi mata ta Dan amsa ahankali tana Hana zuciyarsa bugawa ba daidaiba.

Tsaro da tsarin anguwar ya saka Bena mamakin wainda suke rayuwa a cikinta,
Main gate na shiga gidajensu DD din sai ka nuna Id card naka anshigar da sunanka,
Sunan kaantes dake qarshen sunayensu ya saka securities fahimtar gidan DD kaante suka zo Dan haka aka Bude musu suka wuce.

Daga ka shigo baka horn har saika fita Dan haka ahankali suke tafiya da motan har suka Isa gate na gidan DD Shima akwai security Daya agurin ya Bude musu gate suka shigo madaidaiciyan harabar gidan sukai parking.

Fitowa Zeenah tayi tana kallan Bena da batai niyar fitowa ba tace

“Waye zai iya rarraso baby Amnah ta yarda ta bar daddynta idan bake din ba,kinsan sarai bazata yarda tabar daddynta ba saida dubaru.

Ajiyan zuciya ta Dan sauke tareda ajiye wayarta cikin motar ta Bude ta ziro qafafunta ta fito tareda rufe motan suka nufi ciki Kai tsaye bugun zuciyarta na Dan qaruwa tareda Jin rashin sakewa.

Gioconda door din shiga main sitting room na gidan suka Bude Kai tsaye suka shigo sbd sanin password dinsa na shiga da Zeenah tayi.

Zeenah din ce a gaba kafin Bena wadda sanyin AC da qamshinsa da babu inda babusa a gidan nasa ya sata Dan lumshe rintse idanuwanta tana budesu ahankali.

Komai na rayuwarsa daban yake tin daga kan inda yake rayuwarsa da yanda yake gudanar da ita,

Palonsa babu Abinda yakeda wata kalan bayan fari milk da gold.

Bayason kaloli a komai shiyasa ko kayansa daga black sai fari sai Kuma navy blue Shima kalan Dan tanada duhu ne.

Baiji shigowansu ba sbd Yana can master bedroom dinsa a kwance Amnah Kuma tana palon cikin bedroom dinsa tana rubuce rubuce da kallan cartoon.

Waya Zeenah ta Ciro ta kirasa tana nufar kitchen dinsa Dan Shan ruwa.

A natse cikin sanyi ya dauka yaji ta iso yace ta dauko Amnah din kawai su wuce.

Har cikin palonsa ta Isa tareda Bena
Amnah na ganinsa ta taso da gudu ta fada jikin mamanta tana Kiran sunanta cikin farin ciki sosai.

Itama sake murmushi tayi cikin farin ciki tana daukanta jikinta tace

“Ohhh I miss my baby so much, please kizo muje gida daukanki nazo Yi”

Zaunar da Mummyn tata tayi ta hau jikinta tana taba dogon hancinta tace

“Aa mummy bazanje ba kema bazaki tafi ba Daddyna bayada lafiya ki zauna mu kula dashi idan ya warke saimu koma gurin su Umme tare,
Aunt Z Takoma ita Daya”

Dariya Zeenah tayi tana Jan hancin Amnah din itama tace

“Amnah din Aunt z ta girma tasan yakamata a kula da daddynta bayada lfy.”

Bena kuwa Wani murmushin ta qaqalo tana cewa

“Daddynki bayason hayaniyan kowa shiyasa zamu tafi gidan idan yaji sauki sai akula dashi din,.oya tashi muje gida Umme na jiranki Kuma ga Arabic uncle dinki nata zuwa bakyanan,kinason karatun Arabi naki ya Dena gudu?

Girgiza Kai tayi tana Bata fuska tace

“Banason ya Dena gudu Amma mummy nidai banason Abar Daddy shi Daya dazu yayi Amai fa Kuma Uncle Naseer ya kawo doctor yayi masa allura,
Cikowa idanuwanta sukai da hawaye taci gaba da cewa

“Nidai mummy to ki tsaya anan naje ayimun karatun Arabic Dina yau da gobe saina dawo ke ki tafi”

Shiru Bena tayi tareda matse fuska tace

“Banason Jin kowane magana tashi mu tafi idan na sake Jin maganar Wani ya tafi Wani ya jira I will slap your mouth.”

Fashewa Amnah tayi da kuka Wanda ya saka Zeenah janyota jikinta tana kallan Bena tace

“Meye Hakan?
Gaskia ta fada idan har baida lafiya haka sosai kaman yanda ta fada Wani zai tsaya tareda shi gaskia and it has to be you sbd ita almost 5 days Bata gida karatunta Yana rawa.

Kukan Amnah keyi sosai tareda zarewa daga jikin Zeenah tayi hanyar dakin daddynta da gudu ta shige tana qarawa kukanta qarfi.

Numfashi me zafi Bena ta sauke ranta na Dan Baci da yanda suka lalata ‘yar tasu Amma Kuma bazasu iya hanata Abinda takeso ba koyaushe daga su iyayenta musamman Daddyn nata har kakanninta su Umme shi dad kaante ma Badan daddynta da baya iya kwana biyu baizo ya tafi da itaba Shima kullum itace abokiyan firarsa idan Yana gida kokuma tana gurin dd babba Shima ta ishesa da surutunta.

Kasa cewa komai Bena tayi ta waiwayo ta Kalli Zeenah wadda itama ita ta kalla tace

“Kinsan bazan shiga bedroom dinsa ba dauko ta right??
Kece matarsa kece Zaki iya shiga so please je ki fito da ita mu tafi inada abin Yi gida da sauri.”

Kallan hanyar dakin tayi ta Dan sauke Kai taja numfashi tareda dagowa ta sake kallan Zeenah tace “ko Zaki kira wayansa ne”

Zeenah na ganin Hakan ta miqe ta nufi Kofa zata fice Bena tayi saurin riqota zatai magana suka Jiyo takunsa ahankali tareda Amnah ya fito daga bedroom din zuwa palon.

Zeenah ce ta fara juyowa tana kallansa cikin kulawa tai masa ya jiki kafin ta sake magana ya katsesu da cewan

“Meyake faruwa anan?”
“Amnah na Kuka me ya faru?”

Sai alokacin Bena ta juyo a hankali cikin nutsuwa ta Dan dago ta kallesa daga ita har shi lokaci Daya zuciyoyinsu sukai nauyi ya dauke Kai Yana sake maimaita tambayansa.

Cikin sanyi Bena tace masa “Ina wuni”

Amsawa yayi a gajarce Yana kallan Amnah Dake jikinsa ta lafe yace

“Angel kije gida zanzo gobe na dawo dake,ok??

Maqale kafada tayi tareda sake kwantawa jikinsa cikin kunnensa qasa qasa tace

“Daddy kace mummy ta tsaya anan to”

Idanuwansa ya jefawa Bena wadda tana ganin Hakan tasan me Amnah ta fada ta Maida kallanta kan Amnah zatai magana ya gyadawa Amnah Kai ahankali tareda miqawa Zeenah ita yace “kuje gobe zanzo na tafi da ita.”

Bena na ganin Hakan tayi saurin yin gaba zata wuce Amnah tayi saurin juyowa ta Kalli daddynta
Hannu Daya ya saka ya zagayo shafaffen cikin Bena yayo baya da ita ta jingina da kirjinsa.

Wani murmushin Dadi Amnah ta sakeĀ  suna ficewa tace

“Mummy ki kula da daddy fa kafin nadawo gobe”

Suna ficewa ta Zame da sauri tana waiwayowa ta kallesa tace “zan bisu”

Bai kalleta ba ya juya ya koma bedroom dinsa Yana cewa

“Ki Jira sai goben da Amnah tace”

Da sauri tabi bayansa zatai magana sbd suna wucewa batada yanda zaayi ta fita anguwan sbd securities bazasu bari ba
Bata ankara ba ta bisa har cikin bedroom dinsa tana masa magana suna Kaiwa tsakiyan dakin ya juyo daidai ita Kuma ta zo daf dashi suka tsaya da sauri tana kallan Dan mitsitsin space din Daya rage kirjinsu ya hade.

Shima mayun idanuwansa ya Kai ya Kalli space din Wanda ko fadin batir bazai shiga ba hakama dasun hade din akwai yiyuwan zazzabinsa ya qaru.

Wani siririn yawu ta hadiye tana dago da idanuwanta sama ta kallesa tareda Dan yin baya ahankali ta janye bayan sun shagi numfashin juna.

Juyawa tayi ya fice daga dakin ta koma Palo ya zauna sai alokacin ta Tina da wayarta na mota da handbag dinta Dan haka dai tana tsaka me wuya.

Zaune take shiru a palon daga ita sai makekiyan flat screen tv dake Aiki ba murya sosai can qasa qasa Kuma cartoons ne keta playing Wani bayan Wani a Netflix.

Time na sallan magrib ya sakata miqewa ta rasa ina zata alwala ta taga Wani kofan bedroom din ta Bude ta shiga ta fada toilet tayo alwala Dayake akwai direction na alkiblah sai kawai ta tayarda sallanta.

Koda ta gama qin fitowa tayi tayi zamanta tana tinanin Abinda zata fadawa su Umme da dd babbanta idan takoma bayan ta kwana daya anan.

Saida time na ishai yayi ta miqe tayi abarta tana idarwa ta fito sbd Yunwa yakeji Kuma bazata iya takura kanta da yunwar ba.

Ga mamakinta abinci ne a dining din Jere da alama order dinsa Akai Amma ganin tsadaddun food wormers na gida ya sata tinanin daga KAANTES ne Kuma Zeenah ce ko Umme ta Aiko da abincin.

Zaunawa tayi ta zuba abincin
Tana fara ci taji yaji a abincin take ta miqe tabarsa ta nufi kitchen tana tabbatarda girkin Zeenah ce tayisa sbd har lokacin Bata iya girki ba kokuma a ankaw sabuwar me Aiki gidan wadda batasan baa cin yaji Sam a abincin gidan ba bare wannan baturen gidan da aka kawowa.

Ruwa me sanyi Tasha a kitchen din Dayake ita bawai yaji Yana damunta bane sosai ko rikitata kawai dai Bata taso inda ma zataci abinci me Dadin da har zaa saka musu yajin bane to Kuma tana shigowa kaantes itama dabi’an rashin cinsa da sonsa kwata kwata ta shigeta.

Tana Shan ruwan dauko fresh orange drink da chocolates drinks dake cike da double door fridge din da duk aka cika sbd Amnah sbd ta tabbatarda bashine yake shansu ba.

Fresh orange drink din Tasha da cookies masu shegiyan tsada taci ta koshi ta koma dakin data fito sbd bazata iya zama palon ba Wani irin rashin sakewa da bugawan zuciya takeji.

Shiru shiru taga har 9 tayi Dan haka batada zabin bayan shiga toilet ta Saba da wanka data dawo Aiki Dan haka a takure take tin dazu.

Toilet din akwai komai duk da alaman baa amfani da dakin saidai kullum me aikinsa yazo ya gyare koina ya tafi.

Da Jo Malone body wash dinsa dake toilet din tayi wanka tareda wanke baki da mouth wash dinsa ta Ciro towel din gidan dasuke duk manya ne irin na Maza ta dauro ta fito tana kallan doguwan rigarta datake tinanin yanda zata mayar da ita jikinta ta kwanta.

Kofan dakin taji an Bude ta juyo da sauri tana Dafe towel din da yayi mata nauyi ta Kallo kofar tagansa Dafe da kirji Yana Tari ahankali idanuwansa jajir Yana nuna mata tazo ta duba kitchen dinsa idan akwai taimakon da zata iya Basa duk da wannan yajin baiyi azabar wancan ba Amma tsoron azaba irin wancan tasa hankalinsa ya tashi sosai.

Faduwa gabanta yayi tana Dafe kanta sbd tayi niyar dauke abincin sbd kada ya ci Amma ta manta shaf.

Nufosa tayi da sauri ta fito yabiyo bayanta Yana Dafe da kirjinsa kunnuwansa na juyawa kaman zasu tsinke da azaba.

Littafin ZAFIN KAI na kudi ne akwai regular akwai vip pay at 09033181070

##MAMUH#
#DEBENA
#SAFNAH
#ABABA
#TOO HOT
#ROMANCE

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button