Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 59

Sponsored Links

**********
Zaunawa Zeenah tayi kan couch Ahankali tana Dan kallan Bena datake zaune kan gado tana duba wayarta Dan kawar da Abinda takejin Yana Neman saka zuciyarta nauyi.

Wayar safnah Zeenah ta dauka ahankali tareda miqewa ta nufi Kofa sbd taji bazata iya daga wayan Safnah din gaban Bena ba.
Palo ta dawo ta zauna ahankali tareda daga wayan.

Cikin sautin nutsuwa da bayyanarda damuwa da rashin hakuri Safnah tace

“Ina buqatan address na gidan D zanzo Ina buqatan ganinsa I’ve been calling Him Amma baya dagawa.”

Cikin nutsuwa Zeenah tace

“Bamu gaisa ba ai tukuna ko?”

Qaramin tsoki Safnah ta sake a boye kafin a fili ta Dan sauke numfashi Mai sanyi tana sassauta dacin zuciyarta tace

“Sorry Sis na manta ne sbd hankalina Yana kan D gaba Daya Ina san ganinsa sosai kafin na bar Lagos din gobe,ya kike?
Ya service?
Nima inshallah next year Dani zaayi.”

“Fine Alhmdllh,barka da dawowa to.” Zeenah ta fada tana Jin zuciyarta batajin Safnah da yayanta tafi jinta a ‘yar uwarta kawai.

Sake tambayarta address Safnah tayi Zeenah din datasan bazai yiyuba ta Bata address na Nan gidan bayan Bena na gidan Dan haka ta Zame taqi fada mata qarshe ma ta sanar da ita gobe zai tafi so babu buqatan sanin address Kuma ‘dayan matarsa na gidan.

Kalaman Zeenah sun sosa zuciyar Safnah sosai Dan haka cikin baqin ciki da radadin zuciya ta daure sukai sallama kawai tayi jifa da wayarta tana Jin kanta na daukan zafin wai matar D din na gidansa tareda shi.

Tsoki taja Mai qarfi tareda daukan wayarta ta fasa kwana garin take tasa Akai mata booking ticket na tafiya cikin Daren.

*Bena kuwa bayan ficewan Zeenah daga dakin numfashi ta sauke ahankali sbd ta Dade da mantawa ba ita kadai bace matarda aka aurowa DD ba,
So Daya taji zancen ta sani Kuma tin daga ita har waccan din babu wadda ke gabansa yasaka ita kanta mantawa takeyi da akwai aurensa akanta bare wadda Baa Gani.

Dawowan matar tasa na nufin zai zama magidancin gidansa Dan haka dole tana buqatan kame kanta tinda waccan yar uwarsa ce ta jini ita kuwa tasani darajan Amnah takeci wadda itama duk ranarda ya gano ba itace ta haifeta ba tsanarta zaiyi ita.

Tashi tayi tashiga toilet tayo Abinda zatai ta fito ta shirya cikin kayan bacci masu Dan kauri sbd sanyi tayi kwanciyarta tareda rufe idanuwanta ahankali tana jiran bacci.

Zeenah kuwa bayan gama waya da Safnah da DD ta tsaya palon sukai magana sama sama akan yawan yawonsu da Daren dasuke Kaiwa a waje yace su Dena.

Duk da Bai fito ya fada ba tasan Kila akan Bena ya fada Hakan sbd ita yasan ta Saba a can foreign countries tana dare sosai a waje bakuma komai bane tinda ko saurayi batada shi bare ayi tinanin akwai Abinda yake shiga tsakaninsu.

Bayan sunyi sallama ta shige Shima ya Danyi mintina yana kallan kofan bedroom din nasu kafin ya Dan dauke Kai ya miqe ya shige.

Wanka ya tube yayi kafin ya shirya cikin white Balmain pyjamas ya jikinsa na tashin sanyin qamshinsa ya Kwanta.

Washe gari flight din 10 zai bi Dan haka 8 ya fito a shirye cikin D&G black shirt da Balmain slim jeans sai Fcap din flexfit me tsadan gaske.

Zeenah ce ta hada masa simple light breakfast ya zauna Yana cikin ci ahankali cikin nutsuwan
Bena ta Bude kofan bedroom dinsu ta fito fuskarta fresh sanye cikin kayan baccinta Riga da wando da suka bayyanarda shafewan cikinta kanta ko hula babu slippers ne kawai a qafarta ta nufo dining din cinyoyinta na daukan ido sbd lafiyan brown skin dinta.

Saida ta iso daf da dining din idanuwanta suka gansa zaune Yana jifanta da Wani irin Kallon da mayun idanuwansa.

Cak ta tsaya sbd duka tinaninta yaje akan ya Riga ya tafi.

Kasa juyawa tayi ta Dan dago ahankali ta Bude baki tace

“Good morning”

Sai Daya dago yayi mata kallan seconds kafin ya Dan dauke kallansa akanta ya amsa Yana cigaba da Shan tea dinsa.

Kokarin juyawa takeyi tabar gurin taji muryansa a natse yace

“Zaki bini zuwa gida yau din….

Dakatawa tayi daga tafiyan datakeyi ta juyo ahankali cikin mamaki da sanyi tace

“Yau??

Tasowa yayi daga dining din sbd ya gama ya ratsata ya wuce qamshinta na Dan shiga hancinsa ya nufi kujera ya zauna Yana duba agogon bighead Bottega veneta dake daure a hannunsa.

Rasa abin fada Bena tayi sbd mamaki da fargaba ga Kuma taro me mahimmanci da dd babba ya sakata halarta yau a matsayin me wakiltan department na account din kamfanin kaantes ita da Fahad Yana Nan zuwa Lagos din yau ma,
Yanzu gashi Daddyn Amnah na fadan haka Daman tasan zai iya faruwa Hakan tinda Amnah tayi maganar tanason zuwanta.

Cikin sanyi ta Tako ta iso gurinsa tana sake Dan shiga sanyin jiki a natse tace

“Akwai serious business meeting na kaantes da zanje tareda Fahad Yana hanya and gobe ne Ina buqatan tsayawa please.”

Ambatan sunan Fahad datai ya sakasa Dan waiwayowa ya Kalli gefenta Kai tsaye yace

“Flight na 10 zamu bi.”

Yana fadan Hakan ya miqe yayi bedroom dinsa ya shige.

Zeenah dake zaune tana jinsu kallan Bena tayi cikin kulawa tace

“Kije ki sake rokansa kina buqatan tsawa gaskia wannan meeting din,
Babban opportunity ne karki wasa da Hakan and dd babba zaiyi fushi idan kika koma batareda attending haduwan ba,
Kije ki sake Basa hakuri dole Zaki tsaya gaskia.”

Jin tayi jikinta ya sake mutuwa sosai Sam itama Bata fatan ta tafi tabar wannan aikin datai kusan sati tana wuni da Raba dare aikinsa.

Numfashi ta sauke ahankali tareda nufan dakin tana Isa tayi knocking Ahankali.

Jin shiru ya sakata Bude kofar da hannunta ta tura ta shiga a hankali
Yana zaune Yana amsa waya ahankali cikin rashin hayaniya
Ganinta ya sakasa sallama da Safnah din a hankali tareda ajiye wayar ita kuwa Jin tayi kirjinta yayi nauyi tana Neman kasa mgn sbd fahimtar da matarsa yake wayan.

Boyayyan numfashi ta sauke ahankali tareda daidaita kanta ta dago Bata kallesaba ta fara rokansa akan yabarta din.

Kame fuska yayi sbd baya buqatan Jin zancen nata.

Ganin yaqi ko kallanta ya sakata sake qarasowa daf da shi zatai magana ya dago ya zuba mata fararen idanuwansa
Take ta rude tafara kokarin magana wayarsa tayi ringing.

A tare suka duba wayan sunan Nass ta Gani ta fahimci Naseer ne Kuma tafiyan zasuyi kenan.

Daukan wayar yayi ya Dora a kunnensa cikin nutsuwa yace ok kawai ya kashe wayan ya ajiye.

Miqewa yayi zai wuceta take idanuwanta sukai narai narai sai hawayen data manta Yaya ake tsiyayosu ma.

Dakatawa yayi tareda kallan hawayen nata ahankali ya Kalli fuskanta datai qasa da Kai.

“Meye wannan?
Ya fada Yana kallan hawayenta.

“Shi wannan din Kuka ne ko meye?”

Shiru tayi takasa dagowa

Ajiyan zuciya ya sauke me sanyi kafin ya rabata ya fice daga dakin a sukwane ta biyo bayansa ta fito itama

Yana fitowa Palo ya tadda Naseer ya shigo Dan Haka ya juya ahankali ya koma Dan dakatar da ita daga fitowan sbd kayan jikinta
Yana dowowa tana Sako Kai Dan haka sukai Wani irin hadewan data sakata yin baya ya riqota zuwa jikin bangon kofan Yana zagaye da ita ahankali.

Numfashi me Dan qargi ta hau saukewa tareda kasa dagowa sbd yanayinda suke.

Jin jikinsu manne da juna ya sanyata Bude bakin kasalance batareda ta dago ba ta furta “please kabarni na tsaya”

Qamshin mouthwash dinta ne ya shiga hancinsa tareda numfashinta sbd kusancinsu Dan haka ya juyo da idanuwansa ya Kalli bakin nata tana sake motsasa ahankali gurin rokansa.

Zare hannuwansa yayi daga jikinta tareda janyewa sbd zafin dayaji Yana shigarsa.

Bai waiwayo ba ya gyada mata Kai kawai tareda ficewa daga dakin.

Kafin ta sauke numfashi da ajiyan zuciya ta fito tini suka fice shi da Naseer Dan haka Koda ta fito sun fice.

Ajiyan zuciya da numfashi ta sake saukewa tana godewa Allah cikin ranta sbd babu Abinda yakeda mahimmanci agunta yanxu ta bangaren cimma buri irin kammala komai ta koma ta tsayu da qafafunta tareda taka matakin nasarar da zata Siya yancin mahaifiyarta da kudinta ta dawo hannunta.

Breakfast tayi sama sama sbd Jin duk jikinta yayi sanyi Kuma.

Tana gamawa ta shige wanka ta shirya ta fita Aiki sbd yanzu kam bazata ringa fashi ba a yanda takeso tinda sun kusa gamawa su tattara su koma gida.
#MAMUH#

ZAFIN KAI
Chapter: 60
_Arawabooks@Mamuhgee_
60
Dulkaninsu ranar sal yamma suka dawo kowa a
gajiye Dan haka order abinci sukal Koda aka kano
sunyi wank da salloli abincin kawai sukaci Bena ta
fara Wani aikin a laptop Zeenah ma kusan alkin
tafara du da Rabi wayoyi ne takeyi.
Sal dare sosai Bena ta gama taje ta kwanta kanta na
tananin chwo,
Washe gari da kanta tal
I dauko Fahad
daga airport Dayake sun latti Kal tsaye gurin meeting
din suka wuce,
Duk yanda Bana take tinanin lamarin ya wuce Nan
sbd Manyan mutane ne da lyakacinta jinsu da
ganinsu a media,

Leave a Reply

Back to top button