Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 77

Sponsored Links

77
Koda gari ya waye labarin kwanciyar DD kaante da Bena Asibiti ya yadu a family din kaantes na kusa Dana nesa Dan haka wainda suke kusa tini suka fara zuwa dubasa.
Dd babba Yana komawa gida ya saka Abbakar a Hana labarin fita ko kadan sbd tinda Doctors suka fara maganar zargin qwaya a jininsa yan labarai suna ji zasu yada labarin mutincinsu da sunansu zai tabu hakama Shima DD din nasa mutincin da sunan zai iya lalacewa a idan mutane da Manyan gasa abokan huldarsa Dan haka a Hana ko kalma Daya fita ta cewan ma
Yana Asibitin kwance ba lafiya.
****Safnah da momy Suma kwanan zaune sukai a dare babu Wanda bacci ya gifta idanuwansa,
A zaune qyam suka kwana |do Bude cikin taraddadi,tashin hankali da zaquwa suka Kai har safe suja jiran ta inda labari zai dawo musu.
Babu Allah a cikin ransu suna zaune Akai sallar Asuba aka gama Basu tashi sunyi ba Safnah idanuwanta sunyi Wani jajir da kumbura sbd kukan baqin ciki da zuciyarta
Datake Jin ta qarasa bushewa Dan kuwa wallahi bazata yarda tayi biyu babu ba a yanzu da suka Kai wannan matsayin na Bena ta Riga halasta ga DD kaante.
Sai da gari yayi Shar har karfe 8 Saura basuji
Wani bayani ba suka tashi sukai sallah
Suna gamawa ko addua Basu tsaya Yi ba suka mige Safnah tafara kaida kawo hannuwanta na rawa zuciyarta na qara konewa da bushewa tareda daukan zafi tana rasa ta inda zasuji meyake faruwa.

Momy kuwa babban tashin hankalinta da zafin da kanta ya dauka har Wani hayaqi takeji kaman Yana fitowa kunnuwanta na Abinda zai iya biyowa baya idan su Bena Basu mutu ba.
Komai ya taru ya lalace musu a mummunan yanayi da hanya mara bullewa matiqar su
Bena suka rayu,.
Qarshensu ne zaizo a wulagance su rasa komai su qare inda basason garewan sbd komai a fili zai iya bayyana,
Na farko rashin mutuwar su na nufin zaa gano akwai qwayoyin drugs a jinin DD harma da cocaine suka hada duk suka zuba masa Dan haka akwai babbar matsala idan ya rayu,
Na biyu ma Bena idan ta rayu Hakan na nufin dole Safnah zata bar DD Wanda barinsa shine zai Tona ya bayyanarda ita din ba ‘yar bulama bace haka zalika mutuwar hajiyarsa zata iya dawowa sabuwa ga Rabi tasan sirrinsu suna bugatan itama aikata inda bazata zata tafi da sirrin a cikinta har abada ba dawowa.
(100
Dan haka rayuwar su Bena itace qarshen tasu rayuwar.
Wani mummunan zufa ta share tareda kallan
Safnah wadda itama momyn ta Kallo tinani da momyn takeyi shi takeyi sak.
Babu Wanda ya iya cewa komai sbd babu me nutsuwa ko hankalin furta kowace kalma saisun ji labarin halin da ake ciki.
Har kusan goma na safe ba labari Dan haka
Safnah data kasa zama tana tsaye Tim asubar ta dauki wayarta ta saka Kiran umme Kai tsaye zuciyarta na harbawa kaman zata fado. Momy na Jin ta saka kira ta sa a speaker tayi tsit ko numfashi batason ja sbd fargaban
Abinda zasu jl.
Sai da wayar ta kusa yankewa Umme ta dauka tareda sallama a natse cikin sanyi.
Wani busashen yawu Safnah ta hadiye tareda
Bude baki tana Dan dedeta muryanta dake kokarin yankewa tace
“Ina kwana Umme?
Ya gida yasu Zeenah?
“Lafiya kalau Safnah,ya gidan ya momynki?
Lafiya kalau Umme,Daman Umme nace D kunyi magana dashi kuwa?

Wayoyinsa duka Basa zuwa na kira Naseer
Shima tasa a kashe banajin nutsuwan zuciyata game da rashin samunsa Umme.
Numfashi me dumi Umme ta sauke sbd sai alokacin ta Tina ma Safnah ma nada haqgi akansa Daya kamata tasan meya samesa Dan haka ta Dan sake yin sanyi a natse tace
“Safnah wIh hankula ne suka dauku sbd tashin hankalin da aka shiga na Abinda ya samesa shiyasa aka Manta shaf baa nemeki an sanar dake ba,
Yana Asibiti Tim tsakar dare jiya shi da Bena
Basu da lafiya arziki sukai wuta ta so kama gidansa dake highbridge Kuma ba.
Umme Bata garasa ba Safnah ta Yanke jiki ta zube qasa idanuwanta na juyewa.

Momy ma zubewa qasan tayi tana Neman somewa Amma tayi qarfin halin daukan wayar da Safnah ta saki ta Dora a kunnenta muryarta na yankewa da qyar ta iya cewa
“Shock ya saka Safnah sumewa itama gatanan zuwa zata kawota Asibiti”
Ko amsata Umme bataiba ta kashe wayar tareda migewa tana Gani dishi dishi sbd tsabar tashin hankali ta nufi dakinta a rikice ta janyo drowan gefen gadonta ta Ciro wata allurar jininta Data ke Jin kaman ya Haye zuwa 200+ take tayi wa kanta tana zubewa qasa tana fidda numfashi da sauri sauri Dan dawowa daidai.
Kusan fiyeda Rabin awa ta dauka kafin ta dawo daidai ta tashi jikinta na fizga da tashin hankali da baqin ciki ta nufi Palo Kai tsaye kitchen ta nufa ta dauko ruw ta zubawa
Safnah wadda koyaushe ta some kaman wadda ta mutu take.

Safnah na farfadowa momy ta kalla itama momyn ita take kalla tana cewa
Tashi mu fara kokarin hada kan Abinda muka samu dole mu bace bat mubar qasar gaba
Daya wIh bazanje prison ba.
Cikin bagin ciki da rasa abin fada Safnah tace
“dan munie prison mun samu sassauci da sauki kenan,
Kin manta momy kisa fa mukal,
Hajiya fa muka kashe,
Kina tinanin Dad zai gyale mu ne?
Su kaantes kina ganin zasu bari ko prison din akaimu?
Wih kashemu zaayi kisan wulaqanci Kuma,
Bazan yarda naje prison ba yanzu bare lahira lokacina baiyib,
Muna guduwa ba wahalar bincike zaa Gane mune mukai komai muka gudu Dan haka wIh Neman mu bazai musu wuya ba.
Idan Bena sungi mutuwa to dole Bena tabarsa bari na har abada ta Hakan ne asalina zai rufu
Kuma ta Hakan ne DD da kaantes bazasu taba samun nutsuwar yin bincike sosaiba a komai zasu mayarda hankali gurin Nemanta da tinanin inda ta bace bat babuta ba labarinta har abada haka zalika DD dole nice zanci gaba da zama matarsa.
Jajayen idanuwan momy ta zubawa Safnah tana juya zancen cikin kanta to Amma ta
Yava zasu batar da Bena tinda shegiyar taqi mutuwa a Karo na biyu.
“Kasheta zamu sake Vi” inii Safnah da idanuwanta suka gama rufewa fiyeda kowane lokaci sbd yanzu sun Kai karshen karshe na idan suka rasa wannan Karan to sai lahira ko prison.
Katseta momy tayi cikin zurfafa nata tinanin tace “Bazamu kasheta ba sbd munyi na farko babu nasara,
Munyi na biyu ba nasara
munayin na ukun Nan to tabbas babu shakka kamamu zaayi a saukake.
Shiru Safnah tayi sbd kota yayane dai dole sai sun samowa kansu mafita kafin DD ya farfado duk da Kila zai iya kwana biyu Bai dawo daidaiba kuma zaiya farfadowa kowane lokacin Dan haka Basu da lokacin batawa har mummunan kaddararsu tazo ta samesu suna
zaune.
Tinani suka fada cikin tashin hankali da rashin nutsuwar zuciya da gangar jiki kansu kaman zasu kama da wuta sbd tension.
Safnah ce tinanin da Abinda taketa gujewa yaketa dawo mata cikin Kai Wanda ko sunan ta fada cikin kanta bugawa kan yake Neman Yi sbd tsoro da firgici me tsananin gaske hakama zuciyarta sunansa kawai Neman tsayawa bugawa takeyi Dan duk yanda takai ta goge a duk Wani aikin rashin Imani har gobe Ababa tsoronsa da shakkarsa a cikin jininta yake ba ita kadaiba dukkaninsu yayansa.,
Ababa sunansa kadai jikinta rawa yake dauka idan ta Tino Amma Kuma tana ganin lokaci yayi da zata Kai Kanta gabansa,
‘Idan har zai iya sauya sumayyah data mutu da Benazir ya boye mutuwarta ya bayyanarda benazir matsayin wadda tayi cikin shege ta haihuwa duk akan kudi gashi kudin kaantes dinma dayake Jira ba samu zaiyiba sbd Anne data lalata masa komai Bai saniba tarko sukai masa da zai Kamasa a lokacinda baida gurin tsira.
Dan haka lokaci yayi dazai San Abinda su
Anne sukai masa,
Yasan babu Abinda zai same daga kaantes,
Zasu basa kudin da ko Basuyi yawan Wanda zai samu a Kaantes ba ta xasu kusa sbd ya hade a cikinsu ya tsaya tsam ya Hana bayyanar Safnah ‘yarsa ce kota halin Yaya.
Momy shiru tayi lokacin da tagama sauraran
Safnah da wanna sabon plan din nata da tabbas ko ita da batasan Ababan ba tana Jin tsigan jikinta tashi a duk lokacinda Safnah take fadar halayensa da taurin zuciyarsa cikin tsoro da kyarma.
Idan har yanda Safnah ke fadan Ababa Tim baya haka yake to shigowarsa cikinsu komai zai tafi musu a daidai sbd da alama zaifi su sanin hanyoyin kawowa Kansu nasara,idan ma dukiyar Bulama yakeson a raba daidai dashi bayan sun kammala qwashe komai zasu raba din matiqar xai fiddasu a cikin motsalan dasuke ciki dumu dumu,
Haka zalika shine kadai yakeda mukullin juya rayuwar Bena a duk yanda yaso sbd Annenta
Datake hannunsa wadda zata iya Koma akanta,haka zalika su Kuma kaantes yanzu
Bena ce mukullin dazai iya juya raywarsu da ita sbd tsananin son Dasuke mata hardai yanzu da zasusan ba itace ta haifi Amnah ba.
Momy da lamarin da tsarin sukai mata shegen
Dadi ta saki Wani dariyar samun sanyin zuciya tace
“Idan ba Bai yarda ya dawo cikinmu an samar da mafita ba to Shima watan tonuwar nasa asirin ne ya tsayu,
Daga lokacinda kaantes suka gama sanin ba
Bena ce ta haifi Amnah ba to alokacin zaayi tariyar zancen yanda yayi ha’incin sauyawa
Amnah mahaifiya Yakuma rusa rayuwar
Bena,haka zalika jinin sameerah a hannunsa yake Dan haka daki day zaa Bamu a prison.
Cikin zurfafa tinani da ‘dacin zuciya Safnah
tace

“Ababa babu Abinda bazai iyaba akan kudi,
Jin Abinda su Anne da Bena sukai masa zaisa ko bamu buqaci Basa kudi ya fiddamu a wannan halinba zai iya kashe mana Bena har lahira cikin sauki.
Amma a yanzu banason Bena ta mutu sbd
Anne,
Amma dole zata bar rayuwarmu data DD har abada.
##MAMUH#
#ABABA
#SAFNAH
#MOMY
#SHEGU/MATSIYATA

Leave a Reply

Back to top button