Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 76

Sponsored Links

76
Hankalin tashe cikin toro da firgici Naseer da
Zeenah din suka nufi Asibiti dasu ba tareda sun tsaya sanar da securities komai ba kawai dai Naseer yace musu akwai oven ya kama da wuta a gidan please suje su kashe shi asibiti
zaije.
Yana fada musu yaja motar ya fice da gudu yau Yana karya doka
Su Kuma securities din Kai tsaye gidan suka nufa tareda Isa kitchen suka kashe wutar
Basu tsaya bincika komaiba sbd batareda wata damuwa ko matsala ko zargin Wani abin ba yafada musu Dan haka Suka dauki Hakan a tsautsayi suka rufe gidan suka koma gate kawai. Asibitin kaantes ya nufa dasu cikin mugun gudu kankanin lokaci yakaisu Asibitin cikin gaggawa Aka fito aka karbesu su duka biyun aka shige emergency dasu ta sama.
Ana karbansu aka shige dasu Zeenah ta fidda wayarta cikin tashin hankali da tsoron Daya mamaye zuciyarta ta Nemo numbern Umme ta saka kira.
Harta katse Bata daga ba Dan haka sai Bata sake Kiran ba Kuma Bata nema kowa ba suka fara zarya ita da Naseer kowannensu cikin shiga tinanin da jiran tsammanin dayafi komai azaba sbd matsuwa suje menene matsalar.
Yawo suka ringa yi Zeenah ta kasa zama babban tashin hankalinta da tsoranta idan ba
Wani mummunan al’amarin ne ya samesu ba,
To Amma da alama dai love sukai making a
Karan farko duba da yanayin da aka samesu. Naseer babu Abinda yake ransa da qwaqwalwansa face Jin D ya farfado lafiya.
Ko su Bena dasuke ciki a kwance Basu Kai su
Zeenah din Shan azabar zuciyar ba sbd tashin hankalin Dayake ransu da tsoro yasa idanuwan
Zeenah har sun fara dark circles kanta sai sarawa yakeyi.
Karfe biyu da kusan arbain Umme ta farka shiga toilet kaman ance ta duba wayarta taga misscall din Zeenah,
Da mamaki ta Kalli time na Kiran taga kusan 2 na dare akai Kiran.
Dakatawa tayi daga shiga toilet din ta Kalli dad kaante dake kwance Yana bacci cikin lafiyayyan gadan dakin nasa sai kawai ta saka
Kiran Zeenah sbd taii idan ko jikin Amnah ne data ke da alaman zazzabi ya tashi. Ringing Daya Zeenah a ta cafki Kiran ta daga
Umme na Jin muryarta tasan Bata gida Kai tsaye tace
“Zeenah lafiya kuwa?
Ina kike?
Jikin Amnah ne?
Ya Akai??
Katse ummen tayi da sanar da ita Kai tsaye suna Asibiti da DD da Bena.
Tana fadar Hakan Umme ta Bude murya da kyau tace
“Dawood dai kike magana ko kuwa?
Bena ma?meya same su?
Yaushe?

Meyake faruwa ne? innalillahi.
Bude idanuwa Ras dad kaante yayi Jin Abinda ummen ke fada murya a sake.
Tashi zaune yayi bacci na sakinsa babu Wani sauran magagin bacci ya kalleta yana cewa
“Lafiya?
Meya faru?
Su waye a Asibitin??
Hankali tashe Umme ta juyo ta kallesa tace
“Dawood da Bena ne a asibiti basusan inda kansu yake ba.”
Agogo ya kalla da sauri kafin ya yaye rufar jilkinsa Yana saukowa kan gadon ya qaraso gabanta ya karbi wayar ya saka kunne ya sake tambayar Zeenah da kyau
Ta tabbatar masa da suna Asibiti dasu
Dawood din.
Kashe wayar yayi tareda komawa bedside ya dauki tasa wayar ya fito Palo Yana Neman numbern Abbakar.
Umme ma fitowa tayi ta koma bedroom dinta ta cania doguwar rigar baccinta zuwa doguwar Abaya da mayafi me Dan kauri sbd sanyin tsakar Daren da zasu fita.
Ko data fito dad kaante da Kansa zaiyi tuqi
Abbakar ma tini ya fito daga Dan sashensa dake bayan na Ubandakinsa dd babba Wanda
Shima tini Abbakar ya isar masa da sakon. Motar dad kaante tini tayi gaba tareda Umme shikuma dd babba Shima cewa yayi Abbakar ya fidda mota Suma suje Yana buqatan zuwa Asibitin jikokinsa biyu mafi soyuwa aransa suna Asibiti kwance Rai hannun Allah ana
cewa baa San meyake damunsu ba.
Qanqanin lokaci ya kawosu Asibitin suna isowa kowa Kuma hankalinsa ya Dan sake
shiga damuwa sbd Jin harda wuta aka tadda
a gidan tana ci da baa je da wuri da kilama
mugun labari zaa ji kawai.
A lafiyayyan palon jiran manyansu dake can saman Asibitin suka zazzauna kowa ta girgiza qafa cikin rashin nutsuwan zuciya bayani
kawai suke Jira.
Babu Wani bayani daya zo musu sai kusan karfe 4 Dr Ashley tafara fitowa ta Kalli Zeenah kafin ta Kalli Naseer sbd sune suka taso zuwa inda take da sauri, tanason magana tana kokarin daidaita iya Abinda zata iya fadawa familyn kaantes din a gaban Naseer sbd batasan waye shi ba.
Cikin zaquwa Zeenah tace
“Dr Ashley ki fada koma meye ne wannan din kaman familyn kaantes ne sd Shine kunnuwa da hannuwan DD harma da ganinsa a Alamuransa.

Ajiyan zuciya Dr Ashley ta sake tareda kallans dd babba da ba iya cewa komaiba bayanin Kai yake jira ya gyada mata Kai alaman ta fada kawai suka saurarenta
Ta tausasa murya tafara cewa
“Ita Bena nata ciwon ba komai bane face sex na farkon rayuwarta data samu yau,
Bai Wani je mata da sauki ba ya nuna mata karfi gaskia Dan haka ta jigata ta Kuma tasha wuya sbd na farko ne so rashin saukaka mata muke kyautata zaton ya sakata kasa dauka ta Suma,akwai stitches kadan da Akai mata Dan haka ita inshallah zata farko kowane time sai a fara kulawa da ita da dinkin.”
Shiru gurin ya dauka kowa yayi tsit Zeenah da Naseer suka Kalli juna sbd sune a kusa da juna lokaci Daya kansu na Neman juyawa da
Jin wai sex din farko ga wadda ke da ‘ya.
Umme ma duk rudanin Datake ciki Bai hanata kallan Dr Ashley da sauri ba kafin ta juyo ta
Kalli dad kaante da shi Kuma dd babba ya kalla Wanda Kallo Daya zakai masa kaga babu alaman shock ko mamaki a tareda shi
Basu gama fitowa daga mamakin maganar ba da dauke wuta dd babba ya sake buga kansun da kallan Dr Ashley Kai tsaye yace
“Mun San wannan tinda ita an samu shawo kan tata matsalar Allah ya Yi mata albarka ya Basu zuria dayyaba me albarka da zanyi alfahari dasu,
Shi Dawood din nawa meye matsalarsa???
Shiru Dr Ashley ta Dan Yi Suma suka dawo da kallansu kanta batareda mamakin dd babba yagama sakinsu ba.
Shirunta ya sakasu Jin suna sake shiga damuwa da fargaba.
Numfashi ta sauke jikinta na Dan sanyi ta
Bude baki a natse tace
“DD nasa matsalar kusan ba guda Daya bane gaskia,
Na farko dai Muna kyautata zaton Shima sauke desire me garfin gaske ne a Karan farko
Daya San mace ya sakasa somewa..

Dan shiru tayi ta Dan tauna Abinda zata fada kafin ta sake kallansu taci gaba da cewa
“To Amma Muna zargin akwai mugayen qwayoyin drugs a tareda shi,
Babban tsoronmu akwai kwayan da muke
Zargi wadda idan akwaita a jini take shiga
Nan take Dan haka Kila sai anfitar dashi babu kayan awonta anan,
Muna Koda siyo kayan awonta mukai anan
Muna Yi masa aka Gane zaa soke lasisin wannan Asibitin tamu gabaki Daya, Acan zaa dubata a jikinsa akwai kaman antidote nata da akesha shi kadai yake koneta a jikin mutum idan ba haka ba zai ringa yi ne
Yana taso masa wannan qwayar.
Tsit sukai gurin gabaki Daya sbd babu Wanda ma ya Gane taqamaimai me take nufi sbd rashin yarda da Abinda kunnuwan nasu ke ji musu. Meya hada DD da qwayoyin drugs Kuma?
Bai taba muamalantar su ba rayuwarsa,
Sam shi gyangyamin irin wainnan abubuwan ma yakeyi sbd lafiyarsa,
Yaii ma kaman zai kashesa yake masa bare qwaya,ta na wannan zancen ya fito?
Dd babba Daya kasa yarda ko fahimtar Dr
Ashley din sosai ya Dan gyara zama ya kalleta yace
“Yanzu dai baa tabbatar ba tinani kukeyi right??
Yes Sir” ta fada a natse tana fatan suka tinaninsu kada ya zama gaskia.
Gyada Kai yayi a natse yace

“A bari ya farfado zamuji meya samesa da sauran abubuwan da maganar gwajin ya biyo daga baya.”
Gyada Kai tayi itama tana sake Basu tabbacin inshallah zai farfado lafiya for now dal.
Juyawa tayi tayi sauka zuwa office dinta su
Kuma suka kwasa zuwa dakin DD din Zeenah da dd babba Kuma Bena suka nufi dakinta.
Sosai ta wahala Dan haka fuskarta tayi fayau kaman wadda ta wuni a ciwo bacci yakeyi na wahala da azaba ga zazzabin gaske a jikinta
Daya dauki dumi sosai.
Shiru sukai kowa da Abinda yake ransa yana tinani.

Zeenah kasa Dora zancen cikin Kansa a takeyi wai Bena Bata taba sanin kowane namili ba sai yau,
To ya Akai ta samu cikin Amnah har ta haifeta?
Bangaren su umme ma tinanin suka shiga da damuwa duk da kaf acikinsu babu Wanda ya kama maganar wai qwayoyin maye a jikin DD sod sunsan ba Abu me yiyuwa bane Dan haka
Basu damu da wannan ba sai fatan su farfado kawai su samu lafiya daga shi har Bena din wadda itama Umme tinani ne kala kala cikin kanta game da cewan Bena Bata taba sanin kowane namiji ba sai yau da DD ya sameta a macenta.
To meye Hakan yake nuft?
Idan ana fada musu wannan zancen kenan so ake a fada musu ba Bena ce ta Haifa Amnah ba kokuwa?
Duka kowa Tara tambayoyinsa yayi cikin zuciyarsa da Kansa ya danne har asamu lafiyar su Bena din a koma gida aji gaskiyar kowa daga bakinsa, dashi da ake cewan akwai maye a jininsa da ita da akace budurwace bayan babu wadda zata taba sanin namiii har ta haihu komai shekarun da zatayi Bata sake kwanciva da Wani namiiinba bazata taba hadewa ba kaman budurwar da Bata taba sanin namijinba kwata kwata.
##MAMUH
#DBENA
#LOVE
#ROMANCE
#ABABA

* _Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button