Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 27

Sponsored Links

SAKAYAH

 

27

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

*Al’bishirunku Ma’aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma’aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken  GARKUWAR MA’AURATA*

 

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.

Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

 

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba’a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.

Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

 

 

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu’umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

 

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

 

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA

*(GARKUWAR MA’AURATA)*

 

Isrehjɗɗ. Acan Falon Moddibo kuwa zaune yake akan 2sitter hannunsa riƙe da Kofin Tea yana sha time to time zai ɗaga kansa tare da kallon agogon dake manne abango ahankali ya gyara zamansa tare da kurɓan tea dake tiriri ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan agogon  cinyarsa ya matse da ƙarfi har saida yaji jikinsa na rawa, ƙara matse jikinsa yayi sabida yadda yake jin M ɗinsa na miƙewa yana harbawa cike da zalama, ɗan gajeren tsakiya yaja, cikin sanyin murya a fili yace.

“J har yanzu baka dawo ba”.

Yayi mgnar kamar Jameel ɗin na gabansa.

Sai kuma ahankali yasa hannunsa tare da laluɓar wayarsa a aljihun sa na hagu da dama jin babu yasa yaja siririn tsaki tare da miƙewa cikin wani irin masifeffen kasala da sanyin jiki mai kashe ilahirin gaɓɓai ya nufi bedroom ɗinsa a kuma lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga tare da tsinkewa da masifaffen ƙarfi, da ƙyar ya iya ɗaga ƙafarsa na dama kana ya taka ya shiga Bedroom tare da furta.

“Hasbunallahu wani’imal wakin”.

Jin yanda zuciyarsa ke cigaba da bugawa cikin yanayin tsinkewar zuciya da sanyin jiki ya ɗauki ƙaramar wayar tasa,  kana ya dawo falon ya zauna tare da shiga Call log zai kira M Jameel sai kuma kiran Malam Arɗo yashigo wayar sa.

Zubawa screen ɗin wayar ido yayi tare da jan siririn tsaki kamar ba zai ɗaga ba sai wata zuciyar tace ka ɗaga mana kasan menene Uzirinsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da picking.

 

Acan ɓangaren Ummi kuwa zaune take a falonta kan kujera 3sitter tayi ta tagumi da duka hannunta biyu, kana ta tsirawa waje ɗaya Idanu yayin da ƙirjinta ke bugawa da masifar ƙarfi  zuciyarta na tsinkewa yana bada sautin dif-dif-dif lokaci ɗaya taji wata muguwar kasala na rufe mata jiki haka nan take jin zuciyarta na tsinkewa.

Jiki a mace Asma’u ta fito daga kichen hannunta riƙe da Plate ƙara sawa falon tayi Idanunta akan Ummi data zabga tagumi ta zauna akan 1sitter tare da cewa.

“Ummi har yanzu baki kwanta ba?”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana ta gyaɗa mata kai tare da cewa.

“Eh Asma’u ban kwanta ba”.

Cike da kulawa Asma’u ta ɗaga kanta tare da kalli agogo, tare da cewa.

“Ummi kalli fa har sha ɗaya ta wuce me kikeyi afalo ke kaɗai shiru ga Abban mu yashiga tun ɗazu”.

Lumshe Idanu Ummi tayi still zuciyarta na tsinkewa kana tace.

“Babu”.

Numfashi Asma’u ta fesar tare da ajiye cokalin dake hannunta tace.

“Toh Ummi ko dai baki da lafiya ne?”.

Kallonta Ummi tayi tare da girgiza kai.

“Lafiyata ƙalau Asma’u”.

 

“Ayyah Ummi am to mai yasa baki kwanta ba kin zauna shiru ke kaɗai dubi yanda kika yi tagumi da hannu duka bibbiyu”.

Cewar Asma’u.

 

“Ban sani ba Asma’u ba wai bani da lafiya ba amma ina jin jikina wani iri bai min daɗi ba ina jin zuciyata na tsinkewa sannan ga wata kasala data rufe ni”.

Ido Asma’u ta zuba mata kamar mai son gane wani abu sai kuma tace.

“Toh Ummi ki riƙa maimaita Hasbunallahu wani’imal wakin mana kuma may be rashin bacci ne kinga jiya kwana mukayi muna hira ba kisamu kinyi wadataccen bacci ba, sannan yau da safe ma baki samu kinyi wani ishesshen bacci ba”.

Gyara riƙon da taiwa plate ɗin tayi kana taci gaba da cewa.

“Har yanzu ma baki samu kinyi Ummi, kiyi ƙoƙari kije ki kwanta Insha Allah zakiji dama dama”.

Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.

“Toh ki maida Plate ɗin kichen idan kin gama sannan ki rufe ƙofar kichen ɗin kana kizo ki rufe mana ƙofan falon”.

Kai Asma’u ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

Ta mike tare da ajiye Plate din ta kife Sauran abincin sannan ta rufe ƙofar tare da murza mukulli ta dawo.

Still zaune ta samu Ummi tayi tagumi.

Cike da kulawa tace.

“Ummi kije ki kwanta dan Allah kiyi baccin”.

Ahankali Ummi ta ɗago ta kalleta tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace.

“Toh kije Insha Allah yanzu zan kwanta”.

Kai Asma’u ta gyaɗa kana ta wuce Bedroom ɗin ta Ummi kuwa kasa tashi tayi ahankali ta lumshe Idanunta tare da komawa ta kwanta akan kujeran still zuciyarta na cigaba da tsinkewa tana mai  maimaita kalmar Hasbunallahu wani’imal wakin aƙasan ranta.

 

Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana Picking call ɗin yakai kunnensa tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”. cikin sanyin murya M Arɗo ya gyara zaman wayar akunnensa tare da cewa.

“Wai yanzu yaran nan tsakanin ku da Allah kun bar batun karantarwa Amakarantar nan kenan?”.

Anutse Moddibo ya lumshe Idanunsa kana ya buɗe su cikin yanayin kasala da tsinkewar zuciyar da yake ji ya gyara zamansa tare da cije lips ɗinsa na ƙasa  yace.

“Toh ka asamsa Sallamar da nayi maka mana Before ka fara ƙorafi da zakayi”.

Girgiza kai Malam Arɗo yayi tare da cewa.

“Toh Wa’ailaikum salam kune ai baki ɗaya kuke son caza min kai, baki ɗaya satin nan yashiga har ya fita amma baku zoba toh gashi yau jumma’a gobe Asabar za akoma shiyasa nace bari na kira ku kada ace baku zoba”.

Iska mai zafi Moddibo ya fesar daga bakinsa tare da shafa sajensa kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Gaskiya baza mu zoba”.

Asanyaye Malam Arɗo yace.

“Toh meyesa”.

Muskutawa Moddibo yayi tare da gyara zaman wayar akunnensa kana yace.

“Ai mun riga da mun gama yi maka magana kayi haƙuri kawai ”.

 

“Amma kunsan ina son koyar wanku Amakarantar nan ina jin dadin zama daku sannan ɗaliban ma suna jin daɗin koyarwanku, makaranta na ya cigaba adalilin kune  kada kuyi min haka”.

 

“Malam kayi haƙuri da akwai Uzurin da yake gaban mu, wanda yafi wannan na tabbata badan wannan Uzurin ba babu dalilin da zaisa mubar koyar wa Amakarantar”.

Cikin sanyi murya Malam Arɗo ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.

“Toh shikenan tunda abin ya zama haka dole in sawa zuciyata haƙuri amma kusa marmin wasu Malamai masu Hazaƙa, duk da nasan da wuya asamu kamar ku tabbas nasan nayi rashin zaƙaƙuran Malamai kamar ku”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace.

“Toh ba matsala zamu yi kokarin hakan”.

Cikin sanyi Malam Arɗo yace.

“Toh Nagode saida safe”.

kana ya katse wayar.

Moddibo kuwa cikin sauri zuciyarsa ya cigaba da bugawa yana bada sautin dif-dab-dif-daf ahankali ya ɗago wayar da niyyar kiran M Jameel cikin wani Irin yanayi ya dafe saitin ƙahon zuciyarsa jin yanda yake bugawa da azabebben ƙarfi yana cigaba da bada sautin dif-dif-dif rintse idanunsa yayi still hannunsa na dafe da saitin ƙahon zuciyarsa.

 

Acan ɓangaren Gimbiya Bunayya kuwa har Misalin ƙarfe sha biyu da minti biyu na dare Uncle Naseer da Amina na zaune akan 2sitter suna hira.

Yayin da ita kuma ke kwance a Bedroom ɗin ta kunneta maƙale da waya tana Magana da Hajiya Lami.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.

“Hajiya Lami ni dai yanzu Alhamdulillah buƙata ta biya hankalina ya kwanta, yanzu batun soyayyar Amina da Naseer ya kankama yayi zurfi”.

Atake fara’ar dake fuskanta ya gushe ta mike ta zauna tare da cewa.

“Yanzu kuma hankalina ya koma kan ƴaƴan wannan shegiyar matar mai kama da Mayyar wannan yaro mai ƙwala-ƙwalan ido daya karye nake son kawar dashi tun da shi wancan mai kama da Brolas ɗin Uwarsa ta shayar dashi saɓani, tunda kinga wannan hatsarin ma shi na shiryawa abi takansa amma, ba’a samu babban ba akabi takan ƙaramin”.

Sai kuma ta sauƙe numfashi tare da jan dogon tsaki kana tace.

“Dole saina koma na samu boka Kar’uzu da maganar ayi duk abinda za ayi nikam Haiydar shine babban matsala ta tunda shi Ramadan shine ƙarami akan Aminu, babu yanda za ayi Aminu na raye aɗauki Sarauta abawa Ramadan dole dai sai ɗana ɗin dai”.

Cikin sauri Hajiya Lami ta katseta tare da cewa.

“Kul-Kul Hajiya Bunayya  kada kiyi la’akari da wannan ƙaramin tunanin naki, ba kiji Malam Bahaushe na cewa ɗan hakin daka raina shike tsole maka Ido ba?.

To ki rufa wa kanki asiri ki kawar dasu duka biyun hankalinki ya kwanta ki samu nutsuwa da salama aranki”.

Kana ta saki wani murmushi tare da cewa.

“Kinga idan kika gama dasu ɗaya ce zaki samu nutsuwa akanta itace Raudat da kuma Khausar.

Kinga Khausar kuwa ba ƴar gidan bace babu yanda za ayi agola tavi gadon Sarauta koda na mijine bare kuma mace. Raudat kuwa ƙarama ce kuma mace.

Amman Haiydar da Ramadan dai kaudasu, da kike batun Ramadan shine ƙarami a kan sulaiman, sau nawa manyan Yayu ke zaune ake bawa ƙannen su Sarautar, ni dai shawarar da zan baki yanda zaki gama da Haiydar haka zaki gama da Ramadan”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da gyara zaman wayar akunnenta kana tace.

“Haka ne fa kuma aini duk wannan tunanin bai zo min ba, atunanina idan na kawar da Haiydar shikenan”.

Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da faɗin.

“A’a tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa, har kina wani batun shine ƙaramin akan Aminu ai ba’a wannan zancen kima rufawa kanki asiri, kigama dasu gaba ɗaya to asannan hankalin zai kwanta, ki samu nutsuwa  anan ne zaki tabbatar sarauta ahannun Aminu take, ke kuma kin zama Gimbiyar Gembulan Matar sarki Uwar sarki amma muddin ƴaƴan wancan koɗaɗɗiyar matar na nan keda Saurauta saidai hange daga naisa”.

Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cike da gamsuwa kana tace.

“Aikuwa hakane Nifa duk wannan tunanin bai zomin ba shiyasa nake alfahari dake ƙawata.

Insha Allah zanje muyi magana da boka Kar’uzu asan yanda za’a ɓullowa lamarin”.

Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh nima Insha Allah gobe idan muka je zan faɗa masa ya tsaida rana da Samira zata fara zuwa  wajensa suyi satin, tunda dai yace idan ya kusance tama zai mayar mata da budurcinta ai shikenan”.

Atare suka sheƙe da dariyamai cike da farin ciki da annushawa kana Hajiya Bunayya tace.

“Ai dai haka yafi shiyasa na yarda da aikin Boka Kar’uzu kamar yankan wuƙa dan sha yanzu magani yanzu ne tun yaushe muke bin boka bursunu tsawon shekaru ba biyan buƙata sai asaran kuɗi”.

Jinjina kai Hajiya Lami tayi kana tayi mata Sallama suka katse wayar.

 

Aɓangaren Abban M Jameel kuwa tsaye yake ajikin window falonsa ya tsirawa harabar gidan Ido tun bayan fitar Motar M Jameel ya kasa motsa wa daga wajen.

Hajiya Karima data fito daga Bedroom ɗin sa ta dubesa cike da kulawa tace.

“Ya dai Alhj tun tuni kana tsaye ana ka gaza motsa sama da awa biyu kenan tun bayan fitar motar  Jameel kake tsaye lafiya kuwa?”.

Cikin wani irin yanayi ya lumshe idonsa.

Haka nan yaji ruwan hawaye na tsats-tsafo masa a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da iska kana yace.

“Haka nan dai narasa me nake tunawa awajen nan”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa bayansa kana tace.

“Toh kazo ka zauna mana”.

Girgiza kai yayi tare da fesar da numfashi kana cikin sanyi murya yace.

“Ina ga ko dan garin dana gani da alamun hadari ne ko yaya ne ban sani ba”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh kadawo ka zauna dan Allah tsayuwar tayi yawa”.

Kai ya gyaɗa lokaci ɗaya yaji wani irin masifaffen rauni mai haɗe da bugun zuciya ya rufe sa Atake yaji Idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye masu ɗumi yayin da zuciyarsa ya cigaba da tsinkewa jikinsa na mutuwa tamkar ana zare masa laka cikin sanyi jiki yaja ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya zauna akan kujera tare da kwanciya akan 3sitter kana ya lumshe Idanunsa.

Cike da kulawa tace.

“Ya dai lafiya kuwa kashiga ciki mana?”.

Girgiza kai yayi still zuciyarsa na cigaba da bugawa yayinda muryarsa ke ɗauke da rauni yace.

“Please Karima ki barni in kwanta inaji kamar kaina na ciwo”.

Cikin sauri tace.

“Alhj kad dai BP kane?”.

Girgiza kai yayi still Idanunsa na lumshe yace.

“A’a ba BP na bane bari dai mu gani”.

Zama tayi daga hannun kujeran kana tace.

“Toh kasha maganin ka kuwa?”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Eh sosai ma yan zun nan kafin Jameelu ya fita ya bani nasha”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Eh ƙwarai kuwa hakane toh Allah ya sawwaƙa”.

Ahankali yace.

“Ameen”, Miƙewa tayi tare da shiga Bedroom ɗin sa ta kwanta.

 

Ɓangaren Moddibo kuwa har Misalin sha biyu da kwata yana zaune dafe da ƙirjinsa dake cigaba da bugawa ahankali ya ɗago kansa tare da shafa gefen wayarsa  haske ya bayyana tare da nuna masa ƙarfe 12:15 afili ya furta.

“Har yanzu J bai zoba”.

Yayi mgnar tare da shiga Call log yayi dearling number M Jameel amma ga mamakinsa sai yaji Swich off.

Cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa.

“Ikon Allah lafiya kuwa wayar J arufe?”.

Kallonsa ya mayar kan babbar wayarsa tare da ɗauka kana ya fito da ɗaya number M Jameel ya kira Shima still Swich off.

Miƙewa tsaye yayi  ido a lumshe yace.

“Ha’a ya wayar J akashe kuma dai J baya kashe wayarsa, to amma mai yafaru yau wayarsa akashe toh me yake faruwa bayan ya faɗa min yau zai dawo!?”,l.

Yayi maganar cikin zulumi

“Ya ilahi ya mujabat da’awati, to kuma ko kafin J  ya fito sai da ya kirni yace zaije wajen Abba ya sallame sa sannan yazo amma kuma har yanzu bai zoba”.

 

Atake wata zuciyar tace kasani ko yazo suna tare da Innayi suna can suna ƙus-ƙus atake ya amince da abinda zuciyarsa ya raya masa cikin mutuwar jiki ya nufi ƙofan falonsa tare da buɗewa.

Wani sanyayyan iska ya hurasa ahankali ya ɗaga kansa sama gani yayi hadari ya fara haduwa sai walƙiya dake  haskawa  can ƙasa alamun yanzu hadarin ya fara, garin ya danyu duhu sakamakon rashin wuta ga kuma hadarin,

ahankali yabi sararin samaniyar da kallo ganin yanda hadarin yayiwa garin zobe kana aƙasan ransa yace to kodai wannan hadarin ne ya hana J zuwa sai kuma yace to kodai yana ɗakin Innayi ya faɗa yana taka step ɗin ahankali.

Cikin sauri Innayi ta haske masa ido da touch light mai masifar haske cikin han zari ya Janye hannuunsa dake danne da J ɗinsa ya tare Idanunsa dashi saboda hasken touchlight daya haska masa ido.

Cike da kulawa Innayi tace.

“Moddibo ya dai lafiya ina zuwa Atsakiyar adaren nan?”.

Ahankali ya sake sakƙowa daga kan step ɗin tare da jingina bayansa da jikin filan barandarsa, kana hannunsa na dama na kan flowes dake gefe yace.

“Kece fa kike ganinsa tsakiyar dare ne, dudu shabiyu da rabi ne fa yanzu”.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Tsakiyar dare ne mana Moddibo yanzu fa ƙarfe shabiyu harda rabi ai tsakiyar dare ne, to amma me kafito yi lafiya dai ko?”.

Cikin sanyin murya yace.

“J ne har yanzu bai zo ba kuma ya fito akan zai zo ma ya kirani awaya kan cewa yanzu zai shiga wajen Abbansa ya masa saida safe ya fito, kuma har yanzu bai iso ba sannan nata kiran layukan sa basa shiga”.

Ya ida maganar akasalance.

Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.

“Toh dan bai zoba Moddibo ai ba abin tashin hankali bane, kaga yanayin wannan hadarin daya haɗu zai iya hanasa zuwa wataƙil daya shiga wajen Abban nasa zaice dare yayi kuma ga hadari ya bari sai gobe”.

Da sauri ya katseta da cewa.

“To ai Innayi wayarsa bata shiga fa”.

Saurin Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.

“Ka kira layinsa duka?”.

Kai ya jinjina mata.

“Eh na kira layukansa duka fa basa shiga”.

Cikin yanayin bacci ta kalli Moddibo tare da sakin hamma kana ta aro Jarumtaka tare da cewa.

“To ko dai network ne?”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da Girgiza mata kai kana yace.

“A’a ba network bane cemin akeyi akashe kuma fa Innayi J baya kashe wayarsa, ko zai kwanta komai yaya kuma nasan wayar J baya rasa caji”.

A hankali Innayi ta rufe idonta jin kamar tsinkewar zuciya ya ziyarci ta.

Amma sai ta daure kana tace.

“To amma kaga jiya ma kace min wajen Umminsa ya kwana to ko dai yauma yaje  canne ne ya kashe wayarsa dan kada kayi ta kiransa?”.

 

Jinjina kai yayi tare da faɗin.

“Ok ba mamaki fa bari na kira Ummi”.

Cikin sauri Innayi ta kallesa tare da cewa.

“Aƙarfe ɗaya saura zaka kirasu?”

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh Innayi in dai har wurin Ummi yake nasan yanzu zasu ganshi kamar takwas na dare ne, saboda nasan yanzu suna hira ba suyi bacci ba.

Kai Innayi ta gyaɗa tare da gyara tsayuwar ta kana tace.

“Toh shikenan ka kira”.

 

Dearling number Ummi yayu.

Acan ɓangaren Ummi kuwa kwance take yayin da idanunta ke lumshe cikin tsananin tsinkewar zuciya da kasala jin rurin wayarta yasa ta miƙe firgice cikin yanayi sanyi  sanya hannunta na dama ta janyo wayar tare da ƙurawa screen ɗin Ido sunan Moddibo ke yawo.

 

Cikin sauri tare da rawan jiki tayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnenta batare data amsa Sallamar daya mata ba tace.

“Babana Lafiya?”.

Cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace.

“Ummi lafiya ya naji kamar kin razana?”.

Ahankali ta koma ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunta kana cikin wata raunan’niyar murya mai cike da kasala da tsoro ta fesar da numfashi tare da cewa.

“Gaba ɗaya ma ai. Arazanen nake Babana”.

Moddibo kuwa cikin kasala da mutuwar jiki ya yaja numfashi tare da fesar wa kana yace.

“To Ummi me yafaru?”.

Buɗe Idanunta dake lumshe tayi tare da dafe ƙirjinta da still yake bugawa kana tace.

“Ban saniba amma gaba ɗaya ina jina wani irin gani nan dai kamar mara lfy, kuma ba zance ga abinda yake damuna kai tsaye ba”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.

“Toh amma Ummi lafiyar ki lau?”.

Kai ta gyaɗa masa kamar yana gabanta kana tace.

“Lafiya ta ƙalau,Amma Babana lafiya ka kira yanzu?”.

Numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa kana ya sake jingina bayansa da jikin step ɗin tare da cewa.

“Eh lafiya lau babu komai dama zan tambayeki ne ko dai J yazo yana wurinki ne munyi dashi tun ɗazu akan zai zo har yace min gashi ya fito amma zai sallami Abbansa ne kawai ya taho”.

Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cijan lip ɗin sa na ƙasa kana yace.

“Amma har yanzu be taho ba, inata jiran sa ko ƙofar gida bamu rufe ba, shiyasa nace bari na kira koya biya wajenki, da yake jiya ma nan ya kwana!?”.

Rumtse ida nunta tayi da masifar ƙarfi k cikin wani azabebben tsinkewar zuciya da faɗuwar gaba ta buga hannunta na dama aƙirji tare da cewa.

_“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n. Allahumma Ajirni fii musibati wa’ahlifli khairan min_

bai zo ba kuma yace maka zai zo?

Abbansa kaɗai zai Sallama?”.

Gyaɗa kai Moddibo yayi tamkar yana gabanta kana cikin raunan’niyar murya mai cike da sanyi yace.

“Eh Ummi”.

 

Cikin wani irin yanayi na taraddadin zuciya da rauni Ummi tace.

“Ya Ubangiji Allah ka dubeni da Idon Rahma. Ya Allah ka tsare wannan bawan naka, aduk inda yake Alfarman Annabi da Alkur’ani”.

Jin salatin da kuma yanayin da Ummi tayi Magana cikin firgici ya farkar da Asma’u, Bashir da Malam Ahmad Aruɗe Asma’u ta miƙe tare da dafe kanta da taji yayi masifar sarawa ta sauƙa daga kan gadon.

 

Acan ɗakin  Bashir kuwa Hasbunallahu wani’imal wakin ya furta tare da sauƙa ƙasa kusan atare suka fito falon ko wannensu zuciyarsa na bugawa da kaso tamanin cikin ɗari.

Moddibo kuwa cikin sanyu da ruɗu yace.

“Ameen ya Allah Ummi ameen ya rabbil Izzati”.

 

Cikin zulumi Ummi ta runtse Idanunta kana tace.

“Amma Babana ka kira Abbansa mana”.

Numfashi Moddibo ya fesar tare da kallon Innayi data tsaresa da ido cikin yanayin razani yace.

“Eh Ummi nayi tunanin kiran Abbansa amma sai nace bari na fara kiranki tunda jiya yazo na, sannan Ummi nasan J baya kashe wayarsa rashin shigar wayarsa nema yafi damuna!”.

Girgiza kai Ummi tayi yayinda ruwan hawaye masu masifar ɗumi suka cika kwarmin Idanunta kana cikin raunan’niyar murya tace.

“Tabbas baya kashewa ka kira Abbansa kaji”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh dama zan kirasa amma Innayi tace ko Abbansa ne ya hanasa zuwa ganin hadari”.

 

A hankali tace.

“Anya?,Ka kira sa dai”.

 

“Amma yanzu dare baiyi ba Ummi”.

 

Cikin sauri tace.

“A’a ka kira Babana ka kira Abbansa ɗin duk yanda kukayi ka kirani ka sanar min”.

“Toh”.

Moddibo yace kana ya katse kiran.

 

Asma’u da Bashir kuwa zuru-zuru sukayi da ido domin suna iya jiyo sautin muryar Modibbo.

Durƙusa wa Asma’u tayi tare da toshe bakinta kana tashiga.

Girgiza kanta tare da cewa.

“Ya Allah kada ka jarabcemu da abinda baza mu iyaba ɗaukaba Allah ka tsare Yaya Jameel aduk inda yake ya Allah kada ka bari wani abu na cutarwa ya sameshi”.

Cikin raunin murya Ummi ta kalleta Atake  taji wasu hawaye masu masifar ɗumi sun zubo kuncinta.

Ahankali Malam Ahmad da jikinsa yayi masifar sanyi ya ƙarasa kusa da Ummi.

 

Moddibo kuwa yana katse kiran ya shiga contact tare da fito da Number Abban M Jameel.

Kana ya Kalli Innayi cikin sanyin murya mai cike da tashin hankali yace.

“Kin gani ko Innayi baya can. J baije gidan Ummi ba. Innayi ina J ya tafi bayan yasanar dani cewa zai taho”.

Lokaci ɗaya wani masifaffen tsoro da tashin hankali ya ziyarci Innayi wanda ta kasa ɓoyewa har hakan ya bayyana asaman fuskarta dake nuni da tsantsar ruɗu.

Cikin dakiya da kuma nuna masa babu komai insha Allah ta gyara tochligt dake hannunta kana tace.

“Ka dai kira Abbansa muji wataƙil yana can tare dashi hadarin ne ya hanasa fitowa”.

Kai ya gyaɗa mata tare da dearling number Abban M Jameel yana jin yanda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dumm-dif dumm.

Abba dake kwance kan 3sitter Idanunsa arufe bacci ya fara fusgarsa yaji suwwan wayarsa Atsakiyar kansa afirgice ya miƙe tare da zama kana ya duba screen ɗin wayar nan yaga sunan Moddibo na yawo cikin rawan jiki yayi Picking.

Atare Abba da Moddibo sukayi Sallama.

Ahankali Moddibo ya sauƙe numfashin  tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Wa’alaikum Salam Abba”.

Cikin yanayin firgici da ruɗu Abba ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Na’am Aliyu ya akayi?”.

Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.

“Lafiya Abba”.

Kai Abba ya gyaɗa tare da jingina bayansa da jikin kushin kana yace.

“Ya gida kowa lafiya dai?

Jameelun yaƙara so yana lafiya ko?”.

Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya buga da masifar ƙarfi kana yayi saurin dafe ƙirjinsa tare da cewa.

“Abba baya gidane”.

Wani irin azabebben bugawa zuciyar Abba yayi kana yace.

“A’a bakwa tare ne tun 10:15 ai ya sallameni yace min zai taho wurinka”.

Moddibo kuwa da sauri ya rumtse idanunsa tare da dafe jikin step ɗin yana mai jin kansa na masifar sarawa tamkar zai rabe gida biyu cikin raunin murya yace.

“Abba tun ƙarfe 10:15  ya fita kuma yace wajena zai zo? Abba tun ɗazu fa nake jiransa ko ƙofar gida bamu rufe ba har yanzu J bai zoba sannan fa nata kiran layukan basa shiga”.

 

Cikin tsananin razani da tsinkewar zuciya Abba ya miƙe tsaye kana yace.

“Aliyu mai kace?”.

Araunane Moddibo da Idanunsa ke juyawa ya dafe kansa kana cikin sanyin murya yace.

“Abba na yita kiran layinsa baya shiga”.

 

A ruɗe Abba ya miƙa tsaye tare da cewa.

“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n to lafiya Aliyu?”.

Girgiza kai Moddibo yayi tare da gyara tsayuwar sa kana yace.

“Toh Abba kuma yace waje na ɗin zai taho?Abba J bai zoba bafa”.

ya ida maganar cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali.

 

Atake zufa ya wanke wa Abba jiki duk da iskar dake kaɗawa d ƙarfi ya haɗiye wani abu mai ɗaci kana yace.

“Ko dai gidan Ummin sa yaje”.

Da sauri Moddibo ya girgiza kansa muryarsa na rawa yace.

“Um-um Abba baya can yanzu nayi waya da Ummi itace ma tace in Kira ka Dan ni Ina tunanin dare ma yayi bazan kira ba”.

 

Cikin tsinkewar zuciya Abba ya nufi ƙofar falon Hajiya Karima da sautin muryansa ya farkar da ita tayi saurin fitowa daga Bedroom ɗin Aruɗe ta kallesa kana tace.

“Lafiya Alhj?”.

Girgiza kai Abba yayi tare da cewa.

“Jameelu ba agansa ba wai baije  wajen Moddibo ba sannan baije wajen Umminsa ba”.

Da sauri ta dafe ƙirjinta kana tace.

“Ba agansa ba kuma gashi yanzu ƙarfe ɗaya”.

Kasa cewa komai Abba yayi ya nufi ƙofa da sauri.

Tare da cewa.

“Miƙo min key mota”.

Cikin sauru tabi bayansa tare da Kallonsa ganin Gajeren wando da single ne kaɗai ajikinsa yasa tace.

“Toh yanzu ina zaka je adaren nan??”.

Cikin raunin murya yace.

“Karima ina zanje kike tambaya ta?  Jameelu na fa baya gidansu Aliyu sannan baya gidan Umminsa to ina Jameelu yaje kinsan waye Jameelu da in dai baya nan yana gidansu Aliyu ko gidan Umminsa tabbas da akwai abinda yake faruwa”.

Cikin sauri ta juya tare da komawa Bedroom ta dauƙa Masa Jallabiya da key mota kana ta sanya hijabinta ta fito tare da miƙa masa.

 

Karba yayi yana tafiya yana saka jallabiyar kana ya nufi inda Motarsa yake ya shiga cikin sassarfa tabi bayansa yana shiga mazaunin Driver itama tayi saurin buɗe gefen mai zaman banza ta Zauna.

Kallonta yayi tare da cewa.

“A’a ki koma”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“A’a Alh ya za’ayi in barka ka tafi kai kaɗai muje dai”.

Kai ya gyaɗa batare da yace komai ba ya figi motar.

Suka tafi bayan mai gadi ya buɗe masa ahankali ya fara bin hanyar Yana dudduba gefen titin kana cikin sanyin murya yace.

“To ko dai motarsa ta samu matsale ne?”.

Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana tace.

“Idan ma motarsa ta samu matsala Alh ai saidai ya kira akawo masa wata”.

Kai ya jinjina still Yana cigaba da Driving ɗin yayin da zuciyarsa ke cigaba da bugawa da kaso Cassa’in cikin ɗari suna cikin tafiya har suka isa gidan su Moddibo.

 

Moddibo dake tsaye coumpund ɗin har zuwa lokacin ya gagara koda ƙoƙƙwaran motsi yayi saurin kallon gate ɗin ganin hasken mota Itama Innayi dake tsaye tayi saurin bin wajen da kallo zuciyarta na cigaba da bugawa.

Cikin sauri tare da rauni yace.

“Toh waye wannan ko dai motar J ne?”.

Ya faɗa tare da nufar gate ɗin Innayi kuwa ido ta zuba masa har ya buɗe gate.

Moddibo kuwa yana buɗe gate din idanunsa suka sauƙa akan motar Abba.

Cikin sauri ya ƙarasa jikin motar tare da cewa.

“Abba kaine?”.

Jinjina kai Abba yayi asanda ya ƙarasa fita daga motar kana cikin raunin murya yace.

“Eh Nine Aliyu ina tsammanin Jameelu yana nan to idan ba nan ba ina Jameelu zai je adaren nan.

Amma anya ka bin cika baya gidan Umminsa ba wasa take mana ba?”.

 

Girgiza kai Moddibo yayi cikin mutuwar da jiki da rauni yace.

“A’a Abba baya can tunda nayi magana da Ummi kuma yanzu da muka gama waya da kai ma na kirata nace baya can itama kuka fa takeyi”.

Cikin ruɗu da rashin sanin madafa Abba yace.

“Toh kazo muje can ɗin mu duba may be ko motarsa ta ɓaci ahanya can ya nufa”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.

“To bari in ɗauki motata dan nasan Innayi ma bazata zauna ita kaɗai agida ba”.

Ya faɗa tare da shigewa cikin gida kai tsaye falonsa ya nufa ya ɗauki key sannan suka fito da Innayi acikin motar.

Motar Modibbo ce ta shiga gaba na Abba na biye da ita tuƙi kawai Moddibo yake amma baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa.

 

Acan gidan Ummi kuwa tunda Moddibo ya sanar mata M Jameel baya gidan Abba hankalinta yayi masifar tashi ta fito coumpund ta tsaya tana kuka yayinda Asma’u da Bashir ke taya ta cikin tsanananin kaɗuwa.

 

Cikin rarrashi da nasiyya Malam Ahmad ke tausanta dasu Asma’u.

Cikin sauri Ummi ta ɗaga kanta ganin hasken motoci abakin gate ɗin gidan su.

Aruɗe ta kallesa tare da cewa.

“Ka kalli hasken mota Malam ko dai Jameelu ne?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ki kwantar da hankalin ki Fatima dan Allah ki nutsu Insha Allah babu komai, ba abinda zai samu Jameelu”.

Kai ta girgiza kana tace.

“A’a to ai naga hasken mota ne”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da riƙe hannunta ganin yanda ta firgice kana yace.

“Toh bari naje na duba naga ko waye ne”.

Kai ta girgiza kana cikin raunin murya tace.

“A’a to muje dai”.

Kai ya gyaɗa tare da yin gaba kana tabi bayansa Malam Ahmad na buɗe ƙaramar ƙofa yaga motar Moddibo daf da bakin gate Dai-dai lokacin Moddibo ya buɗe Murfin motar ya fito.

Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da leƙa motar dake bayansa kana tace.

“Babana”.

Cikin sanyin murya yace.

“Na’am Ummi J bai zo nan ba dagaske?”.

Cikin muryan kuka ta girgiza kai kana tace.

“A’a bai zo bafa Babana idan yazo ya za ayi in ɓoye muku”.

 

Cikin mutuwar jiki Abba ya buɗe Murfin motar tare da fita kana ya kalli Ummi da hawaye ke bin kuncinta yace.

“Fatima”.

Saurin Kallonsa Ummi tayi tare da cewa.

“Abban Jameel”.

Cikin yanayin tashin hankali yace.

“Da gaske Jameelu bai zoba?”.

Kai ta gyaɗa Masa still Hawaye na bin kun cinta tace.

“Bai zoba kuma nata kiran wayoyinsa basa shiga”.

Cikintashin hankali da ruɗu suka haɗa baki wajen furta.

_“Innalillahi Wa’inna Ilahi rajiu’n Allahumma Ajirni fii musibati wa’ahlifli khairan minha”_.

Cikin sanyi Moddibo ya kalli Abba da idanunsa suka sauya launi saboda tashin hankali kana yace.

“Abba mu koma ta hanyar gidaku mu duba ko dai motarsa ta samu matsala ne ko kuma yayi hatsari ne?”.

Kai suka gyaɗa cikin sauri Ummi ta juya tare da kallon Moddibo kana tace.

“Bari na ɗauko hijabina muje tare”.

Bata jira jin abinda zasu ce ba ta juya da sauri ta koma tare da ɗaukan hijabinta ta fito coumpund ɗin kallon Asma’u da Bashir tayi wanda har zuwa lokacin suna cikin ruɗani, cikin Muryan kuka tace.

“Asma’u ku  kula da kanku zamu duba hanya ko Allah zaisa mu gansa”.

Cikin sauri Asma’u tace.

“Ummi zamu biku”.

Girgiza kai Ummi tayi tana tafiya tace.

“A’a ku zauna kada ku fito”.

Daga haka ta fice Malam Ahmad na ƙoƙarin ɗauko mota Moddibo yace.

“Ummi kuzo ku shiga motata kawai”,

 

Kai ta gyaɗa kana tashiga bayan motar kusa da  Innayi.

Malam Ahmad kuwa a gaba, kana suka fara tafiya koda da irin tunanin da yake Aransa duk wani inda suke tunanin mota zai iya maƙalewa ko kuma hatsari sun duba amma babu M Jameel da motarsa babu dalilinsa har unguwar su Abba suka koma amma still Babu shi babu dalilinsa.

 

Cikin yanayin gajiyawa da ɗimuwa Abba ya buɗe Murfin motar ya fito kana Moddibo da sauran ma duk suka fito.

Cikin raunin murya me nuni da razani Abba yace.

“Gashi mun biyo har nan ma amma baya nan, to mu gwada zuwa asibiti mu duba ko dai yayi hatsari ne ko yaya”.

Cikin raunin murya Moddibo ya Girgiza kai kana yace.

“Abba hatsari kuma? Ai da hatsari ne da munga mota kuma da ankira mu”.

Kafin Abba yace wani abu Innayi ta kalli Moddibo tare da cewa.

“Eh muje dai asibitin saboda Kore shakku”.

Jinjina kai sukayi tare da shiga motar kana suka nufi Asibitin.

Ahankali Moddibo ya kalli Innayi kana yace.

“Toh wani asibitin zamuje kin san dai bawasu manyan asibiti muke dasu ba”.

Cikin sanyi malam Ahmad yace.

“Mu fara zuwa babban asibitin idan yaso sai mu duba sauran daga baya”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da nufar babban asibitin Abba na biye dasu.

Suna isa suka tarar da gate din asibitin arufe kasancewar har biyu tayi,sauran asibitin suka shiga zagayawa amma ko wanne arufe in sun buga an buɗe musuma in sun shiga bashi ba lbrinsa.

Cikin han zari Abba ya cewa Moddibo su nufi Private hospital ɗin Abba haka kuwa akayi.

Suna isa Moddibo ya sauƙa tare da nufar cikin Hospital kana ya tambayi Norse dake aiki ko M Jameel yazo suka ce a’a juyawa yayi ya shiga motar kana suka ci-gaba da nemansa.

Wasa gaske fa babu Jameel ba dililinsa ba motarsa, gaba ɗaya sun shiga ruɗu  da zulumi gamida tsoro.

 

Misalin ƙarfe uku hankalin su ya kai ƙololuwa wajen tashi baki ɗaya sun cika da damuwa zuwa wannan lokacin sun tabbatar ba lafiya domin M Jameel baya yawo sannan Gembulan ba wani babban gari ne da keda charking point ba bare su kai report.

Moddibo kuwa banda tasbihi da kiran sunan Allah babu abinda yake Aransa yayin da kasala da mutuwar jikinsa ke ƙaruwa fiye da farko kana ga hadarin da zuwa yanzu yayi gangami asama da alamar ruwa na gab da sakƙowa, dan tuni aka fara yayyafi.

 

Abba kuwa tunda suka fito a asibiti ya kifa kansa ajikin motar zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi cikin raunin murya yace.

“Acikin wannan daren ga hadari na kira layukan Jameeluna duka basa shiga a wannan yanayin ina Jamilu na ya shiga”.

 

Cikin  raunin murya mai cike da karaya Modibbo ya fesar da numfashi mai zafi kana yace.

“Yanzu acikin daren nan ina J yake?.

Wani hali yake ciki?.

Wani irin yanayi yake cikin a wannan daren da kuma hadarin da yake tasowa ina J ɗina yake!?”.

 

Cikin ƙarfin hali Malam Ahmad ya numfasa kana yace.

“Insha Allah ba komai mu bari muga zuwa safiya abinda Ubangiji zai yi”.

 

Cikin tsanananin rauni Ummi ta kife kanta da jikin kujeran Motar  kana ta fashe da wani Marayan kuka mai gunji”.

 

Cikin damuwa da kuma tausayawa Abba ya juya tare da kallon Malam Ahmad kana yace.

“Malam ku tafi gida kaima Moddibo ku koma gida da Innayi kada ruwan nan ya saƙƙo muna nan duk inda ya kamata mu duba mun duba baya nan bari mu gani zuwa safiya”.

 

Girgiza kai Moddibo yayi  Araunane yace.

“Abba ya za ayi mu koma mu shiga cikin gida mu samu mafaka bayan bamu san halin da J yake ciki ba. Abba ina kake tunanin zamu koma mu samu nutsuwa acikin wannan yanayin bayan bamu san ina J yake ba!?”.

 

Kallonsa Abba yayi cike da rauni yace.

“Toh Aliyu ina zamuje mu duba?, Duk inda ya kamata mu duba mun duba sannan wayoyinsa basa shiga wannan shine babban tashin hankalina mu koma gida muyi alwala mu sanar wa Ubangiji halin da muke ciki Aliyu”.

Jinjina kai sukayi atare cike da gamsuwa da abinda yace sam tashin hankali da ruɗanin da suke ciki yasa sun kasa samun nutsuwar da zasuyi addu’a.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh Abba”.

Sannan suka shiga mota Abba yaja ya nufi gidansu cikin tashin hankali da ɗimuwa yayin da Hajiya Karima ke kuka Abba kuwa ko da kallonta ya gagara yi bare kuma ya iya lallashin ta.

Ya yinda Moddibo ya nufi gidan Ummi babu abinda ke tashi acikin motar banda sheshsheƙan Kukan Ummi ta rasa shin wani irin tunani zata yi shin ina Jameelunta yake awannan tsohon daren Akuma irin wannan lokacin.

Moddibo kuwa cikin tsananin damuwa da zulumi da macewar jiki ya cigaba da Driving har ya isa kofar gidan yayi Parking.

Fita Malam Ahmad yayi Ummi ma ta sauƙa suka nufi cikin gidan.

Ganin hasken mota yasa Bashir miƙewa da sauri tare da buɗe ƙaramin gate ɗin.

Cikin sauri Asma’u da har zuwa lokacin take zaune ta ɗago kanta tare da miƙewa ta riƙe hannun Ummi kana tace.

“Ummi Ina Yaya Jameel Ummi kunga Yah Jameel?”.

Cikin sanyi Ummu ke jujjuya mata kai.

Ita kuwa a ɗimauce tace. “Ummi to ina yashiga awannan daren dubi hadari fa wani hali yake ciki?”.

Girgiza kai Ummi tayi tare da fashewa da kuka kana tace.

“Ban saniba Asma’u Bansan inda Jameelu na yake ba, bansan halin da yake ciki ba Asma’u zuciyata zafi take jinake tamkar kaina zai rabe gida biyu!”.

Aruɗe Asma’u tace.

_“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n Allahumma Ajirni fii musibati wa’ahlifli khairan minha_, nashiga uku Yah Jameel”.

Cikin sauri Malam Ahmad ya riƙe hannun Asma’u ganin kamar bata hayyacinta kana yace.

“Subhanallah Asma’u da iliminki kike kirawa kanki shiga uku kada ki sake haka Addu’a ya kamata mu masa kunji ko?”.

Kallonsa ya mayar kan Bashir kana yace.

“Kuzo mushiga muyi masa addu’a ayanzu ba kuka Jameelu yake da buƙata daga wajen muba face adduoi”.

Kai suka gyaɗa sannan ya sake hannun Asma’u ya riƙe na Ummi Bashir kuma yarike hannun Asma’u suka shiga ciki kai tsaye ko wannensu toilet yashiga ya ɗaura Al’wala kana ya fito suka shimfiɗa Sallaya tare da fara jera nafillah suna roƙon Allah daya fitar da M Jameel aduk halin da yake ciki.

 

Moddibo kuwa suna isa gida yayi Parking tare da rufe ƙofar kana ya wuce falonsa yayin da Innayi ma tashige sashen ta yana shiga kai tsaye toilet dake falon ya shiga ya ɗaura alwala kana ya fito ya shimfida Sallaya cike da nutsuwa ya fara Sallah kana duk sujjadar da zaiyi sai ya roƙi Ubangiji ya kare J ɗin sa aduk inda yake”.

Baki ɗaya su haka suka raya wannan daren cike da bautar Ubangiji tare kuma da rokon Allah daya bayyanar da M Jameel kana Allah yaraba sa da duk kan sharrin Mutum da Aljan.

 

Bayan an kira Assalatu Moddibo ya fito ya nufi masallaci ana idar da sallah kai tsaye gidan Abba ya nufa.

Yana isa kiran Ummi na shiga wayarsa ciki. Sanyin jiki  ya ɗaga wayar tare da kaiwa kunnensa kana yayi Sallama.

Cikin dashashshiyar murya Ummi ta amsa Sallamar sa kana tace.

“Babana ya labarin Jameelu na?”.

Cikin sanyin murya yace.

“Ummi nima gashi yanzu nazo wajen Abba naji ko ya dawo gida”.

Dai-dai lokacin Abba ya buɗe gate ya fito ganin Moddibo tsaye yasa ya isa wajensa ahankali Moddibo ya zare wayar daga kunnensa bayan yace anjina zai kirata.

 

“Aliyu dama yanzu zanje wajenka”.

A hankali Modibbo yace.

“Abba to yanzu ya zamuyi”.

Numfashi Abba ya fesar tare da cewa.

“To mu tafi police station  Jiya Baki ɗaya ba muyi tunanin zuwa can ba”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana suka shiga motarsa yaja Abba kuwa jingina da jikin kujera yayi baki ɗaya zuciyarsa ta tushe ya rasa wani irin tunani zaiyi yayin da Idanunsa suka tsats-tsafo da ruwan hawaye.

Moddibo kuwa Driving yake amma baki ɗaya baya fahimtar komai ko gilmawar mutum ya gani sai yaga kamar J ɗin sane.

Suna isa yayi Parking atare suka fito daga motar tare da shiga station din Dpo dake ƙoƙarin fita yayi Murmushi tare da cewa.

“Alh Bashiru maidala Barka da zuwa kaine da kan ka?”.

Jinjina kai Abba yayi kana cikin sanyin murya yace.

“Na kawo report ne ɗana Jameelu ne bamu ganiba”.

Cike da mamaki da kuma  al’ajabi Dpo da sauran folisawan suka ce.

“Ɗan ka Jameelu kuma?”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Eh tun jiya ba agansa ba kuma babu motarsa sannan akira layukan sa basa shiga”.

Cike da jimami Dpo yace.

“Subhanallah Alhj mai yasa baku kawo report tun dare ba!?”.

Numfashi Abba ya fesar kana yace.

“Yanayin hadari ne sannan baki daya hankalin mu baya Jikin mu sai mukayi tunanin bari muyi addu’a mu kaiwa Ubangiji kukan mu”.

Daga nan yayi miki bayanin dukkan abinda ke tafiya.

Kai Dpo ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan Alhj insha Allah yanzu zamu kira hedquater mu na cikin Taraba afaɗa musu halin da ake ciki”.

Kai Abba ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan mun gode”.

Moddibo kuwa tun da suka shiga ya jingina da jikin bango Ya Lumshe Idanunsa yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi bai ce komai.

 

Wunin wannan ranan baki ɗaya haka gidaje uku sukayi sa cikin zullumi,fargaba da kuma tsantsar tashin hankali Moddibo kuwa duk bayan minti biyu sai ya kira Number M Jameel aƙalla daga Jiya da daddare zuwa yau ya kira wayarsa yafi sau ɗari.

Acan ɓangaren Ummi ma haka yakasance bini-bini zata kira layin sa amma amsar ɗaya ake basu shine Switch off.

Haka zalika Abba time to time zaiyi try number M Jameel amma akashe Wunin wannan ranan baki ɗaya sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasancewa suna cikin tsananin tashin hankali da ɗimuwa duk inda ya kamata su nema ko su bincika duk sun nema sun bincika amman ba lbri.

Abba kuwa zama yayi afalonsa tare da kira duk wani danginsa ko kuma abokin arziki ko zaiji Jameelu yaje amma kowa amsa ɗaya yake basa baije ba.

Haka zalika Ummi baki ɗaya ta kira danginta ko M Jameel yaje amma suma dai amsar ɗaya ce baije ba.

 

Wunin wannan ranan har dare babu M Jameel babu labarin sa zuwa wannan lokacin tsananin tashin hankali da ruɗun da suke ciki ba zai misaltuba.

 

Da daddare Misalin ƙarfe goma Moddibo ne zaune a falon Abba kansa aƙasa yayinda idanunsa suka kaɗa sukayi ja jawur kana jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya haka zalika yauma koda runtsawa ne yakasa kana ya sanya duka hannunsa biyu ya dafe kansa dashi zuwa lokacin baki ɗaya ya kasa control ɗin kansa kife kansa yayi ajikin kujera tare da fashewa da kuka mai gunji.

Cikin wata raunan’niyar murya mai cike da karkarwa yace.

“Abba ina J yake? Abba ina J ya tafi ya barni Abba wani hali J yake ciki?”.

Hajiya Karima ce  tashigo falon bakinta ɗauke da Sallama tare da kallon Moddibo dake kuka tamkar ƙaramin yaro lumshe Idanunta tayi tare da cewa.

“Haba Aliyu kuka kuma kai da ya kamata ka tausashi Mahaifinsa sannan kuma ka zauna zakuyi ta kuka atare kenan?”.

Karo na farko kenan arayuwar data yi masa magana cikin taushin lafazi.

Ahankali Moddibo ya ɗago kai ya kalleta still yana kuka yace.

“Aunty Karima ina J yake Ina J ɗina yashiga ya barni?”.

Cikin rauni Abba ya ɗago idanunsa da hawaye ke zuba Akuma dai-dai lokacin wayar Abba ta ɗauki ruri yana ɗagawa yaga number ce ba suna sai ya mayar ya ajiye.

Kallonsa Moddibo yayi tare da faɗin.

“Abba waye ne?”.

Ciki Sanyin Abba ya kalli wayar kana yace.

“Numbar ce ba suna”.

Cikin muryan kuka Moddibo yace.

“Toh Abba ka ɗaga mana ko za’a faɗa mana anga J ne”.

Cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da cewa.

“Assalamu Alaikum”.

Daga ɗaya ɓangaren cikin wata bauɗaɗɗiyar murya aka amsa da.

“Wa’alaikum Salam kaine Alhaji Bashiru Maidala mahaifin Malam Jameelu?”.

Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da miƙewa tsaye kana yace.

“Eh nine mahaifin Jameelu”.

Cikin sauri Moddibo ya miƙe tsaye,

itama Hajiya Karima cikin sauri ta miƙe tsaye.

Gyaran murya yayi kana yace.

“Toh Jameelu yana wajen mu”.

Cikin rawan baki Abba yace.

“Jameelu yana wajen ku yana cikin halin lafiya? To a ina kuke?”.

Kai tsaye yace.

“Eh gashi ma kaji muryarsa”.

Ya faɗa tare da miƙawa M Jameel wayar.

Cikin sauri Abba yace.

“Jameelu”.

M Jameel kuwa cikin wata raunan’niyar murya me cike da galabaita da tashin hankali kamar wanda yayi kuka yana sauƙe ajiyar zuciya yace.

“Abbana”.

Cikin rawan jiki da rauni Abba yace.

“Na’am Jameelu Meye sameka?,Aina kake?”.

Ajiyar zuciya mai nauyi M Jameel ya sauƙe cikin rauni da yanayi wahala yace.

“Abba nima ban sani ba  bansan inda nake ba Abba ina A.J”.

Cikin muryan kuka Abba ya kalli Moddibo da jikinsa ke rawa kana yace.

“Gashinan”.

Ahankali M Jameel dake sakin ajiyar zuciya yace.

“Abba ka bashi wayar”.

Miƙawa Moddibo wayar Abba yayi cikin sauri Moddibo ya amsa tare da mannawa akunnensa kana Yace.

“Jyyyyyy”,yaja sunan cike da taraddadi.

Fesar da numfashi M Jameel Yayi tare da cewa.

“AJ”.

Cikin yanayin rauni da tausayawa ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“J ina kake?”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“AJ ban sani ba bansan inda nake ba, ban san ida suka kawoni ba”.

Cikin sauri aka Fisge wayar daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya akace.

“Ka bawa mahaifinsa waya”.

Ahankali kuma cikin sanyi Moddibo yace.

“Waye kai ina J yake?”.

Cikin wata razananniyar tsawa yace.

“Kabawa mahaifinsa waya ba da kai muke son magana ba?”.

Moddibo kuwa Girgiza kai yayi kana yace.

“Toh me kuke so ku faɗa min ko mameye”.

Cikin sauri Abba ya janye wayar daga kunnensa tare da sa wayar a handsfree kana yace.

“Gani mahaifin Jameelu”.

Daga ɗaya ɓangaren mutumin yace.

“Jameelu yana hannunmu bawai mun sace sa dan mu kashe sa ko wani abu bane amma idan kuka yi mana taurin kai zamu iya kash”…

 

 

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

 

 

 

*By*

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button