Bad Boys Hausa NovelHausa Novels

Bad Boys 6

Sponsored Links

You guys should manage and wait for next episode🥰
*_🐹BAD BOYS🐹_*
By…
Oum Aphnan

006
___________________
“Salima..?
Salima…??
Saliiiiimaaaaa???”

Daga kitchen Taji Ya sheikh Yana kwarara mata kira ,da gudu ta fallo zuwa bedroom din tana zuba haki
“Ya Sheikh … Ga ni” tayi magana tana ɗan rusunawa kaɗan alamun girmamawa

Watsa _Pads_ Audugan matan hannunsa yayi akan Gado ,yana sake ƙidayasu guda uku

“Salima ya akayi kika ƙarar da tulin Audugan nan a Al’adan wata ɗaya? A wannan tsadar rayuwan ,haba Salima ,Wai cin Audugan nan kikeyi ne? Kin ƙarar da pads guda 9 saura 3 ? A period din wata guda ?”

A daburce ta bashi amsa mai ƙunshe da rainin wayo kuma
“Hmm kasan tunda muka rasa breadi a gidan nan na koma shan tea da pad ɗin”

Zazzaro mata ido yayi “Ba wasa nike Maki ba ,banason iya_shege”

“Kaga ina dariya ne?🤨😡” ta haɗe rai kamar hadari

Sauke murya yayi cikin sigar lallaɓawa “Salima ,ko dai kin raba ma ƙawayenki ne ,fada mun gaskiya ta yaya zakiyi amfani da pads guda ɗai_ɗai_ɗai har bakwai a wata guda?”

Ji tayi kamar ya watsa mata ruwan zafi
“Ya Sheikh ! Kawayena suna da gudun zuciya ,tun sanda na aure ke da suka lura suka gane cewa kai din ɗan ƙwaƙwaf ne suka daina cin abin gidana….matan auren ƙawayena kuma sun wadatu da komai mazansu sun tsare masu shi facafaca ba maƙo…”

“Salima in Zaki yimun magana yimun magana kai tsaye ,banason jirwaye mai kamar wanka…”

“Ba jirwaye nake ba gsky ne…wannan binbinin na menene?Ace daidai da pad din da nike using in Ina menstruation sai ka ƙirga? Haba don Allah !”

“Au don bana barinki ki Almubazzaranci ? Fadin Allah ne

_‘Innal budhirina kanu min ikhwanish shayaɗin,Wakanash shaiɗani li rabbihi kafura…..Sadaƙallahul azeem.’_

Yanda ya yanko mata aya nan take shi ya ƙara hasalata . Wai A zalunceka a jawo maka aya kaƙi bi anemi kafurta ka,wohoho auran Sheikh ya zame mata masifa😞.

Ɗaura hannu tayi aka tana sharɓe “Oh Allah, Nikam me nayiwa Ubangijine ya jarrabeni da …da ” sai kuma tayi shiru ta kasa cewa auran shi .

Zarya ya fara yi yana kaiwa da komowa

“La (No) ,Ki amayar da abinda ke ranki meye na gintsewa ? Faɗi mana Salima ,na gane ƙawayen da nike bari suna zuwa gidan nan sun tasar ma bushe maki kunne,haka ne?”

Ko bi ta kansa batayi ba ta samu gefen gado ta zauna tana karkaɗa ƙafa kamar zata fashe.

Da ya gaji da tsayuwa ba’a kulashi ba ,sai ya saki gyaran murya “Uhm uhmmm,Salima ,zan sake siyo maki pads Mai guda 12 in kin hada da 3 nan sun zama 15 ,sai kiyi amfani dasu na waya 3 ,ba abunda ya shafeni in kin ga dama ,ki salwantar dasu a sati ɗaya…”

Tsayawa tayi tana kallonsa ,zuwa wannan lokacin abun ya daina bata mamaki sai tsoro .Cikin Muryar kuka_kuka ta ke tambayar sa

“Ya Sheikh ribar me zakaci in ka ringa ƙididdige pads dina?”

“Bazan yarda da Almubazzaranci bane ba ……… Uhm kinga bari ina ajiye Pad din ma karkice tunda hannuna sun taɓa bazakiyi amfani dasu ba” Ya kare magana yana riritasu akan gado kamar jarirai en uku.

“To a wannan karon bazan ɗauka ba in na kamu da infection auro wata macen zakayi ,don haka indai ina Al’ada pads sau uku zansa ,safe ,rana da kuma daddare kafin in kwanta…”
Ta ɓalle ƙofa ta fice da sauri ta barshi tsaye.

***
Lili

Daga wannan haduwar nasu a kitchen ita da Aiman suka jone kamar mata da miji ,Shaƙuwa na musamman ke tsakaninsu ta yanda har kishin en matan Aiman Lili keyi ,kazalika shima har koran mata manema yakeyi ,don haka duk wanda zai tsaya da ɗayansu sai da yardar ɗan uwansa…..
Iyayen su ba karamin jin daɗi suke ba ganin yanda Allah ya haɗe masu kan ƴaƴa ,to ashe…ashe….

***
Yau week end babu aiki ba school ,ga Aiman ya koma NDA gaba-daya zaman gidan yayima Lili fadi ,In tayi shiru tayi tagumi tunanin Sayyada Salima take ,shedan na kara kawata mata surorinta a ido,wani mugun sha’awarta yina taso mata ,haka nan taji bazata iya jurewa ba ,tayi zumbur ta mike ta shige bathroom ta sheƙo wanka ta fito tana bin jikinta da moisturizer tana raya tashin hankali a ranta
“Yau koda tsiya ko da lallami sai na ƙwaƙuli Du*rin Salima,Bako Sayyada ake ce mata ba ko jaira ce”

1.35pm yayi mata a falon Salima .

Ai Salima tana ganin Lili ta mike da gudu No*nuwa suna tsalle sabal sabal cikin riga mai jikin roba_roba ,ba brazier dama bata damu da sakawa ba,Haka taje da gudu ta rungume ta ,dama kadaici ya isheta ita kadai a gida .

Lili tana jin ƙirjinta ya gogi kan tsinin lausassun dukiyar ƙirjinta ta wani kai hannu ta damƙesu .

Zabura Salima tayi ta ja baya da sauri tana kallon Lili .
Da sauri lili ta waske gamida ɗaura hannu a kai tana sosa ƙeya “Sorry it was a mistake”

Salima baiwar Allah ,washe baki tayi “Hnnnnn La dhair Sadiƙati”(Hnnn ba laifi ƙawata)

Ta nuna mata kujera ita kuma ta wuce dinning area ta buɗe firinji ta tsaya tana kallon drinks din ciki ,guda biyu ne dai kuma tana taɓa Sheikh zai gane . A sanyaye ta ɗauki glass cup ta mirɗe bakin ɗaya ta tsiyayi kadan ,yanda baza a gane ba ta sake ,buɗe wani ta tsiyayi kadan shina ta maida ta rurrufe kamar ba’a taɓa ba ,kana ta tako wajen Lili tana murmushin yaƙe.

“Ƙawata ga drinks ko?” ta mika mata tana zama a hannun kujeran da take.

Lili kallon ɗan tingin drinks din da aka tsiyayo mata tayi kawai ta saki shuumin murmushi
“Hmmm Slay queen knn ,me zanyi da wannan?”

A ruɗe Salima ta dafe baki “Ke ! Wlh dabara nayi na ɗan tsitstsiyayan maki a different bottles saboda kar ya gane”

Dafe baki Lili tayi “Uhm uhm wlh bana sha ,ke kaɗai ma da na gani kawai sai naji duk na ƙoshi😉”

“You too funny,Shiknn bari in sauri in maida masa karma ya dawo yaga an taɓa”

Miƙewarta yayi daidai da shigowar ya Sheikh da ledoji biyu a hannu shaƙare da manya manyan kaji an yanke su an gyaresu .
Yana ganin baƙuwa yaji gaban sa ya yanke ya fadi

“Shikenan ta gayyato mana jarababbun ƙawayenta zasu rage mun aukin kaji,Yooo ko wuya aka bata ai an cuceni”

Yana tsaye a bakin ƙofa ya kasa shiga ya kasa juyawa ,sai ji yayi lili da karuwar muryarta tace “Inayini Sirrr”
Ji yayi kamar ta watsa masa ruwan zafi ,kawai sai ya ɓalle da tsiyan ƙwatan kai.

“Subuhanallahi…Salima,wato ainahin wato sakinki da nayi kiyi hulɗa da kowa har ya kai ki da ƙawance da en isskaaa” Zaro ido lili tayi ,ita kuwa Salima ta daki kirji da tafukan hannunta “Subhanllh Ya Sheikh waye er iskan aina ka gansu kuma”

Nuna Lili yayi da yatsa wacce ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya .

“Gatanan tana min ƙifi ƙifi da ido da wasu dogayen gashin ido kamar fiffiken kaza ? Ji gashin kanta fa a warwaje Ibilisai duk sun gama mata fitsari a ka…”

Furgicewa lili tayi ta fara gyara zaman veil din kanta da tayi rolling ,bakinta na rawa tace “Ya malam ba haka na fito ba saboda na shigo falon ta ne”

“Aihooooo ,to ai na gane tashi maza baki ba mata na ,bazaki lalata mata tarbiyya ba ,maza fita Allah ya shiryeki” ya shiga Zaro mata bayani kalalau kalalau kamar sakarai .

Lili miƙewa tayi jiki a mace ,ba abunda yafi mata ciwo wai waye lashes dinta Kamar fiffiken kaza .

“To ai shknn ,Na bar maka matarka daga zumunci?”

“Eh karki sake zuwa ,in Kuma kika sake shigo mun gida sai na kakkaryaki wlh,banda laifi ma Addini ya sani ,ke kika biyomun mata har gida”

Lili sin sun sun ta fice a gidan ,sayyada tana ta kiran sunanta tayi mata banza shikuma tana zuwa ƙofa yayi zumbur ya daka tsalle da ledojin kajinsa ya shigo falon ,sayyada zata bita ya janyo kafadunta

Ya kama mata magana a kunne cikin rada “Ke dawo ki mana dabgen kaji ,yanzu da na koreta kinga ai yayi mana auki”

Leave a Reply

Back to top button