Bakar Ayah Hausa NovelHausa Novels

Bakar Ayah 24

Sponsored Links

Page 🖤24🖤

 

Bugun ƙofar da ake ne yafarkar da ita daga baccin gajiyar daya ɗauketa.
A hankali take buɗe idonta har ta waresu akan rufin ɗakin,wanda aka haɗa da zare da kuma jarida.
Tashi tayi ta zauna a tsakiyar gafon tareda yin wata kyakykyawar hamma,kaman wanda ta shekara bataci komai ba.
Kallon gabas da yamma kudu da arewa tayiwa ɗakin,ta tabbatar dai ita kadaice ta kwana a ɗakin kenan,angonnata bai shigoba da alama,to mai yahanashi zuwa ta faɗa a ranta,ganin hakan zai bata mata lokacin yasa ta bar ma zancen.
Sake bugun ƙofar akayi a karo na ba adadi,sai sannan ma ta tuna da abinda ya tasheta.
Cikin kasalalliyar tafiyah ta nufi ƙofar tareda buɗewa.
Da indo suka haɗa ido tana rike da kwano a hannunta,saida tayi mata kallon sheƙeƙe kaman bata girmeta ba kafin ta ce.
“Menene kike ta bugun ƙofah kaman naci muku bashi,dama ake yiwa baƙo ne?”
Kallon ta indo tayi na ƴan sakanni kafin ta ajiyemata kwanon ta tafi,danta kula neman magana ne a gun amaryar yayannata,dan tun ranar datayi tujarar nan tasan an kawo musu wata alaƙaƙai ɗin,gwanda ma tayi aurenta ta tafi ta huta,banda mutuwar da mijinta yayi na farko ma da bazata ganta ba bare tayi mata.
Sai bayan taga ƙulewar indo tukunna ta tsugunna ta ɗauki kwanon tareda buɗewa.
Doyace da ƙwai aka soyata sai ƙyalli take,haɗiyar yawu Bombee tayi kafin tace.
“Hhhhh nasan ba wannan abincin suke ci ba ni akayiwa saboda ina baƙuwa,hmmm kar nake ma ko sunsaka guba a ciki fah….kai yaushe zasu saka guda hauka ma suke.
Kai koma menene ciki aradu sainaci,inabanci ba gaba ba samu zanyi ba,kuttt sai yanzu ma na tuna,ance ana kaiwa amaryah kaza in ankawota,dan tsabar iskanci shine suka kawomin iyah doyahhhh wlh sun rainani”
Ai tana gama faɗin haka ta rufe kwanon tareda yin cikin gidan,dan sauri kaman zata tashi sama.
Jauro shida iyalinsa suna karyawa kawai sai ganin Bombee sukayi a kansu rike da kwanon da indo takaimata yanzu.
Suma abinda aka kaimata suke ci,da alama ƙwan irin na kajin gidanne ta ci karo dasu sunata yawo.
Jauro ne yaɗaga kai dan tana kusada shi yace,
“Yarinyah lafiyah koba kya cin doyar ne a samo miki wani abun”
“Da ansan da wani abun aka kawomin doyar,ni nayi zaton nikadai ma akayiwa ashe hardakuma ita kukeci…….kowacce amarya ina ance kaza ake bata idan an kawota sai taci ta ture,shine ni za’a kawomin iya doyah dan an rainan”
“Tohh yarinya wannan fah abincin karyawa ne,kaza kam ina mijinki yakai miki jiya da daddare koh?”
“Jiya yaushe aka kaimin wata kaza,an kaimin zanyi karyane,ni banga wata halitta ba a ɗakin nan bayanni,bare kuma wani abu waishi miji”
Jauro yanajin abinda Bombee tafaɗa yajuya ya kalli Inna daayi da Alamar tambaya.
“Kee daayi yarinyar nan dagaske take goje bai dawo gida ba jiya?”
“Eh….eh to mlm ni banganshi ba nima bai faɗamin inda yaje ba”
“Yanzu a ɗaura masa aure jiya a kawo matar amma kuma yazagaya yayi tafiyarsa,saboda ya maidamu ƙananan mutane kon”
Saida yagama faɗansa Bombee tana tsaye kam batada alamar tafiyah,juyowa yayi ya kalleta tareda cewa.
“Kinga kiyi hakuri yanzun kije kici wannan ,in yaso yanzu zansa Indo ta dafamiki kazar akawo miki,karki damu zan yi masa faɗa kinji,kuma don Allah kar iyayenki su san wannan maganar”
Lallaba Bombee jauro yafarayi,saidai ita duk maganar dayayi bata dameta ba,abinda yafaɗa wanda tagane shine dayace za’a daho mata sai taci ta ture,shine abinda yasakata tafiyah tabasu waje.
Ruwa ta kandama a randar inna daayi tayi wankanta da safe,da ɗauko sabon kaya daga cikin kayan da akayi mata saka.
Doguwar rigace sai mayafinta data ɗora a kanta,takalmi ma sabo da tasaka,daga nan tafito zata fita wani wajen.
Indo ce taga zata fita,da gudu taje da faɗawa inna daayi abinda yake faruwa.
“Inna ga can Bombee fah zata fita waje”
Zaro ido inna daayi tayi tareda saurin fitowa daga ɗakin.
Hanyar wajen ta nufa daidai lokacin da Bombee take shirin fita.
“Ke mekikeyi haka, zaki fita daga kawoki jiyah,anya kuwa baki samu tabun kai ba wannan?”
“Hhhh tabun kai,ai kannawa ma inaga a rushe yake ba tabun kai ba,miye laifi a ciki dan an kawoni gidan jiya zan fita yau,kuɗin wani naci daza’a tuhumeni,ko kuma da wanda nace yaraka ni wani wajene?.
Kinga dan Allah kina bata min lokaci,ina da wani abu dazanyi ne ba zan daɗe ba,inkin dafamin kazar a jiyemin a ɗakina”
“Huh to in daga gidanku aka kawo kazar saikisaka a dafamiki ai,ƴar rainin wayo kawai”
Indo ce tafaɗa cikin hassala,dan taga abin Bombee yawuce a zuba mata ido,tunda take bata taba ganin wacce aka kawota gidan miji jiya da daddare ba,kuma da safe tashirya ta fice,abin ai ko hankali ma bazai dauka ba.
“Badaga gidanmu aka kawo ba,amma tunda ubanki yace a dafa sai an dafa,wlh idan nadawo ba’a dafamin ba,duk saina kashe kajin gidannan a yau basai gobe ba,in kuna tantama ku gwadani dan Allah”
Cikin gadara take maganar tana nuna garken kajin dasuke wani fili a cikin gidan.
Haka ta fita tabarsu basuda ko bakin magana.
Tunda tafita da safe ba ita tadawo ba sai bayan la’asar. Kofar ta tawuce kai tsaye bata ko shiga cikin gidan ba.
Da kwano taci karo a bakin ƙofar ɗakinnata,tana buɗewa kuwa taga farfesun kaji ne guda biyu manya,wani murmushin jin dadi tayi tareda cewa a ranta.
Ashe kuna son kajinnaku da alama,da karku yimana ku gani,banda shiga shirgin mutum ina ruwanku da fitata,ko baban bai isa hanani fitaba ballanta ku.
Zama tayi baje baje taci tayi nakk ta kora da ruwa,kafin ta tuntsire a wajen sai bacci,da alama dama a gajiye ta shigo gidan.
Lokacin data buɗe idanuwanta duhu ya fara,rana tana shirin faɗuwa,tashi tayi ta cire kayan jikinta tareda sake yin wani wankan kafin magriba tayi.
Ana sallahr magriba taji muryar wani gardin a tsakar gida,kana jin maganar kaji irinta tantirannan wanda suke yinta a shashshaƙe cikin isa da gadara.
“Huh inna kenan me kike so kicemin ita harta ta isa ma tafice batareda izinina ba,menene take taƙama dashi dan babarta a garinnan,hmmm zakuwa ta yabawa ayah zakinta,ki barni da ita,zanyi maganinta,zatayi laushi ta yanda sai abinda naga dama zata aikata”
“Yawwa goje nasan bazaka bani kunyah ba,so nake kamaida ta komai na gidan nan ita zatayi shi,badai tana ji da yarinta ba.
Yawwa wai ina ka tafine? Ran mlm ya baci sosai da fitar ka jiya.
Bai kamata ace a kawomaka amaryah jiya baka nan ba”
“Kinga inna wai miyene za’a takuramin dan kawai nayi aure,nine fah nace zanyi aurennan ba wani ne yasaka ni ba,dan haka abinda naga dama zanyi.
Sannan naji kina wani zancen zata dunga yi muku aiki,kar na sake jin wannan zancen,nina kawota gidannan,nikaɗai nake da ikon sakata aiki ba wani ba. Tana ina tadawo ko kuma har yanzu tana waje?”
“Bamu sani ba,da babu wanda yaga shigowarta”
Bagazam bagazam yayi hanyar ƙofar tasu kaman zai tashi sama.
Duk abinda suke Bombee tana jinsu,wani murmushin gefen baki tayi tareda cize baki jin furucin mijinnata. Tana nan tsaye a baranda kuwa ya shigo ƙofar yana muzurai.
“Oh kin dawo ma kenan,nasan duk abinda nake faɗa kina jina,ina so kifaɗamin gidan uban wa kikaje dazu,sannan kuma da izinin wa kika fita?”
Shuru yayi domin bata damar amsa tambayarsa,amma har tsawon minti biyar Bombee bata ce komai,saima juyawa datayi tashige ɗakin.
Hakan datayine yaƙara ƙular da goje,dan dama a sama yake ya bankami angurrr.
“Ke ina miki magana kika yimin banza,da uban me kike taƙama”.
Nan ma batace masa komai,hakanne yasa cikin bazata ya sauƙe mata mari a kuncinta na hagun.
Dafa wajen tayi da hannunta na daman,tareda saka manyan idanuwan ta a cikin jajayen nasa idon.
Ko ba’a faɗaba duk wanda ya kalli idon nata a bayyane zai hango tarin baƙin cikin dayake ciki.
Rintse ido tayi tareda haɗiyewa abinda yake shirin taso mata,matsawa tayi daga gabansa takoma bakin gadon ta zauna tana kallon wani wajen daban.
Har sannan bata buɗe bakinta ba ballantana wani harafin yasamu damar fita.
Takowa inda take yasake yi tareda shafar gefen fuskarta,sannan kuma yafara magana cikin sanyin muryah mai cikeda yaudara dakuma son cikar muradi.
“Ohh kiyi hakuri fah,kece kika batamin rai sannan kika kaini bango,amma idan ba haka ba mai zai sa nakai hannuna kan wannan lallausar fuskarta ki da niyyar cutarwa.
Saidai karki damu,indai zaki kasance mai biyayya hakan bazai sake faruwa ba,idan san ladabtaki ma ta hanyar jin daɗi,nasan zaki so hakan koh??,har yanzu ban huce da fitar dakikayi ba,saboda bansan wajen wa kikaje ba,saidai zan hukunta ki fa hanyar samunki akan shimfiɗina.
Banajin zan iya binki ta hanyar sauƙi,duk da kuwa kedin sabon hannunce,dan daga ganinki zakiyi daɗi sosai,dannasan baƙaramin shirya min ke akayi ba”
Yana maganar yana matsowa inda take,har saida yazamo ya zauna a bayan ta yana shafa bayan ta.
Saƙalo da hannunsa yayi zuwa cikinta,a hankali yaɗaga rigar ya zura hannunsa yana shafa fatar cikinta.
Saurin buge hannunsa Bombee tayi tareda tashi ta tsayah tana kallonsa,jin yana mika hannunsa sama zuwa ga albarkatun jikinta.
Sai a sannan Bombee take ƙaremasa kallo saboda hasken da fitilar ɗakin tabayar ta batir.
Farine tass yana da gashin baki,sannan kuma yana ɗan jiki sosai,musamman ma tasaman ƙirjinsa,kana ganinsa kasan ƙaƙƙarfane sosai,kuma babu alamar mutunci a tattare dashi.
Murtuƙe fuska yayi ganin yanda Bombee ta buge hannunsa lokacin dayake tabb ta kaiwa ga muradin ransa.
Tashi yayi yafara takawa zuwa inada take,yana nufarta tana matsawa harsaida yakaita bangon ɗakin.
Kallon idonsa takeyi wanda suka fara ƙaduwa ganin yanda Bombee take sauke numfashi kirjinta yana ɗaga tacikin rigar dake jikinta.
Bata ankara ba sai gani tayi ya sutale dogon wandon dage jikinsa,zaro ido tayi kaman zasu faɗo ganin abinda tayi arba dashi.

 

 

_*Sadi-sakhna ce*_

Share
Comment
Like
Follow
Fisabilillah 🙏🏼

 

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK1_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

 

*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03

*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna

______________****_______________

 

 

Leave a Reply

Back to top button