Hausa NovelsHausa NovelsTabarmar Kashi Book 2

Tabarmar Kashi Book 2 Page 7

Sponsored Links

Book 02 Page 7

Har afifa ta gama wayar idanun saahar yana kan wayarta tana chart,ido tadan zuba mata zarginta yana sake tabbata,yadda sãahar me shakulaton bangaro tare da nuna halin ko inkula da dukka abinda ya shafi bikin ya sake tabbatar mata da zarginta,uwa uba ko sau daya ita dai idanunta basu taba nuna mata kiran toufeeq jarma ba

“Kina jina muna magana amma bakice
komai ba?” Dan duban afifan tayi,sai ta saki
murmushi

“To me kikeso nace?,salon nayi rash-in
kunya?,kuma ma ai kin gama komai,duk
abinda nake bugata ko zance ke kin isar
min,duk abinda ya samu ayi,wanda bai zama
lallai ba ko bai samu ba sai a haqura ko?” Kai
afifa ke girgizawa tana kallonta

“Amma dai ba haka kikayi ba a aurenki da
adamu” ajiye wayar tayi gefe wani murmushi
dake cakude da zallar nishadin da takeji
gasan ranta ya kubce mata ta zuro gafafunta
gasa cikin zummar shiga bandaki sannan ta
amsawa afifa

“Banda abinki hajiya afifatu,ai kullum dan
adam dada wayo da hankali yakeyi ko?,don
zanyi aure bawai ba hakan yana nufin na
mance da asalin su waye maza ba,ko kuma na manta radadi da daci da suka dasawa rayuwata ba”

“‘Anzo gurin” afifa ta fada tana zagayowa gabanta da sauri,ta jawo stool ta zauna akai tana fuskantar sãahar wadda ke mata duban mamaki

“Bestie bandaki zan shiga,yaa haka?”

“Inason nasan gaskiya ne bestie,yau ashe anzo wata gaba da zaki dinga boyemin wani abu a rayuwarki? meye ainihin gaskiyar magana akan aurenki da toufeeq jarma,duk yadda naso na basar nayi kaman ba komai na kasa bestie,ki gayamin gaskiya” murmushi tayi hankali kwance

“Ki barni naje nayi fitsarin mana”

“Na barki” ta fada tana dubanta. A nutse ta miqe ta wuce bandakin,ba jimawa ta dawo ta koma inda ta tashi ta zauna. Komai ta warware mata,abun sai ya sanya afifa murmushi me kama da dariya

“Allah ya sanya alkhairi,abu kuma yay kyau,hakanan hankalina ya kwanta da bayananki,amma ke dashi dukka ku shirya ranar karbar sakamako a tsakaninku”

“Sakamakon me?,kefa wani lokacin kin fiya jaye jaye”

“Lokaci zai bayyana komai”. Tasan halin afifan da iya saqa zance,sai kawai tabar zancanta,ta maida qafafunta saman gadon tayi kwanciyarta cikin nutsuwar data jima bata jita cikin ruhinta ba. Yayin da afifa ke duba kiran da ya shigo mata,sajjad ne,migewa tayi ta dauki scarf dinta ta fice a dakin, sãahar data fuskanci meke faruwa ta bita d kallo tana tabe baki

“Hmmm,soyayya manya,mun jima da dawowa daga rakiyarta,mu da ita ko a lahira mun raba jaha” ta fada qasa qasa kamar me qunquni tana gyara kwanciyarta,sai kuma ta tuna zata yiwa maama gyaran wardrobe,don haka ta miqe ta sauko,ta kama gashinta me santsi ta daureshi waie daya,ta dora hula a kanta ta zura slippers ta fice.

********Ya jima a zaune yana juya wayar hannunsa,dukkansu mamaki suke bashi qwarai, nadeeya maji ga kuma mai gayya mai aiki fadeela. Yadda suke nuna tsantsar zakwadi da kuma farinciki akan wannan auren abun daure masa kai yakeyi. A yau sun jima suna waya da majiirin wayar da basu taba yin me tsaho irinta ba,duk da cewa kamar dai ko yaushe itace tayi kiransa bashi ne yayi kiranta ba. Dole bayan ya gama mamakin lamarin ya ajiye wayar gefe,dai dai lokacin sajjad ya shigo gurin bakinsa dauke da sallama.

Guri ya samu ya zauna yana kallonsa yana kwance cikin lounge chair

“‘nata jira naji daga gareka” kyawawan zagayyun idanunsa kawai ya daga ya kalli sajjad din

“Game da me fa?” Takaici ya kama sajjad din,kamar bazaiyi magana ba amma ya cije

“Ba aure zakayi bane malam?”

“Aure zanyi sai mene?”

“Bakasan kana da buqatar yin wasu abubuwa ba,mace fa zaka ajjiye cikin gidanka,a ina zata zauna?,ka hada mata lefe?,dinkunan biki da sauransu”

kamar bazaice komai ba,sai ya miqe ya zauna sosal sannan ya zura qafafunsa qasa yadda zaiji dadin zaman,idanunsa akan sajjad din

“Ce maka akayi wani aure ne duk da za’a tsaya masa wannan hidimar? kawai a daura ta shigo taci gaba da aikinta,ni kuma na bata gurin zama da ciyarwa da suttura that’s all,duk wadan nan abubuwan da kake jerowa sai ku masu auren farko,tun wani zamani da ya shude muka rufe wanan batun” sai ya miga hannu ya janyo plate din apple da Jacob ya ajiye masa.

Ido sajjad ya zuba masa,kaman zaiyi magana sai kuma ya fasa,ya saki qaramin murmushi sannan ya miqe

“Zaka gane kurenka,indai macece ba’a cika musu baki,i pitty you duk lokacin da ka fada tarkonta,saboda haka kabi a hankali,shawarace kyauta na baka” baice masa komai ba sai qaramin miskilin murmushin da ya subuce akan fuskarsa,wannan maganar ta sajjad bata da banbancin da tatsuniya a gurinsa. Banda fadeela,babu abinda zai sanya ya biya sadakinta ta amsa sunan matarsa a bakunan al’umma bare azo gurin da sajjad din ke magana a yanzu.

*********Karo na biyu ya sake gwada kiran qanwar tasa,wannan karon ta shiga sabanin lokutan bava da kiran yake yankewa.

Spoon din hannunta ta ajiiye lokacin da kiran ke shigowa,wani hamshagin murmushi ta saki,yadda yayan nata yake bata kulawa tun daga wancan zamanin zuwa yanzu yana y mata dadi matuga,kuma har yau bata canza zani ba sanadiyyar jajircewarta

“Assalamualaikum barka da warhaka yaaya” hajiya qarama ta fada bayan ta saka wayar a kunnenta

“Yauwa barkanki dai FAUZIYYA” Cikin kulawa suke gaisawa da juna,ya tattambayeta yanayin kayan da taje siyowa a qasar. Tsahon mintuna goma suna tattaunawa sannan ya fara maganar da itace maqasudin kiran

“Kwanaki kusan bakwai ina kiranki na kasa samunki har ina tunanin akwai matsala ne”

“Babu yaaya wani lokaci ajiye wayar nake a nan hotel idan banason yawan kiran”

“To yayi kyau, Allah ya taimaka,amma inajin ai dole ki yanki ticket na dawowa sati me zuwa ko satin sama ma,don yaronki ya tashi aure,Allah ya amsa addu’armu” Wani irin mummunar faduwar gaba me hade da wani tashin hankali ne suka rufto mata,tamkar wadda ake juyewa duwatsu saman kan nata

“Yaron….na? wanne kuma?” Ta fada tana qoqarin boye gigicewar da tayi. Dan murmushi dr jarma ya saki

“Kina da wani d’an ne bayan toufeeq?,inda
‘yarki nace saiki tambaya nadeeya ko
HASEENA?” Sarawa kanta yayi da matsiyacin qarfi,wani zazzafan gumi ya karyo ilahirin jikinta ta kowanne sashe,taji kamar an saka allura da zare ana daure kanta,cikinta ya juya take bayan gida ya matsota

“Yaya?,ka manta haseena naketa ajjiyewa toufeeq? tunda anyi na farko ba’a dace ba?,ita kanta yarinyar bata taba kula kowa ba saboda ta sanya ranta akan TOUFEEQ din,ko yanzu haka sati uku ne kacal ya rage ta gama karatunta ta baro hannun babanta ta dawo nan nigeria don su daidaita kansu ita dashi”

“Banda abinki mijin mace hudu ne faidan yaga yana da ra’ayi uku ne sauran da zai cike ma,sannan ita kanta yarinyar bata da matsala,na santa farin sani,itace wadda ta taba rige president na kamfani na,kuma kema kin santa,wadda ke kula da fadeela kafin tahowarki”

“Kanbun uba!” Ta fada gasan ranta har bakinta yana motsawa

“Nanny fa yaya!” Ta fadi cikin daukaka sauti

“Ba nanny bace fauziyya,kawai tayi sha’awar aikinne,amma badon ta rasa komai ko kuma bata da gata ba,infact ‘yar Dr mamman girema ce,wanda kikaso a baya,kikace matarsa ce ta hanashi sauraro da kulaki” wani bala’in kawai bayanan yayan nata suka qara mata,Dr mamman da baya ganin kowacce mace a gabansa sai matarsa?‚buzuwar nijer,wadda koda wasa mamman din bai taba kallon wata mace ya taya da zummar zai aureta ba saboda yadda ya samu kula biyayya da dukkan wani jin dadin rayuwa da d’a namiji yake bugata da muradin samu daga wajen diya mace? ‚matar data wahalar da ita ta kuma kafa tarihi ta zama mace ta farko da tayi mata shamaki da abinda takeso? bayan tafiyarta toufeeq ya koma gidan,yarinyar tayi amfani da wannan damar kenan ta ja hankalinsa? har sai daya kamu da soyayyarta me zafin da ya kasa sukuni cikin sati uku kacal ya nema aurenta?,to itakam fauziyya tana me? wanne irin sakewa tayi haka?. Kamar dr jarma shima yanason canzawa,ta yaya yake maganar idan toufeeq din yana so?,bata saba jin wannan kalamin daga bakinsa ba a duk sanda ta bugaci wani abu daga garesa, komai tsananinsa kuwa

“Ya kikayi shuru?” Ya jefa mata tambayar. Cikin duniyanci da wayancewa tace

“‘Ina lissafin randa zan dawo ne,da abinda ya kamata na taho dashi na hidimar biki,sanann wannan karon abun yayimin banbarakwai ne,ba kamar aurensa na baya ba da akayi komai dani,wanann lokacin labari kawai naji” dan murmushi dr jarma yayi

“Kinsan kowanne aure da yadda yake
Zuwa,amma dai batun haseena karki damu,indai sun daidaita kansu shikenan,zanfi kowa farinciki da wannan,tuwo na,mai na”

rintse ido tayi tana jin zafin abinda yake fadaidan sun daidaita kansu kuma?,ba ruwansa kenan bazai shiga ba bare ya tilasta yiwuwar abun?. Har yanzu batasan me yasa ta kasa bude wata qofa guda daya tal ba,duk da tarin nasarorin da taci take kuma kan ci,amma har yanzu qofar bada umarni ga toufeeq bata kammala buduwa. A duk abinda ta umarta da yayi,musamman abinda ya shafi janibin rayuwarsa akwai yiwuwar yayi ko kada yayi,bata manta lokacin da ta umarceshi da kada ya dawo da Ameesha,sai ganinsa tayi da matarsa a wancan lokacin,ribar kawai da taci shine watsewar lamarin da yayi babu jimawa dutse a hannun riga. Da tana da wannan cikakkiyar damar,to da a yau zata umarceshi da ya dakatar da komal,ya ajjiye batun auren ya saurari zuwan yaruwarsa nan da sati uku masu zuwa.

Gefe guda babu abinda ya sake dagula mata lissafi irin haseena,batasan yadda zata tunkareta da zancan ba,bata iya jurewa tashin hankali,bata da juriya sam ko iya cinye abu,ta tabbatar babban bala’i da tashin hankali ne zai biyo baya. Dole tayi iyakar bakin gogarinta na ganin ta toshe dukka wata kafa da zata zamu labarin wannan auren,kafin sannan ta shirya fada mata tare da yi mata bayanin komai yadda zata fuskanta. Bacin ran haseena dai dai yake da nata bacin ran,ita daya qwal ta mallaka a duniya,tafi qaunarta sama da komai a rayuwarta,kai koda kuwa dukiyarta da take mutuwar so,take tattali da fadin tashin tarawa tsahon shekaru,ai dukka tana yine saboda ita haseena din.

Migewa tayi dole tsaye,tanajin kamar hawan jininta zai tashi ta zare rigar jikinta tana jin duniyar na juye mata cike da tashin hankali, tashin hankalin data jima bata afka cikinsa ba,tsahon shekaru batasan tashin hankali ba,saboda dukka abinda ta nema tana samu,zallar farinciki da wanzuwar kwanciyar hankali kadai ta sani,sai gashi yau yarinyar da suka dauka aiki a matsayin nanny tana neman ruguza duk wani lissafi nata data dauki shekara da shekaru tana yinsa. Inda ace tana da masaniyar abinda zai faru kenan,da kanta zata koreta kafin tabar gidan,amma inaa.…..sai gashi wani qatoton tsautsayi ya gifta wanda ba zata taba barinsa ya zama qaddara ba.
Dole ta qara gaba itama, haseena ce kadai tafi dacewa ta mallaki toufeeq din,yadda ta qarasa rainonsu har suka girma,lallai su sukafi cancanta suci amfaninsa.

Qara kadai wayarta tayi amma sai da gabanta ya fadi,bakinta yahau addu’ar Allah yasa ba haseena bace don batason tayi kiranta ta fuskanci akwai wani abu. Hajiya mansura ce,sai da taja tsaki sannan ta koma ta zauna,cikin ranta tana jin me yasa ma ta
¡awo matar nan ta maidata daya daga cikin ahalinta?,a shekarun nan gaba daya tsanarta takeji cikin ranta. Sai da wayar ta kus tsinkewa sannan ta daga. Akwai tashin hankali me yawa cikin muryar hajiya mansura sanda take magana da hajiya qarama

“Kinji abinda yake faruwa?”

“Naji,menene?”

“Baki tambayi halin da labiba take ciki ba,kin ganta can ta kulle kanta a daki,nayi mata maganar duniya taqi fitowa,ki taimaka don
Allah ki kirata kuyi magana ko hankalinta zai kwanta” yatsine fuska hajiya qarama tayi tana iin kamar ta rufeta da duka ta wayar

“‘Mansura!” Ta kirayeta da tsurar sunanta,mamaki ya hanata amsawa,itama kuma bata jirayi ta amsa din ba ta dora da jawabinta

“Yanzu labiba ta fara kuka ai,don bata dace sam da toufeeq ba” mamaki ya kusa sanyawa hajiya mansura faduwa,sai data lalubi gurin zama

“Me kike fada ne?,ko kin canza daga alqawarin da kikayi mata?”

“Tun wacce shekarar?,ai daga lokacin da haseena tazo hutu tun tana da shekara sha takwas,ta nuna muradinta akan TOUFEEQ alaqawarin dake wuyan labiba ya sauka ya koma kan haseena,ko don kinga inata muku kara ke da ita?,ban fito kai tsaye na nuna mata bazata sameshi ba?” Ta qarashe maganar da tambaya,tambayar da rawar da bakin hajiya mansura yakeyi yasa ta gaza amsa mata

“Ai na dauka kuna da qwaqwalwar da zata gaya muku gaskiya,me muka hada daku da zamu dauki TOUFEEQ mu jingina shi da yarinyar da har yanzun ba’a da tabbacin ubanta ubanta ne!”

“Ke fauziyya dakata!,ya isheki haka!” Hajiya mansura ta fada cikin matsanancin bacin rai.
Shu’umin murmushi hajiya garama ta saki tana jinjina kai

“Uhmmm,ni kike dagawa murya ko mansura? ni ba? inajin kin manta cewa ba yau na fara fidda matan wana daga gidansu ba,wadda ma take da zuri’a damu na kadata ta koma qasarsu ballantana ke da babu abinda muka qaru dake sai gatoton kashi da kike ajjiyewa suckaway,ki iya bakinki idan ba haka ba nan gaba kadan zakiyi nadamar da zata zame miki har qarshen rayuwarki”
[14/09, 7:44 pm] Mimah Yusuf: *HUGUMA*

*_TABARMAR KASHI_ *

Leave a Reply

Back to top button