Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 14

Sponsored Links

 

📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

 

*SAKAYYAH*

_Pape 14_

 

NA

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

*Free page ne ƴar uwa saura uku kacal mu gama free page, har yanzu baki makaraba ki biya*

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin wani kanki. SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana sai in saki a Group, ɗin da zan rinƙa posting.*

 

 

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

 

_Ina kuke Ma’aurata masu sha’awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau’ikan sirrin sahihan magungunan ma’aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki…Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba’a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al’khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni’ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni’imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu…Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu’umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba…._  _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan  Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu’uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)…Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji  Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu’uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa ‘yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma’aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba’a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma’aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah ‘yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci…._

 

 

 

🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,

 

 

Washe garin washe gari.

Da daddare  watan Ramadan ya bayyana.

 

Haka yasa dukkan ɗauka cin Musliman duniya suka cika da farin ciki tare da yin niyan ɗaukar azumin watan Ramadan ɗin, kana kowa yana shirya bukatunsa dan miƙa su ga Ubangiji Mabuwayi gagara Misali.

 

Washe gari Ranar Litinin gaba ɗaya al’ummar Musulman duniya sun tashi da azumin watan Ramadan abakinsu gaba ɗaya ɗaukan farko ɗauka ɗaya akayi duk duniya abinda aka daɗe ba’a yiba tsawon lokaci mai yawa wannan shekarar ansamu  kowa na cike da farin cikin wannan al’amari azuciyar musulmai.

 

Da daddare Misalin ƙarfe 9:00 pm Babban masallacin juma’a dake ƙofar gidan Sarki cike yake da.

Al’ummar Musulmi maza da mata wanda duk shekara idan aka shigo Ramadan bayan an idar da sallar isha’i M Jameel da Moddibo ke gabatar da Tafseer Alkur’ani mai girma duk shekara Moddibo ke jan baƙi yayin da M Jameel keyin Tafseer yana fassarawa.

 

Masha Allah kamar yanda suka gabatar ashekarar Bara ayau ma hakane Cikin Masallacin Maƙil yake da dubban jama’a yayin da Moddibo ke zaune akan wani ƙayatenccen kujera gabansu babban table ne dake ɗauke da system jikinsa sanye da Jallabiya Armygreen mai yauƙi da sansti kana gaba ɗaya ilahirin jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi tularensa, idanunsa alumshe yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake.

Yayin da M Jameel ke zaune gefensa cikin shiga na alfarma Bugaggiyar shadda ce fara sol anyi masa ɗin kin ƴar ciki da gariya sai hula baƙa sosai yayi kyau gaban jikin rigarsa maƙale da microphone.

 

Cikin tsantsar nutsuwa da kamala M Jameel ya hura microphone ɗin tare da gyara zamansa kana yace.

_“A’uzubillahi Minal Shaiɗanir rajeem Bismillahir Rahmanir Rahim. Innal hamdillah Nahmud wanastainuhu wanastaghfiru, wa’nazubillahi min shuriri anfusna, wamin sayyi ati a’amalina, manyah dillahu fala mudillah waman yudil fala hadiyala, Wa’ash hadu Allah ilahalillahu wahdahu lasharika lahu Wa’ash hadu Anna Muhammad Abduhu warasuluhu._

Ya ɗan sauƙe numfashi tare da sauƙe numfashi kana ya sakin ajiyar zuciya sannan ya cigaba da cewa.

_“Ya ayyuhallazina amanut taƙullaha haƙƙu tuƙatihi wala ta mutunna illah wa’antum Muslimun ya ayyuhan nabiyu taƙu rabbakummalazi wahida wakalaƙa minha zaujuha wabassa min huma rijalan kasiran wani sa’a wattaƙullahal lazi tasa aluna bihi wal arhama innalaha bikum kana alaikum raƙibaaa_

 

Baki ɗaya ciki da wajen masallacin ya kacame da sowa da sassarfan waɗanda ke harabar masallacin da suke shigowa da sassarfa.

 

M Jameel kuwa idanu ya lumshe tare da buɗesu kana yace.

“Amma ba’ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum Warahmatullah Wabarkatuhu”.

 

Gaba ɗaya cikin masallacin da harabarsa suka amsa da faɗin. “Wa’alaikum Salam Warahmatullah wabarkatuhu”.

Gyara zama M Jameel ya yi tare da kallon ɗumbin jama’ar dake masallacin kana a hankali ya numfasa sannan yace.

“Insha Allahu zamu cigaba da Tafsirin Alkur’ani mai girma kamar yadda muka saba, zamu kuma ɗaura daga inda muka tsaya bara. A cikin suratul Nisi’i awancan shekarar mun tsaya akan aya na ɗaya wanda ya zamana shi muka karanta Ramadan ya ƙare cikin ikon Allah gashi ya sake sada mu acikin watan wanda da yawa wasu daga cikin wanda mukayi tafsiri dasu wancan shekarar yanzu basa nan kana da yawa wanda muka fara ayau da ƙyar zamu ga ƙarshen amma muna roƙon Allah daya nuna mana ƙarshen wannan wata mai falala da kuma al’barka  lfy”.

 

Baki ɗaya wajen suka amsa da faɗin.

“Ameen”.

Domin wasu daga cikin masu sauraron karatun suna zuwa ne saboda yanda M Jameel ya ƙware awajen Tafseer gashi kuma yana da zafi nama da kwarjinin tafsir.

Juyawa M Jameel yayi tare da kallon Moddibo da kansa ke ƙasa ya tsirawa System ɗin sa idanu ya gyara zamansa tare da cewa.

“Bismillaha Alaramma  jeka cikin Suratul Nisa’i ka karanto mana muji abinda Allah ma ɗauka kin sarki yake faɗa”.

 

Jinjina kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa kana ya jingina bayansa da jikin kujera sannan ya lumshe idanunsa cike da nutsuwa ya motsa laɓɓansa kana yayi gyaran Murya cikin Sanyayyar muryarsa mai daɗin saura da sanya nutsuwa  da ratsa zuciyar bani adam ya fara kamar haka;

“Bismillahir Rahmanir.

 

Gaba ɗaya illahirin yaƙin da sautin muryarsa ya ratsa kunnuwansa, sit sukayi babu abinda wani sauti ko hayaniya, wurin yayi sit kai kace babu mai rai a wurin bare numfashi, gaba ɗaya an nitsu, wanda hakan kuma a jinin Modibbo yake, duk hayaniyar wuri muddin yayi basmalla a take kab za’a nutsu.

 

Idanunsa ya ɗan lumshe kana ya buɗe su a hankali yana kallon taron al’ummar Annabi dake tare maƙil, cike da nitsuwa ya fara karatu cikin zaƙin murya ya kawo aya ta biyu cikin suratul Nisa.

.2-Wa’atul ystamaa amwalahum,Wala tatabaddalul khabisa biɗɗayyir,Wala ta’akuluu Amwalahum Ila amwalikum,Innahu kana huban kabira”._

Atake mutanen da masallacin suka shiga lumshe idanunsa yayin da wasu suka shiga sakin ajiyar zuciya Moddibo mutum ne mai ƙwarjini duk yanda waje keda hayaniya da zaran sautin muryarsa ya fita zakaji wajen yayi stit.

M Jameel kuwa ya Jinjina kai yayi yana mai jin ayan na ratsa sa cikin yanayin faram-faram ɗinsa yace.

“Gabaaa jeka aya ta gaba Aramma muji mai Allah yace”.

Sanyayyar iska mai sanyi Moddibo ya furzar tare da gyara zamansa kana ya cigaba da jan Ayar kamar haka;

_3-Wa’in hiftum Allah tuƙsiɗu fil yatama fankihu ma ɗabala lakum Minal Nisa Masna wasulasa waruba ,Fa’in hiftum Allah ta’adilu fawahidatan Auma malakat aymanukum,Zhalika adnaa Allah ta’aluun_.

 

Cikin jin daɗin sauraron muryarsa mafi yawan Ƴan matan dake sauraron karatun suka lumshe idanunsu suna burin Allah ya mallaka musu shi amatsayin mijin Aure.Yayin da magidanta suke burin ƴaƴan su suzama kamar Moddibo.

Cikin ɗaga sauti M Jameel ke gyaɗa kansa kana yace.

”Je gaba Aramma muje gaba muji me Ubangiji yace”

 

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da jingina bayansa ajikin kujera kana ya lumshe Idanunsa tare da gyara system dake gabansa ya cigaba.

_“4-Wa’atunnisa’a saduƙatihinnah Nihylah,Fa’in ɗibna lakum anshay’in minhu nafsa fakuluhu hani’am mariyya.5-Wala tu’utussahafa’u Amwa lakumallati ja’alallahu lakum ƙiyama warzuƙuhum fihaa warkusuhum waƙulu lahum ƙaulan ma’arufah”_.

Ya ƙarashe jan ayar cikin zazzaƙar muryarsa.

Shiko M Jameel  gyara zaman Microphone dake gabansa yayi kana yace.

“Masha Allah Aramma”.

Atake masallacin ya kaure da kabbara wasu na buri da fatan Allah ya azurtasu da baiwan murya irin na Moddibo da yawa daga masu zuwa Tafseer ɗin suna zuwa ne Saboda zaƙin muryan ƙira’ar Moddibo da kuma nutsuwarsa musamman yanda Laudspeaker ke fitar da zazzaƙan murya Moddibo tare da sanya nutsuwa,

M Jameel da Moddibo sun iya Tafseer domin shi M Jameel mutum nai mai zafin jini Moddibo kuma ya kasance mutum mai sanyi komai nasa cikin nutsuwa yake hakan yasa mutane ke matukar ƙaunar Tafseer ɗin su mutane kan tsallake unguwar su suzo  su saurari nasu.

 

M Jameel kuwa cike da tsantsar ƙwarewa da kuma sanin abinda yake yi ya fara tafsirin ayoyin bayan yayi muƙaddima ya fara fassarar kamar haka :

_”Aya ta(2) Allah madaukakin sarki nacewa

(Kuma ku baiwa marayu dukiyoyinsu kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau.kuma kada kuci dukiyoyinsu zuwa ga duniyoyin ku, Lalle shiya kasance zunubi ne mai girma”_

Mafiya yawan mutanen dake wajen jikinsu ne yayi sanyi domin ji sukayi Ayar tamkar dasu take magana cike da nutsuwa suke sauraren.

M Jameel ya numfasa kana ya cigaba da cewa.

_“Aya ta (3) Allah yana cewa.

_Kuma idan kunji tsoron ba za kuyi adalci ba acikin marayu to(akwai yadda za’a yi)ku auri abinda yayi muku dai-dai daga mata biyu-biyu,Uku-uku ko huɗu-huɗu sa annan idan kunji tsoron baza kuyi adalci ba to ku auri guda ɗaya ko kuwa abinda hannayenku na dama suka mallaka.wannan shine mafi kusantar zama baku wuce haddi ba”._

Numfashi wasu daga cikin mata masu kishi suka saki jin Allah da kansa ya bawa maza ikon su ƙara aure yi shin to wai menene abin kishin hauka duk da cewa dole ne ayi kishi amma ya kamata su rika sassauta.

 

M Jameel kuwa juyawa yayi tare da kallon Moddibo daya zubawa system ɗin sa idanu numfashi ya sauƙe cikin yanayin zafin jinjinsa ya cigaba da cewa.

_“Acikin aya ta (4). Allah Mabuwayi gagara Misali cewa yayi.

Kuma ku baiwa mata sadakin su sauƙin bayarwa sannan idan suka yafe muku wani abu daga gareshi a daɗin rai to kuci shi da jin daɗi da saukar da hadiya”._

Ya ɗago kansa tare da kallon jama’ar dake masallacin cikin ɗaga sautin murya ya gyara zaman hular dake kansa kana yace.

“Kai Kuce Allahu Akbar”.

Atake masallacin ya ɗauki kabbara da faɗin Allahu Akbar Allah ya ƙara maka nisan kwana.

Murmushi yayi tare dasa hankie ya goge gaban goshinsa kana ya cigaba da cewa.

 

_“Kada ku baiwa wawaye  dukiyar ku Wanda Allah ya sanya ta agareku kuna tsayuwa (ga gyaranta)kuma ku ciyar dasu cikinta,kuma ku tufar dasu kuma ku gaya musu magana sanyayya ta alkhairi”_.

Atake masallacin ya jure da kabbara cike da jin daɗin tafsirin.

 

Agefen ɓangaren mata Asma’u ce zauna tare da Innayi sai Khausar dake can gabansu Matsawa Asma’u tayi tare da taɓa bayan Khausar,juyawa Khausar tayi ganin Asma’u yasa tayi murmushi tare da miƙewa daga inda take ta dawo kusa da Asma’u.

Tana murmushi ta gyara zamanta tare da cewa.

“Asma’u ya Ummi amma ɗazun da mukayi waya baki ce min zaki zo Tafseer ba”.

Murmushi Asma’u tayi kana tace.

“Ai nadawo gidan Innayi da zama zan riƙa taya ta aiki sai Azumi ya ƙare zan koma gida”.

Bata jira jin Abinda Khausar zata ceba ta juya tare da kallon Innayi data tattara nutsuwarta zuwa ga tafsirin da  jikokin ta keyi hannunta Asma’u ta riƙe kana tace.

“Innayi ga Khausar ƙawata”.

 

Murmushi Innayi tayi tare da kallon Khausar,Ita kuwa khausar ƙasa tayi da kanta cike da nutsuwa  ta gyara zaman hijabinta kana tace.

“In wuni ya ibada?”.

Murmushi Innayi tayi tare da cewa.

“Lafiya lau Alhamdulillah”.

Haka nan Khausar taji tsohuwar ta burgeta Kallon Asma’u tayi cikin ƙasa da murya ta kalli Asma’u tare da cewa.

“Wacece?”.

Asma’u na murmushi ta juya ta kalli Khausar kana tace.

“Kakar Moddibo ce”.

Taɓe baki Khausar tayi kana tace.

“Itakam tana da kyawawan hali ba iri jikanta ba ko ina ya gado baƙin zuciya ohon mishi mugu”.

Dariya Asma’u tayi amma batace Komai ba.

 

Bayan M Jameel yayi tafsirin Ayoyi guda goma,ya duba lokaci ganin ƙarfe goma saura minti takwas ya numfasa tare da faɗin.

“Wasubhanakal Lahumma wabi hamdi Nash’hadu Allah’ila ha Illah anta nastagfirka wanstubu Ilaik”.

Ya rufe system ɗin sa tare da cewa.

“Dan Allah kamar yanda aka saba maza suyi haƙuri mata su fara fita”.

 

Sai da duk matan suka gama fita kafin maza acan mota Innayi da Asma’u suka jira M Jameel da Moddibo har gida aka kaisu bayan sun isa gidansu Moddibo kasancewar duk Ramadan agidansu Moddibo M Jameel keyi saboda yawan hidimarsu.

Suna isa kai tsaye sashen Moddibo M Jameel suka nufa Asma’u da Innayi kuwa sashen ta suka nufa suna shiga ciki Innayi ta cire dogon hijabin dake jikinta tare da kallon Asma’u tana ajiye hijabin ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.

“Asma’u ɗauki abinci ki kaiwa Yayunki tun da akayi buɗa baki ƴaƴan itatuwa da kunu kaɗai suka sha basu ci wani abu ba”.

Jinjina kai Asma’u tayi kana tace.

“Toh”,Sannan ta ɗauki Faranti Perpesoup ɗin kaza,da Couscous da miyan ƙwai sai perper cheking sai juice ɗin Abarba da kwakwa sai kuma fruit salad.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga zaune ta same su M Jameel na kan 2sitter yayin da Moddibo ke kan 3sitter Idanunsa alumshe ajiye wa tayi tare da juyawa zata fita.

 

M Jameel ya ɗago kansa tare da kallon Asma’u dake shirin fita yace.

“Asma’u zo ki zuba mana yunwa nakeji wallahi kinsan Magana ba wasa ne dashi ba”.

Murmushi tayi kana tace.

“Hakane”.

Kam sannan ta tsugunna ta buɗe Warmers din Atake ƙamshi ya bugi hancinsu da sauri M Jameel ya Kalli Asma’u tare da cewa.

“Asmeey wayayi wannan girkin?”.

Tana zuba musu miyar ƙwoyin akan Couscous ɗin ta ta ajiye kana tace.

“Ya Jameel nice Nayi”.

 

Ware ido M Jameel yayi.

“Kai Asmeey ki faɗi gaskiya dai”.

Murmushi tayi da faɗin.

“Allah da gaske ni nayi yaya Jameel”.

Abincin ya ɗiba ya kai bakinsa tare da lumshe idanunsa kana yace.

“Waya koya Miki wanna girkin?”.

Dariya tayi kana tace.

“Khausar ce ta koya min Allah yaya Jameel yawanci idan naje gidan take koya min”.

Moddibo dake kwance ya harareta kana yace.

“Ke dai Arayuwarki komai baki iya ba sai dai wata ce ta koya miki, ki bari mana akoya mikin kawai akayi ba magana ta ƙare ba ba sai kince ga wacce ta koya miki ba”.

Ya ƙare maganar kamar bashi yayi ba.

Murmushi Asma’u tayi kana tace.

“Allah Yaya Moddibo Khausar ta iya girki sosai saboda kullum tare suke shiga kichen da Mommy ta”.

Baki ya taɓe da faɗin.

“Naji jeki ki gaida Innayi”.

 

Kai ta gyaɗa tare da yin murmushi har ta kai ƙofa zata fita sai ta kuma ta sake juyawa tare da komawa ciki kana tace.

“Yaya Jameel ƙofan Innayi babu wata gashi kuma naga nan akwai wuta”.

Moddibo dake kwance ya shafa sajensa kana yace.

“Itace tace bata so gashi har cikin kicin ɗinta taƙi a kaishi ɗakinta”.

 

Baki Asma’u ta tura tare da Marerece fuska kana tace.

“Nikam gaskiya zama ba wutan nan baimin ba”.

M Jameel dake cin Chicken Peper ya kalleta tare da cewa.

“Toh kije ki faɗa mata wata ƙil wala Allah idan ke kin faɗa ta yarda asa mata”.

 

Kai Asma’u ta jinjina kana ta miƙe tare da faɗin.

“Toh”,Sannan ta fice ta nufi sashen Innayi.

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga ɗakin Innayi zaune ta samu Innayi da lantarta azaune hannunta riƙe da carbi tana ja.

Zama tayi daga gefen Innayi kana tace.

“Innayi naga an kawo wuta a sashen su Yaya Moddibo Nan kuma babu wallahi rashin wutar nan beyi ba”.

Anutse Innayi ta juya ta kalleta kana tace.

“Ayyah Asma’u am ni tsoron wutan nan nake ji bana son irin wannan abubuwan ke kuma kina so ko?”.

Jinjina Kai Asma’u tayi tare da faɗin.

“Allah Ni dai inaso”.

Innayi ta kalleta kana tace.

“Zafi kike jine?”.

 

Girgiza kai Asma’u tayi tare da cewa.

“Ba zafi ba haske dai Innayi ɗan tv nan dai idan alasa zamu riƙa kallon sunna Tv”.

Jinjina kai Innayi tare kana tace.

“Shikenan sai asaka tunda haka kike so insha Allah gobe zan faɗa musu asaka mana”.

Da sauri Asma’u ta miƙe kana tace.

“Bari Inje in faɗa musu yanzu”,Ta ida maganar tare da ficewa.

 

Kai tsaye sashen ta koma bakinta ɗauke da Sallama tashiga Idanunta akan Moddibo dake kurɓan Juice ɗin fuskarta ɗauke da murmushi kana tace.

“Yaya Moddibo Wallahi Innayi ta yarda aja mata wuta kuma dan Allah asamar mana Tv zamu riƙa kallon Tafseer kaga ita yanzu sai dai tayi ta rungumar Radio komai sai dai taji ta Radio”.

 

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Toh shikenan Allah ya kaimu goben”.

M Jameel kuwa kallon Asma’u yayi fuskarsa ɗauke da murmushi ya ajiye Plate ɗin hannunsa kana yace.

“Tafff lallai Asma’u ke ta musamman ce kinyi babban sa’a babu yanda ba muyi da ita ba muja mata wuta taƙi”.

Murmushi Moddibo yayi kana yace.

“Ai Asma’u ta hannun daman Innayi ce”.

Murmushi Asma’u tayi tare da ficewa ta koma falon Innayi suka kwana Misalin biyu da rabi Innayi ta farka kana ta tashi Asma’u suka fita alwala sukayi suka gabatar da nafilla tare da adduo’i ƙarfe uku dai-dai Innayi da Asma’u suka shiga kichen Innayi tayi musu ɗumanen tuwan jiya tare da tafasa ruwan shayi daya ji kayan ƙamshi sai kuma ta ɗumama perpesoup ɗin kazan ita kuwa Asma’u attaruhu da albasa ta jajjaga tare da ɗauraye tukunya ta sanya akan gas wanda zuwan Asma’u ne Moddibo suka kawo mai ta zuba kana ta zuba jajjegen tare da zuba spices da Maggi da kuma Curry ta zuba kana ta zuba sanwa Bushesh-shen kifi dake gyare ta zuba sannan ta ɗauƙi carrots,da grean beans,da kuma cabbage ta shiga gyarawa jin ruwan na tafasa ta tsaya ta zuba Spaghetti leda ɗaya sannan ta cigaba da gyarawa sai daya kusa tsotsewa sannan ta zuba cabbage,grean beans,Carrot,aciki Nan da nan gidan ya kaure da ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta zuba sauran a plate ta haɗa kayan duka a babban faranti ta ɗauka bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon.

 

Moddibo dake zaune riƙe da Alkur’ani ya ɗago kansa tare da amsa Sallamar bayan ya kai ƙarshen ayan Moddibo kuwa idanunsa ya ɗauke daga kan system ɗin tare da kallon Warmers din sai kuma ya Kalli Asma’u dake ajiyewa akan center table ya shafa sajensa tare da cewa.

“Asmeey ya naga kuloli da yawa haka?”.

Murmushi tayi kana tace.

“Wannan ɗumame ne Innayi tayi muku ɗayan kuma ɗumamen perpesoup ɗin jiya ne wannan kuma jollof nayi muku na Spaghetti”.

Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.

“Ni dai kamar nafi son ɗumamen Amma bari naga jollof ɗin naki”.

Ya ida maganar tare da buɗe Kulan cikin sauri ya lumshe idanunsa jin ƙamshin daya ratsa hancinsa.

Kallonta yayi kana yace.

“A’a bazan ci ɗumame ba”.

Juyawa Moddibo yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Ai kuwa baka Isa ba ɗumame zaka ci, Asma’u Allah ya miki albarka”.

Sai kuma ya sake kallon M Jameel dake murmushi kana yace.

“Ai dolenka ɗumame zaka ci dan kaine Innayi ke yin ɗumame ko wani shekara sai ka ishemu da ɗumame saboda kai ake liƙa mana”.

 

Murmushi M Jameel yayi kana yace.

“Ai ɗumamenta yana da daɗi kai kan ka in faɗa maka zakayi missing ɗumanenta idan baka kusa yanzu ma dan kana tare dashi ne”.

Murmushin gefen baki Moddibo yayi kana yace.

“Um naji amma dai yau shi zaka ci”.

Dariya M Jameel yayi tare da cewa.

“Ba matsala ai ɗumamen Innayi nace”.

Miƙewa Asma’u tayi tare da ficewa Moddibo da M Jameel kuwa Matsawa sukayi tare da fara cin ɗumamen kaɗan suka ci sannan suka ci jollof ɗin taliya suka sha tea perpesoup din kazar kuwa ko buɗewa basuyi ba bayan sun gama suka miƙe suka tafi masallaci tare da idar da sallah saida sukayi Azkhar kafin suka dawo gida suka kwanta bacci kafin wani lokaci su tashi su tafi Tafseer acikin makarantar su.

 

Ƙarfe Goma da rabi dai-dai suka farka atare Moddibo ya miƙe bakinsa ɗauke da addu’a kana yashiga toilet yayi wanka tare da daura al’wala zama yayi tare da shafa lotion mai ƙamshi sannan ya sanya Jallabiya Marron colour tare da ɗaura baƙin Alkyabba akai kana ya naɗa hirami akansa sosai yayi kyau tamkar balarabe kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi sallah walha ya gabatar tare da zama ya fara ƙira’a cikin Suratul Maryam.

Sha daya da rabi dai-dai M Jameel ya fito daga ɗaya Bedroom din cikin shiri da alama ya gabatar da sallar walhar shima kallon hadaɗɗen agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yayi kana ya maida kallonsa kan Moddibo tare da cewa.

“A.J sha biyu ta kusa fa mutafi kasan ana jiranmu”.

Dai-dai lokacin da wayar Moddibo yayi ruri kallon screen ɗin yayi tare da kallon M Jameel kana yace.

“Gashi ma malam Arɗo ke kirana da alama zai ce mu ake jira masallaci ya cika”.

Jinjina kai M Jameel yayi kana yace.

“Mu tafi”.

Kai Moddibo ya gyaɗa tare da ɗaukar mukullin motar suka fice.

 

Kai tsaye masallacin dake cikin makarantarsu suka nufa wanda yake cike da maza da mata ko wanne na ɓangaren su sai dai mata sunfi yawa ƙarfe 12:00 ya musu acikin masallacin.

Gyaran Murya M Jameel yayi cikin nutsuwa da kuma yanayin zafin jinjinsa ya gyara zamansa tare da cewa.

_“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa’nazubillahi billahi min shuriri anfusna wamin sayyi ati a’amalina manyah dillahu fala hadiyala waman mudillah fala hadiyala Wa’ash hadu Allah ilahalillahu Wa’ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu amma ba’ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_.

 

Suka amsa da.

“Wa’alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.

Ya numfasa tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe sai kuma ya gyara zamansa kana yace.

“Duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah subhanahu wata’ala mai kowa mai komai daya sake nuna mana wannan wata mai cike da falala da kuma rahma Allah ya nuna mana ƙarshen sa lafiya kamar yanda ya nuna mana farkon sa Awancan shekarar mun tsaya aƙarshen Suratul Jinni insha Allah yau zamu ɗaura acikin Suratul Muzammil Aramma jeka cikin suran muji mai Allah yace”.

 

Gyaɗa kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa cikin nutsuwa da sanyin Muryansa tare da kamala kana yayi A’uziyya tare da basmala ya fara kamar haka;.

_“1-Ya Ayyuhal Muzammil,2-Ƙumullaila illa ƙaliliah 3-Nisfshu awinƙus minhu ƙalila”_

Atake masallacin yayi tsit tamkar babu mahalukin dake numfashi yayin da karatun ke ratsasu.

 

Shikuwa M Jameel Kai ya gyaɗa da faɗin.

“Yawwa Aramma ci gaba mai Allah yake cewa acikin aya ta gaba”.

Jinjina kai Moddibo yayi tare da manna bayansa da jikin kujera ya cigaba da cewa.

_“4-Auzidhu alaihi warartilill ƙur’ana tartila5-Inna sanulƙi alaika ƙaulan sakila”_.

 

Numfashi M Jameel yayi kana yace.

“Suratul Muzammil Makiyya ce tana da ayoyi guda ashirin.

Ya numfasa tare da lumshe idanunsa kana ya cigaba da cewa.

“Suratul Muzammil tana karantar da tarbiya da juriya ga Muslimi,domin susami damar tsayuwar da umarnin Allah”.

Still wajen yayi tamkar babu mahalukin dake numfashi jama’ar dake wajen su tattara duk kan nutsuwarsu suna sauraron abinda Allah yace Moddibo kuwa System ɗin gabansa ya zubawa Idanu tare da lumshe idanunsa.

M Jameel ya numfasa tare da cewa.

_“Ya Ayyuhal Muzammil,Ma’ana ya kai wanda ka lulluɓa da mayafi”_

Atake masallacin ya kaure da kabbara suna faɗin.

“Allahu akbar, Allahu akbar Allah yakareka Malam”.

Zama M Jameel ya gyara tare da kallon jama’ar bayan sunyi shiru ya ɗaura da cewa.

_“ƙumillayla illa ƙalila,katsaya domin yin Sallah acikin dare(suka) face kaɗan”._

Nanma kabbara suka sake kaurewa dashi.

Shi kuwa M Jameel numfashi ya sauƙe kana ya cigaba da fadin.

_“Nisfshu awin minƙushu ƙalila,Rabinsa ,ko ka rage Abu kaɗan daga gareshi._

Haka suka cigaba da tafsirin ayoyin.

Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi ɗaya da kwata sukayi Sallar azahar zama sukayi acikin masallacin suka fara Muraja’a tun daga suratul tauba zuwa Nahal jin kiran la’asar yasa suka dakata kana suka tashi Moddibo ne yaja Sallar M Jameel kuwa shi yayi ladanci bayan sun idar ne suka fita kai tsaye masallacin dake Unguwar su Moddibo suka nufa ƙarfe biyar suka fara gabatar da tafsirin acikin suratul hujurat wannan kuma na maza ne zalla ƙarfe shida dai-dai suka tashi.

 

Bayan sun tashi M Jameel yashiga mazaunin Driver Moddibo kuwa gefen mai zaman banza ya zauna tare da lumshe idanunsa yana sakin numfashi Kallonsa M Jameel yayi tare da murmushi kana yayiwa motar key.

Wayar Moddibo ne ya hau ruri Anutse ya sanya hannu ya ɗauka ganin sunan Ummi yasa ya gyara zamansa cike da nutsuwa yayi Picking tare da Sallama kana yace.

“Ummi ina yini”.

Daga ɗaya ɓangare cike da so da kulawa Ummi tayi murmushi kana tace.

“Babana”.

Moddibo ya amsa da.

“Na’am Ummina”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Babana sannuku da ƙoƙari nasan yanzu baki da hutu Ramadan ya shigo”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.

“Ga munan dai kam Ummi muna fama”.

Cike da kulawa da kuma ƙaunar su tace.

“Allah sarki Allah ya biya ku Allah yaƙara rufa asiri”.

Ya amsa da.

“Ameen”.

Ummi ta gyara wayar akunnenta kana tace.

“Babana nashirya muku abin buɗa baki kuzo kusha ruwa”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh Ummi mun gode muna nan tafe yanzu ma Insha Allah zamu zo”.

 

Kasancewar M Jameel na Jin Komai saboda wayar a handsfree yake yasa ya juya akalar motar zuwa hanyar gidan Ummi adai-dai ƙofar gidan Ummi M Jameel yayi hong mai gadi ya buɗe musu suka shiga…!

 

Yau dai ba editing. Dan muna cikin hidiman bikine

 

 

By

*GARKUWAN MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button