Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 20

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

20

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

Ujnr. Tana shiga ta sauƙe numfashi ganin babu. Gimbiya Dadu, falon shiru ba kowa sai Uncle Naseer dake zaune kan 3sitter yana riƙe da system akan cinyarsa da kuma wayarsa.

Yana ganinta yayi saurin rufe system ɗin kana ya zira wayarsa acikin aljihu tare da tsira mata idanu afili ya furta.

“Wowww Masha Allah kinsha kyau My Dear”.

Batare da tace komai ba ta ƙara sa shiga falon tare da yiwa kanta masauƙi akan 1sitter.

Tsuke fuska yayi tare da zuba mata idanu kana yace.

“Meyesa ba zaki zauna akusa dani ba My Khausi?”.

Kallonsa tayi da lumsassun idanunta kana da alamun bacci acikin Muryanta tace.

“Unclr Naseer nan ma yayi”.

ta ƙarasa maganar tana mai lumshe Idanunta.

Ido ya tsira mata yana kallon yanda ta lumshe sexy Eyes ɗin ta miƙewa yayi tare da dawowa kusa da ita ya zauna a hannun kujeran, yana shaƙan daddaɗan ƙamshin turarenta, Khausar kuwa jin alamu sa akusa da ita yasa tayi saurin buɗe Idanunta dake lumshe kana ta miƙe da niyyan barin wajen.

 

Cikin hanzari ya sanya tafin hannunsa dake ɗauke da zoben azurfa ya riƙe nata yana binta da wani mayataccen kallo.

fuskarta ta yamutsa cikin ɗaure fuska kana da rashin walwala tace.

“Me haka Uncle Naseer?”.

Langwaɓar da kai yayi tare da tsaida idanunsa cikin nata kana ya karyar da murya tare da faɗin.

“Guduna zakiyi?”.

Kai ta girgiza masa tare da lumshe Idanunta jin bacci na fusgarta kana tace.

“A’a ba gudunka nake ba kawai dai ai baidaceba”.

Karyar da muryarsa yayi tare da yi mata kallon Up and down kana yace.

“Toh ki zauna anan ni dodone, ko kuma cinye ki zanyi mai yasa kike min haka ne Khausar”.

Kai ta girgiza tare da gyara hijabinta kana tace.

“Bai dace bane Uncle Naseer haka baiyi ba ni ka sakar min hannu”.

Wani kallo ya watsa mata kana yace.

“Bazan sakar miki hannu ba”.

Ya ida maganar yana latsa mata hannu tare da yi mata tafiyar tsutsa.

Cikin fushi ta.

Fisge hannunta tare da galla masa harara kana tace.

“Ni gaskiya banason abinda kake min banaso sam”.

Ta Faɗa tare da juyawa zata bar masa falon.

Da sauri ya miƙe tare da shan gabanta kana ya durƙusa akan gwiwoyinsa tare dasa hannunsa duka biyu ya riƙe kunnensa cikin wata. Sanyayyar murya mai cike da lallashi ya zuba mata ido tare da cewa.

“Na tuba dan Allah kiyi haƙuri, bazan ƙara ba Insha Allah, ki gafar ceni kinji My dear.

Dan Allah Dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) kiyi haƙuri ki koma ki zauna naji Ni zan zauna a ƙasa”.

Jin haka yasa ta saki ajiyar zuciya tare da komawa ta zauna.

Murmushin gefen baki ya saki tare da miƙewa ya zauna aƙasan Capet mai taushi dake malale Atsakiyar falon tare da yin tagumi kana ya tsira mata Idanu, tare da saki ajiyar zuciya langwaɓar da kai yayi kana yace.

“Khausar ina sonki, ya zanyi idan har kikayi fushi dani rayuwata ba zata yimin daɗi ba. Duniyar nan zata yimin duhu matuƙar dai kikayi fushi dani, hankalina ba zai kwanta ba.

Kada ki mancefa na yarda nabi duk dokan da aka samin nacewa kada in sake inyi miki maganar soyayya har saikin kammala Secondary school, ni Kuma na kammala karatuna”.

Ajiyar zuciya ya saki tare da fesar da numfashi kana yace.

“Bisa wannan sharaɗin aka hanani koda jin Muryan kine Koda na Kira Mommy mun gaisa baza ta baki mu gaisa ba, haka nayi ta dakon soyayyarki azuciyata, duk tsawon shekarun nan da nayi a India ina ɗauke da dakon soyayyarki Khausar, Ina son ki³ kinsan tsawon shekara shida ba wasa ba I miss you, I really love you Matata, kece farin cikina kece sirrina kece duniya ta Khausar will you Marry me?”.

Ahankali tayi ƙasa dan kanta har ga Allah batasan mai zata ce dashi ba.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Khausar zaki Aureni!?”.

Lallausan tafin hannunta tasa ta rufe fuskarta batare data bashi amsa ba.

Shi kuwa Naseer murmushi ya saki kana yace.

“Nagode My Khausi”.

Domin shi duk azatonsa kunyarsa da kuma rufe fuskar da tayi sonsa take.

 

Cikin Sanyayyar murya mai taushi da kulawa ya kalleta kana yace.

“Kece Sirrina duk abinda zanyi aduniya dole ke sirrina ce, dake zanyi shi abubuwa biyu ne suka dawo dani ƙasar nan Khausar,

akwai mahaɗin abinda ya dawo dani ƙasar nan sai kuma burin mallakar ki da fatan  kasancewarki mallakina na har abada”.

 

Cikin sanyin murya mai ratsa zuciyar duk wanda ya saurara tace.

“Uncle Naseer kace Ubangiji ya mana zaɓi msfi al’khairi, duk abinda muke so aduniya mu barwa Ubangiji  zaɓi kaji ko Uncle Naseer”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Naji Nagode amma ina da wata alfarma da nake so in nema awajenki shin zakiyi min shi?”.

Cikin sanyi da alamun bacci a idanunta tace.

“Eh Uncle Naseer in baifi ƙarfina ba zanyi maka shi”.

 

Gyara zamansa yayi tare da cewa.

“Kinyi alƙawari?”.

A hankali ta buɗe Idanunta sosai akansa kana tace.

“Toh  ai ban sani ba yafi ƙarfina ko baifi ba”.

Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.

“Baima fi ƙarfin kiba Khausar. Insha Allah bai fi ƙarfin ki ba zaki iya ba abune na kokuwa ko dambeba sannan ba mugun abu da zai saɓawa Addinmu bane”.

Ajiyar zuciya ta saki kana tayi murmushi tare da cewa.

“Allah dagaske!?”.

Ka ya jinjina mata kana yace.

“Eh dagaske”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan Uncle Naseer”.

Idanu ya tsira mata  tare da faɗin.

“Kinyi alƙawari zakiyi min!?”.

Wara manyan Idanunta tayi tare da cewa.

“Bana so ina ɗauki al’ƙawari bansan kuma menene bane!”.

Cike da manufa ya karyar da murya tare da cewa.

“Ni dai nafi son kiyi min al’ƙawari, zaki te maki rayuwata, da kuma cigaban mu, da Kuma jin daɗin ki kinji ko Khausar, saboda jin daɗina da jin daɗin ki nakeso muyi wannan abin kuma wannan sirrin mu ne amatsayin ki na matata dan ko mahaifiyata bata san wannan sirrin ba!”.

 

Nan-nauyan ajiyar zuciya Khausar ta saki Idanunta akansa tace.

“Toh wannan wani irin sirrine ka faɗa min mana”.

Kai ya Girgiza tare da cewa.

“A’a har sai kinyi al’ƙawari zaki min abun zan faɗa miki”.

Girgiza kai tayi kana tace.

“Yaya Naseer bana so in maka al’ƙawarin da ban sani ba ko bazan iya ba”.

 

fesar da iska mai sanyi yayi tare da kallonta kana yace.

“Zama ki iya”.

Kallonsa tayi ganin yanda ya marairaice yasa ta saki Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Toh shikenan sai nayi shawara”.

Da sauri ya kalleta tare da cewa.

“Shawara kuma da waye zakiyi shawara? bana faɗa miki siririn mu bane! Sirrina ne dani dake kasancewar abu ɗaya zamu kasance, zaki kasance matata kuma uwar ƴaƴana kece zaki kasance ruwa mai kashe min ƙishina”.

Sauƙe sanyayyar Ajiyar zuciya tayi tare da faɗin.

“Toh shikenan sai nayi tunani”.

Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.

“Zuwa yaushe?”.

Shiru tayi alamar tunani sai kuma tace.

“Zuwa gobe ko jibi”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh shikenan ba damuwa Allah ya kaimu muyi hira mana”.

Marairaice fuska tayi kana tace.

“Ayyah Uncle Naseer bacci nake ji”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Toh shikenan muje inda rakaki”.

Batace komai ba tashige gaba yana biye da ita, tare da zubawa ƙugunta idanu saida ta shiga falo sannan ya koma ya shiga motarsa ya wuce gida.

 

Acan ɓangaren Moddibo kuwa awannan dare haka ya kwana cikin mawuyacin hali saboda wani azabebben yanayi dake damunsa sai. Wajajen ƙarfe uku da rabi  wani irin bacci mai shegen daɗi ya ɗauke sa.

 

Can cikin baccin nasa ya fara wani irin bahagon mafarki, ganinsa yayi tare da Khausar, suna kwance akan gado ɗaya cikin wani irin ni’imtaccen bargo fari ƙal mai masifar taushi, kana babu komai a jikinsu yana rungume da ita hannunsa na dama nakan yalwataccen sumar kanta mai ƙamshi da sheƙi yana shafawa, yayin da ɗaya hannun ke kan caɓullenta yana murzawa.

Cikin Sanyayyar murya mai cike da shagwaɓa Khausar ta sakar masa wani irin narkekken kuka tare da cewa.

“Tsoro nake ji nikam bazan iya ba Moddibo kabar ni bazan iya ba”.

Shi kuwa Moddibo karyar da murya yayi cikin tattausan murya mai cike da salama yake lallashinta.

Ƙarfe huɗu dai-dai ya farka sakamakon kiran sallar assalatu da akayi miƙa yayi tare da furta.

_“Alhamdulillahi lazi ahyana bada amatana wa’ilaihin nushur”_.

Kana ya tashi zaune yana kallin Boxes ɗinsa da ya bada damshi alamar yayi ta liking.

Cikin sauri ya furta.

“Ya Salam Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n nashiga Uku”.

Da sauri ya miƙe tare da dafe kansa kana yace.

“Innalillahi Wa’inna ilahi rajiu’n, shin wannan wace irin Masifa ce mai nacin tsiya da bibiyata, madadin abin nan yayi baya kullum sai gaba-gaba yake yi, yanzu abin har yakai matakin mafarkin yarinyar nan nakeyi wannan wace irin rayuwa ce? In banda ma rashin kunya da raini ya za’ayi yarinyar nan ta biyoni har cikin bacci na”.

Sake kallon boxes sa yayi dan tabbatar wa still gani yayi zahiri ya jiƙe da yarinyar amafarki, cike da tafasan zuciya ya shafa Dk ɗin sa dake bayyana zalamarsa duk da cewa yayi liking.

Amma bai nitsuba ba zama yayi abakin gado tare da dafe kansa da hannu biyu ji yake tamkar ya fashe da kukan takaici.

“Tabbas da ace mafarki na zama gaskiya to da sai na sumar da yarinyar nan, ta yadda har abada bazata sake zuwan min ba”. yayi mgnar a sama lips inshi.

 

Ahankali kuma sautin muryanta yashiga dawowa cikin kunnensa tana cewa.

“Tsoro nakeji bazan iya ba Moddibo”.

Wani dogon tsaki yaja kana cikin wani irin fushi ya miƙe tare da lumshe idanunsa tabbas badan amafarki bane da sai yayi maganin yarinyar.

Toilet yashiga tare da wanka  kana ya ɗaura Al’wala duk zuciyarsa babu daɗi bayan ya shirya ya tafi masallaci.

 

Bayan kwana biyu kamar ko yaushe Anutse Khausar ce ta fara miƙewa kana tayi submitting ɗin Booklet ɗin ta yayin da sauran ɗalibai ke cizon gindin biro sosai Exam ɗin Nahwun ya basu wahala ahankali. Khausar ta fita tana lumshe Idanunta duk da cewa ta saba answering questions kafin abasu amsa amma na yau ya wahalar da ita ajikin Up stair ta tsaya tare da ɗaura hannunta akan step ɗin sama kana ta zu bawa farfajiyar makarantar Ido, sanyayyan iska na kaɗata tsayuwar ta da kamar minti biyar wata baƙar mota tazo ta faka ta bada baya.

Cikin sauri ta zare Ido tare da kallon number motar  cike da mamaki da al’ajabi ta mitsika Idanunta tare da sake kallon number motar cikin rawan murya tace.

“Wannan Motar Again?”.

Tabbas wannan shine motar da tagani a Jauro Yaya a lokacin da suka tafi Rafi dasu Dija still, kuma aranan aka kashe Baffa Umaru tabbas kamannin motar da kuma Number ba zasu taɓa ɓace mata ba to amma mai yazo yi amakarantarsu.

Kallon motar ta sake yi still Yana tsaye cikin sauri ta fara taka step ɗin tana haɗawa bibbiyu har ta sauka kana ta nufi gate.

 

Da sauri Baba Mai gadi ya miƙe tare da cewa.

“Khausar ina Zakije?”.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Saƙo zan amsa awajen masu wancan motar”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Kinsan dokar makarantar nan bata bari idan anshiga afita amma kina amsa ki dawo”,

Kai ta gyaɗa tare da ficewa shi kuma yabi bayanta.

 

Ahankali ta tsirawa number motar Idanu kana cikin sanyin jiki ta nufi motar.

Mutanen dake Cikin motar kuwa sam basu lura da ita ba saida taje gab dasu suka lura da kamar tana leƙa su ne, kana ga dukkan alamu Idanunta na kan Plate number motar cikin sauri suka ɗaga glass ɗin motar dake ƙasa.

Khausar kuwa cikin sauri ta nufi gaban motar dan ganin fuskokin su waye ne, mutumin dake zaune a mazaunin Driver ne yayi saurin figar motar da mugun gudu suka tafi.

Cike da mamaki Khausar ta dafe kuncinta tare da cewa.

“Ha’a to meyesa haka?”.

Anutse ta juya bayanta jin Muryan Baba mai gadi na cewa.

“Toh ya kuma ba abinda suka baki suka ja mota da gudu haka suka tafi?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon Baba mai gadi kana tace.

“Agaskiya bansan suba fa, amma dai na taɓa ganin motar acan Rugar mu shiyasa yanzu na saƙƙo inga shin wannan motar ce ko kuma watace, kuma na gane motar ita ɗin ce, kuma awannan ranan ma dana gansu haka suka gudu”.

 

Kai  Baba mai gadi ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh Allah yasa dai lafiya?”.

Nan-nauyan ajiyar zuciya ta saki tare da furzar da iska mai zafi daga bakinta kana tace.

“Ka kula gaskiya Baba mai gadi, ka kula duk sanda kasake ganin wannan motar ka faɗa min”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Toh shikenan amma ai kalar motoci da yawa taya zan gane wannan?”.

Sauƙe numfashi tayi tare da faɗin.

“Aina riƙe number”.

Bata jira cewarsa ba ta janyo biron dake kanta tare da yagar ƙasan Qautions paper ta rubuta masa number tare da miƙa masa kana tace.

“Gashi ka riƙe duk sanda ka sake kallon tazo bakin makarantar nan, ka faɗa min ni ban yarda da motar nan ba, dan ko can Rugar da suje adaren ranan akwai abinda ya faru”.

Ajiyar zuciya ta saki tare da rintse Idanunta kana ta cigaba da cewa.

“Haka nan naji na tsargi motar duk da bani da tabbaci sannan still yauma. Kaga tazo ta tsaya mana abakin makaranta Indai tazo ka sake ganinta ka sanar min ko kuma ka sanarwa Malamai”.

Jinjina kai Baba mai gadi yayi tare da cewa.

“Toh shikenan insha Allah ”.

Kai ta gyaɗa tare da buɗe ƙaramin gate ta koma cikin makaranta tana koma suka haɗu da M Jameel na ƙoƙarin zuwa office.

Da Mamaki M Jameel ya kalleta kana yace.

“Daga ina kike Khausar kaddai yanzu kika zo?”.

 

Kallonsa tayi tare da girgiza kai tayi kana tace.

“A’a tun ɗazu nazo na gama Peper nama shiyasa na fito”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“To mai kika je yi awaje?”

Murmushi tayi tare da cewa.

“Wani abu naje na ɗan duba?”.

Gyara tsayuwarsa yayi kana yace.

“Wani abu kika je dubawa bayan kinsan doka da ƙa’idar makarantar nan, in anshiga ba’a fita yanzu kiyi laifi idan ansaki kaɗe ɗankwali kice rayuwar bauta kike baki da cikekken ƴanci ko?”.

Ƙasa tayi da kanta tare da cewa.

“A’a wata mota ce muka gani nida Baba Mai gadi”. Dai-dai lokacin kuma ta hango Moddibo ya fito daga corridor da zai sada ka da office ɗin su zare ido tayi cikin sauri ta juya tare da hawa step ɗin class ɗinsu.

Murmushi M Jameel Yayi tare da girgiza kai Dramer Moddibo da Khausar na sanyashi nishaɗi.

Khausar kuwa na haurawa ta samu Asma’u ta fito tayi submitted Booklet din ta ba daɗewa kowa ya fito sannan suka tafi.

 

Motar na parking Khausar ta fito dai-dai lokacin Mommy ta shigo tsayawa Khausar tayi har Mommy ta ƙaraso kusa da ita.

Kallon ta Khausar tayi tare da cewa.

“Mommy daga ina haka naga kamar kin fita Unguwa?”.

Kai Mommy ta gyaɗa mata kana tace.

“Eh Khausar na fita Unguwa naje gidan Aunty Asiya ce yau ta haihu Allah ya sauƙeta lafiya”.

Wara Ido Khausar tayi cike da farin ciki tace.

“Laaaa Mommy Aunty Asiya ta haihu? Mai ta haifa Mommy?”.

Jinjina kai Mommy tayi tana tafiya tace.

“Ta haifi ƴa mace”.

Jinjina kai Khausar tayi tare da faɗin.

“Masha Allah bari nayi wanka naje na duba Baby”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.

“Ai dai kam ya kamata dama anats cewa wai yarinyar na kama dake”.

 

“Dani kuma Mommy?”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da zama akan 2sitter tana cire hijabinta tace.

“Eh toh da Raudat take kama Raudat kuwa kinga dake take kama shiryasa kowa ke cewa Jaririyar kamar Khausar ²”.

 

Murmushin fuskarta ta faɗaɗa kana tace.

“Aikam bari nayi wanka Inje inga mai kama dani”.

Ta ida maganar tare da wucewa Bedroom  akan beside drawer ta ajiye tarkacen hannunta kana ta cire Uniform ɗin ta ɗaura towel tashiga toilet.

Tayi wanka tana fitowa ta zauna gaban Dressing mirrow tare da shafa Lotion ɗin ta, kana ta sanya dogon rigar material Sky blue ta yane Kanta da baƙin gyale, sannan ta feshe jikinta da turaruka masu daɗin ƙamshi ta fice.

Mommy dake zaune a falo ta kalleta tare da cewa.

“Khausar ko abinci fa baki ciba?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“A’a Mommy sai na dawo”.

 

“Adawo lafiya”.

 

Anutse ta fita tafiya kaɗan tayi ta isa gidan mutum uku kawai ta samu aɗakin.

Kusa da Aunty Asiya dake mata murmushin ta zauna tare da cewa.

“Aunty Asiya ina baby?”.

 

“Gata nan”.

Ta faɗa tana nuna mata matar dake gefenta.

“Masha Allah, wata tana kama da niko? Allah ya raya mana”.

Murmushi Aunty Asiya tayi tare da faɗin.

“Ameen Khausar ga Baby”.

Da sauri Khausar ta karɓe ta tare da cewa.

“Bari inga mai kama dani”.

Ta faɗa tana zubawa Jaririyar Ido farace sol da ita ga wani yalwataccen gashi daya kwanta asaman goshinta kana girar tama da yelwataccen gashi bakinta yayi pich da dogon Eyelashes.

Da sauri Khausar ta ɗago kanta da murmushi afuskarta tace.

“Aunty Asiya wallahi kam Baby kam tayi kyau Masha Allah”.

Jinjina kai Aunty Asiya tayi tare da cewa.

“Aikam dake take kama, wai Gimbiya Dadu tace idan kinzo kitso ina yawan kallonki shiyasa na haifi me kama da ke”.

Baki Khausar ta taɓe tare da cewa.

“Uhm Ita kuma duk duniya akwai wanda yafi ta kallona ne?”.

Murmushi Aunty Asiya tayi, Khausar kuwa Jaririyar ta miƙa mata tare da miƙewa kana tace.

“Bari in tafi Aunty Asiya Allah ya raya”.

Karɓar Jaririyar Aunty Asiya tayi kana tace.

“Toh ki Gaishe da Mommy da gajiya”.

Amsawa Khausar tayi da cewa.

“Za taji” kana ta fice.

 

Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zaune ta samu Mommy a inda ta tafi ta barta kusa da Mommy ta zauna da murmushi afuskarta tace.

“Wallahi Mommy Jaririyar muna kama nima naga kamar mu”.

Jinjina Kai Mommy tayi tare da ajiye wayarta kana tace.

“Nima gaskiya naga kamar ku sai naga kamar lokacin kina Jaririya,  kuma haka Raudat ma take shiyasa ake ganin kamar dake take kama”.

Veil dake kanta ta janye tare da cewa.

“Ai dai kam”.

Miƙewa tayi tare da cewa.

“Mommy bari na ɗauko abincina”.

Kai Mommy ta gyaɗa mata sannan ta wuce kichen ɗin.

 

Bayan kwana shida; Alhamdulillah a yau ne su Khausar suka rubuta Final Exam ɗin su cike da tsananin farin ciki ko wanne ɗalibi ya fito daga hall da suka rubuta Exam ɗin, cikin tsanananin farin ciki Khausar ta nufi jikin tap ɗin ruwa tare da buɗe wa ta cika wani ƙaramin Bocket kana ta nufi kan Asma’u dake tsaye.

Rungumeta tayi tare da sheƙa musu ruwan tace.

“Thank God My Asmeey Alhamdulillah yau mun taka matsayi na farko  a fannin karatun mu”.

Cike da farin ciki Asma’u da jikinta ke ɗigan ruwa ta kalleta kana tace.

“Sosai kuwa Khausar mun godewa Allah”.

Baki ɗaya ɗaliban haka suka ringa jiƙa jikinsu da ruwa cike da matsanancin farin ciki kasancewar an hanasu penday yasa suka shiga jiƙa jikinsu.

Khausar kuwa kallon Samira sani da itama jikinta ke jiƙe tayi tare da miƙa mata hannu kana tace.

“Assalamu Alaikum, Alhamdulillah yau kam abinda ya haɗa ya raba”.

Hannunta Samira Sani ta riƙe tare da murmushin gefen baki sai kuma ta watsa mata Harara dama can ba wani haushin Khausar take jiba tunda Moddibo ba wani kulata yake ba sai dai yadda tafisu ƙwazone ke bata haushi.

 

Acan ɓangaren Malamai kuwa baki ɗaya sun hallara a inda suka tanadar dan yin taro Moddibo ne kaɗai baya wajen bayan duk ɗalibai sun hallara.

M Jameel ya miƙe tare da hura Microphone kana yace.

“Assalamu Alaikum warahmatullah Wabarkatuhu”.

Baki ɗaya Suka amsa da. “Wa’alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.

Yayi gyaran murya tare da cewa.

“Da farko amadadin dukkan malamai da shuwagabannin wannan Makaranta muna taya ɗaukakin Ɗaliban wannan makaranta murnan kammala jarrabawar su na gama makarantar.

Allah ya bada sa’a Ubangiji ya baku ikon fitowa da sakamako mai kyau”.

Baki ɗaya wajen suka amsa da.

“Ameen”.

Tsayuwarsa ya gyara tare da cewa.

“Insha Allah shugaban makaranta zai bada Award da hannunsa ga dukkan ɗaliban da suka cancanta Malam Bismillahi”.

Miƙewa Malam Arɗo yayi tare da karɓan Microphone ɗin kana yace.

“Ina taya ɗaukakin Ɗaliban wannan makaranta ta *AL,ANSAR Academic School* murnan kammala karatun su na matakin farko Allah ya Albarkanci karatunki Ubangiji ya ɗauka ku aduk inda kuke”.

Baki ɗaya suka amsa da.

“Ameen”.

Gyaran murya yayi tare da cewa.

“Zamu miƙa award ga ɗilibar da tafi ko wacce ɗaliba.

Hazaƙa da tsafta”.

Baki ɗaya wajen sake nutsuwa yayi dan jin wacece wannan.

“Khausar Usman Abubakar Lelewal itace ɗalibar da tafi ko wacce ɗaliba Hazaƙa da kuma tsafta”.

Atake wajen ya kaure da kabarra masu taya ta murna irin su Asma’u da Aunty Ruƙayya nayi yayin da masu baƙin ciki irinsu Samira da sauransu keyi.

Cike da nutsuwa Khausar ta miƙe tare da ƙara sawa ta amshi Award cike da tsananin farin ciki.

 

Gyaran murya Malam Arɗo yayi  tare da cewa.

“Ɗalibar da tafi ko wacce ɗalibai Nutsuwa da biyayya itace Asma’u Ahmad”.

Cike da farin ciki Asma’u ta miƙe tare da ƙara sawa ta amshi Award ɗin ta haka aka kira sauran mutum uku aka basu Award .

Cike da farin ciki Khausar ta koma gida kallo ɗaya zaka mata ka tabbatar da cewa tana cikin farin ciki zaune take afalon hannunta riƙe da bowl na Fruit Salat.

Haiydar ne yashigo falon bakinsa ɗauke da Sallama kallon Khausar yayi tare da cewa.

“Addah Khausi Uncle Naseer yana kiranki afalon Abba”.

Murmushi tayi tare da ajiye bowl din Fruit Salat ɗin kana tace.

“A’a lallai kam ina zuwa”.

Murmushi Mommy dake zaune gefenta tayi tare da cewa.

“Yau kam Alhamdulillah gidan nan muna cike da farin ciki Khausar an gama Secondary school tare da samun Award”.

Miƙewa tayi tare da cire hijabin Uniform da har zuwa lokacin yake jikinta wurgi tayi dashi tare da faɗin.

“Yau kam nayi hannun riga da Uniform daga yau nayi bye bye da uniform, shiyasa ko aiki banason aikin da zai kasance min da Uniform,  daga yau na wurgar da Uniform aduniya shiyasa Insha Allah Jenouelist zan zama in dinga zaƙulo gaskiya aduk inda yake ”.

Murmushi Mommy tayi tare da cewa.

“Toh Allah ya taimaka Ubangiji ya cika miki burinki”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.

Ta faɗa tare da shigewa Bedroom kana ta cire Uniform ɗin ta tare da shiga toilet ta sakarwa kanta shawer bayan ta gama wankan ta fito Lotion ta shafa tare da sanya doguwar rigar atanfa mai golden kana tayi ɗaurin ture, ta feshe jikinta da turarukanta masu daɗin ƙamshi kana ta fice. Jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin kai tsaye falon Abba ta nufa bakinta ɗauke da Sallama.

 

Lumshe Idanu  Naseer dake zaune kan 2sittee yayi tare da zuba mata idanu yana shaƙan daddaɗan ƙamshin turaren yace.

“Congratulation My Khausi yau kin gama makarantar ki, nayi matukar farin ciki abubuwa na tafiya yanda ya kamata”.

Murmushi Khausar tayi cike da farin ciki ta jinjina masa kai.

Ahankali Naseer ya ɗauko Flowers dake jikin wata leda anyi wrapping ɗinsa tare da ɗauko kwalin waya iPhone  tare da tarin Choculate ya miƙa mata.

“Ga gift ɗin Graudion ɗin ki”.

Wara Ido Khausar tayi tare da kallon Uban gift ɗin cike da tsanananin farin ciki ta ɗago manyan Idanunta tare  da kallon sa kana tace.

“duka wannan na wane?”.

Kai ya jinjina mata tare da faɗin.

“Yes My Wife duka naki ne”.

Langwaɓar da kai tayi kana tace.

“Mommy ta hanani riƙe waya tace sai na gama Secondary school duka ko lokacin da muke Ss duk abinda zanyi da waya tace sai dai in karɓi nata yanzu kuma kaga”.

Saurin katseta yayi tare da cewa.

“Ai me ai kun gama kin manta yau kukayi final Exam”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Eh haka ne fa Uncle Naseer”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Kada kice komai kawai kice Allah yamin Albarka, ya mallaka min ke Insha daɗin zama dake”.

Shiru tayi tare da ƙasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta.

Miƙewa yayi daga kan 2 sitter da yake zaune ya dawo gabanta ya zauna aƙasan rock ɗin daya mamaye ɗakin kana cikin narkar da murya yace.

“Naga yau kina cikin farin ciki?”.

Kai ta gyaɗa masa tare da cewa.

“Sosai ma kuwa Uncle Naseer”.

 

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da narkar da murya kana yace.

“Nima ki sani cikin farin ciki mana”.

Tana wasa da yatsun hannunta ta ɗago kanta tare da cewa.

“Toh me kake so in yimaka?”.

Karyar da murya yayi tare da faɗin.

“Ki cika min alƙawarin da kika ce zaki yimin, kince sai kinyi shawara nan da kwana biyu amma yau kusan kwana goma kenan da yin maganar mu kullum idan na tambayeki,  sai kice baki yi tunani Ba dan Allah yau dai kiyi min”.

Cike da farin cikin kammala karatun ta da kuma nasaran data samu ta kallesa tare da cewa.

“Nayi alƙawari Uncle Naseer duk abinda kake so zanyi maka matuƙar bai saɓawa addinin Musulunci ba”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da gyara zamansa kana yace.

“Naji daɗi My Khausi, Khausar ɗina ina sonki My life is nothing without you, you are my World”.

Kallonsa kawai take Amma batace Komai ba.

Ahankali ya sanya hannunsa acikin aljihu tare da ciro wani farin ƙyalle fari ƙal yana fitar da wani irin ƙamshi mai masifar hawa kai tare da birkita lissafi, ƙyallen ya miƙa mata ba tare da ta karɓa ba ta tsaida Idanunta akansa kana tace.

“Wannan kuma na menene?”.

Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.

“Ki karɓa mana”.

Girgiza kai tayi tare da faɗin.

“Toh ka faɗa min na menene sai na karba”.

Marerece Murya yayi kana yace.

“Ki karɓa mana zan faɗa miki ai ba dai kinyi al’ƙawari ba?”.

Kai ta gyaɗa tare da karɓa..

Murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Ki shin shina ƙamshin mana”.

Kai ta girgiza tare da jan siririn tsaki asaman laɓɓanta kana tace.

“Haka ma yayi dan inajin ƙanshin yana hawa kai!”.

Zama ya gyara tare da cewa.

“Allah ko?”.

Matsar da ƙyallen tayi daga jikinta saboda irin ƙamshin da yake fitarwa mai masifan hawa kai.

Anutse ta ɗago manyan Idanunta dake lumshe ta kallesa tare da cewa.

“Toh Uncle Naseer mai zan maka da wannan ƙyallen?”.

Matsowa kusa da ita yayi har gwiwan ƙafarsa na taɓa yatsun ƙafa ta cikin wata siga ya karya murya tare da faɗin.

“Khausar kinyi min al’ƙawari ko?”.

Kai ta gyaɗa tare da cije lips ɗin ta kana tace.

“Eh nayi al’ƙawari”.

 

Ajiyar zuciya ya sauƙe  tare da kallon ƙofan falon kana yace.

“Kuma na faɗa miki cewa sirrine tsakanin mu dake”.

Kallon farin ƙyallen tayi tare da juyawa ta kallesa kana tace.

“Eh nasani”.

Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace.

“Sannan kinsan na faɗa miki cewa ci gaban mu ne. Ni dake da kuma  ƴaƴan da zamu haifa?”.

 

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Eh nasani ka faɗa min mana”.

 

Langwaɓar da kai yayi tare da narkar da murya kana yace.

“Zan faɗa miki amma da farko ina so ki.

Sirrinta min dan nasan duk duniya babu wanda zan roƙa ya min inba keba”.

 

Aƙage ta kallesa tare da faɗin.

“Toh ina jinka ka faɗa min menene?”..

Kallon fuskarta yayi tare da sakin ajiyar zuciya kana ya sunkuyar da kansa.

Idanu Khausar ta zuba masa tare da kallon yanda ya sunkuyar da kansa ƙasa sannan tace.

“Ka faɗa kawai”.

Ɗago kansa yayi cikin sigar rauni yace.

“Kinyi al’ƙawari ba zaki faɗawa kowa ba ko?”.

Jinjina kai tayi tare da cewa.

“Nayi al’ƙawari bazan faɗa ba”.

Sauƙe Ajiyar zuciya yayi tare da faɗin.

“Kin tabbata?”.

Aƙage ta gyaɗa masa kai batare da tace komai ba dan tagaji da wannan tambayar tasa.

Iska ya furzar daga bakinsa kana yace.

“Khausar nasan dai tuntuni kin daɗe da fara period ko?”.

 

Cikin sauri tayi ƙasa da kanta cike da mamaki da kuma kunyar tambayarsa.

Ya shafa ƙyeyarsa tare da karyar da murya kana yace.

“Ya kikayi shiru?”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.

“Babu komai”

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata idanu kana yace.

“Ki faɗa min gaskiya tsakanin ki da Allah nasan dai kin daɗe da farawa?”.

Ƙin cewa komai tayi sai ƙasa data sake yi da kanta.

“Ki faɗa min gaskiya kiyi haƙuri na haɗa ki da Allah”.

Still Nan ma shiru tayi Zuciyarta na bugawa.

Zama ya gyara tare da faɗin.

“Nasan dai kin fara tabbas”.

Ataƙaice ta gyaɗa masa kai.

 

Zare Ido yayi tare da cewa.

“Yauwa Alhamdulillah

kin fara period din ko?”.

Kai ta gyaɗa fuskarta babu walwala tace.

“Eh”.

Sajensa ya shafa tare da cewa.

“Alfarma to nakeso kiyi min”.

Gyara zamanta tayi tare da  ɗago kanta kana tace.

“Toh wace iriyar alfarma ce zanyi maka?”.

 

lumshe idanunsa yayi tare da buɗe su akanta kana yace.

“Bance ki bani kuɗi ba, ban kuma ce kibani ranki, ko lafiyarki ba, kuma bance ki mallaka min kanki ba, kawai abinda nake so ki sammin Period ɗin ki”.

Atsorace ta zare Idanunta tare da ɗago kanta kana cike da mamaki tace.

“In san maka Period Kuma Uncle Naseer? Kamar yaya ban gane ba”.

Tayi mgnar jikinta na rawa kana ta miƙe cike da tsoro tana ja da baya.

 

Da sauri ya ɗaga mata hannunsa  cikin sassauta murya yace.

“Karki manta fa kinyi al’ƙawari zaki sirranta min maganata, kuma shiyasa na faɗa miki dan nasan cewa zaki siririn ta min ki zauna mana kiji”.

Ya ƙare mgnar yana kuma yin mgnar zuci.

“Wannan yarinya sirri baya kamata da wuri, duk da ta shaƙi ƙamshin turaren nan amman ga yadda take min gardama”.

Yayi mgnar cikin ƙoƙon zuciyarsa dan baiyi zaton zata iya musa mishiba.

Ita kuwa Khsusar kallonsa tayi jikinta na rawa ta girgiza kai tare da faɗin.

“Toh ai ban fahimci mai kake nufi bane! wannan wace iriyar magana ce?  me hakan yake nufi kenan?”.

Marerece Murya yayi da alamun damuwa yace. “Dan Allah dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) kiyi shiru kar kuyi magana da ƙarfi kiyi magana ahankali zaki fahimceni”.

Lokaci ɗaya tashin hankali ya bayyana afuskarta cike da tsoronsa tace.

“Toh mai zanyi maka?.

Kai ya langwaɓar tare da karyar da kai tamkar mai shirin fashewa da kuka yace.

“Nasan kina Period”.

Cikin fusata da yanayin tsoro tace.

“Ni ka daina maimaita min wannan maganar”.

Matsota yayi tare da cewa.

“Dole in maimaita Miki wannan maganar tunda abinda nake sone kuma kikayi al’ƙawarin zaki yimin!”.

Girgiza kai tayi still jikinta na rawa tace.

“A’a ai ko al’ƙawari idan abu yafi ƙarfin ka ba zaka yiba zaka janye sa”.

Cikin sauri ya kalleta tare da cewa.

“No baifi ƙarfin kiba Khausar bafa cewa nayi kiyi min komai ba, idan Period ɗinki yazo kika fara kawai zaki ɗauki ƙyallen ne sai kisa shi agabanki madadin kisa Pad Idan yayi awa ɗaya sai ki cire kisa min aleda zanzo in karɓi abuna shine kawai abinda nake so Khausar abinda kaɗai nake sofa”.

Ya ida maganar cikin yaudara murya tamkar zai fashe da kuka.

Ya cigaba da cewa.

“Kuma kada ki manta al’ƙawari kika yimin kuma baifi ƙarfin ki ba sannan ba kanki nace kibani ba”.

Cike da mamaki take Kallonsa cikin yanayin damuwa da alamun tsoro ta zare Idanunta kana tace.

“To me zakayi dashi Uncle mai zaka yi dashi wannan wani irin abune?, Wannan wace iriyar magana ce zaka ce min haka Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n”.

Cikin sauri ya riko tsintsiyar hannunta tare da Marerece fuska kana yace.

“Ki yiwa Allah da Annabi ki nutsu Khausar kar ki manta cewa kinyi min al’ƙawari.

Kuma wallahi idan kika faɗawa wani zan miki abinda ba kiyi tsammani ba!”.

 

Cike da fushi da kuma tsoro tace.

“Toh me zaka yimin tukunna?”.

Karyar da murya yayi tare da saurin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Zanyi fushi dake”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da sakin murmushi har tayi zaton ko wani mugun abu zai mata tura madaidaicin bakinta tayi tare da cewa.

“Nidai gaskiya banyi al’ƙawari ba Uncle tsoro nakeji, amma tukunna mai zaka yi dashi?”.

Ɗan hararanta yayi tare da cewa.

“Ke dai me ruwanki? Maganin abu zanyi da shi maganine ance sai na samu Period ɗin zanyi maganin?”.

Kallonsa tayi still zuciyarta na cigaba da tsinkewa tace.

“Wani irin maganine wannan wanda saida period ɗin mace za’ayi shi?”.

Wani irin kallo ya watsa mata kafin ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Magani ne kawai nace miki magani zan haɗa amma kamar baki yarda dani ba inada matsala ne ke dai in Zaki yimin in samu lafiya in kuma baza kiyi min ba shikenan dama can aikinsa inada ciwon kai ko?”.

 

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da jinjina kai kana tace.

“Eh nasani toh shine ake cemin saina samu yanzu idan kika samin a farin ƙyalle, da daddare in zan kwanta ne zangoga shi asaman goshina ance insha Allah daga ranan na rabu da shi kenan”.

 

Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da lumshe Idanunta kana tace.

“Tsakaninka da waye?”.

Ahankali yace.

“Tsakanina da Allah Wallahi dagaske na faɗa miki. My Khausi Magani zan haɗa kuma kinsan duk sanda ciwon kan nan ya tashi  kamar zan mutu”.

Khausar kuwa jinjina kai tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace.

“Toh shikenan  ba damuwa insha Allah zanyi maka”.

Ta faɗa tare da juyewa ta fice bayan ta dauki ƙyallen.

 

Tun da Khausar ta koma ɗaki ta rasa meke damunta baki ɗaya ƙamshin ƙyallen na damunta ahankali ta buɗe drawer ta ɗauki leda ta jefa ƙyallen aciki sannan tasake saka wani ledan saida ta ninka masa laida biyar sannan ta fita bakyard ta ajiye sai asannan ta samu nutsuwa baki ɗaya ƙamshin ɗaga mata hankali yake.

 

Bayan kwana biyu Ya kama yau ne ake sunan Aunty Asiya misalin ƙarfe goma Mommy, Hajiya Bunayya, Amina, Raudat, Ramadan duk suka tafi sunan Aunty Asiya gidan ya rage saura Khausar ita kadai kasancewar. Mommy tace da ita dai idan ta dawo zata je dan kada abar gidan.

 

Khausar dake zaune a Bedroom ɗin ta tayi saurin miƙewa jin muryan Asma’u afalo  atare Asma’u da Haiydar suka shigo falon da alama daga koyon Machine ya dawo saboda hannunsa dake riƙe da ƙaton L, kwanciya yayi akan 3sitter tare da kunna TV bayan sun gaisa da Asma’u, Khausar kuwa cike da farin ciki ta rungume Asma’u.

Ahankali Asma’u ta janye jikinta daga na Khausar kana tace.

“Ya naji gidan shiru kamar ba kowa?”.

Kai Khausar ta jinjina cikin sanyin murya da alamun damuwa atare da ita tace.

“Eh babu kowa sunje gidan Aunty Asiya yau sunanta, nima so nake inyi wanka sai Inje in duba su. Mommy nake jira baya ga haka ma jikina duk amace yake”.

Ta ida maganar lokacin da suka shiga ɗakin ƙaramin fridge dake ɗakin Khausar ta buɗe tare da ciro Friut ta ɗauki Plate akai ta zuba mata kana ta ajiye mata agabanta.

 

Cike da kulawa Asma’u tace.

“Khausar ya dai na ganki Asanyaye kamar akwai abinda ke damunki?”.

Girgiza kai Khausar tayi tare da cewa.

“Babu komai Asma’u kici Fruit”.

Kallonta Asma’u tayi tare da girgiza kai kana tace.

“A’a Taya zan sha Friut baki faɗa min abinda ke damunki ba?”.

Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.

“Wallahi Asma’u wani Abu ke damuna, yake kuma bani tsoro nasha faɗa miki al’amarin Uncle Naseer.

Yana bani tsoro kince ba haka ba ko to kinji abinda ya faɗa min kwanaki”.

Atake ta kwashe dukan yanda sukayi da Naseer ta faɗa mata“.

Atsorace Asma’u ta dafe ƙirjinta tare da cewa.

“Kai Khausar kada ki yarda ki sanya Period ɗinki akan wannan ƙyallen ki bashi muka san mai zaiyi dashi  ke har kin yarda dashi”.

Girgiza kai Khausar tayi cike da damuwa ta langwaɓar da kai kana tace.

“Nasan yana da ciwon kai, amma baki ɗaya ban yarda cewa maganin ciwon kai zaiyi dashi ba”.

Ajiyar zuciya Asma’u ta sauƙe kana tace.

“Gaskiya kar ki yarda ki kiyaye”.

Cike da damuwa Khausar tace.

“Toh yanzu ya zamuyi?”.

Gyara zama Asma’u tayi tare da faɗin.

“Gaskiya dai kam Khausar kada ki yarda kisa jininki akan wannan ƙyallen, hakan ma bazai yuba mukasan me yake nufi dashi, kika san me zaije ya aikata dashi ai haka baza ta yuba?”.

Lumshe idanu Khausar tayi kana tace.

“Toh shikenan ai dama bazan saba”.

Mommy ce tashigo tare da ɗaga labulen bayan tayi sallama.

Amsawa suka yi kana cike da ladabi Asma’u ta gaishe da Mommy.

Cikin sakin fuska Mommy ta amsa tare da tambayarta yasu Umminta.

 

Kallon Khausar Mommy tayi tare da cewa.

“Khausar ki ɗauki Plate da Spoon ki Kai gidan Aunty Asiya”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”,Juyawa Mommy tayi ta fice.

Miƙewa Khausar tayi tare da cewa.

“Asma’u muje ki rakani”.

Kai Asma’u ta gyaɗa tare da miƙewa direct kichen ta nufa ta tare da ɗaukar Plate da Spoon suka fita kai tsaye gidan Aunty Asiya suka nufa.

 

Ahankali Asma’u ta zubawa raguna biyu dake rataye a coumpund ɗin ido, da alama na suna ne duk angama gyarasu  an cire kayan cikinsu ana jiran su tsantsame.

Har suka shiga cikin gidan suka kai Plate ɗin baki ɗaya hankalin Asma’u na kan ragunan dake coumpund ɗin bayan sun fito Asma’u ta kalli ragunan cikin sanyin murya ta kalli Khausar tare da cewa.

“Khausar ga dama ta samufa”.

Da sauri Khausar tace.

“Wacce damar”.

Cikin yin ƙasa da murya Asma’u tace.

“Dauko ƙyallen nan zamuyi muzo musaka jinin wuyan ragon nan”.

Jinjina kai Khausar tayi cike da gamsuwa tace.

“Ƙwarai kuwa Asma’u muje mu ɗauka”.

Cikin sauri suka fice cikin sa’a koda suka shiga basu samu Mommy a falon ba tana toilet. Haiydar kuwa baya nan kai tsaye backyard suka nufa Khausar ta ɗauki ƙyallen a inda ta ajiye sannan ta since.

Da sauri Asma’u ta kawar da kanta gefe jin yanda ƙamshin jiki ya bugeta.

Cikin ya mutse fuska tace.

“Kai Wannan wani irin ƙamshine mai tada hankali ba daɗin ji”.

Baki Khausar ta taɓe kana tace.

“Hmm nima dai haka naji”.

Ahankali suka juya suka fita kai tsaye gidan sunan suka nufa Baba Mai gadi dake zaune yace da.

“Hajiya Khausar ya gida?sai yanzu kika leƙo?.

Murmushi tayi tare da cewa.

“A’a ɗazu ma nazo bamu ganka bane”.

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Ayyah wataƙil na zagaya ne”.

Cikin sa’a babu kowa a coumpund ɗin kallon Khausar Asma’u tayi cikin ƙasa da murya tace.

“Kinga mai gadi na kallonmu sai munje dai-dai wajen ragon zan durƙusa kamar takalmina ya tsinke ke kuma saikiyi saurin daddalan jinin ajiki”.

Kai Khausar ya gyaɗa suna isa wajen Asma’u ta tsugunna tana taɓa ƙafarta.

Khausar kuwa cikin sauri ta matsa jikin ragunan ta ciro ƙyallen cikin leda sannan ta manna ƙyallen ajikin wuyan ragon dake ɗigar da jini kaɗan-kaɗan sannan ta sake dan dala tayi haka har sau uku ajikin wuyan ragon cikin sauri tace.

“Asamu’u nayi mu tafi”.

Miƙewa Asma’u tayi suka nufi ƙofa,Baba mai gadi yace.

“Ya dai Asma’u ta kalmin tsinkewa yayi ya kuka tafi baku shiga ba?”.

Murmushi Asma’u tayi tare da cewa.

“A’a kawai dai na ɗan gurɗene naji ƙafar na yimin ciwo sannan mun manta ɗauko abinda Mommy ta aiko mu mukawo”.

Daga haka suka fice daga gidan.

Kai Baba ma gadin ya jinjina musu,

Tare  da juyowa, cikin gidan,

Wani irin zazzaro idanu waje yayi cike da tsanani tsoro da mamaki Baba Mai gadi ya buɗe baki da ido da hanci duka gani, cikin raguna biyu dake rataye ɗaya ya ɓace ɓat……!

 

 

 

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276,*

 

 

 

 

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button