Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 55

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

55

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

 

*GARKUWAR* taku ce dai MA’AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike  maimaita muku dararen forkon kuruciya*

 

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

 

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

 

Ga masu buƙata ga number’ wayata wanda nake whatsApp dashi 08069423567 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu,  ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.

0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi  gida.

GARKUWAR MA’AURATA

 

 

 

Cikin wani irin su yan rai Modibbo ya kife kanshi  bisa cinyar Abban Jameel  dake kusa dashi cikin rawan murya da jiki.

Ya bude baki da nufin yin mgnar, sai kuma yayi saurin rumtse idanunsa sabida wani irin raunataccen kuka daya taso mishi daga ƙasan zuciyarsa, cikin Shesh-sheƙan kuka ya ɗago fuskarsa da tayi jazir ya kalli Bappa Jimeta da Lamiɗo da idanunsa dake kwaranyar da zafafan hawaye, sai kuma ya juyo ya kalli Abba da Mlm Arɗo tare dasa hannunsa duka biyu ya kamo hannun Abban cikin wata irin murya mai nuna zahirin abinda ke zuciyarsa yace.

“Abba akan abinda J ɗina ya somin ya kuma zaɓamin kuke kokonta, zan aminta dashi. Shin Abba baka gaya musu waye ne J a wurina ba, Abba ka tambayi Ummi kaji tunda muke tsawon rayuwarmu ra’ayinmu bai taɓa ban bantaba muddin naso abu to J zai soshi nima duk abinda J yakeso sai na soshi, wannan ita jarabawar ƙarfin amintakarmu bamu taɓa samun saɓanin ra’ayi ba kan komai”.

Sai kuma ya rumtse idanunsa da ƙarfi domin tuno abubuwa da yawa na cikin ransa da suka zame dalilinsa na kyara da hantarar Khausar, cikin fuzgar numfashi yace.

“Abba kace musu zan rayu da ita cikin yaƙini, da kuma kiyaye farin cikinta da haƙƙinta, amman kalmar amana da sukace min tayi min nauyi tamin ƙarfi, ta zarta iyawata.”

Cikin zubda hawaye Abban Jameel ke shafa kansa tare da ɗan bubbuga bayanshi kaɗan.

Sai kuma ya kalli Dr Jameel tare da cewa.

“Jameel ɗaukeshi ku tafi, ka rarrasheshi, ka zame mishi madadin Jamiluna, wanda nake da ya ƙinin da yanzu yana raye bazai taɓa barin hawayen amininshi ya zuboba”.

Cikin gamsuwa Dr Jameel ke gyaɗa kai.

Bappa Jimeta kuwa cikin sanyin jiki da kuma tausayin Modibbo yace.

“Kayi haƙuri Aliyu na fahimci yadda kakeji a zuciyarka, amman dolece tasa nake baka amanar Khausar”.

Cikin rawan jiki ya  yunƙura tsaye sabida jin Dr Jameel na ɗagoshi.

So yake yayi mgn amman ina ya gaza,

Cikin Tausayawa Malam Arɗo da Lamiɗo suka haɗa baki wurin cewa.

“Jameel kuje”.

wanda hakane yasa dole yabi bayan Dr Jameel dake jan hannunsa.

 

Kai tsaye Side ɗin Didi ya nufa da shi.

 

A falo suka samu Didi dasu Lalla Khadijah, bisa alamu Khausar da Lalla Hafsat kuma na cikin bedroom ne.

 

Da sauri Didi ta ɗago kanta tare da zuba mishi ido.

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin sanyin jiki gami da rauni da raɗaɗin ciwon mutuwar J ɗinsa, da kuma raunin ɗa idan ya kasance gaban mahaifiyarsa, ya isa gareta, tare da direwa bisa guiwowinsa cikin yanayin da bazai iya jumrewa ba, ya kife kanshi bisa cinyoyinta tare da saki wani irin maraitaccen kukunda yasa.

Zuciyar Didi wani irin gigitaccen bugawa, yayinda Lalla Khadijah kuwa da sauri ta dawo gareshi.

Tana mai zama gefenshi.

Cikin yanayin tsoro Didi ta buɗe baki a hankali tacewa Dr Jameel.

“Jameel meya sameshi?”.

Da sauri Dr Jameel ya zauna gefen Didi ganin alamu ta shiga ɗimuwa yace.

“A’a fa Didi babu abinda ya sameshi, maganar wasiyar da Amininshi Jameel mai kama da ni, ya bar mishine ya sashi cikin wannan yanayin”.

Wani nannauyan ajiyan zuciya Didi ta sauƙe sai kuma ta daura hannunta bisa kanshi tana ɗan shafawa tare da sa ɗaya hannun kuma tana ɗan bubbuga bayanshi, cike da tsananin tausayinshi da kuma raunin da yasa itama ta fara zubda hawaye.

Lalla Khadijah kuwa a hankali ta sauƙe numfashi kana ta koma gefe ta zauna.

Lalla Hafsat da Khausar da yanzu suka fito ne, cikin sauri Lalla Hafsat ta matso kusa dashi cikin sanyi  tace.

“Kayi haƙuri Aliy… Sai kuma tayi shiru ganin Didi ta ɗaga mata hannun kana tayi mata alamun da ta barshi yayi kuka, domin yin kukan zaisa yaji sanyi.

Ita kuwa Khausar cikin wani irin yanayi mai cike da rauni ta zauna tare da rumtse idanunta.

 

Rahman dake zaune gefen Khausar dake kusa da Lalla Hafsat kuwa sai yanzu ta dire numfashin dake bayyana tsoron data shiga.

 

Ita kuwa Khausar a hankali ta buɗe idanunta, wani irin kallo take bin Modibbo dashi wanda yake tafe da tsananin tausayi rauni jinƙai domin itace kaɗai tasan irin aminci da shaƙuwar dake tsakanin Yah Jameel din da kuma Modibbo.

Ganin yadda yake wani irin kukanda ke gab da ficewa da numfashin sane yasata jin wasu irin tagwayen hawaye masu masifar zafina kwaranyo mata tamkar an ɓalle bakin pampo.

Da sauri Lalla Khadijah ta dawo kusa ita tare da sa hannun ta fara sharce mata hawayen da ta sharcesu wasu zasu meye gurminsu.

Didi kuwa kallon Khausar ɗin take cike da so da ƙauna sai kuma ta lumshe idanunta tare, da jingina kanta jikin kujerar.

 

Zuwa yanzu Khausar kam itama kukan ya subce mata, sosai ya taho mata da Shesh-sheƙan mai danne numfashin, wanda hakane yasa Didi yin guntun murmushi tare da yiwa Lalla Hafsat alamun ta ɗauki Khausar su shiga ɗakinta.

 

Haka yasa Lalla Hafsat tallabe Khausar tare da janta suka, shiga ɗakin Didi mai cike da ƙawa na al’farmar, bakin gado ta ajiyeta, tare da buɗe fridge ta dauko goran ruwa mai sanyi ta ɓalle marfin kana tasa matashi a baki wanda dole yasa tasha.

Shan ruwan ne yasa ƙarfin kukan nata raguwa sai dai Shesh-sheƙan dake fitowa daga ƙahon zuciyarta, cikin sanyin jiki Lalla Hafsat ta jawota ta jinginata da jikinta kana a hankali ta fara mgna.

“Kiyi hakuri Khausar ki daure ki koyawa zuciyarki dauriya, tunda kinga mijinki mutum ne da wasu mahimman abubuwan ke sashi kasancewa mai rauni, to dole ke ki kasance jaruwa  ki iya kwantar mishi da hankali da tausarsa, a duk sanda kika ga ya kasance cikin irin wannan yanayi, ba kuka zakiyiba, lallai ne da wuya mu mata buga mazanmu cikin damuwa mu iya hana kanmu kuka, toh amman tunda kinga a duk sanda akayi mgnar Jameel ko tunanin Jameel ya dawo zuciyar mijinki yana ɗimaucewa da raunata, Please na roƙeki ki daure kike hana kanki kuka, nasan ciwon da kikeji a zuciyarki domin babu abinda ke raunata mace kamar kukan mutum hudu miji, uba, ɗan uwa yaya ko Kani da kuma ɗanka, musamman in sun girma domin muddin kaga namiji na kuka tofa abin babbane, amman duk da haka ki koyi kontar mishi da hankali, dan na lura in ba haka ya samuba zai iya kamuwa da cutar damuwa”.

Ta ƙare mgnar da cikekken yaƙinin ganin tsananin tausayin mai jagorantar so da Khausar keyiwa ɗan uwan nata.

Ita kuwa Khausar cikin raunatacciyar murya tace.

“Aunty Hafsat tausayinshi nakeji, komaifa na rayuwar Duniya da Yah Jameel yakeyi, ko abinci baya iya ci sai da Yah Jameel, tunda nake tare dasu a rayuwata sau biyu na taba ganinsu ba a tareba, ranar da nayi rabuwa ta karshe da Yah Jameel, da kuma wata rana da naje wurin Ummi shi ya maidani nan ma yaje neman Yah Jameel din ne.

Aunty Hafsat shifa baida wani aboki a duniya sama da Yah Jameel komai tare sukeyi”.

Sai kuma ta fashe da kuka.

Hakane yasa Lalla Hafsat ƙara ruggumeta.

 

A can falon kuwa kusan tsawon 21 minutes Modibbo yayi yana kuka mai ciwo a rai.

Kana a hankali ya ɗago kansa ya kalli Didi dake zubda hawaye, cikin rauni yace.

“Didi J ya tafi ya barni a lokutan da zanfi buƙatarsa, Didi J fa, shine mutumin da duk abinda yasan inaso in dai yana da damar mallaka minshi koda rasa abin zai iya zame mishi ajali yakan sadaukar min dashi.

Didi J fa shine yayi min zaɓin matar aure, ya kuma tabbar da yayi dukkan abinda zai ta yadda gashi har bayan ransa saida abin ya tabbata, Didi J fa shine mutum ɗaya a duniya yake gane dukkan gaskiyar dake zuciyata da motsin jiki a koda na ɓoye abin, Didi J shike riganin sanin abinda nakeso ni kaina.

Didi akan zaɓin da J yayi minfa iyayenta ke bani Amana, Didi ta yaya zan iya cin zarafi da gaza ankilta zaɓin J na? Didi zato suke inada muguwar zuciyar da zan iya wofintar da zaɓin J ne. Didi ki gaya musu me sukeso inyi a duniya da zai nuna musu halaccin da zanyiwa zaɓin da J na yayi min Didi J fa ya gane wacece ita a ƙasan zuciyata duk da kafiya da nacin da nayi wurin ɓoyewa saida ya gane shi yasa ya zaɓa min ita”.

Zuwa yanzu kusan duk hawaye suke zubdawa.

 

Didi kuwa a hankali tace.

“Ba kai kadaiba Aliyu dani da ahlinka duk zamu tayaka ankiltawa da kyautawa zaɓin J dinka kuma zamu kasance masuyi mishi Addu’o’i a cikin dukkan sallolinmu.”

Sai kuma tasa hannunta duka biyu ta tallabe habarshi da yayi zafi jau.

tare da share mishi hawayen da wasu ke korar wasu kana taci gaba da cewa.

“Kayi haƙuri Babana amanarsu bazata gareka riƙewaba tunda sirrin zuciyar kace da J ɗinka ya gane”.

Kanshi ya kuma jifewa yana mai ci gaba da kukan.

Jin an kira sallan azabtar ne yasa tai ta kara bashi karfin guiwar tare dasa Dr Jameel ya kama hannunshi suka tafi.

 

Kana su kuma duk sukayi al’wala.

 

Zakariyya ma dake tare da Asiya a falon ƙasa jin kiran sallame yasa ya ɗan kalleta cikin salon so yace.

“Baby bari muje muyi salla,  kafin mu dawo kun gama shiri sai mu fita ko”.

Cikin kunya da kuma so haɗin da jin daɗi Asiya ta kali santalelen Balarabe da Allah yayi mata zaɓi dashi duk da hantarar data sha na rashi miji a wurin uwarta taki yarda aje wurin boka gashi Allah ya mata zaɓi, cikin nitsuwa tace.

“Toh ayi mana addu’a”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Me kikeso in roƙa mana?”.

Murmushi tayi tare dasa tafin hannuntan ta rufe fuskarta kana tace.

“Twince muke so”.

Wani irin murmushi mai cike da jin daɗi Zakariyya yayi domin wannan kalmar kaɗai ta isheshi gamsuwa Asiya ta yarda dashi, sai kuma ya bita da ido ganin ta juya ta tafi da sassarfa.

Ibraahim ya kira kana suka tafi masallaci.

 

A can side ɗin Didi kuwa cikin sanyi Khausar ta juyo ta kalli Lalla Hafsat dake gefenta bayan sun isar da sallan murya a tausashe tace.

“Aunty Hafsat kijifa a cikin sallama kuka yakeyi har aka idar da sallan baibar kukaba”.

Cikin sanyi Aunty Hafsat tace.

“Wlh naji Khausar ni kaina bansan sanda naita zubdawaye ba”.

Ita kuwa Khausar kife kanta tayi a gefen kujerar da take zauna a gabanta tana mai sassayan kuka.

 

Ita kuwa Hafsat ɗakin da Didi ta shiga ta nufa.

 

Bayan an isar da sallan kuwa Modibbo gyara zamanshi yayi cikin masallacin tare da fara karatun qura’an.

Ganin hakane yasa su Dr Jameel da Zakariyya kuwa fitowa suka nufi cikin gida.

 

Bayan daworsu ba ɗaɗe su Ummi suka fito.

 

Ummi da Hajia Bunayyah na bayan motar Dr Jameel, Asmau kuwa a gaba ta zauna gefenshi.

Hajja Umma da Aunty Rukayya kuma a motar Ibrahim, sai kuma Aunty Hajara dake gaba gefenshi.

Dan Hajja Nana da innayi sunce su bazasu jeba.

 

Asiya kuwa motar Zakariyya ta shiga, gaba kusa dashi sai kuma Haiydar da Hakim dake baya.

 

Sai su Abban kuwa da Abualeey yasa amintattun hadimansa suka fita dasu cikin motoci na al’farmar.

Su maza wuraren tarihin kasar aka kakkaisu da abinda ya shafi masarautar.

 

Su Dr Jameel kuwa kai tsaye The exotic bouknadel garden Rabat suka wuce.

 

 

Abujan Nigeria

Tun bayan da Unclee Naseer ɗin ya sake fita, Amina ta komai cikin bedroom bata sake fitowa falonba, sai bayan sallam azahar wanda ita ba sallan tayiba.

A hankali ta fito saɗab-saɗab tana ɗan lelleƙawa  tare da jujjuya ido.

Shiru ba komai falon, wanda hakanne yasa ta kunna TV tashar MBC Max kana ta zauna bisa kujera tare da maida hankalinta kan Film ɗin da akeyi.

 

Dai-dai lokacin kuma Unclee Naseer ke zaune cikin tsakiyar taron abokansa ƴan mafiya, da suka zagayeshi da jan ƙyalle suna surutai haɗin da surkulei suna watsa mishi wani irin ruwa, bisa alamun dai gashi nan zaune a tsakiyarsu amman ruhinsa bai wurinsu.

Babban cikinsune wanda ya fisu mummunar shiga yake mgna kamar cikin raɗa da bada izini yake faɗin.

“Kayi maza ka juya, ka bayyana gareta, kana sane yau kwananku takwas da aure wanda tun daren forkonku akeso ka fara zuƙo mana jininta amman ka tsaya nawa, yanzu dai kwana biyu ya rage maka ka fara kawo mana jininta in kuwa ka bari ka cika kwana goma baka kawoba toh aikinka ya ɓaci”. Sai kuma duk suka fara surutai da watsa mishi ruwan

 

Dai-dai lokacin kuma Amina tayi wani irin saurin naɗe ƙafafunta ta daurasu bisa kujera, sabida ba zato kawai taga macijin nan gabanta.

Ga mamakinta sai taga ya kwanta lip yana kaɗa mata jelarsa.

Da sauri ta kira wayar Unclee Naseer ɗin.

 

Bugu ɗaya kuwa ana biyu aka ɗauka cikin tsoro tace.

“Uncle Naseer gashifa ya sake dawowa”.

Cikin Wata iriyar  murya yace.

“Bafa abinda zai miki, ki sauƙe ƙafarki ki gani”.

Cikin ɓatan basirar batasan ya akayi yasan ƙafarta na sama ba,  ta sauƙe ƙafar nata.

A hankali ta sunkuyo jin wani sanyi a ƙafar tata, ga mamakinta sai taga wannan ƙaton macijin ne ke lasar kafar tata, wani irin fitinennen abu taji yana bin tafin ƙafar tata har zuwa tsakiyar kanta.

Da sauri ta sauƙe numfashi jin muryar Unclee Naseer ɗin nacewa.

“Kin gani ko babu abinda zai miki.

Ko kanki ya nuna zai hau karki hanashi”.

Cikin jin bazata taba iya bujirewa umarninsa ba tace.

“To”.

Sai kuma ta zame tayi ƙasa jin yana ce mata ki sauƙo ƙasa ki zauna.

 

Ido ta zato cikin tsoron da yasa jikinta rawa ganin ƙaton macijin nan ya mirgina ya hau bisa cinyarta, ga mamakinta sai gashi yana cusa kanshi cikin rigarta.

“Ki barshi ya shiga rigarki babu abinda zai miki, zai ɗan gaida kayan daɗi nane ƙadan”.

Taji muryar Unclee Naseer na faɗi mata, zuwa yanzu bazata iya mgnar ba sabida tsabar tsoro sai kai kawai ta gyaɗa kamar yana gabanta.

Aiko haka macijin nan ya fara lasar cikinta har zuwa kan nononta.

Saida yayi kusan minti biyar yana lasarta kana ya zaronkanshi ya fitar sannan ya mirgina ya koma cikin wannan ɗakin dai daya fito.

Ajiyan zuciya mai nauyi ta sauƙe jin dariyar Unclee Naseer ta waya yana ce mata.

“Ba gashiba babu abinda ya mikinko?”.

Cikin wata irin murya tsoro tace.

“Eh ta koma ciki mahhh”.

Dariya ya kumayi tare da cewa.

“Gani nan dawowa yanzu, amman fa kada ki faɗawa kowa”.

Da sauri tace.

“Toh”.

 

Rabat Marocco

 

Sosai fa su Ummi suka ga gari, sai ƙarfe biyar da rabi, suka nufi hanyar gida, wanda tuni su Abban Jameel kam sun koma gida.

 

A hankali Dr Jameel ya kalli Asma’u dake gefenshi tare da ɗanyin ƙasa da murya yace.

“Sweetheart”.

Cikin sauri ta juyo ta kalli su Ummi dake baya, sai kuma ta juyo ta kalleshi ganin su Ummi hotunan da suka yi a cikin Kasbah Oudaia Andalusia garden Rabat suke kallo a wayar Asma’u.

Shi kuwa Dr Jameel cikin sanyi ya ɗan karkarto gefenta tare dayin mgn a hankali yace.

“Sweetheart bari mu ɗan shiga Mahaj Ryad Shopping mall in ɗan sama miki chocolate ko?”.

Cikin jin dadi da son zaƙinta tace.

“Toh Yah Jameel”.

Kai ya ɗan jujjuya mata tare da cewa.

“Habibi Jameel zakice”.

Cikin kunya ta rufe fuskarta da tafukan hannunta.

 

Daga nan kuwa suka shiga aiko ya jijjido mata kayan kwalama kam kala-kala.

Daga nan suka biya hotel ɗin suka ɗauko komai na Modibbo.

Sai gab da magriba suka koma gida.

 

Suna shiga Ummi ta kalli da bisa alamu yanzu ta fito ban ɗaki dan yin al’wala tace.

“Khausar bata zoba”.

Cikin jinjina kai Innayi tace.

“Bana gaya mikiba, al’adun masarautar ba”.

Cikin sanyi Ummi tace.

“Toh yanzu muda jibi zamu tafi kuma kenan haka zamu tafi bazamu gantaba?”.

Da sauri Innayi tace.

“Eh toh bari dai kafin mu tafin zanyiwa Didi mgn in kuma akai abunan dole za’a Abu nan”.

Take mgnar da kurman baƙi.

Hajja Nana ce ta taɓe baki tare da cewa.

“Koma menene dai ki jawa jikanki kunne karya karmi jika dan ƙaramace”.

Hajia Bunayyah ce ta taɓe baki kana ta juya ta nufi ɗakinsu.

 

A sashin Didi kuwa, koda Lalla Hafsat tazo ta gaya mata Khausar nata kuka, da sauri taje, ga mamakinta, sai suka samu tuni tayi bacci hakanne yasa Didi gyara mata zaman zuwa kwanciya.

 

Suko suka fito falon, Didi kuwa da kanta ta shiga kitchen ta haɗawa Modibbo da Abualeey  lunch sai dai ga mamakinsu ba shigoba har akayi sallan la’asar da aka idar ne Didi ke tambaya Abualeey shine yake ce mata yanzuma yana can masallaci.

Cikin sanyi tace.

“Tun safe ba, bai kuma cin komai ba gashi yanzu har biyar ta kusa”.

Cikin kulawa Abualeey yace.

“Naso inyi mishi mgn sai kuma na fahimci karatunan da yakeyi ne kaɗai ke ɗan sama mishi nitsuwa, shiyasa ban matsa mishi ba, amman yanzu sarki fada ke cemin ya wuce sashinsu”.

Cikin sauri Didi tace.

“Yauwa to bari inje insa matarshi ta kai mishi abincin.

 

Moddibo kuwa a hankali yake tafiya cikin wani irin rauni mai haɗe da zafin jiki, ya tura ƙofar falonshi ya shiga.

Sai kuma ya kunshe idanunsa domin hawayen da suka cika mishi ido ya hanashi ganin gabanshi.

Wasu sabbin hawayene suka biyo bayan waɗanda suka zubo ɗin, wanda har yanzu ya gaza hana kanshi kuka.

A hankali ya wuce bedroom kai tsaye ya faɗa Bathroom.

 

Duk da sanyin da aka fara tsulawa alamun yau garin zaiyi sanyi, hakan bai hanashi sakarwar kanshi ruwan sanyi ba.

 

Didi kuwa ta kalli Lalla Hafsat tare da cewa.

“Ina ɗiyartawa, na shiga ɗakin na samu bata nan”.

 

“Eh ta farka daga baccin kuma, sai naji tana cewa Rahama tana son zuwa wurin su Ummin”.

Da sauri Didi tace.

“Yanzu ina take”.

“Ta shiga ɗakin Rahama wai zata kirata tazo ta rakata wurinsu”.

Da sauri Didi ta kuma cewa.

“Toh kada taje kira min ita”.

To tace kana ta shiga ɗakin Rahama ta kirata.

A tare suka fito, cikin sakin fuska Didi ta kamo hannun Khausar ɗin tare da jawota kusa da ita kana a tausashe tace.

“Ɗiyata, kizo ki kaiwa mijinki abinci, kinga tun safe babu abinda yace, sai kuka daya wuni yi.

Ki kai mishi abincin kisashi ya ɗanci kafin ya tafi sallan magarib, kada ki bari ya tafi da yunwa kiji ko?”.

Cikin sanyi ta gyaɗa kai.

Ita kuwa Didi wani ɗan Kekkyawan basket mai masifar kyau da sheƙi wanda ke ɗauke da womers guda biyu sai plate spoon and fork sai kuma wani ɗan Kekkyawan roba mai kama da saƙeƙƙe dake cike da fruits sai kuma goran ruwa mai sanyi a gefe. Komai dai na buƙata na ciki.

Cikin kula tace.

Kiyi sauri kije kinga biyar har ta gota.

 

Cikin sanyi tace to kana tasa hannunta ta amshi kondon, sai kuma ta ɗan kalli Didi murmushi Didi yayi tare da nuna mata hanya da hannun.

A hankali tace.

“Didi mu tafi da Rahama”.

Cikin kulawa Didi tace.

“A’a bari dai  Hafsat ta rakaki”.

Kai ta gyaɗa alamun to.

Ita kuwa Hafsat murmushi tayi kana tayi gaba tare da cewa.

“Muje to”.

A hankali tabi bayanta, ita kuwa Didi da murmushi ta rakasu.

 

A hankali Hafsat ta tura ƙofar corridor tare da cewa shiga to.

Ɗan murmushi tayi tare da cewa.

“Toh kiyi gaba”.

To tace kana tayi gaba, ita kuma tana biye da ita a baya.

 

Dai-dai lokacin Modibbo kuwa ya fito daga cikin bedroom ɗinsa yana mai zuba wani irin ni’imtaccen ƙamshi mai daɗin shaƙa tattausar jallabiya ce a jikinsa red color sai kuma al’kyabbar da ya ɗaura a samanta fara ƙal mai shara-shara.

 

A hankali ya zauna bisa 2 str dake fuskantar ƙofar shigowa falon, wayarshi dake kan santa table dake gabanshi ya ɗauka.

 

A hankali ya cire pin din wayar.

Hotonshi dana J ɗinsa dake fuskanta wayar tashi ya zubawa ido, wasu sabbin hawayene yaji suna zubo mishi wani na korar wani.

Karo na forko kenan tun bayan rasuwar Jameel da yaji, bari ya shiga WHATSAPP ɗin kan number’n J ɗinsa yaga irin hirarrakin da sukeyi in kamar ace basa tare.

WHATSAPP ɗin ya shiga bayan ya buɗe date inshi na whatsapp ɗin ido ya zubawa kan number’n J ɗinsa da shine a sama.

Cikin sauri ya shiga cikin cart ɗin nasu ganin akwai saƙon da bai buɗe ba, cikin tarin mamaki da rauni yake kallon time and date da J ɗinsa ya tura mishi saƙon.

A hankali ya motsa lips inshi tare da cewa.

“Innalillahi kenan a ranar aka ɗauke min J nane ya turo min saƙon”.

Sai kuma yayi sauri yayi playing voice note din da ya gani na tsawo 2 minute and 36 second.

 

Wani irin tsuma ne da kuma kuka mai sautine suka kubce mishi a tare jin kalmar forko da M Jameel ya fara yi mishi a wannan ranar.

Wani irin rauni da tawayar zuciya ne sukayi mishi gamayyar data haifar mishi da matsanancin kuka mai haɗe da raunin da zai iyasa wanda ya jishi yin kuka.

Dai-dai lokacin kuma Khausar ta tura ƙofar falonshi, bisa umarnin Hafsat dake can bayanta.

 

“Yah Salam”. Shine abinda ya fito kan lips ɗinta ba tare da sanintaba lokacin da taji sautin muryarsa da kuma ganin yadda yasa hannunshi duka biyu ya tallaɓe haɓarsa yanayin wani irin raunataccen kuka mai tsuma zuciya.

 

Cikin wani irin matsanancin rauni ta ƙarasa ciki a hankali.

Ta ajiye basket ɗin bisa table ɗin dake gefensa.

Cikin raunin murya tace.

“Har yanzu kuka kakeyiwa Yah Jameel”.

Kamar daga sama yaji sautin muryarta, wanda ya sashi ɗago kanshi tare da kallon fuskarta da fuskarshi da tayi jazir sabida tsananin kuka.

 

Da ƙarfi ya rumtse idanunsa tare dasa hannunsa duka biyu ya kamo hannayeta ya jawota gabanshi.

Kanshi ya manna kan cikinta tare dasa hannunsa duka biyu ya zagaye ƙugunta, tare da sakin kukan da ya zarta na forkon.

 

Cikin tausayi, rauni, gamida jinƙai. Khausar tasa hannunta duka biyu ruggume shi.

Tare da fashewa da kuka.

 

Dai-dai lokacin kuma Lalla Hafsat ta ɗan turo ƙofar da niyar shigowa.

Da sauri ta koma baya tare da jan ƙofar ta rufe sabida ganin yadda ƙanin nata ya ruggume matar tashi gam-gam.

 

Su kuwa cikin falon, cikin wani irin sanyin jiki Khausar ta ɗan sunkuyo kanshi hawayenta na ɗiga bisa kan fuskarshi daya tallabe da hannunta duka biyu.

Idonshi dake kwaranyar da hawaye ya buɗe a hankali.

Sai kuma ya jawota jikinshi gaba ɗaya ta faɗa kanshi.

Ruggumeta yayi tsam a jikinshi tare da cusa kanshi bisa ƙirjinta ya kife kanshi tsakanin Caɓ…..

 

 

 

 

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER’N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan, Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al’khairi gumbar uku al’khairi, gumbar da ba’a baiwa mai kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al’ajabu shu’umar Humra, da duk sauran kan ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan… Manyan set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

 

Labarinfa yanzu ya gama jiƙa.

Yayi zaƙi shane kawai naku masu karatu. Idan har kin san baki biyaba to wlh ki biya ki karanta cikin aminci.

1k ne da kacal sis 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA wlh ki biya ki karanta wannan littafin yafi miki salama dan samun shi one by one.

 

 

 

 

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button