Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 75

Sponsored Links

75
Hankali tashe momy tayi parking motarta ta fito gashi dare ne sosai ba wasu motaci dake wucewa bare mutane Dan haka kamata tayi tareda rufe motan Safnah din ta barsa anan ta Jata zuwa tata ta shigar taja motar suka
qarasa gida.
Maigadin gidan yayi mamaki da tsoron ganinsu wannan lokacin Amma hakanan ya Bude musu gate suka shiga momy tayi parking suka fito tareda nufar kofan qarasawa
ciki suka shige.
A Palo suka zube dukkaninsu kowannensu gafafunsa da hannuwansa na rawa kaman yanda zuciyoyinsu ke harbawa da rawa tareda
zafi me tiririn gaske.

Babu Wanda yake iya magana acikinsu sbd kowa ta zuci na can na cinsa,.
Safnah Wani irin zufa take fesowa tana tsiyaya sbd tsananin quna da tafasar da Kirjinta yakeyi
Amma jikinta kaf baya iya ko doguwar motsi sbd somewan datai tayi tsabar shock da bugawar da kanta ke Neman Yi.
Momy kuwa kaida kawo take yi itama Bata iya cewa komaiba tana fatan kafin safe DD da
Bena sun gone kurmus ko soyayyan jikinsu kar asamu sbd idan suka rayu su suna ruwa kwance,
Safnah dai aure tsakaninta da DD kaante ya haramta har abada matiqar Bena tana da Rai,
Idan Bena ta tabbata matar Dawood kaante to dole Safnah zata barsa sbd bazasu cigaba da boyewa haduwarta da Bena ba har abadaidan anie Neman dalilin barin aurenta da DD dole sai Anji cewan uwa Daya Uba Daya suke, To idan akaji Hakan aka Kuma San Hakan kenan Safnah ba jinin bulama bace daganan Kuma sunyi Tara babu,
Ba auren DD kaante ba zamansu qarqashin bulama sbd zai San safnan ba yarsa bace,
To daga Nan menene makomarsu????
Wannan shine zancen da momy keyi tana kaida kawo cikin palon kaman zata zauce sbd tinani na lissafi
Kallan Safnah tayi da jajajen idanuwanta tareda zaunawa suka fuskanci juna murya a qage tace
“Meya yakai Bena gidan bayan kince shi Daya ne a gidan Kuma babu Wanda yasan ya Dawo?
Ya akai ita ta sani?
Garin Yaya?
Meyasa Zaki bari duk tsanani duk rintsi Hakan ta faru? Safnah data koma kaman kurba bayan rawa babu Abinda hannuwanta keyi da qafa
Ta Kalli momy da jajayen idanuwanta da sukai jajir tanason tayi magana ta kasa sai alokacin
Wani irin kukan bagin cikin gaske me tsananin nauyi da azaba ya kufce mat ta fasa shi tana zube qasa kan tiles daga kujerar Datake Kai.
Duk da dare ne Safnah kasa riqe kanta tayi ta ringa Kuka Mai tsananin radadi da baqin ciki tana Jin kaman zata mutu sbd baqin ciki.
Kukanta ya saka momy sake shiga baqin ciki da takaici me tsanani itama zuciyarta na sake bushewa da fatan mutuwar DD da Bena tana cikin wannan daren.
Bata rarrashi Safnah ba sbd itama Daman tata zuciyar quna take tana sake shiga lissafi da zurfafa tinani sbd rashin mutuwar su DD Wani binciken zai tsananta akan qwayar Dake jikinsa wadda lefin kama mutum da ita kawai shekara 50 gidan yari ne bare a kama ka da ita kana amfani.
Dole idan DD ya rayu zaa San akwai wannan
kwayar a jikinsa Dan haka taji tana sake jiquwa
cikin zufa da tsananta fatan mutuwar su DD
din tana wannan daren.
******Zeenah data kasa bacci sbd sake Kiran
Bena data samun tabbaci a bakin Nafisat
cewan yaran Daddyn Amnah ne yazo ya
dauketa
Hakan na nufin DD ya dawo kenan tabbas to Amma ko yayane ya kamata Ce Bena ta
kirasu Dan bata taba iya bacci batai magana
da Amnah ba hakama Shima DD din Amma
dukkaninsu babu Wanda ya kira.
Umme dataji Bena din na highbridge ta
tabbatarda DD ya dawo Bai fadawa kowa bane Dan haka tace a kyalesu su huta Dan Allah kafin ya dawo Kaantes.
Kowa ya shige,Zeenah na bedroom dinta tana
Aiki a laptop har kusan 12 na dare kafin ta daure ta kashe tareda daukan wayarta ta sake saka kiran Bena.
Rashin daga wayar Bena din ya sakata Dan shiga mamaki sbd tasan Bena ko acikin baccin tsakan dare sosai daga wayarta takeyi bare yanzu datasan Daren baiyi sosai irin hakanan ba.
Kwantawa tayi gadonta kafin ta a sake saka
Kiran Bena din wayar taci gaba da ringing baa dagawa.
Canjawa tayi ta kira wayar DD shikuma wayarsa a kashe ma gaba Daya, Bata hakura ba sbd ita tinda Bena ta samu accident din baya Shima kusan haka tayita kiranta Bata dauka karshe suka sameta a accident Dan haka Bata wasa Sam da kiranta taji Bata dauka to hankalinta baya kwanciya barema Amnah da tin yamma tayi Wani sukuku jikinta yayi zafi babu Kuma alaman ciwo a jikinta fatanta Allah yasa ba Wani Abu yarinyar taji a jikinta zai samu mummynta ba
Dan haka sai kawai ta nema numbern Naseer ta saka kiransa tana kallan time lokacin 1 daidai.
Shima baiyi bacci ba sbd Yana Aiki Daman wasu lokacin yana Kaiwa har fiyeda 1 dinma baiyi bacci ba.
Kiran Zeenah kaante na shigowa wayarsa da Dan mamaki ya Kalli sunan ya Dan Maida idansa kan time ya kalla yaga karfe dayan dare. Daukan wayar yayi cikin kasa boye mamakinsa da tinanin dole akwai Abinda ya faru sbd babu ta yanda Zeenah da ko da Rana Basa waya bare da irin wannan lokacin, Yana dauka Kai tsaye yace
“Hello Allah yasa lafiya dai”
Ajiyan zuciya ta sauke itama Bata Wani tsaya
Jan wata gaisuwar ba ko batawa juna lokaci ta tambayesa Abinda yasakata Kiran nasa tace
“Bena fa tinda ka dauketa ka tafi da ita baa samunta har yanzu idan aka kira Bata dauka shikuma D tasa ma Bata shiga.”
Shiru yayi tareda sake kallan time yace Shi D Daman wayarsa a kashe suke tin kafin na baro ya bugaci Hakan na kashe masa su,
Ita Kuma Bena din banajin zata qi daga wayar ba dalili gaskia.
“Abinda nake tinani kenan Nima shiyasa na kira, please ko zaka kira ka bincika ko securities na bakin gate din highbridge din zaka tintinba.”
Dan ajiyan zuciya ya sauke sbd Shima gameda lamarin da duk ya shafi DD baya wasa dashi
Dan haka idan har Zeenah tafara tinanin ko ba lafiya ba dole zaije ya duba sbd DD shine top priority nasa a yanzu.
Sallama sukai ya kashe wayar tareda sake kallan lokaci ya sauke laptop dake qafafunsa ya ajiye gefe ya miqe tsaye ya nufi bedroom dinsa Kai tsaye ya dauko key ko kayansa Bai
Wani tsaya canjawaba sbd gajeran wando ne me tsayi da Fadi sosai sai short sleeve shirt takarmi kawai ya zira ya fice.
Gidansa bayada Wani Nisa Sosai da
highbridge sbd DD Dan haka Yana fitowa
yahau titi ba Daman banka gudu tsakar dare ne a kamasa a dauka me lefi ne kafin a gama
gano gaskiyarsa an Bata masa lokaci Dan
haka ya taho a natse Yana Yi Yana duba time
har ya iso highbridge din.
Take aka Bude masa gate ya shige sbd sanin
shi waye sun masa farin sani ire irensu basuda
shamaki da shiga highbridge a ko yaushe suka
ZO.
Duka duka su Safnah Basu rufa 45 min da fita
highbridge dinba ya shigo
Kai tsaye gidan ya nufa yana Isa yayi parking
ya fito Kai tsaye ya dosa kofa ta saka
password Yana sake saka Kiran wayar Bena
datake shiga. Wani mummunan hagayi da qauri ne ya cike palon Wanda ya sakasa shiga mamaki da tsoro da gudu ya nufi hanyar kitchen din wuta yakeci sosai ga ruwa na zuba na kashe wutan sosai Amma Basa Kaiwa koina da wutar take tsabar rudewa ma shi saiya kasa tsayawa kashe wutar ya fito da sauri Yana sake saka
Kiran Bena yaji vibrating din wayar palon Yana dubawa yaga wayar ma dap take da mutuwa
Dan haka ya kashe wayarsa tareda nufar hanyar bedroom din DD Kai tsaye ya Isa da sauri cikin tashin hankali,
Kama kofar yayi zai saka password ya Bude sai ya dakata tinawa da D din ba shi kadai bane a ciki kaman yanda ya Saba akwai yiyuwar Bena ma tana ciki tinda tana gida.
Sakin hannun kofan yayi tareda fara bugawa da karfi sbd yasan ba lallai akejin bugun kofarba.
Yanda yake buga kofan babu alaman motsinsu aciki ya sake saka hankalinsa mummunan tashi Yana kokarin juyawa ya koma kitchen ko wutar ya garasa kashewa
Kiran Zeenah ya shigo wayarsa a rikice ya dauka ya sanar da ita tabbas ba lafiya ba ya tararda gidan wuta tana kokarin kamawa daga kitchen hakama suna ciki Yanata kiransu ba response.
“Ganinan zuwa Nima” Zeenah kawai ta fada masa tana kashe wayar.
Bata bari kowa ya saniba itama ta zari key dinta ta fito daga kaantes ta nufo highbridge itakam a mugun speed sbd Bata damu da
Wanda zai kamata ba tana nuna Id dinta sukaga kaantes zaa saketa batareda Bata lokaci ba.
Ko data iso highbridge securities duk da sunga id card dinta na kaantes daya nuna ita qanwar DD kaante ce Basu barta ya shiga ba sbd lokacin barin masu ziya su shigo ya wuce
Daman da 1 ta wuce duk Wanda ba acikin highbridge din yakeba Basa barin ya shiga. Ranta Baci yake Neman Yi ta kira Naseer dole shi ya kira gate din aka barta ta shigo.
Data shigo ne dole ta Hana kanta gudu da mota Saida ta Isa tayi parking ta fito Kai tsaye tayo cikin
Itama Tari ta fara toro na kamata sosai da ganin hayaqin ta nufi kitchen da mugun gudu ta tadda Naseer duk ya jiqe gurin taimakawa ruwan kashe wutar sbd kamar wutar asiri yakasa kasheta duk da Bata cika kitchen dinba iya inda oven din yake ne taqi mutuwa Kila salya gama cinyewa.
Zeenah fitowa tayi a rikice tayi hanyar bedroom dinsu tana Isa Bata tsaya komaiba ta saka password Kai tsaye ta bude dakin duhu babu haske sosai.
A kan gadonsa ta fara sauke idanuwanta takuma gansu duk su Biyun a kwance kan gadon rufe cikin bargo babu me numfashi a Ihu taso fadawa cikin tsoro da rawar jiki ganin tashigo babu Wanda ya motsa a cikinsu Dan haka da sauri iikinta duka Yana rawa ta zagaya gurin Bena data lura kaman babu kaya jikinta dukkanin hannuwanta rawa sukeyi ta dauki kayan data Gani qasa ta dawo jiki na rawa ta dagata daqyar ta iya saka mata su duk a rude tana gama saka mata ta qwala Kiran Naseer baiji ba ta fito da gudu ta kirasa yaje dakin ita
Kuma ta tsaya Palo tana sake shiga tashin hankali ya taimakawa D Daya Dan motsa alaman Yana yanada sauran Rai ajikinsa ya shirya dole Naseer ne ya dauki Bena yakaita mota ya dawo ya dauko D Shima Wanda yake
Bude Amma Basa buduwa sbd a lokacin ne asalin qwayoyin jikinsa na mummunan maye suke Aiki sbd na desire sun sauka tinda ya sauke bugatansa.
#MAMUH
#DBENA
#LOVE
#ROMANCE
#ABABA

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button