Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 17

Sponsored Links

 

📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

 

*SAKAYYAH*

_Page 17_

*LAST FREE PAGE*

_NA_

*AYSHA ALIYU GARKUWA*

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

*DAGA WANNAN PAGE ƊIN FREE PAGES SUN ƘARE, IN MA KIN SAKE GANIN LITTAFIN SAKAYYAH A WAJE TO. NA SATANE NA ALLAH YA ISA ne, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal yar ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 kiyiwa da Annabi in dai kin san kin sayane don ki fitarmin da littafin na kiyi min mgn in mayar miki da kuɗinki. In kuma kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina, wasu Groups ɗin, kiyiwa Allah da Manzonsa ki bar kuɗinki na yafe cinikin bana buƙatar sa*

 

 

Alhamdulillah su Moddibo sun sauƙa lfy a ƙasa Mai Tsarki cikin ikon Allah Mabuwayi gagara Misali sunyi Umarah sun samu goma shabiyar na watan acan cike da ɗumbin farin ciki.

Yau yakasance ranace ta Sallah angama azumi lfya. Al’ummar Musulmai na duniya sun cika da farin ciki kowa kagani fuskarsa ɗauke da yalwataccen farin ciki, kana kowa yayi shiga ta haiba da kamala.

Alhamdulillah bayan an saƙƙo daga sallar  idi ko wani gida kashiga zaka samesu cikin farin ciki da shiga ta kamala kana da Lafiyayyan abinci.

Kamar yanda ko ina na faɗin duniya ya cika da farin cikin wannan ranan haka yakasance Agidan Lamiɗo.

Acan falon Mommy kuwa hallare suka gaba ɗayan su Khausar ce tsaye riƙe da waya ahanununta cikin shiga ta alfarma da kamala wani rantsatstsen less ne Blue da ratsin fari ne ajikinta ɗinkin riga da skirt yayin da skirt ɗin ya fitar mata da shape din  ƙugunta rigan kuwa tayi ɗass ajikinta ma dai-dai-tan dukiyar fulaninta sun cika fam yayin da tayi ɗaurin ƴar Minister ta zubo yalwataccen sumar kanta zuwa baya daga gaban goshin kuwa ya kwanta luf-luf wuyanta maƙale da sarƙan Gwal da ɗan kunnensa kana fuskarta ɗauke da simple make up daya sake ƙawata kyawun fuskarta.

Yayin da Raudat ma ke sanye cikin irin shigar dake jikin Khausar sai dai nata ɗinkin dogon riga ne.

Haiydar kuwa sanye yake cikin wata Bugaggiyar shadda Sky blue anyi masa ɗinkin samarin zamani rigar ta tsaya iya gwiwarsa, kansa sanye da hula yalwataccen sumar irin na fulanin Usul yana kwance lib aƙeyarsa haka ma Ramadan sanye yake cikin irin shigar Haiydar Yayin da Mommy ke sanye cikin Atanfa mai Golden mai masifar kyau anyi mata ɗinkin riga da zani fuskarta ɗauke da simple make da Khausar tayi mata.

Baki ɗaya falon wani sanyayyan ƙamshi yake fitarwa wanda ya haɗu da ƙamshin jikinsu.

Cike da tsantsar farin ciki Khausar dake ɗaukar su hoto ta juya ta kalli Mommy kana tace .

“Kuce Chesss”.

Dariya suka fashe dashi kana suka ce.

“Cheeessss”, Akuma dai-dai lokacin ta ɗauki hoton.

Sosai hoton yayi kyau kallo ɗaya zaka musu ka tabbatar da cewa suna cikin tsantsar farin ciki da annushawa tare da nutsuwa.

 

Suna cikin hoton Hajiya Bunayya tashigo cikin shiga ta alfarma da kamala sosai tayi kyau.

Zama tayi bayan tayi Sallama Idanun ta akan Mommy tace.

“Barka da Sallah ƙanwata fatan anyi Sallah lafiya?”.

Murmushi Mommy tayi kana ta zauna kusa da ita tare da cewa.

“Ayyah Yaya ina shirin zuwa wajenki ma”.

Murmushi Hajiya Bunayya tayi kana tace.

“Ayyah babu komai nima cewa nayi bari na rigaki zuwa in samu ladan gaisuwar. Fatan munyi Sallah lafiya?”.

 

Jinjina Kai Mommy tayi kana tace.

“Lafiya Lau Alhamdulillah Yaya Ubangiji Allah ya amshi ibadun da ayyukanmu na Al’khairai Allah ya nuna mana na baɗin baɗaɗa da rai da lafiya”.

Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa kana tace.

“Ameen ya Allah Ƙanwata”.

 

Khausar kuwa kallo ɗaya tayi mata ta kawar da kai gefe.

Hajiya Bunayya kuwa kallonta ta mayar kan Khausar dake ɗaukar Haiydar, Ramadan, da Raudat hoto, cike da makirci tayi wani murmushi kana tace.

“Khausar Barka da Sallah”.

Anutse Khausar ta juya ta kalleta babu walwala afuskarta muryarta ta saisaita kana tace.

“Yawwa Barka dai Ummah”.

 

Hajiya Bunayya ta mayar da kallonta kan Haiydar dake tsaye gefenta hannunsa ta kama tare da damƙa masa key da murmushi afuskarta tace.

“Ga Barka da Sallah ka Babana”.

Zare ido Haiydar yayi tare da buɗe hannunsa ya kalli sabon key ɗin mashin dake cikin tafin hannunsa,

cike da tsananim farin ciki mara misaltuwa ya faɗa jikin Hajiya Bunayya tare da rungumeta cike happy ya saƙi ƙara kana yace.

“Wayyo Ummah na Nagode. Allah ya saka da al’khairi. Allah yaƙara miki nisan kwana mai amfani. Allah yarabaki da sharrin Mutum da Aljan, gaskiya nayi farin ciki kinyi surprise ɗina da kince sai bayan Sallah da kwana biyu.

Cike da farin ciki tayi murmushin gefen baki kana tace.

“Ameen,Ameen Babana, Eyyyy dama sunce sai bayan Sallah da kwana biyu sai kuma suka kawo jiya da daddare”.

 

Khausar kuwa cike da takaicin halayyar matar ta riƙa watsa mata harara wani irin haushin ta takeji, aƙasan ranta kam cewa take shegiya muguwa aniyar ki ta biki da izinin Allah babu abinda zai samesa.

 

Mommy kuwa kallon Khausar dake bin Hajiya Bunayya da harara tayi kai ta girgiza tare da cewa.

“Khausar jeki ɗauko mana abinci a kichen ki kawo kin tsaya kin tsare mutane da ido baza ki iya taya ɗan uwanki samun abin farin cikin da yayi ba”.

Zumɓura baki Khausar tayi  tare da miƙewa batare da tace Komai ba tashiga kichen.

 

Haiydar kam Kallon Mommy Yayi kana yace.

“Mommy Ummah ku tashi nayi muku hoto”.

Miƙewa sukayi da murmushi afuskarsu Haiydar yashiga ɗaukar su.

Khausar kuwa fitowa tayi hannunta riƙe da Warmers dake ɗauke da soyayyun kaji ta ajiye a dining kana ta koma ta sake ɗauko wasu Warmers ta ajiye.

Dai-dai lokacin da Mommy ke cewa.

“Yaya mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi Agaskiya nayi farin ciki”.

Fuskar Khausar ta ɓata kana tace.

“Haba Mommy irin wannan godiyar sai kace wacce aka biyawa Kujeran Hajji”.

Kallonta Mommy tayi kana tace.

“Ai kujeran hajjin ne Khausar, mutumin daya so ɗan ka arayuwa har yayi masa alkhairi ai babu kamarsa ”.

Kai Khausar ta girgiza kawai aranta tace Mommy har yanzu baki san wacece wannan makirar matarba, shiyasa kike yabonta wannan matar da kike gani tafi kwalba sharri afili kuwa cewa tayi.

“Hmmmm Allah ya kyauta”.

 

Murmushin da be wuce saman laɓɓaba Hajiya Bunayya tayi kana ta miƙe tare da cewa.

“Nikam zan wuce”.

Miƙewa Mommy tayi tare da cewa toh mungode Yaya Allah yaƙara girma da ɗaukaka”.

Ita kuwa Hajiya Bunayya ficewa tayi Yayin da Haiydar yabi bayanta zuwa sashen Lamiɗo.

yana shiga yace.

“Abba gashi Ummah ta siya min Mashin zan hau?”.

Kai Lamiɗo ya gyaɗa kana yace.

“Babu damuwa tun da kana son hakan, amma kafin nan sai an sake koya maka mashin ɗin na tsawon wata biyu kafin ka fara hawa kai ɗaya kaga ai ka sake koya”.

Jinjina kai Haiydar yayi kana yace.

“Toh shikenan Abba babu Matsala ”.

 

Bayan sallah da kwana biyu jirginsu Moddibo ya sauƙa a Nigeria cike da farin ciki Moddibo, Innayi da M Jameel Ummi suka dawo gida yayin da Hajja Nana ma ta sauƙa ta Ɓadamaye cike da farin ciki da kuma murna.

 

**********

 

Ahaka rayuwa ta cigaba da tafiya komai yana tafiya dai-dai cikin ikon Allah Akwana atashi asaran mai rai, sekonni na juyawa izuwa Mintuna, Mintuna na tafiya izuwa awanni.

Yayin da awanni ke juyawa izuwa kwanaki, kwanaki na tafiya izuwa Makonni.

Yayin da Mokonni ke juyawa izuwa Watanni. A hankali kuma  watanni ke tafiya Izuwa shakara ko shekaru…

 

Alhamdulillah su Khausar sunyi nisa kiwo aski yazo gaban goshi, yanzu suna shirye shiryen zana jarabawar Ƙarshe na kammala secondary School WEAC and NECO baki ɗaya kansu ya ɗauki zafi basu da wani lokaci saina karatu sosai suka maida hankalin su suna karatu tuƙuru domin fitowa da kyakkyawan sakamako Inda yanzu ya rage saura Exam biyar ya rage su kammala Neco.

 

Khausar ce tsaye gaban Dressing mirror jikinta ɗaure da towel da tsawon sa ya kai gwiwarta,

Zuwa yanzu ko ina na jikinta ya cika fam, dukkan ƙirar girma maƙerin budurci ya ƙenƙesa matashi, musamman Dukiyar fulaninta da kuma hips dinta da suka cika ƙugunta, yalwataccen sumar kanta irin na Fulanin Usul ya sake tsawo da sansti.

Manyan Idanunta sun sake girma tare da lumshewa siririn dogon hancinta ya sake tsawo yayin da madaidaicin bakinta ya sake tattarewa izuwa pich collor, yana yin ƙiranta kamar kolbar Coca cola Yayin da Tsananin kamanninta da Kajol ya sake bayyana ayanzu tana da shekara goma sha tara a duniya.

Cikin sauri ta shafa Lotion ɗin ta tare da shafa powder sama-sama sai kuma ta shafa kwalli amanyan Idanunta lipstick kaɗan ta shafa asaman laɓɓannta cikin sauri sauri ta sanya Uniform ɗin ta daya sha guga tulin sumar kanta tayi acuci dashi kana ta feshe jikinta da turarukanta masu masifar daɗin ƙamshi da sanya nutsuwa.

Cikin Sassarfa ta fito falo harara Mommy ta maka mata kana tace.

“Ke dai Khausar ba zaki canza ba kin girma amma kullum shiririta kike ƙarawa tun yaushe Ake jiranki, ga Amina ma can tanata jira amma sai ɓata musu lokaci kike”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da riƙe kunnenta kana tace.

“Sorry Mommy”.

Fuska ta tsuke tare da ce wa. “Kin dai san Amina in ta gaji da jiran ki”.

Cikin ɗan sauƙe numfashi tace.

“Uhumm ai yaseen in ta gaya min mgn ramawa zanyi in banda asarama tun tuni yaci ace ta gama, amman kullum taba cikin dakon aji har wai sai yanzu zamu gama tare”.

Mommy na juya zata fita tace.

“A’a ni bana son fitina”.

Ta ida mgnar tana fita,

 

Haka yasa ta biyo bayan Mommy da ɗan sauri yayin da ko wanni gaɓa na jikinta ke motsa wa baki ɗaya alamun Budurci sun bayyana ajikinta ta ko wanni fanni ta zama cikakkiyar budurwa ƴar gayu First class.

Bayan motar ta buɗe ta shiga bayan ta ƙarasa wajen gani tayi duk Amina ta wani babbaje.

Kamar ba zata ce komai ba sai kuma tace.

“Ɗan matsamin in zauna”.

Kallon banza Amina ta watsa mata cikin ya mutse Fuska ta kalli Khausar kana tace.

“Keɗin har nawa kike da wannan wajen ba zai ishe ki ba?”.

Cikin juya ido tace.

“Kinsa cikakkiyar sura ta ƙasaitattun mata Allah ya min dole wurin bazai isheni ba tunda ba irin baki bane”.

Cike da fusata Amina tace.

“Eh lallai yarinyar nan wuyanki ya kai yanka, amman dadin ta dai bada ɗuwawunki nake zamaba kuma bada ƙugunki nake ɗaura zabi ba”.

Taɓeki tayi tare da juyawa ta kalleta.

Har kamar zata yi magana sai kuma ta fasa ganin yanda lokaci ke tafiya sannan ya Exam na Geography zasuyi tasan muddin aka fara Moddibo na iya hukuntata baya ga haka ga kuma alamun yau akwai  hadari a garin wanda yau kimanin kwana tara kenan ba’ayin musu ruwan saman ba.

Gefen Haiydar ne ya matsa mata ta shiga kana Driver yaja suka tafi.

Suna Isa Khausar tayi saurin ficewa tare da nufar Hall da zasu zana Exam ta nufi Hall ɗin yayin da Iska mai sanyi ya soma kaɗawa gari ya fara duhu suna cikin rubuta Exam ɗin hadari ya fara haɗa gangami sosai a hankali gari ya fara duhu.

Basu wani ja lokaci ba suka kammala rubuta Exam ɗin atare Khausar da Asma’u suka fito.

Asma’u ma ta zama cikakkiyar budurwa komai na Budurci ya bayyana ajikinta.

 

Juyowa Khausar tayi  ta kalleta ƙirjinta rungume da Questions da suka gama rubutawa,  murmushi ta ɗan yi kana tace.

“Asmeey ki gaida min Ummi dan Allah, wallahi nayi missing ɗinta, rabo na da ita fa ya kai wata biyu”.

 

Hararanta Asma’u liƙa mata kana tace.

“Ai baki da kirkine sannan babu saƙon  ki da zan fada mata in da gaskene kizo”.

Ta ƙare mgnar tana mai ɗaga kanta ta kalli sama, ganin yadda gaba ɗaya garin ya rufa yayi duhu.

Da sauri Khausar ma ta fara juye-juye tana cewa.

“Yah Salam wannan hadari haka, ina Haiydar suzo mu tafi, kar ruwa nan ya rutsamu a nan.”

Murmushi Asma’u tayi tare da cewa.

“Allah yasa ya rutsa kin dai muga ta tsoro”.

Ta ida mgnar tare da yin murmushin mugunta dan tasan yadda Khausar ke masifar tsoron walƙiya da tsawa.

“Ba Amin ba”.

Khausar ta faɗa tare da tura baki.

Ita kuwa Asma’u dariya tayi tare da jan hannun Bashir sukayi gaba saboda yanda hadarin ke sake gangami ko ina yayi ɗib.

Murmushi Khausar tayi kana tace.

“Bashir dan Allah kagaida Ummi, dan naga yau mutuniyar Black Stomach take ji dashi”.

Asma’u na ƙoƙarin shiga mota tayi murmushi kana tace.

“Oho dai ance zuwa da kai ai yafi saƙo”.

Khausar kuwa murmushi tayi tare da bin bayansu ganin Haiydar yayi gaba.

Da ɗa  sassarfa ta  tashiga bayan motar ta zauna kusa da Haiydar tana ɗan kallon harabar makarantar da duk aka watse sai mutane ɗaɗɗaya har malamai da alamun sun tattafi da sauri ta juya ta kalli Haiydar kana tace.

“Ina Amina kuma?”.

hannu ya buɗe mata alamar bai sani ba, bata sake cewa komai ba,

ta lumshe idanunta tare da jingina bayanta da jikin Kujeran sassayan iskan  hadarin dake bugawa na ratsata.

 

Acan harabar makarantar kuwa Amina ce da Samira Sani ke tafiya.

Cikin taɓe baki Samira ta kalli Amina kana tace.

“Ni wallahi tunda nake ban taɓa kallon mutum Irin Moddibo ba ace mutum kamar dutse sam baya fahimtar komai”.

Murmushi Amina tayi kana tace.

“Hmmm ke dai Samira bari M Jameel ɗin ma meyene, duk tsawon lokacin da muka ɗauka muna aiki da maganin fa yanda yake wani shan min Ƙamshi”.

Harara Samira ta watsa mata cike da takaici tace.

“Amma Wallahi Amina baki da godiyar Allah ki dubi yanda mutumin nan ya fara sake miki, yana amsa gaisuwar ki da fara’a, yana kula ki da ace nice nasamu wannan damar, awajen Moddibo ai dana godewa Allah”.

Jinjina kai Amina tayi kana tace.

“Haka ne kuma amma gaskiya har yanzu sai mun sake sabon shiri akansu domin har yanzu Malam Jameel yafi ji da wannan shegiyar yarinyar akaina”.

Da wannan hira suka isa jikin motar wani matsiyacin kallo Amina ta watsawa Khausar dake bayan mota Idanunta alumshe cike da gadara da kuma Izzah ta ya mutse fuska kana tace.

“Iyeee ƙarfin hali yau naji Agola da ƙarfin hali, motar na gidan Ubankine da zaki shiga baya kiyi kane-kane aciki, to ni kuma a ina zan zauna ji yanda kika tara ƙannenki kuka lafe abaya ku gaku ramukan kura ko daga ke sai ƙannen ki, wai ma tukunna ni akanki zan zauna ne!? Da kika wani baza masaka-masakan duwaiwaka”.

 

Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe ta zuba mata su tana kallonta cike da mmki, amma ba tace komai ba sai gyara zamanta da tayi tare da buɗa mata inda zata zauna.

 

Ya mutse fuska Amina tayi cike da jaraba da kuma gadara ta dubi inda Khausar ta matsa mata kana tace.

“Wannan wani irin iskanci ne da raini ne ko kuma ni sa’ar kice ke badan kinyi sa’ar Babanki ya mutu ya bar uwarki tayi zawarci babana ya kwasa ba ai koda hanyar da nabi baki isa ki biba. Agola kawai mara galihu ƴar matsiyata”.

 

Cike da ɓacin rai Khausar ta ɗago kanta babu walwala afuskarta ta kalli Amina tare da cewa.

“Wai Meyesa kike son zagina ne? Baga shi na gyara niki ba wannan ɗan ɗuwawun da kamar an ɗaurawa kare zani me zai hana filin isarki, baki shigo  kin zauna kinga wurin bai ishi tsamurarrun mauzanki da suke kamar an matse lemon tsamiba kawai saboda kin saba da Akuyanci da kuma karnukan ci sai kin tsaya anta masifa dake da raba hali, saboda ke Jaka ce baki san darajar mutane ba,  zaki tsaya kina ta goranta min akan wani Akwalar mota! To ki sani ni dai bazan zagi iyayenku ba musamman mahaifinki da yake mumini uwarki kuwa zaginta ma asarane don ko zagi akan mai tsarki yake fatan a aikeshi”.

Harara Amina ta watsa mata kana Afusace tace.

“Eh koda Akwalar ce aiba Ubanki bane ya saya idan kuma Ubankine ya saya sai inji? koda yake nasan har matsiyacin Ubannaki ya mutu bai taɓa mallakar irin wannan na kansa ba!”.

Cike da matsanancin ɓacin rai Khausar ke kallonta idan akwai abinda tafi tsana aduniya kana yake saurin fusata ta shine zagin mahaifinta.

Azuciye ta sauƙa daga motar yayinda Haiydar da su Ramadan ma suka sauƙo,

cikin nuna Amina da yatsa tare da ƙanƙantar da idanunta kana tace.

“Kada ki sake zagin Ubana domin Ubana yafi ki daraja koda Agaban Ubangiji”.

 

A yatsine Amina ta watsa mata mugun kallo kana tace.

“An zage sa ƴar iskan yarinya mai hana ruwa gudu ƴar matsiyata”.

Cikin wani irin fushi Khausar ta ɗaga hannunta tare da kife Amina da wani irin azabebben mari hagu da dama cikin nunuta da yatsa tace.

“Ki sake zagar min  Uba kiga abinda zan gwada miki”.

Dafe kuncin Amina tayi cike da Mamaki take kallon Khausar kana tace.

“Ni kika mara Khausar?”.

Harara Khausar ta watsa mata da manyan Idanunta kana tace.

“An mare ki”.

Ahankali Habu Driver ya leƙo kansa tare da faɗin.

“Khausar kiyi haƙuri”.

Sai kuma ya kalli Amina dake huci kana yace.

“Amina kema sam baki kyauta ba taya zaki zagi Ubanta ai duk Abinda zakuyi tsakaninku ne”.

Wani shegen kallo ta watsa masa Afusace tace.

“Habu ka rufe min baki ka fita Idona na zagi Uban nata idan taji haushi tabar mana gidan mu ta tafi gidan Ubanta ƴar matsiyata ƴar jarababbu Angola ta bar nan garin ta koma can dajin nasu mana”.

Ta ida maganar tare da shiga motar taja murfin ta rufe da ƙarfi.

Sai kuma ta sauƙe glass ɗin motar  tare da cewa “Haiydar, Ramadan, da Raudat ku shigo motar tunda ku dai ta  Ubanmu ne”.

Cikin takaici Haiydar ya girgiza kai alamar a’a su tafi.

Ita kuwa Khausar ciki takaici ta ɗaga Raudat da Ramadan ta sakasu cikin motar tare da nunawa Haiydar ƙofar motar alamun ya shiga.

Murya a cushe yace.

“Toh kefa Adda Khausy”.

Cikin danne fushinta tace.

“Kada ka damu zan shiga Napep”.

Zai yi mgn tayi tayi saurin cewa.

“Dan Allah kada kace komai shiga kuje”.

Ta ƙare mgnar tana turashi ciki, dole ya shiga.  Ita kuwa Amina tsaki taja tare da cewa.

“Dole su kam shiga ke kuma sai kije can kishiga naki na Uban”.

 

Kallon Habu tayi kana tace.

“Haba kaja motar mu tafi”.

Da mamaki Habu drive ya kalleta kana yace.

“Haba Amina taya zamu tafi mu barta anan dubi hadarin daya taso sannan babu kowa a haraban makarantar ya za’ayi mutafi ne”.

Harara ta galla masa kana tace.

“Mu tafi kuma wallahi idan ka ƙi na rantse da Allah saina sa Ummah tasa akoreka”.

Ahankali Haiydar ya juya ya kalli Amina wanda tun da suka fara magana bai sa baki ba yace.

“Haba Addah Amina Meyesa haka Fisabilillah ai koma menene bai kamata ki hanata shiga mota ba dubi hadari fa kuma kin san yadda take tsoron yanayin ruwan sama”.

Harara ta watsa masa kana tace.

“Rufe min baki an hanata ɗin rufe min baki ɗan Iskan yaro zaka nuna min ƴan Ubanci kenan ruwan ya cinyata, ta mutuma kawai kowa ya huta”.

Da ɓacin rai Afuskarsa ya kalleta kana yace.

“Ni dai bazan nuna miki ƴan Ubanci ba, saboda bamu tashi da shiba, kuma wallahi idan na koma gida na faɗawa Ummah ma ke kanki kinsan sai tayi miki faɗa”.

Dogon tsaki taja tare da cewa.

“Kayi sauri kada ƙuda ya rigaka”.

Jin haka yasa Haiydar yin shiru sai kuma ya kalli Amina tare da cewa. “Matsa min In ɗauki jakata bazan iya tafiya in barta anan ba”.

Girgiza kai Khausar tayi kana tace.

“A’a Haidar kada ka ɗauka ka shiga dasu Ramadan ku tafi nima yanzu zan biyo bayanku”.

Amina kuwa kallon Habu Driver tayi kana tace.

“Mu tafi”.

Jin haka yasa Khausar jan marfin motar tare da rufewa kana tace.

“Pless dan Allah Haiydar zauna ku tafi, in Sha Allah babu abinda zai sameni”.

Dole ya zauba ba don ya soba,

Shi kuwa Habu ba yanda ya iya haka yaja motar ya tafi.

 

*Yar uwa littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, in dai kin ganshi a waje to na satane, a Groups ɗina na sakayya ne ɗai ya halatta, 1k ne biya ki karanta cikin Salamah 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ban yafe ba a karanta min littafi ba’a biya ba in kin tura kuɗin ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

 

Khausar kuwa shiru tayi tare da bin motar da kallo har ya fice aharabar makarantar,  ahankali ta juya ta kalli cikin makantar babu ɗalibi ko ɗaya duk sun watse haka zalika ma Malamai duk sun watse shiru tayi sai kuma ta ɗaga kanta sama ganin yanda hadari ya taso ga iska dake kaɗawa da ƙarfi.

Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa aciki haka ta fara jan ƙafanta har ta fice acikin Makarantar tsayawa tayi abakin titin koda zata samu Napep amma takai minti biyar babu abin hawan da yazo ya gifta sakamakon hadari daya taso sosai a garin yasa dukkan ababe hawa tsagaita zirga-zirga tana nan tsaye har aka fara ɗan yayyafi hakan yasa ta fara tafiya ahankali a gefen titin.

Ba tayi nisa da makarantar ba taji an buɗe gate ɗin makarantar da ɗan sauri ta juya, akan motar Moddibo Idanunta suka sauƙa da sauri ta kawar da kanta gefe kana ta cigaba da tafiya.

Acikin mota kuwa Moddibo ne da M Jameel yayin da Moddibo ke  Driving M Jameel na gefen me zaman banza.

Kallo ɗaya Moddibo yayiwa bayanta ya ganeta, baki ya taɓe Aransa yace yau kuma wannan wani sabon rashin kunya tayi musu suka sauƙeta, sai kuma ya ɗage kafarɗarsa alamun ita ta jiyo.

M Jameel kuwa sam bai ganeta ba saida suka gifta wajenta sannan yaga fuskarta.

Da mamaki ya furta.

“A’a Lelewal”.

Cikin sauri ya ɗaura hannunsa kan Moddibo tare da cewa.

“A.J tsaya Please dubi duk ɗalibai sun watse amma sai ita kaɗai mai ya tsayar da ita anan kuma ga hadari baƙiƙƙirin dubi fa yanda garin yayi duhu ko Babba hadarin na bashi tsoro yakeyi!”.

Juyawa Moddibo yayi tare da Kallonsa cikin yanayin nutsuwarsa yace.

“To ina ruwanka da ita!?”.

Wara Ido M Jameel yayi kana yace.

“Ban gane ina ruwana da ita ba? ɗalibarmu cefa! sannan kullum a mota ake kawo su sannan zuwa ake aɗauke su, kana mun ganta ba’a tafi da ita ba sannan ka duba ita kaɗai ce a layin nan dubi fa yanda layin babu kowa”.

Kallon gefen Ido Moddibo yayi masa kana ya taɓe baki.

Da sauri M Jameel ya cigaba da cewa.

“Haba A.J ya za’ayi kace haka?”.

Moddibo kuwa juya idanunsa yayi kana yace.

“Toh Meye haɗin mu da ita? kasan Meye Uzurin daya tsayar da ita?

Sannan kasan Meye dalilin tsayuwarta! Wata ƙil ma wani bishiyoyin anguwar takeson hawa”.

 

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“Ai koma mene sai mu tsaya mu tambayeta ko?”.

Kallonsa Moddibo yayi kana yace.

“Nifa bazan tsaya ba”.

Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana cikin sanyin murya yace.

“Dan Allah A.J da darajar Annabi Muhammad (S.A.W) mu taimaki yarinyar nan.

Yanzu idan Asma’u ce zaka iya barin ta awajen nan ne?”.

Da sauri Moddibo ya kallesa kana yace.

“Asma’u kuma mai ma zai tsayar da ita anan mai zai haɗa ta faɗa da wasu har tayi musu rashin kunya su sauƙeta amota, ai Asma’u baza ta kasance haka bama!”.

Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace.

“Amma kayi tunani ƴa mace ce ita ko addininmu ya koyar mana da kula dasu da kuma kula da al’amuran daya shafesu A.J bai kamata ba na roƙe ka dan Allah ba danni ba kuma badan ita ba dan Allah da kuma darajar Manzon mu kayi haƙuri ka tsaya! In ma bazaka ɗauketa ba, ni ka sauƙin bazan iya tafiya in bar Khausy cikin wannan yanayin A.J bazan iya barin ta ananba”.

Ya ƙarashe mgnar cikin wata iriyar raunatacciyar murya mai fito da sirrin dake binne cikin zuciyarsa.

Hannu Moddibo ya sanya tare da dafe goshinsa alamar ya gaji da damuwar M Jameel ahankali yasanya lallausan tafin hannunsa ya shafa sajensa ba tare da yace komai ba ya taka burki ya tsaya.

Yana mai kallon yadda M Jameel ya sauƙe numfashi.

Ganin ya tsaya ya sanya M Jameel sakin murmushi tare da buɗe motar ya fita cikin sassarfa da ɗan gudu ya nufi inda Khausar take dan sun ɗanyi mata nisa kana ga yayyafin da aka fara da ƙarfi da kuma rugugi alamar ana gaba da kecewa da ruwa mai ƙarfi.

Moddibo kuwa da kallo yabi M Jameel ta mirror motarsa.

Aransa yace Ohhh J ji yanda yake gudu kamar wani yaro ko ya gani a wannan ƴar nan har yake jinta cikin zuciyarsa.

Khausar kuwa tana ganin M Jameel ta saki nannauyan Ajiyar zuciya tare da cewa.

“Yaya Jameel”.

Cike da kulawa ya kalleta tare da cewa.

“Lelewal mai yafaru yana ganki anan ke kaɗai, bayan baki ɗaya student’s sun watse”.

Ahankali ta kallesa sai kuma tayi saurin lumshe Idanunta tare da cewa.

“Wallahi Yaya Jameel Amina ce ta hanani shiga motarsu yau kam masifa take ji dashi”.

Girgiza kai yayi tare da faɗin.

“Subhanallah gaskiya bata kyauta ba, maza zo ki shigo mota mutafi”.

“Toh”,tace tare da bin bayansa cikin sassarfa yayinda ko wanne gaɓa na jikinta ke motsawa.

Ɗan guntun tsaki Modibbo yaja, tare da kauda kansa daga kan madubin, ganin yadda suka wani jero da J ɗinsa.

Suna isa wajen motar M Jameel ya buɗe mata bayan gefen da Modibbo yake tashiga, sannan shi kuma ya zagaya  ya shiga a hankali Khausar ta ɗaga kanta tare da kallon gaban motar ai kuwa idanunta suka sauƙa akan Moddibo da batasan yana cikin motar Ba gashi ta zauna asaitin bayansa.

A kuma dai-dai lokaci  ruwa ya kece tamkar da bakin ƙorya, key Moddibo yayi wa motar tare da figarta a dan guje suka fara tafiya.

 

Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.

“A.J kasan zamu biya ta gida ka sauƙe ni tun safe Abba ke kirana wai Inje Yana son magana dani muje ka sauƙe ni”.

Kallon sa Moddibo yayi tare da cewa.

“Baza ka bari sai anjima ba?”.

Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.

“A’a muje dan Allah ka sauƙe ni saboda bansan me yake sona dashi ba yanata ne mana tun tuntuni”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.

“Toh naji”.

Yayi mgnar tare da haharan M Jameel ɗin,

Sannan ya cigaba da Driving ɗin sa.

Shi kuwa M Jameel murmushin yayi tare da ɗan mishi alamun zunɗe.

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, daga gobe in dai kinga littafin SAKAYYAH a wani wuri to na satane, yar uwa ki biya 1k ne kacal ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin kowa a kanki littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa kada ki karanta in baki biyaba 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

 

Khausar dake zaune abayan motar kuwa ƙanƙame jikinta tayi saboda yanda ɗumin motar ke ratsata sam cikin motar babu sanyi da yawa ba kamar waje da iska ke kaɗawa ba.

 

Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da gyara Questions peper dake hannunta ta sake rungumesu aƙirji sai kuma ta gyara zaman wuyan hijabinta wanda har tattausan gashin gaban goshinta mai sansti ya bayyana.

 

Baki ɗaya cikin motar a wadace yake da wani irin ni’imtaccen sanyayyan ƙamshi mai daɗin shaƙa yakeyi, Ahankali Khausar ta maida kallon kan bayan Moddibo da take fuskanta sanye yake  cikin ɗanyen Boyel fari ƙal yasha guga sosai yayin da kansa ke sanye da hula zanna bukar wadataccen sumar ƙeyansa ya kwanto lib-lib gwanin kyau sai sheƙi da ƙyalli yake zubawa.

Ƙeyar tasa ta zubawa ido sai kuma ta gallawa ƙeyar tasa harara  tare da murguɗa masa baki.

 

Tana ɗago Idanunta suka sauƙa akan Idanun Moddibo ta madubin jikin motar yana kallonta cikin mugun sauri tayi ƙasa da kanta zuciyar ta na mai bugawa da ƙarfin tsiya.

Moddibo kuwa Ƙoffa yayi tare da haɗa harshensa da hoƙorinsa ya fitar da wani sauti kana yace.

“Hmmmm!”.

Kallon sa M Jameel da Idanunsa ke lumshe yayi kana cike da kulawa yace.

“Ya dai A.J?”.

Shiru Moddibo ya masa tare da watsa masa Harara!.

Ware Ido M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana yace.

“Ya dai kake ta harare-harare acikin mota!”.

Ƙin tanka masa Moddibo yayi ya cigaba da Driving ɗinsa tare da ƙara tsuke fuska.

Khausar kuwa shiru tayi sai kuma ta sake ɗago kanta ahankali ta kalli madubin ganin ya kawar da kansa gefe yasa ta sake liƙawa ƙeyansa harara tamkar  idanunta zasu manne bisa ƙeyar tasa, kana ta ɗago hannunta na dama ta ɗan haɗe kan yatsun tare da buɗe su ta watsa masa alamar Jarabebbe! Mayatacce!! Masifeffe!!! Fitinenne!!!! sai kuma ta sake watsa masa Harara tare da kai hannunta ƙeyarsa kamar zata kai masa ronƙwashi.

A kuma dai-dai lokacin ya ɗago ya kalleta ta madubin.

Azabure taja baya tare da jinginar da bayanta da jikin kujeran zuciyarta na bugawa.

Cikin fushi Moddibo ya watsa mata mugun kallo tare da cewa.

“Anh zan karyaki wallahi kakkarya ki zanyi in watsar dake atiti inyi tafiyata, ƴar rashin kunya fitsararriya”.

Ita dai Khausar rumtse Idanunta tayi da masifan ƙarfi tare da sake rungume question peper ta aƙirji gam-gam.

M Jameel kuwa daya ta kure jikinsa waje ɗaya idanunsa alumshe saboda sanyi da ake yayi saurin buɗe idanunsa yayi tare da kallon Moddibo dake Driving tamkar bashi yayi maganar ba cikin tsaresa da Ido yace.

“Ha’a wai mai yake faruwa a motar nan ne kake abubuwa iri-iri daga Harara, Ƙoffa, tsaki, tsuke fuska,  yanzu kuma sai cewa zaka kakkarya!,To waima wa zaka karya ne kam?”.

 

Cikin fushi Moddibo ya juya ya kallesa kana yace.

“Ai duk wanda zan karya ya sani!

Karya yarinyar nan zanyi fitsararriyar banza mara kunya idan kina sake kuskuren kallon min ƙeyata saina gutsitsi-tsiraki na ƙwaƙule miki manyan mayatattun idonun ki masu kama da na yan maye na jefar! A titi ko na samu salama”.

Lokaci ɗaya tsoro ya dirarwa Khausar jin wai zai Kakkarya ta ya ƙwaƙule mata ido cike da tsoro ta kuma ƙara rumtse Idanunta tare da ta kure jikinta ajikin kujera ita kanta batasan dalilin da yasa yake mata haka ba ita dai tasan da zata samu dama itama karyashin zatayi ta kuna tsitstsige gemunshi.

Akuma dai-dai lokacin suka isa ƙofar gidan su M Jameel Moddibo yayi Parking.

Ɓude Murfin motar M Jameel yayi tare da fita duk da ruwan da ake tsugawa bai hana sa saka kansa ta cikin glass ɗin side da Khausar take ba, cikin ƙasa da murya yace.

“Lelewal be careful don’t Misbehaving kinga bana nan yaseen kika mishi ba dai-dai a titi zai wurgaki ya tafiyarsa”.

Kai ta gyaɗa masa cike da alamun tsoro sai taji kamar ta fita ta bisa.

 

Shikuwa M Jameel kallon Moddibo yayi tare da cewa.

“Toh Allah ya tsare Allah ya kaiku lafiya A.J Amana ce, dan amana A.J ka kularmin da ita”.

Daga haka ya juya da gudu ya nufi cikin gida zuwa lokacin duk ya jiƙe saboda yanda ruwan ke sauƙa da ƙarfi.

 

Acikin motar kuwa lumshe idanu Moddibo yayi ba tare da yaja motar ba.

Khausar kam ƙasa da kanta tayi aranta tace wannan dai akwai bahagon mutum, fisabilillah yana kallon yanda ake tsuga ruwa kamar da bakin ƙwarya amma yaja ya tsaya jifa yanda ruwan ke sauƙa.

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan na gama Free page, 1k ne kuɗin samun damar karantawa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, biya ki karanta cikin Aminci*

 

Sun kai kusan minti biyar ahaka ita batace komai ba, haka zalika shima baice komai ba banda sautin ƙaran ruwa babu abinda ke sauƙa ɗago Idanunsa yayi dai-dai lokacin da itama Khausar ta ɗago Idanunta ta kalli madubin cikin motar,

idanunsu ne suka sarƙafe cikin na juna.

Harara ya watsa mata kana cikin wata razananniyar murya da shi kansa  bai san yana da ita ba yace.

“Uban me kike abayan mota koni.

Driver kine harda wani hakimcewar ki abaya a dole kega Sarauniya kin samu Driver!

Kifita idona fa, nifa ba J bane zan karya kifa”.

Cikin sauri ta buɗe bayan motar ta fita aranta tace Gwanda inyi yanda yake so dan yanda yake kiran zai karya nin nan inda yazo da tsautsayi sai yajawa Mommy asarata, gaban motar ta buɗe ta shiga amma duk da haka saida ta ɗan jiƙe sabida ruwan da ya fara ƙarfi, tana zama yaja motar suka tafi.

Akuma dai-dai lokacin ruwan ya sake kecewa da ƙarfin gaske tamkar da bakin ƙwarya ake tsuga ruwan.

 

Khausar kam lumshe Idanunta tayi aranta tace ya Allah ka kaimu gida lafiya ka rabani da wannan bawa naka lafiya,

domin akwai rata tsakaninsu da gida sosai ahankali ta buɗe Idanunta ta kalli titin da yayi shiru babu hayaniyar sai ƙugin motarsu da kuma yanda tayun ke fesar da Iska da ruwan kan kwalta fuuuu kana har zuwa yanzu garin ɓakiƙƙirin yake duk da kuwa yadda ake sheƙa ruwan alamar har yanzu ruwan bashi da niyyar ɗauke wa.

 

Suna cikin tafiya akayi wani irin walƙiya mai haske.

Da sauri Khausar ta rumtse idonta tare da furta.

“Bismillahi”.

A lokacin guda kuma ta sake buɗesu da sauri sabida

jin wani irin rugugi da akayi mai bada sautin rududuuu-duuuuhhh kana ga walƙiya daya haska da wani irin sauri Khausar ta rungume jikinta waje ɗaya aranta tace.

_“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n Hasbunallahu wani’imal wakil Subhanal Lazi yusabbihul ra’adu bi handihi  wal Mala’ikatu min hiyfatin”._

 

Cikin tsananin tsoro tayi addu’ar domin arayuwarta babu abinda take masifar tsoro a damuna kamar tsawa da walƙiya  sam bata yarda ta haɗa ido da walƙiya da zaran taga za’a yi walƙiya zata rufe Idanunta ta sunkuyar da kanta.

Shi kuwa Moddibo tafiya ya cigaba dayi yayin da titin yayi shiru babu hayaniyar komai sai bishiyoyi dake rangaji ruwa na sauƙa akansu Sanyayyar iska mai cike da Ni’imah na kaɗasu baki ɗaya shaguna dake gefen titin arufe suke baki daya garin babu hayaniya sai jefi-jefi suke hango Mutane.

 

Suna cikin tafiyar aka sake wani walƙiya mai masifar haske ja, alamun yanzu za’a ƙara kecewa da ruwa.

Atsorace cikin ɗaga sautin murya tace.

“Innalillahi wa’inna ilahi rajiu’n”.

Ta ida addu’ar tare da kife kanta akan gwiwarta yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa A ɗan juya kai Moddibo yayi kalleta, domin shi kansa zuciyarsa ta harba sabida walƙiyar saida ta ɗauke masa ido saboda yanda walƙiyar tazo da haske mai ƙarfin gaske sosai yaji tsoron walƙiyar amma sai yayi addu’a aransa kana yana cigaba da tafiya bai tsaya ba.

Bayan walƙiyar ba daɗewa aka saki wata tsawa mai sautin rututuuuu alokaci ɗaya zuciyarsu ta buga domin ji sukayi tamkar ƙasa zai tsage.

Atake wani matsananci tsoro ya sake lulluɓe Khausar yayin da jikinta yashiga rawa tamkar mazari kanta ta kife acinyarta zuciyarta na cigaba da bugawa da masifan ƙarfi kana har zuwa lokacin kanta na sunkuye akan ƙafafunta tun daga wannan rugugin.

Yayinda gaba ɗaya mazauna garin Gembu Mebila suke cike da taraddadi sabida bisa dukkan alamu yau da tsawa da rugugin ruwan yake sauƙa.

 

Acikin haka ne aka sake walƙiya mai masifar haske irin walkiyar nan mai zuwa tamkar an watsa dogon bulala koko tafiyar maciji,

Da masifar haske da tarsatsi yazo tamkar an watsa bulala Sharrrrrr sai kuma a take aka saki wata iriyar tsawa mai masifar ƙarfi yabi yo bayansa wanda ke fitar da sautin felelelelelelelen  da masifar karaji da gigita dukkan bani adam

 

Cikin wani irin tsananin tsoro da gigita Khausar ta saki ƙara mai masifar  sauti tare da furta. _“Hasbunallahu wani’imal wakil. Subhanal Lazi yusabbihul ra’adu bi hamdihi wal Mala’ikatu min hiyfatihi”._

Atake aka sake sakin wani walƙiyar haɗe da wata iriyar firgitacciyar tsawa mai masifar kara mai razana dan adam dasa hanjin mutum kaɗawa.

Cikin tsananin tsoro da masifar gigita ta dari ta ɗago kanta a kiɗime ta afkawa jikin Moddibo yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa shi kansa Moddibo wani irin tsoro ne ya kamasa saboda hasken walƙiyar saida ya tsaga glass ɗin gaban motarsa tare da bada sautin ƙarararassss!!!.

Wani irin bugawa zuciyarsa keyi da masifar ƙarfe yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ya ɗauki rawa ƙoƙarin taka burki yake amma ya gagara saboda yanda ta takure jikinta ajikinsa ta kanainayeshi, bashida wani kataɓus ɗin motsa wa, sabida yadda ta kife kanta afaffaɗan ƙirjinsa hannunta ɗaya na zagaye da bayansa yayin da ta cusa hannunta na dama akan maransa.

 

Moddibo kuwa wani irin masifaffen rawa jikinsa ya farayi tamkar mazari yana wani irin tsuma ji yake tamkar ana tsikara masa allurai ne agaba ɗaya ilahirin jikinsa lokaci ɗaya wani irin baƙon yanayi ya ziyarcesa ga fargaban tsawar da har zuwa lokacin bai gama tsayawa ba.

Tsawan na tsayawa wani mai masifar rugugi ya sake sauƙa.

Wani irin masifaffen tsuma jikin Khausar keyi yayin da numfashinta ke fusga saboda tsananin tsoro Allah ya sani tana masifar tsoton tsawa hakan yasa ta sake ƙanƙamesa tamkar zata tsaga jikinsa ta shige ciki.

 

Shi kuwa Moddibo baki ɗaya jikinsa tsuma ya shiga yi saboda yanda ta kanainayesa kar-kar-kar haka jikinsa ke rawa  yayin da baki ɗaya tsikar jikinsa ya miƙe daga tsakiyar kansa har zuwa babban yatsan ƙafarsa yaji wani irin yanayi wanda bai taɓa jiba a iya tsawon rayuwarsa, sai  yau kuma yanzu ya jishi.

 

Wani irin harba zuyarsa da sashi mafi daraja a jikinsa sukayi a tare da wani irin azaban ƙarfi.

Akuma lokacin aka sake sakin tsawa da walƙiya.

 

Ita kam Khausar cikin tsananin gigita da tsananin tsoro kana da ficewar hayyaci ta sake rungumesu tare da sake tura hannunta ka maransa yayin da yatsun hannunta suka sauƙa akan cibiyar sa.

Tsawar da aka sake yine ya razana illahirin wani abu mai rai dake yankin Gembu,

yayinda hakan take a wurin Modibbo ma wani  cikin rashin sanin makaman kamawa ya ya buɗe hannayensa ya rungumeta da azaban karfi tare da taka burkin motar da ƙarfi wani irin sautin ƙuuuuuuu motar tayi tare da cigaba da tafiya sabida tsantsin kwaltan da yayi sabida ruwan sama da kuma tsantsin sabbin tayoyin da ƙyar ya samu motar ta tsaya a tsakiyar titin, sake Rungumeta yayi da masifar ƙarfe kana ya cusa kansa atsakanin kafaɗarta da wuyanta.

Lokacin da aka kuma sakin wani irin rugugin nan da zakaji kamar ƙasa na amsawa.

Atake zuciyarsu ya buga da mugun ƙarfi tare da bada sautin dib-dab-dib-dab-difffh yayin da yake jin wani irin masifaffen abu na tsirgar masa lokaci ɗaya lafiyarsa sa ta shaida mushi  kasantuwarsa cikekken Namiji.

Ita kuwa khausar tana jin yatsarta cikin ɗan hudan cibiyarsa amma tsananin tsoron da take ciki yasa ta kasa fahimtar menene sai cusa kanta da ta kumayi a kirjinsa.

Shi kam Moddibo wani irin rungumeta yayi da masifar ƙarfi yana mai sakin wani irin amintaccen nish….!

 

*Free page sun ƙare daga wannan, ko kin ga littafin a wani wuri na satane, littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin da nan kadai zanke posting*

 

 

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

 

_Ina kuke Ma’aurata masu sha’awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau’ikan sirrin sahihan magungunan ma’aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki…Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba’a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al’khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni’ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni’imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu…Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu’umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba…._  _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan  Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu’uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)…Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji  Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu’uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa ‘yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma’aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba’a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma’aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah ‘yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci…._

 

 

 

🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,

 

*By*

*GARKUWAN MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button