Hausa NovelsMr. Romantic Complete Hausa Novel

Mr. Romantic 6

Sponsored Links

*💋MR. ROMANTIC💋*
Multi dimensional story.

Page 6

Mamanteddy.

Don’t compare yourself to others. Everyone has their own unique journey and path🤓.

Hausa novel 📚 .

Gaba ɗaya Fulanin wannan ruga sun maida hankalin su bisa ga jawabin da Billy ke yi masu da jama’ar ta ,wanda dukan shi ƙanzon kurege ne , babu ɗaya na ɗauka haka na gaskiya duka shafa shuni ne . Ƙarya da ƙarairayi.

Da fari kaman yanda kuka sani , Ni dai sunana Bilkisu Tukur , haifaffiyar Garin Adamawa , mazauniyar Garin Abuja .

Muryar liman ne ya katse su yana Girgiza kai cike da yabawa da kuma jin dadin jawabin nata yana faɗin ” Allahu Akbar” ashe duka mune Fulani , shiyasa naji na gamsu da jawaban nata har na tara mata Mutane don suma su gamsu wanda suke ra’ayi suna iya bin bayan ta .

Muryar Billy ne ya katse su inda take cigaba da cewa ” Sosai naji dadi da yanda aka bani kadan daga cikin Al’adun ku na wannan Ruga . Mashaallh. Da fari Ni macace mai son Ganin cigaban Rayuwar ya’ya mata , Domin kuwa su ne rahma su ginshiƙi ne ga Rayuwar Al’umma baki ɗaya . Aure shine babban hanya na cigaban Rayuwar ya mace , aure shine ke ƙaudar da mace daga duk kan wasu fitinu tare da ƙalubale na rayuwa . Alhamdulillah naji tsari ko nace Al’ada ta Wannan Ruga cewar yara Tun suna yan shekaru 7 ake auran dasu , daga lokacin da suka tasa Suka ka fara zama yammata daga shekaru sha uku ake kai su dakunan Mazajen su haka ne ? “Tayi maganan tana mai kallon fuskokin gaba ɗaya ilahirin jama’ar Fulanin” .

Gyada mata kai suka yi cikin gurɓataciyar Hausar su suka furta ” Kwarai kuwa ” .

Hakan yayi kyau , Amma…..ke Da’allah rufe ma mutane baki , keda ba Hausa kike jiba sosai dama kin tashi ne kin tafi don zaman ki baya da Amfani . Aradu Hasile ke fitinanniya ce .!

“Muryar wasu daga Ƴammatan Rugar ne ya katse Billy dake jawabi,wanda saɓani ya shiga tsakanin su , Hasile ce da ƙawayen ta .

Maida Hankalin ta tayi ga Wurin inda Hasile ke watsa ma Dijama harara tamkar idanun ta zasu faɗo ƙasa . Yanda take yi tamkar ba yar cikin wannan ruga ba saboda Tsiwa da faɗa . Dijama tashi wannan Jawabin ba amfanin da zai maki ke , saura kwana nawa ne bikin shaɗin ki .?

Wani irin kallo Dijama ke bin Hasile dashi kana tace ” Hasile ba zan tashi ba ,wani yace kizo daga baya , kije can ki nemi wani wurin mana , amma nidai ba zaki kai Ni baya ba ke kuma ki shiga gaba na ba . “Mtswww ”
Hasile taja dogon tsaki tana buɗe bakin ta da zummar cigaba da Sababi ne Muryar Billy ya katse su tana cewa ” A’a Ƴammata meke faruwa ne anan ? Eiye ƙanni na ?” . Kallon juna Dijama da Hasile suka yi suna mamaki furucin Billy da take kira su da ƙannin ta , nan take suka juya harshen su zuwa fulatanci suna cewa ” Gaskiya matar nan tana da kirki , jube mu fa wai amma ta kira mu da ƙannin ta ?. Muryar Billy ne ya katse su itama tana mayar masu da magana ta hanyar fulatancin wanda duka basu tsammani jin hakan daga gare ta ba . ” Ai Dani da daku duka daya ne , ba kyama ko wani abu ,sai dai naga na inganta rayuwar ku ta hanyar cigaban ku duka .

Gyada kai liman da sauran jama’ar suka yi , kana ta cigaba da cewa” Abun dake tafe dani shine Yaran ku mata ake bukata kaman guda biyar zuwa kasa da haka , wannan tallafi ne na gomanti wanda ta dauki nauyin komai na yaran ku na tsawon Shekaru uku zasu dawo rugar nan . Abun da gomanti ke so anan shine Ganin yaran sun sami tarbiyyar Addini ingantacce ,kuma zasu kasance suna dan wani aiki don dogoro da kai . Duka jawabin bisa Harshen fulatanci take yin shi ,yayin da Mabiyan ta su kan su mamakin sheiɗana irin na Billy suke yi , ita dai ba Yar Adamawa Bace Sam da ta faɗa ,yar Zariya ce , sannan inda ta iya fulatanci basu sani ba . Niko nace wannan kaɗan ne daga Halayyar Bilkisu Tukur Billy .

Muryar Baffa Harɗo ne ya katse Billy inda yake cewa ” Gaskiya wannan ba abinda da zamu amince dashi bane . Saboda duka yaran nan da kike ganin su na gaban ki ko wanne da Auren sa da mijin sa ,bikin shaɗi ne kaɗai ya rage a kai su ga Mazajen su . Idan mu iyaye mun amince su kuma mazan fa ?.

Wani irin gintse fuska Dijama tayi tana kallon su Hasile wanda suma maganan Baffa Harɗo ƙanin mahaifin Hasile bai masu dadi ba . Hasile ya zamuyi mu bi wannan matan ?. Shiru Hasile tayi kana cike da Hauka da wauta tace ” Shekara uku dai ai ko ta yaya sai munje bakya jin ana cewa ilimi gishirin zaman duniya? Zanje zan roƙi umma ta Ni dai ta amince.

Dijama ce tace ” To baki ji mene baffan ki yake cewa ba?. Ina ruwa na ai umma idan ta amince Shikenn . Ma’u ce ta katse su tana cewa ” Gaskiya Hasile kinji dadin ki ke , Kinga Baban ki ya rasu Umman ki ce kadai ,mu kuwa bamu isa ba , ko umman mu sun amince idan Abba basu amince ba dole muyi haƙuri . Murmushi Hasile tayi Wanda sai da gyefen Kuncin ta ya loɓa kana tace ” Ku mu cigaba da sauraren su kila kuma ayi tafiyar daku . Kallon ta Dijama tayi tana cewa ” Ai Hasile a jikina nake jin tafiyar nan fa zai wuya ba dake za’a yi ba , Saboda Kinga Ke fa Sulaimanu da aka yi maku aure shekarun sa Uku kenan da Mutuwa , Dama baki da igiyar kowa akan ki. Don Allah idan kinje birnin duk ilimin da kika koya ki koyo damu sai idan kin dawo ki koya mana . Cike da jin dadi da barazana da kuri irin na Hasile ita kawai taga tafiyar ma ,nan tace ” Kar ku damu Dama Ni a jiki na nake ji Ni mai ilimi ce , shiyasa sam bana kula mazan Rugar nan don sai na fisu ilimi da wayewa ashe birni zan tafi .

“Muryar Billy ne ya katse tana cewa ” A’a Baba , Ka fahimci wannan tafiyar namu . Cike da tuburewa Baffa Harɗo yace ” Ban yarda ba , babu wanda zasu sauya mana Al’adu, Ilimi suna yin allo yaran mu mata , Don haka ban yarda a dauki mutum daya daga tsitsona ba .

Yana Gama fadin haka ya mike yana gyara Hular sa ta Fulani tare da barin Wurin ,duk yanda liman yaso dakatar dashi amma hakan ya cutura . Ganin Baffa Harɗo ya tafi kuma gashi dama A rugar sun yi ittifaƙi babu mai ilimi da hangen nesan shi , shiyasa duk abin da yace ake amince masa nan take , wannan yasa iyayen fara tasa yaran su suna barin wurin , kowa na goyan bayan maganan Baffa Harɗo. Su kuwa matasan Fulanin ihu suka hauyi suna ma Su Billy yeho tare da cewa ” Kowa ya tarkata ya bar mana ruga mu Rayuwar Musulunci muke yi Bama buƙatar kyalkyal din duniya .

Tirr Allah wadaran Lamiɗo.!

Hasile ta furta tana cabe baki tare da juyawa tana faɗin Dijama komai ya lalace .

Wayyo Baffa Harɗo bai duba mana ba Aradun Allah wannan Cigaba ne na rayuwar mu . Cewan Dijama tana matso Ƙwallah na bakin ciki . Kallon su Hasile keyi tana faɗin ku mu tafi kawai , tana maganan ne amma ita kadai tasan Abun da take sakawa a zuciyar ta . Wata zuciyar ne ta furta mata ” A yau kiyi masu kallon sallama sai bayan shekaru uku kuma , Don wannan cigaba ba zan bari ta wuce Ni ba , dama sau daya take zuwa A Rayuwa ” .

**
Bakin sa Ɗauke da Sallama ya shigo dakin hannun sa dauke da ledoji biyu daya biredi ne guda daya ,dayan kuma ledan madara ne da sugar nescape da sauran kayan hadin tea , Wanda duka yayi hakan ne don ya faranta ma Sakina.

“Turus ” Yayi ganin Sakina na aikin haɗa kayan ta wuri Guda na kullewa tana kulle su haka na akwati tana zuba su . Jiki a sanyaye Rayyanu ya aje Ledojin don yasan Kwanan da suka yi jiya tana masa Sababi wannan yasa shi fita tun asalatu ,daƙyar ya samu kudi bashi a hannun wani Maƙocin su ,shine yayi mata Wannan siyayya .

“Sakina”.

Ya furta sunan ta yana takowa zuwa inda take . Dakata.! Don Allah Rayyanu ka dakata daga inda kake ,kar ka kuskura ka ƙariko inda nake , yau karshen komai ne yazo, ka ganni da kake ganina din nan ? Daga nan gidan iyaye na na nufa , ba zan zauna da Wanda kashin arzikin mu bai zo daya ba . Kullum talauci karuwa mana yake yi , kaga Rayyanu wannan rabuwar mu duka kan mu muka taimaka. Tana maganan tare da bige Hijabin ta tana sakawa. Wani irin gumi ne yaji yana sauko masa , a hankali ya kai Gwiwowin sa kasa yana zubewa a gaban Sakina . Sakina don Allah ki mun rai , sakina Kiyi Haƙuri ki zauna dani , Allah ne mai rufa ma bawa wata rana …..kai da Allah malam bani wuri . Wallahi ko menene zaka faɗa wannan shine ƙarshen zamana da kai yau din nan kenan. Don haka idan kai haifu cikin Lauratu da Saminu ka sake Ni .!

“Innalillahi wa’inna ilaihir raji’un ” .

Muryar Inna n Rayyanu ya katse su wanda shigowan ta gidan kenan tun daga tsakar gida take juyo hayaniyar Sakina da cin mutuncin da take mawa Ɗan nata .

Kallon inda Inna ke shigowa Sakina tayi tana cabe baki tare da zabga mata harara ,kana tace ” Eh nace ,idan kin yi zuciya kisa dan ki ya rabu dani yanzu.

Girgiza Kai Inna tayi tana sakin wani murmushi wanda yafi kuka ciwo , kana tace ” Inshallahu zan nuna Miki na isa da dana Sakina , izayar da kike masa ya isa haka . Rayyanu ina mai umartar ka yanzu ka sauwake ma Sakina ta tafi gidan su . Wani irin bugawa kan Rayyanu yayi , jiri na dibar sa , duhu na gilama masa . Inna saki fa ? Inna ina matukar Kaunar Sakina . Ita kuma Bata son ka Rayyanu tafi kaunar kyalkyal banza . Don haka umarni nake baka idan ba haka ba zaka ga ɓacin raina .

Wani irin kuka Rayyanu yake yi tamkar karamin yaro , tashin hankali ya gama gani a wannan lokaci, a hankali ya juya yana cewa ” Sakina na sake ki .

“Mtswww” tafi nono fari .

Wannan shine furucin da Sakina tayi tana kai hannu tare da ɗaukar kayan ta tana barin falon da gidan baki daya . Kallon Inna Rayyanu yayi yana Zubewa a ƙasa tare da fashewa da kuka yana dafe kai .

“Rayyan”.

Inna ta kira sunan shi tana kai hannu tare da dafa Ƙafadan sa . Komai yayi zafi maganin sa Allah . Kayi hakuri Allah zai saka maka Abun da Sakina tayi maka tun daga Auren ku har wannan lokaci . Jan Ajiyar zuciya Rayyan yayi kana yace ” Inna Ba zan taɓa so kaman yanda naso Sakina ba , huhmmmm Sauke Numfashi yayi yana ɗago da idanun sa wanda suka yi jaa kana yace ” Ba zan taɓa kuma tsanar wata ya mace kaman yanda na tsana Sakina ba …! Hannun sa yakai yana sakawa a Aljihu kana ya fiddo da Wani takarda yana miƙa ma Innar tasa .

To mata muyi Hattara mu sani rayuwar mu tiƙa ce kadan , Allah shine mai azurta bawa a duk lokacin da ya so . Babu mai yi ma wani arziki sai ilahi , Allah ka barmu da Wadatar zuci .!

**

Asabe amma ke kina ganin Babu wata matsala ? Kin amince da mu’amalar tamu ? Mijin ki fa?.

“Cewan Mai Wada yana maganan yana wani Karkaɗa mukullin mashin din hannun sa “.

Kai dama ka fara nema na da Wannan buƙata na dauka miji na tsayayye ne shiyasa ban amince maka ba , amma a yanzu ko Allah zai bani uzuri don ba zan zauna yunwa ta kashe Ni ba. shi bai bani ba Ni kuma na zauna , gwara na dingi haduwa da irin ku ,na biya maku ɓukatar ku ku biyani da kudin da zanji daɗin rayuwa ta “.

“Hahahaha” Mai Wada ya saki wani dariya na basawa kana yace ” na dade ban hadu da Wayayyiya irin ki ba ,wacce Tasan Rayuwa da hakkin kan ta . Asabe muje daga ciki ko ? . Yana maganan yana buɗe dakin sa inda yayi nesa da cikin jama’a . Kutsa kai Asabe tayi tana shigewa cikin wannan daren babu ko tsoron Allah bare jama’a .

Kullum zaki dinga zuwa warhaka ne . Yayi maganan cikin Muryar raɗa ta ƙwaratan maza .

Tsayawa Asabe tayi don ita dai Tasan ƙawayen ta suka fara kokarin sata a hanya ,amma bata taɓa yi ba sai a wannan karon,wannan yasa ta tsayawa tana kasa Sanin inda zata nufa . Hannun mai Wada taji yana shafa Kirjin ta tare da janye mayafin jikin ta . Hannun sa yasa yana kama wulaƙantattun nonon ta wanda suka yi yaushi kaman Rama . Ahhhh Kai Asabe Wannan Nonuwa naki dam² dasu tamkar baki taɓa shayarwa ba ?.

Kuji iskanci da ƙarya😹 .

A’a haba dai mai Wada yara shida ba Wasa ba ai . Tayi maganan tana dan Murmushi a dole an yabeta .

Jikin sa na rawa irin na kwarata ya fara sauke malunmalun kana yace ” Zauna anan a gadon nan Asabe “. To Mai Wada amma bamu yi maganan nawa zaka biya ba ? . Ai ko kaina ne zan baki Indai na samu gamsuwa da biyar buƙata dake ,kawai ki saki mun jikin ki abun da nake so kenan….!

To my luvs ku bari mu tara a page na gaba shafi na 7 zamu Waiwayo muji yanda ta kaya da Asabe da mai Wada . Yanzu bari muyi saurin nufar Ɓangaren Abdool Maleek jibo .

A hankali jirgin mai saukar ungulu take sauka a filin saukar jirgin , Inda daga nesa na hango motoci wanda sun kai goma rerasss a layi dukan su kalan baƙi sai guda ɗaya ne kiran Camry ya kasance fari . Gyefe securities ne fiye da goma sha biyu suke tsaye tare da jiran Saukar Sir Abdool Maleek jibo. Abun mamaki baya karewa duk wannan tarin mutanen babu mace sai mutum daya Wato Nihla, wacce take sanye cikin shigar crazy , Riga da Wando ne amma dagani kasan na marasa ji ne . Jogging Pant na mata mai fadi , sai Rigar t.shirt ta yafa karamar Mayafi tare da Ɗaura malfa daga sama . Ƙafarta kuma cikin Boot mai kama dana maza wasu irin manya masu tudu daga ƙasa . Gaba ɗaya ta kosa tayi tozali da Annurin zuciyar na ta…….!

 

To makaranta mu tara a page na bakwai 7 inshallah .

Wanda suka shirya fara payment na littafin mr romantic ga tsarin yanda yake.

Regular payment ₦500
Vip payment ₦1000

Zaki iya turo da katin MTN ta Wannan number 08081202932 ko ki tura kudin ki kai tsaye ta wannan Account number 6037312299 Mohammed A’isha keystone bank sai ki turo da shaidar biya ta wannan number 08081202932 .
*Maman-teddy*

Leave a Reply

Back to top button